Prime Time News Hausa

Prime Time News Hausa Hausa reliable online Newspapers

Gidauniyar Dr. Magashi Garba da Ma’aikatar Jinkai Sun Gudanar da Taron Kwana Daya Akan Samar da Asusun Agajin Gaggawa a ...
25/08/2025

Gidauniyar Dr. Magashi Garba da Ma’aikatar Jinkai Sun Gudanar da Taron Kwana Daya Akan Samar da Asusun Agajin Gaggawa a Kano

Gidauniyar AMG karkashin jagorancin Dr. Aminu Magashi Garba tare da haɗin gwiwar Ma’aikatan Jinkai na Jihar Kano sun gudanar da taron kwana ɗaya da ya mayar da hankali kan yadda za a samar da Asusun Agajin Gaggawa domin inganta bangaren lafiya da ilimi a jihar.

A jawabin sa, shugaban gidauniyar AMG, Dr. Aminu Magashi Garba, ya bayyana cewa an shirya taron ne domin tattauna matsalolin da al’umma ke fuskanta a fannoni daban-daban. Ya ce lafiya da ilimi su ne ginshiƙan ci gaban kowace al’umma, saboda haka akwai buƙatar gwamnati ta dauki ƙarin matakai na musamman domin samar da asusun da zai tallafa wa lafiyar al’ummar Kano baki ɗaya.

A nasa jawabin, shugaban Ma’aikatan Jinkai na Kano, Hon. Adamu Aliyu Kibiya, ya jaddada bukatar haɗin kai tsakanin gwamnati, kungiyoyi masu zaman kansu da sauran masu ruwa da tsaki wajen ciyar da jihar gaba. Ya ce idan aka samar da wannan asusu, zai taka muhimmiyar rawa wajen rage radadi da matsalolin da al’ummar Kano ke fuskanta, musamman a lokacin bala’o’i da rashin lafiya.

Wakiliyar Prime Time News Hausa ta rawaito cewa mahalarta taron sun bukaci gwamnatin tarayya da ta jiha da kuma ‘yan kasuwa su haɗa hannu wajen kafa Asusun Agajin Gaggawa domin kare rayukan jama’a a lokutan hadari da kuma inganta walwalar al’umma.

Kwamishinan Yada Labarai ya Jaddada Bukatar Gogewa da Kwarewa a Aikin JaridaDaga Safiya Usman Aikin jarida na bukatar go...
14/08/2025

Kwamishinan Yada Labarai ya Jaddada Bukatar Gogewa da Kwarewa a Aikin Jarida

Daga Safiya Usman

Aikin jarida na bukatar gogewa da kwarewa a aikace domin yada labarai masu inganci, a cewar Kwamishinan Yada Labarai da Ayyukan Cikin Gida na Jihar Kano, Comrade Abdullahi Ibrahim Waiya.

Waiya ya bayyana haka ne a yayin wani taro da Kungiyar ‘Yan Jarida ta Kasa (NUJ) reshen Kano ta shirya tare da hadin gwiwar ma’aikatarsa, wanda aka gudanar a Kano, bisa sahalewar Gwamnan Jihar, Injiniya Abba Kabir Yusuf.

Ya ce taron ya mayar da hankali ne kan tattauna hanyoyin bunkasa aikin jarida a jihar, tare da kara baiwa ‘yan jarida masu tasowa horo da shawarwari domin inganta basirarsu a fagen aikin jarida.

“Gwamnatin Jihar Kano ta shirya tsaf domin cigaba da baiwa ‘yan jarida masu tasowa horo, ganin ido da kuma samar da damar kwarewa a aikin jarida,” inji Waiya.

A nasa jawabin, Shugaban NUJ na kasa, Comrade Alhassan Yahaya, ya nuna farin cikinsa kan wannan taro da ya gudana a Kano, inda ya ce yana da nufin inganta albashin ‘yan jarida da ci gaba da bai musu horo domin inganta aikin jarida.

