WDN Hausa

WDN Hausa WDN Hausa a shirye muke wajan cigaba da kawo muku sahihan labarai da shirye shirye masu nishaɗantarwa da ilimantarwa

23/07/2025

Hukumar kula da jami'oin Najeriya, ta amince da dawo wa da Northwest University sunanta na asali.

Mataimakin shugaban jami'ar, Farfesa Mukhtar Atiku Kurawa, ne ya bayyana hakan lokacin da yake tattaunawa da manema labarai a ofishinsa dake jama'ar a Kano.

Ga jawabinsa a harshen turanci da Hausa

23/07/2025

Rundunar Hisbah ta jihar Kano, reshen ƙaramar hukumar ta sanya Jumaʼa 1 ga watan Ogusta, a matsayin ranar ɗaura auren matasan da s**a taɓa ɗaurawa kansu aure ba tare da sanin iyaye ba, wato Aliyu da Fatima, dukkan su mazauna unguwar Yakasai dake ƙwaryar birnin Kano.

Shugaban hukumar Hisbah a ƙaramar hukumar birnin Kano Hamidan Tanko Alasaka, shi ne ya sanar da hakan lokacin da yake zantawa da DNN Hausa, yana mai cewa an cimma matsaya tsakanin iyayen yaran da Hisbah, akan cewa za’a ɗaura wannan sabon aure a ofishin Hisbah ta karamar hukumar birni a ranar 1 ga watan Ogusta na wannan shekara.

Akan haka ne hukumar ke neman al’umma su tallafawa masu niyyar yin auren, musamman waɗanda s**a yi alƙawarin bayar da tallafi tun farko. Inda ya ce akwai mutanen da s**a yi alƙawarin bayar da tallafi ga masu shirin zama ango da amaryar amma kawo wannan lokaci tallafin bai zo hannun Hisbah ba.

Idan za’a iya tunawa a kwanakin baya ne, wasu matasan s**a ɗaurawa kansu aure ba tare da sanin iyayen su ba, saboda tsananin ƙaunar da suke yiwa juna, wanda hakan ne yasa iyayen Fatima garzayawa ofishin Hisbah da manufar a kashe auren, saboda bai cika sharuɗan addinin Islama ba.

13/07/2025

Allah Ya yiwa tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari rasuwa a yau ranar Lahadi yana da shekara 82 da haihuwa. Wata sanarwa da Garba Shehu mai magana da yawunsa ya fitar ta ce Buhari ya rasu a wani asibiti da ke birnin Landan. Fadar shugaban Najeriya ta ce ya rasu da misalin ƙarfe 4:30 “sakamakon d...

Mai martaba Sarkin Kano Khalifah Muhammadu Sunusi Na Biyu,ya ce Sai Iyaye da sauran Alumma sun Koma bin koyarwar Addini ...
02/06/2025

Mai martaba Sarkin Kano Khalifah Muhammadu Sunusi Na Biyu,ya ce Sai Iyaye da sauran Alumma sun Koma bin koyarwar Addini da kuma Inganta tarbiya matukar ana son fita daga halin gubacewar marasa da ake fuskanta fadin jihar Kano da Kasa Baki daya.

Sarkin ya bayana hakan lokacin saukar karatun Alkur’ani Mai girma na dalibai Saba’in Karo na takwas da ya gudana Jiya Lahadi a makarantar Ma’ahad Abdulhamid littahfezil Kur’an dake Unguwar Shatsari cikin karamar hukumar dala a nan Kano.

Mai martaba Sarkin na Kano Wanda Jarman Kano Alhaji Ahmad Umar, ya wakilta ya Kara da cewar Kula da tarbiya da Kuma Ilimin adidini abune da kowa ya kamata ya Kula da shi dan ceto matsa daga halin da suke shiga.

Gwamnatin Najeriya ta shigar da ƙarar Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, saboda zargin ɓata s...
23/05/2025

Gwamnatin Najeriya ta shigar da ƙarar Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, saboda zargin ɓata suna da ta yi a gidan talabijin kai-tsaye.

Gwamnatin na zargin dakatacciyar ƴarmajalisar, da ''yin ƙage, duk kuwa da ta san cewa hakan zai shafi ƙimar mutum'', tana mai kafa hujja da cewa yin hakan laifi ne da ke ɗauke da hukunci ƙarƙarshin sashe na 392 na kundin tsarin mulkin ƙasar.

Daga cikin jerin mutanen da gwamnatin da sanya a matsayin shaidun da za su tabbatar da zargin, har da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio da tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello.

