WDN Hausa

WDN Hausa WDN Hausa a shirye muke wajan cigaba da kawo muku sahihan labarai da shirye shirye masu nishaɗantarwa da ilimantarwa

Kwamitin Yaki da Shaye-shaye da Sauran Laifuka da gwamnatin jihar Kano ta kafa ƙarkashin jagorancin, Barista Muhuyi Maga...
06/08/2026

Kwamitin Yaki da Shaye-shaye da Sauran Laifuka da gwamnatin jihar Kano ta kafa ƙarkashin jagorancin, Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado, ya ziyarci Kwamandan Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi na jihar, DY Lawal.

Manufar ziyarar ita ce domin ƙara ƙarfafa aniyar ɓangarorin biyu na yin aiki tare cikin tsari, da inganta haɗin gwiwa, tare da ƙara wayar da kan jama’a domin magance matsalar shan miyagun ƙwayoyi da kuma kare al’umma daga illolinsa a fadin jihar Kano.

10/07/2026

Dalibai da Malamai da akayi garkuwa da su a Jihar Oyo sun shaki iskar 'yanci.

A wani bidiyo, Malamar ta Godewa Shugaban Kasa Bola Tinubu da sauran shugabanni da s**a bada gudun mowa har aka sake su daga inda akayi garkuwa da su.

DA DUMI-DUMI: ICPC ta k**a likitan El-Rufai Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta  ICPC ta zargi tsohon gwamnan Jihar ...
07/07/2026

DA DUMI-DUMI: ICPC ta k**a likitan El-Rufai

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ICPC ta zargi tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da karya sharuddan da kotu ta gindaya masa na fita domin duba lafiyarsa yayin da yake tsare a hannunta.

A wata sanarwa da kakakin hukumar, John Odey, ya fitar, ICPC ta ce El-Rufai ya ƙi zuwa kotu a ranar farko ta shari'arsa, yana mai neman ganin likitansa na kashin kansa, Farfesa Bello Abubakar.

Hukumar ta ce bayan kotu ta amince da ziyarar jinyar, jami'anta sun raka shi zuwa wani sashe na Asibitin Ƙasa da ke Abuja. Sai dai daga baya ta gano hotuna da aka wallafa a Facebook da ke nuna El-Rufai tare da wasu baƙi, ciki har da ɗan siyasa Isa Ashiru Kudan da kuma likitansa, lamarin da ta ce ya saɓa wa manufar ziyarar jinyar da kotu ta amince da ita.

ICPC ta ce za ta sanar da kotu game da abin da ta bayyana a matsayin karya umarnin kotu, tare da bayyana cewa ta k**a Farfesa Bello Abubakar bisa zargin bayar da bayanan ƙarya, kuma ana ci gaba da bincike a kansa.

Hukumar ta jaddada cewa za ta ci gaba da mutunta doka, amma ba za ta lamunci amfani da sassaucin da take yi ta hanyar da ba ta dace ba.

07/07/2026

An shiga ruɗani yayin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya rera tsohuwar waƙar taken ƙasa yayin ganawa da ministoci da sauran mambobin majalisar zartarwa ta gwamnati.

05/07/2026

An samu gagarumin ci gaba a yaƙi da matsalar tsaron Najeriya ƙarƙashin shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan Harkokin Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Malam Abdulaziz Abdulaziz ya ce matsalar ta daɗe ta na yaɗuwa a cikin mutane amma zuwa yanzu an ci ƙarfinta.

29/06/2026

Kalli yadda Hukumar NDLEA ta lalata miyagun ƙwayoyi da sauran kayayyakin da aka kwace yayin samame da ayyukan yaki da safarar miyagun ƙwayoyi a Jihar Kano.

Ƙungiyoyin farar hula masu yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Jihar Kano sun yi kira ga gwamnati, iyaye, malamai ...
27/06/2026

Ƙungiyoyin farar hula masu yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a Jihar Kano sun yi kira ga gwamnati, iyaye, malamai da sauran masu ruwa da tsaki da su haɗa kai domin daƙile matsalar shaye-shaye, wadda s**a bayyana a matsayin babbar barazana ga makomar matasa da ci gaban al’umma.

An bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin gangamin wayar da kai na “My Voice Against Drugs Walk”, da aka shirya domin bikin Ranar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Duniya, ranar da Majalisar Ɗinkin Duniya (UN) ta ware a duk shekara domin wayar da kan al’umma kan illolin shaye-shaye da fataucin miyagun ƙwayoyi

24/06/2026

BIDIYO: "Yanzu Hanya Ta Fara Sauƙaƙa" — Ra’ayoyin Direbobi Kan Amfanin Aikin Titin Kano–Abuja Ga Arewacin Najeriya

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when WDN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share