Ya kuma yi kira ga mambobin NUJ a Kano da su ziyarci asibitoci domin yin inshora don kare lafiyarsu da ta iyalansu.

A nasa bangaren, daya daga cikin gogaggun ‘yan jarida a Kano, Ahmad Aminu, ya ce taron ya kunshi tattaunawa kan hanyoyin da za su kawo ci gaba a aikin jarida tare da samar da tsare-tsaren horo ga ‘yan jarida.

Taron ya samu halartar manyan ‘yan jarida da tsofaffin kwamishinoni na Ma’aikatar Yada Labarai da Ayyukan Cikin Gida, ciki har da Baba Haliru Dantiye, Farfesa Umar Faruk Jibrin, da sauran mahalarta taron.

‎‎Yadda Sauyin Yanayi Ke Jefa Mata Masu Juna Biyu Cikin Hadari"‎‎‎Daga Safiya Usman ‎‎A wani bincike na musamman da aka ...
29/07/2025


‎Yadda Sauyin Yanayi Ke Jefa Mata Masu Juna Biyu Cikin Hadari"



Daga Safiya Usman


‎A wani bincike na musamman da aka gudanar, an gano cewa sauyin yanayi, musamman lokacin zafi, na haddasa matsaloli masu tarin yawa ga mata masu juna biyu, inda hakan ke jefa su cikin hadurran lafiya da ke bukatar kulawa ta musamman.

‎A cikin hirar da muka yi da Hajiya Fatima, wata gogaggiya a fannin kiwon lafiya da wayar da kai kan batutuwan sauyin yanayi, ta bayyana cewa mata da yawa ba su da isasshen ilimi dangane da yadda sauyin yanayi ke shafar lafiyar su, musamman lokacin da suke dauke da ciki.

‎ “Akwai lokacin da mace ke samun canje-canje na jiki saboda juna biyu. Sauyin yanayi, musamman zafi, na kara tsananta lamarin. Mafi yawan matan da ba su da ilimi kan hakan kan fada cikin mawuyacin hali,” in ji Hajiya Fatima.



‎Zafin Rana Da Hayakin Gawayi Na Kara Dagula Lamura

‎A cewar Hajiya Fatima, zafi mai tsanani na hana mata masu juna biyu sukuni, kuma hakan na iya janyo hauhawar jini, bugun zuciya da ma faduwar gwiwa. Ta kara da cewa amfani da gawayi wajen dafa abinci, duk da cewa yana saukaka kashe kudi, na iya jefa lafiyar mata cikin hadari.

‎ “Hayakin gawayi yana da illa ga huhu, musamman ga masu ciki. Sannan wahalar hurawa da saurin konewar sa na kara wahalar da mace mai juna biyu,” ta ce.



‎Ta yi kira ga mazaje da su dinga bai wa matansu kulawa ta musamman, ta hanyar tanadar musu da wuri mai iska, da amfani da hasken rana (solar) domin saukaka zafin daki da kare lafiyar uwargida da jinjirin da ke cikin ta.

‎Bitar Rayuwar Mata Masu Sana’ar Gurasa a Kwanar Dala

‎A wani bangare na wannan bincike, Hajiya Fatima ta kai ziyara unguwar Kwanar Dala a Kano, inda ta gana da wasu mata da ke gudanar da sana’ar gurasa. Ta yaba da kokarinsu na jurewa kalubalen sauyin yanayi da hayakin wuta da ke barazana ga lafiyarsu.

‎“Matan suna yin gurasa ba dare ba rana. Ko da ruwa ya sauka, su kan ci gaba da aiki. Wannan jajircewa ta burge ni matuka,” in ji ta.



‎Matan sun bayyana cewa suna fuskantar zafin wuta da hayaki, amma babu wata mafita ta zamani da za ta taimaka musu wajen gudanar da sana’ar cikin sauki da kariya ga lafiyarsu.

