17/05/2026
Yadda akayi nasarar ceto wani bawan Allah da rai bayan ya shafe sama da awanni 9 a binne a cikin tarkacen ginin da ya rushe.
Mutun biyar ne s**a rasu a wannan gini mai hawa uku da ake ginawa da ya rushe a yankin Durumi 3, kusa da Kasuwar Gudu, Abuja, a yau Asabar.
Tuni Ministan Abuja Nyeson Wike, ya bada umurnin kula da lafiyar wayanda iftila'in ya rutsa dasu a asibiti kyauta.
Sakatariyar Lafiya ta Hukumar Babban Birnin Tarauya (FCTA), Dakta Dolapo Fasawe, ta tabbatar cewa mutun biyar ne s**a rasu wanda galibi leburori ne.