25/04/2025

Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA) tare da Hukumar Hana Fataucin Mutane (NAPTIP) sun kafa wata rundunar jami’an su domin hada karfi tare wajen yaƙi da safarar miyagun kwayoyi da safarar mutane.

Wannan mataki ya fito ne a lokacin da Shugabar NAPTIP, Binta Lami Adamu Bello, ta kai ziyarar girmamawa ga Shugaban NDLEA, na Kasa Birgediya Janar Mohammed Buba Marwa, mai ritaya a hedikwatar NDLEA dake Abuja, yau jumma’a 25 ga Afrilu, 2025.

Gwamnatin jihar Kano ta ce zata gudanar da bincike bayan gano wani guri da take zargin ana yin aikin tashar saukar jirgi...
28/03/2025

Gwamnatin jihar Kano ta ce zata gudanar da bincike bayan gano wani guri da take zargin ana yin aikin tashar saukar jirgin sama ba bisa kaida ba tare da rufe hanyar da manoma ke zuwa gonakinsu a garin Tiga dake karamar hukumar Bebeji.

Sakataren kwamitin gwamnatin Kano dake yaki da gine-gine ba bisa kaida ba Hamid Sidi Ali, shi ne ya bayana hakan ga manema labarai lokacin da kwamitin ya ziyarci gurin da ake aikin da safiyar ranar Jumma’a.

19/03/2025

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya yi alƙawarin baiwa sarakunan Kano da hakimai dukkanin goyon bayanl da gudunmawar da su ke bukata domin gudanar da hawan sallah karama.

Gwamna Abba Kabir Yusuf na wannan jawabin ne yayin da yake gabatar da shan ruwa tare da sarakunan a fadar gwamnatin jihar ranar talata.

Gwamnan ya ce yana kira ga sarakunan Kano Rano Gaya da Karaye da su da hakimansu kan su fito domin gudanar da bukukuwa hawan sallah kamar yadda aka saba.

12/03/2025

Rundunar 'yan sandan jihar Katsina ta horar da sabbin kananan 'yan sanda yadda ake gudanar da aiki cikin kwarewa

Bayanin hakan na a cikin wata sanarwa daga kakakin rundunar 'yan sandan jihar DSP Sadiq Aliyu Abubakar.

Hukumar kula da yanayi a Najeriya tayi gargaɗi da cewa akwai yiwuwar a fuskanci tsananin zafin rana a wasu jihohin arewa...
11/03/2025

Hukumar kula da yanayi a Najeriya tayi gargaɗi da cewa akwai yiwuwar a fuskanci tsananin zafin rana a wasu jihohin arewacin Najeriya na tsawon kwanaki huɗu.

Hukumar ta ce mutane za su ji sauyin al’amura a tsawon lokacin da za a kwashe ana tsala zafin ranar.

Jihohin sun haɗa da Neja da Kwara da Taraba da Sokoto da Kogi da Nasarawa da Adamawa da Kaduna da Zamfara da Plateau da Benue da kuma birnin tarayya Abuja.

Sanarwar da Nimet ta fitar ranar Litinin a birnin Abuja, ta ce mutane su guji fita cikin tsananin zafi musamman daga karfe 12 na rana zuwa karfe 3 na yamma.

Tsohon gwamnan Kaduna Nasir El-Rufa'i ya fita daga jam'iyyar APC zuwa SDP.Tsohon gwamnan ya sanar da hakan ne ta cikin w...
10/03/2025

Tsohon gwamnan Kaduna Nasir El-Rufa'i ya fita daga jam'iyyar APC zuwa SDP.

Tsohon gwamnan ya sanar da hakan ne ta cikin wata sanarwa da ya fitar yau Litinin.

Majalisar wakilan Najeriya ta gabatar da ƙudirin da zai ƙwace wa hukumar zaɓen ƙasar ikonta na yi wa jam'iyyun siyasar ƙ...
07/03/2025

Majalisar wakilan Najeriya ta gabatar da ƙudirin da zai ƙwace wa hukumar zaɓen ƙasar ikonta na yi wa jam'iyyun siyasar ƙasar rajista da kula da ƙa'idojin jam'iyyun.

ƙudurin wanda kakakin majalisar wakilan ƙasar Hon.Tajudeen Abbas tare da haɗin gwiwar Hon Marcus onobun daga jihar Edo s**a gabatar, ya buƙaci a samar da wata hukuma mai zaman kanta da za ta kula da batun yi wa jam'iyyu rajista da kula da ƙa'idojinsu da ɗaukar nauyin jam'iyyun.

Tuni dai ƙudirin ya wuce karatu na biyu a zauren majalisar.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when WDN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share