‎Shirin Muryarta Raya Muhalli Ya Taimaka

‎Hajiya Fatima ta bayyana irin rawar da shirin “Muryarta Raya Muhalli” ke takawa wajen wayar da kai kan illolin sauyin yanayi da hanyoyin da za a bi don kare kai. Ta ce ta koyi darussa masu yawa daga shirin, wanda hakan ne ya karfafa mata gwiwar ci gaba da ilimantar da mata a unguwanni daban-daban.

‎Kira Ga Gwamnati Da Kungiyoyi Masu Zaman Kansu

‎A karshe, Hajiya Fatima ta bukaci Gwamnatin Jihar Kano da kungiyoyin ci gaban al’umma da su rika kai dauki ga mata masu sana’ar gurasa da sauran al’umma da ke fama da matsin rayuwa sakamakon sauyin yanayi.

‎"Tallafa wa wadannan mata zai ba su damar amfani da hanyoyin zamani wajen sana’ar su, sannan hakan zai rage hadurran lafiyar da suke fuskanta,” ta jaddada.



Gidauniyar AMG Ta Kaddamar Da Shirin Tallafawa Marasa Lafiya a KanoDaga Safiya Usman Gidauniyar AMG ta bayyana cewa kula...
26/07/2025

Gidauniyar AMG Ta Kaddamar Da Shirin Tallafawa Marasa Lafiya a Kano

Daga Safiya Usman

Gidauniyar AMG ta bayyana cewa kula da lafiyar al’umma, musamman marasa ƙarfi da masu fama da cututtuka daban-daban, na daga cikin muhimman abubuwa da s**a kamata a mayar da hankali a kansu domin inganta rayuwar jama’a a fadin Jihar Kano.

Wannan bayani ya fito ne daga Shugaban Gidauniyar, Dr. Aminu Magashi Garba, yayin wata tattaunawa da aka gudanar a shelkwatar gidauniyar tare da haɗin gwiwar ma’aikatar lafiya da taimakekeniya ta jihar Kano.

A cewar Dr. Aminu Magashi, babban burin taron shi ne kara wayar da kai da kuma tallafa wa marasa ƙarfi ta hanyar yi musu rijista a asibitoci daban-daban, samar musu da magunguna kyauta da kuma kula da lafiyarsu ba tare da wata wahala ba.

"Za mu ware sama da naira miliyan biyu (₦2,000,000) a wannan shekarar domin ci gaba da wannan aikin alheri, musamman a kananan hukumomi daban-daban na jihar Kano," inji Dr. Aminu.

A nasa bangaren, wani daga cikin mahalarta taron, Malam Salisu Umar Durumin Iya, ya bayyana cewa lokaci ya yi da masu hannu da shuni za su fito su tallafa wa marayu da marasa ƙarfi domin samun lada da kuma taimakawa wajen rage radadin rayuwa da suke fuskanta.

Ya ce kwamitin da gidauniyar ta kafa zai gudanar da aikin zakulo mabukata cikin tsari domin yi musu rijista kyauta a asibitoci.

A ƙarshe, Alhaji Sha’ibu Ahmed Indabawa, ɗaya daga cikin mahalarta taron, ya yaba da ƙoƙarin Gidauniyar AMG wajen tallafa wa mabukata. Ya kuma yi kira ga sauran masu hali da su shiga cikin irin wannan aiki domin taimakawa rage mace-mace da barace-barace da ke yawaita a fadin jihar Kano.

Taron ya ƙare da ƙudurin ci gaba da irin wannan aikin alheri don tabbatar da ingantacciyar rayuwa ga kowa da kowa.

A Kano, Matasa Sun Fara Jagorantar Yaki da Wariya ga Masu BukataDaga Safiya Usman Kano, Najeriya – Bashir Ali Haruna, wa...
23/06/2025

A Kano, Matasa Sun Fara Jagorantar Yaki da Wariya ga Masu Bukata

Daga Safiya Usman

Kano, Najeriya – Bashir Ali Haruna, wani matashi da ke fama da larurar kafa ya bayyana yadda rashin tallafi daga gwamnati da tsangwama daga al’umma s**a shafi rayuwarsa. A cewarsa, lokacin da yake karatun diploma, ya sha fama da rashin sauki, amma hakan bai sa ya daina fatan alheri ba.

