WDN Hausa

WDN Hausa WDN Hausa a shirye muke wajan cigaba da kawo muku sahihan labarai da shirye shirye masu nishaɗantarwa da ilimantarwa

17/05/2026

Yadda akayi nasarar ceto wani bawan Allah da rai bayan ya shafe sama da awanni 9 a binne a cikin tarkacen ginin da ya rushe.

Mutun biyar ne s**a rasu a wannan gini mai hawa uku da ake ginawa da ya rushe a yankin Durumi 3, kusa da Kasuwar Gudu, Abuja, a yau Asabar.

Tuni Ministan Abuja Nyeson Wike, ya bada umurnin kula da lafiyar wayanda iftila'in ya rutsa dasu a asibiti kyauta.

Sakatariyar Lafiya ta Hukumar Babban Birnin Tarauya (FCTA), Dakta Dolapo Fasawe, ta tabbatar cewa mutun biyar ne s**a rasu wanda galibi leburori ne.

17/05/2026

Kabiru Alasan Rurum Ya Bayyana Matsayarsa Kan Dangantakarsa Da Sanata Kawu Sumaila

15/05/2026

Yadda Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya yi ban kwana da Maniyatan farko 560 da suke shirin tashi zuwa Madina daga filin jirgin sama na Malam Aminu Kano a daren Juma'a.

Gwamnan ya roki Alhazan da su yiwa Kano da Najeriya Adu'oin samun zaman lafiya da cigaba a kasa mai tsarki.

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana cewa ya yi watsi da matsin lamba daga magoya baya, abokai ...
14/05/2026

Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, ya bayyana cewa ya yi watsi da matsin lamba daga magoya baya, abokai da ‘yan uwansa da s**a nemi ya tsaya takarar kujerar Sanata a babban zaɓen 2027.

Zulum ya bayyana hakan ne yayin da yake jagorantar taron manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Maiduguri, gabanin zaɓen fidda gwani na Majalisar Wakilai da aka gudanar ranar Alhamis.

“Duk da irin matsin lambar da na fuskanta daga magoya baya da mutanen da ke kusa da ni, na fifita haɗin kai da zaman lafiyar jam’iyya fiye da burina na kaina.

08/05/2026

BIDIYO: Rikici ya ɓarke tsakanin mazauna garin Ishi da na Itali a Ƙaramar Hukumar Abaji da ke Jihar Kogi, lamarin da ya jawo asarar rayuka da dukiya da ba a tantance adadi ba.

Aminiya ta rawaito cewa, rikicin ya fara ne bayan wasu ɓatagari da ake zargin ramuwar gayya s**a zo yi s**a afka wa garin na Ishi, inda s**a halaka mutane da dama, tare da ƙona gidaje da shaguna.

Garuruwan biyu dai sun shafe shekaru da dama suna rikici a tsakaninsu, wanda ya samo asali daga rikicin gonaki da rafukan kamun kifi.

🎥: Tijani Labaran

HOTUNA: Yadda tsohon Gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau, wanda a yanzu ke neman tsayawa takarar Sanatan Kano ta ...
08/05/2026

HOTUNA: Yadda tsohon Gwamnan Jihar Kano, Malam Ibrahim Shekarau, wanda a yanzu ke neman tsayawa takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a jam'iyyar APC, ya mika fom ɗinsa, inda ake raɗe-raɗin cewa A.A. Zaura, ya rasa takara a jam'iyyar.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when WDN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share