12/03/2026
Shugaban Hukumar Finafinai ta Nijeriya, kuma Sarkin Kannywood, Ali Nuhu Mohammed, ya nuna karamci da tausayi a wannan wata mai alfarma na Ramadan ta hanyar bayar da tallafin azumi ga wasu daga cikin ‘yan fim na Jihar Katsina.
Wannan tallafin da ya bayar ga ‘yan uwa da abokan sana’a, ya bada ne domin su samu saukin gudanar da ibadar azumi cikin walwala.
Irin wannan taimako yana nuna muhimmancin hadin kai, kauna da taimakon juna a cikin al’umma, musamman a wannan lokaci mai albarka na Ramadan.
‘Yan fim da dama sun nuna godiya tare da yi masa addu’a, suna rokon Allah Ya saka masa da alheri, Ya kara masa daukaka da arziki.
Wannan dai ba shi ne karo na farko da Ali Nuhu ya saba tallafawa 'yan fim din jihar Katsina ba, ko a shekarar da ta gabata ya tallafawa wasu daga cikin su tallafin Shinkafar Azumi da kuma kudade.