“Na kammala diploma, amma na dade ina neman aiki kafin na samu wajen wani gidan rediyo mai zaman kansa,” in ji Bashir. Duk da haka, ya sake komawa makaranta domin daukar darasi a matakin HND.

A yau, Bashir ya mayar da karatu tamkar mafita, yana kira ga gwamnati da kungiyoyi masu zaman kansu da su bude damammaki ga masu bukata ta musamman – musamman wajen koyar da sana’o’i da samar da ayyukan yi. “Karatu shine gatan mai bukata. Koda akwai kalubale, kada a karaya,” in ji shi.

A cikin wani yunkuri na fahimtar halin da masu bukata ta musamman ke ciki, rahotanni sun bayyana cewa dubban ‘yan Najeriya masu fama da larura na fuskantar kalubale daga gwamnati da al’umma, lamarin da ke hana su cika muradunsu na yau da kullum.

Wasu daga cikin wadannan kalubale sun hada da rashin samun ilimi mai inganci, kiwon lafiya, damar koyon sana’a da kuma shiga aikin gwamnati – abubuwan da s**a zama ‘yancin kowa a karkashin dokokin kasa da kasa. A mafi yawan lokuta, ana ware su ne ba tare da hakki ba, kuma ba tare da la’akari da irin gudunmuwar da za su iya bayarwa ba.

Yarima Sulaiman Ibrahim, Matashi ne kuma shugaban wata kungiyar farar hula da ke fafutukar kare hakkin masu bukata ta musamman ne aa kano. ya ce shi kansa ya rasa gani a wani lokaci na rayuwarsa, kuma tun daga wannan lokaci yana rayuwa da kalubale.

“Da zarar mutum ya kamu da wata larura, ana jefar da shi kamar babu darajarsa,” in ji shi.
A cewarsa, akwai bukatar gwamnati ta daina nuna halin ko in kula: “Ilimi, lafiya, sana’a – wadannan ba wai taimako ba ne, hakkinsu ne,” ya jaddada. Kungiyarsa na kokari wajen kwatar hakkin masu bukata daga jami’ai, jami’an tsaro da ma’aikatu, duk da cewa hakan na fuskantar turjiya.

Hakkin Masu Bukata ta Musamman da Abinda Doka Ta Tanada
A Najeriya, Dokar Kare Hakkin Masu Bukata ta Musamman ta 2018 (Discrimination Against Persons with Disabilities (Prohibition) Act, 2018) tana da cikakken tsari da manufar kare ‘yancin duk wani dan kasa da ke da larura ta musamman. Wannan doka an kirkiro ta ne domin tabbatar da cewa masu nakasa suna samun adalci da damar rayuwa kamar kowane dan kasa.

Daya daga cikin muhimman abubuwan da dokar ta tanada shi ne haramta nuna wariya ga duk wanda ke da nakasa ko wata larura ta jiki ko ta hankali. Wannan yana nufin cewa ba a yarda a hana mutum wani hakki ko damar rayuwa saboda larurar da yake da ita ba.

Haka kuma, dokar ta bayyana cewa masu nakasa suna da hakkin samun ilimi, lafiya, aikin yi, sufuri da shiga gine-ginen jama’a ba tare da wata tangarda ba. Wannan yana tabbatar da cewa za su iya rayuwa cikin kima da mutunci kamar kowa a cikin al’umma.

Dokar ta umarci gwamnatin tarayya, jihohi da kananan hukumomi da su samar da muhallin da ya dace da masu larura, wanda zai ba su damar shiga makarantu, asibitoci, kasuwanni da sauran wuraren aiki cikin sauki.

An bai wa gwamnati shekaru biyar (daga 2019 zuwa 2024) domin ganin cewa dukkan gine-gine da motocin sufuri da ake amfani da su a kasar nan sun dace da bukatun masu bukata ta musamman. Wannan tanadi yana da matukar muhimmanci wajen rage wariya da kara musu damar rayuwa mai inganci.

Matakin Kasa (Gwamnatin Tarayya)
A shekarar 2024, Gwamnatin Tarayya ta karawa Hukumar Kare Hakkin Masu Bukata ta Musamman (NCPWD) kudin kasafinta da kashi 500% fiye da shekarar 2023. Wannan karin ya nuna irin jajircewar da Shugaba Bola Tinubu ke nunawa wajen ganin an aiwatar da dokokin da s**a shafi samun damar shiga gine-gine da rayuwa cikin kima.

Domin shekarar 2025, an tsara cewa hukumar NCPWD za ta samu kusan naira biliyan 2.1, domin aiwatar da shirin karfafa tattalin arzikin masu bukata, da kuma shirye-shiryen da s**a shafi mata masu nakasa da ci gaban su.

Sai dai kungiyoyin farar hula kamar CISLAC na ci gaba da kira da a kara kasafin kudi a cikin kasafin kudin karin gaggawa na 2024, tare da tabbatar da cewa an biya bukatun masu nakasa a kowane mataki.

Matakin Jihar Kano
A cikin kasafin kudin 2023, Gwamnatin Kano ta ware naira miliyan 100 ga Asusun Tallafa wa Masu Larura (Disability Trust Fund) da kuma Hukumar Kula da Mutanen da ke da Bukata ta Musamman, karkashin Ma’aikatar Harkokin Musamman.

A shekarar 2024, an kara kasafin wannan asusu zuwa naira miliyan 197.3, domin ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen tallafi, musamman wajen samar da horo da ayyukan yi ga masu larura a jihar.

A wani rahoto, an bayyana cewa jihar Kano ta ware kusan naira miliyan 158 don shirye-shirye na tallafi da karfafa gwiwar masu bukata ta musamman, ciki har da ayyuka na musamman da horar da sana’o’i.

Baya ga hakan, gwamnatin jihar na shirin kafa Hukumar Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, domin kula da aiwatar da tsare-tsaren da s**a shafi walwalar masu nakasa.

Shawarwarin Masana
Dr. Nasir Yakubu Malami daga Jami’ar Bayero, Kano, ya ce lokaci yayi da gwamnati za ta tsara gine-ginen jama’a da su dace da masu larura.

“Asibitoci, makarantu, kasuwanni – ya kamata su kasance wurare masu saukin shiga da fita ga dukkan nau’in nakasa,” in ji shi.

Ya kuma jaddada cewa akwai bukatar tsare-tsare daban-daban na lafiya, ilimi da walwala da s**a dace da bangarorin larura – na gani, ji, motsi da sauransu.

Dr. Binta Bala, daraktar ayyukan jinkai a jihar Kano, ta ce babbar matsala ita ce rashin wakilcin masu bukata ta musamman a cikin manyan kujeru na gwamnati. “Ana basu mukamai na SA ko PA kawai, ba a basu dama su zamo cikin masu yanke shawara ba,” ta bayyana.

Ta kuma bukaci gwamnati da ta tabbatar da aiwatar da dokokin da aka tsara domin kare rayuwar masu bukata ta musamman da hukunta duk wanda ya ci zarafinsu.

A yayin da kalubale ke ci gaba da bayyana, matasa da kungiyoyin masu fafutuka suna nuna cewa lokaci ya yi — ba na tausayi ba, sai na adalci. Masu bukata ta musamman ba za su tsaya a gefe ba har abada.

Al’ummar Sheka Sun kuduri aniyar  Kawar Da Fadan Daba Da Shaye-shaye Tsakanin MatasaDaga Aisha Abubakar Mai AgogoA wani ...
01/06/2025

Al’ummar Sheka Sun kuduri aniyar Kawar Da Fadan Daba Da Shaye-shaye Tsakanin Matasa

Daga Aisha Abubakar Mai Agogo

A wani yunƙuri na tabbatar da zaman lafiya da daidaita rayuwar matasa a yankin, al’ummar Sheka da ke cikin karamar hukumar Kumbotso a Jihar Kano, sun gudanar da taro na musamman a safiyar yau domin tattauna hanyoyin da za su magance matsalolin fadan daba da shaye-shaye da ke addabar matasa.

Taron, wanda aka gudanar a filin makarantar firamare ta Sheka, ya samu halartar manyan baki daga sassa daban-daban ciki har da masu rike da sarautar gargajiya, malamai na addini da na boko, da kuma wakilan kungiyoyi masu zaman kansu.

A jawabin sa, Dagacin Sheka, Alhaji Abubakar Musa Zakari Sheka, ya bayyana cewa kafa kungiyar da aka yi na da nufin samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin al’ummar. Ya ce, "Wannan kungiya za ta zama wata kafa ta kawo sauyi mai kyau a tsakanin matasa, ta hanyar ba su shawarwari da tallafi domin su canza rayuwarsu."

Shi ma da yake bayani, Shugaban Karamar Hukumar Kumbotso, Hon. Abdullahi Ghali BASAF, ya jaddada cewa matasa za su gyaru ne idan aka rungume su da kulawa da fahimta. “Idan har za a rinka jin matsalolin matasa, ana ba su tallafi ta hanyoyi daban-daban, babu shakka za a samu nagartattun matasa a gaba,” in ji shi.

Kungiyar Muryar Mutanen Sheka, wacce ta shirya taron, ta bayyana kudirinta na samar da ayyukan yi ga matasa, da kuma ba wasu jari domin su fara sana’o’i, yayin da wasu za a mayar da su makaranta don samun ilimi da tarbiyya.

Al’ummar Sheka sun bayyana wannan taro a matsayin sabon babi na fatan dorewar zaman lafiya da ci gaban yankin, tare da bukatar hadin kan kowa da kowa domin cimma nasara.

Mutumin da ya ƙirƙiro maganin zubar da ciki ya mutuDaga Aisha Abubakar Mai Agogo Ƙwararren mai binciken kimiyya wanda ya...
31/05/2025

Mutumin da ya ƙirƙiro maganin zubar da ciki ya mutu

Daga Aisha Abubakar Mai Agogo

Ƙwararren mai binciken kimiyya wanda ya ƙirƙiri maganin zubar da ciki, Étienne-Émile Baulieu ya mutu yana da shekara 98 a duniya.

Dr Baulieu ya ƙirƙiro maganin zubar da cikin ne a shekarar 1984.

Bayan ƙirƙiro shi, maganin mifepristone ya kawo sauyi a tsarin haihuwa a duniya kamar yadda kafar yada labarai da BBC ta ruwaito.

TINUBU SHEKARU BIYU A MULKI: Gwamnati na Fama da Kalubale Duk da Yunkurin SauyiDaga Aisha Abubakar Mai AgogoYau Alhamis,...
29/05/2025

TINUBU SHEKARU BIYU A MULKI: Gwamnati na Fama da Kalubale Duk da Yunkurin Sauyi

Daga Aisha Abubakar Mai Agogo

Yau Alhamis, 29 ga watan Mayu, 2025, Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya cika shekaru biyu da zama a kujerar shugabancin ƙasar. Wannan lokaci mai ɗan gajeren zango ya kasance cike da muhimman sauye-sauye da s**a shafi fannonin rayuwa na yau da kullum – daga batun man fetur, tattalin arziki, walwalar jama’a, zuwa batun tsaro.

Tun daga ranar farko da ya hau mulki, shugaban ya ɗauki mataki na cire tallafin man fetur – wata doka da ta janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a da masana. Gwamnati ta bayyana wannan mataki a matsayin hanya ta dakile asarar kuɗi da magance zambar da ta dabaibaye tsarin tallafin. Sai dai sakamakon hakan ya jefa talakawa cikin mawuyacin hali, inda hauhawar farashin kaya da faduwar darajar Naira s**a tsananta.

A cikin wadannan shekaru biyu, matsin rayuwa ya ƙaru – daga tsadar kayayyaki, karancin albashi, zuwa ƙarancin aikin yi. Jama’a a kasuwanni da gidajen mai na ci gaba da fuskantar kalubale, yayin da gwamnati ke jaddada cewa tana kan tafarkin gyara, duk da cewa hakan na zuwa a hankali.

A bangaren tsaro kuwa, gwamnatin Tinubu na fuskantar manyan ƙalubale, musamman a arewacin ƙasar, inda hare-haren 'yan bindiga, satar mutane, da rikice-rikicen ƙabilanci da addini ke ci gaba da addabar al'umma. Duk da ɗaukar sabbin dabaru da ƙaddamar da ayyuka na yaki da ta'addanci, tsoro da rashin kwanciyar hankali har yanzu na addabar jama’a.

Duk da cewa an samu cigaba a wasu fannonin, da dama daga cikin 'yan ƙasa na ganin cewa tsadar rayuwa da matsalolin tsaro har yanzu na barazana ga jin daɗin rayuwa da kwanciyar hankali. Yayin da Tinubu ke shirin shiga shekara ta uku a ofis, idanu na ƙasar na karkata wajen ganin ko mulkinsa zai iya cika alkawurran da ya ɗauka.

Jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Kabo : Manuniya Kan Kyawun Alaka Tsakanin Shugaba Tinubu da Sanata BarauDaga Abba Anwar Da ...
28/05/2025

Jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Kabo : Manuniya Kan Kyawun Alaka Tsakanin Shugaba Tinubu da Sanata Barau

Daga Abba Anwar

Da farko ya zama dole a yabawa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu saboda mayar da Babbar Makarantar Kimiyya da Fasaha ta Gwamnatin Tarayya ta Kabo zuwa ga Jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Kabo. Abinda kamar yadda a ka ce, ba a taba samun wani shugaba ya yi haka cikin kankanin lokaci ba.

Bayan hobbasa da kokarin gaske da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa ta Kasa, Sanata Barau Jibrin CON, ya yi wajen samar da wannan Babbar Makarantar, a shiyyar Kano ta Arewa, canza sunan Babbar makarantar da ba ta matsayin Jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Gwamnatin Tarayya, wata manuniya ce ta kyakkyawar alakar da ke tsakanin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da kuma Sanata Barau.

Tun yanzu tun ba a je ko ina ba, shugaban kasa Tinubu ya na nuni da cewar alakarsa da Sanata Barau mai kyau ce kuma zartacciya. Wacce yanayi ya nuna za su iya aiki tare dan ci gaban kasar nan. A dukkan matsayin da mai karatu zai iya tunani.

Kamar dai yadda Sanatan da kansa ya nuna, a cikin shekaru biyu kacal Shugaba Tinubu ya samar da manyan makarantu guda biyu ga jihar Kano. Bayan daga likkafar babbar Kwalejin Ilimi ta Gwamnatin Tarayya ta Kano, zuwa ga matsayin Jami'a. Wacce a da an taba mayar da ita Jami'a amma wasu dalilai na siyasa su ka sa a ka soke hakan. Amman Tinubu ya dawo da waccan daga martabar da a ka soke. Duk bisa kokarin Sanata Barau da abokan aikin sa 'yan majalisa.

Tare da kuma canza mata suna zuwa ga Jami'ar Ilimi ta Yusuf Maitama Sule. Dan tunawa da mazan jiya tare da rike sunan sa a cikin al'umma saboda irin gudummawar da ya bayar wajen ci gaban Arewa da kuma kasa gaba daya.

Sai kuma ita Jami'ar Fasaha da Kimiyya ta Kabo ga kuma Kwalejin Tarayya ta Kimiyya da Fasaha ta Rano. "Wannan ba karamin kyakkyawan baya shugaban kasa ya kafa ba a wannan jihar ta mu ta Kano, " in ji Sanata Barau.

Kalli dai irin babban kokarin da Sanata Barau ya yi fa tun daga matakin Majalisa zuwa ga sahalewar da shugaban kasa ya bayar na mayar da Babbar Makarantar Fasaha da Kimiyya ta Kabo zuwa Jami'ar Fasaha da Kimiyya.

Shi da kan sa Sanatan ya ce "A cikin wata biyu da su ka wuce na gabatar da kudurin neman a mayar da Babbar Makarantar Tarayya ta Fasaha da Kimiyya ta Kabo zuwa Jami'ar Tarayya ta Fasaha da Kimiyya ta Kabo. Wanda ina godewa majalisun mu na Dattawa da na Wakilai. Wanda a cikin wata biyu kacal su ka yarda da wannan kundin kudurin.

Abinda ya rage mana shine samun sahalewar shugaban kasa kan ya sa hannu a mayar da abin ya zama doka. Kafin ma majalisa ta kai masa wannan kudurin na samu shugaban kasa na yi masa bayanin muhimmancin mayar da makarantar ta zama Jami'a.

Bayan ya yi alkawarin zai sa hannu bisa hakan. Da kai masa kuduri ba tare da bata wani lokaci ba, ya rattaba hannu a kai. Kamar yadda ya yi alkawari."

Sanatan ya ci gaba da cewa," Na nunawa shugaban kasa muhimmancin samar da ilimin kimiyya da fasaha ga matasan mu. Wanda Kano ce ta fi kowace jiha yawan matasa a kasar nan. Saboda haka ya zama wajibi da kodayaushe a tallafawa neman ilimin su.

Ba fa wannan ne kawai abubuwan dubawa ba a wannan babban kokari da Sanata Barau ya yi na mayar da wannan makaranta zuwa Jami'ar Kimiyya da Fasaha ba, akwai maganar an samar da wani yalwataccen bigire na samarwa da jama'a aikin yi. A halin da a ke ciki na rashin ayyukan yi ga matasa.

Sannan kuma irin kwasa-kwasan da za a karanta a wannan makaranta na bagarorin kimiyya da fasaha, wanda abinda zamani ke nema kenan ruwa a jallo, su ma su na nuni ga yadda al'umma za su amfana matuka da gaske.

Hatta kayan aiki da samar da yanayi mai kyau ga wannan jami'a dan cimma babban burin kafa ta, Sanatan ya yi alkawarin ci gaba da jajircewa wajen ganin ta mike sosai ta amsa sunan ta na jami'a.

Ya ce zai ci gaba da bibiyar ganin an samar da malamai da kuma yanayi mai kyau na koyo da koyarwa. Hatta ci gaba da gine-gine dan samun gamsassun wurare da kuma bangarori na yin karatu cikin kwanciyar hankali da nutsuwa a cikin zuciyar malamai da dalibai da kuma ma'aikatan wannan jami'a.

Irin hangen nesan da Sanata Barau ke nunawa wajen tafiyar da wannan ofis na sa na dan majalisar dattawa mai wakiltar Kano ta Arewa, da kuma babban mukamin da yake rike da shi na Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, kullum ya na kara haska mana waye Sanatan. Wakili na gari, wanda yake amfani da ilimi wajen tafiyar da harkokin sa na wakilci. Ga kuma dattako da sanin ya kamata.

Bayan yabawa da Sanatan ya yi ga shugaban kasa wajen wannan abin alheri na mayar da makarantar zuwa jami'a, ya ci gaba da cewa, "Kamar yadda kowa ya sani ne cewar su fa matasa sune kashin bayan ci gaban kowace irin al'umma.

Saboda haka kokarin da mu ka yi na mayar da wannan makaranta zuwa jami'a abu ne da ya dace da bukatun zamani na harkokin ci gaban al'umma. Ya zama dole mu yi duk mai yiwuwa wajen ganin mun ba matasan mu goyon baya da dukkan tallafin da ya kamata na su bayar da ta su gudummawar na ci gaban kasa. Dan mu gudu tare mu tsira tare."

Ga dukkan mai lura da al'amuran yau da kullum zai fahimci cewar Sanata Barau ya na da tsahon da zai iya yi wa jama'arsa aiki a ko ina ne cikin fadin kasar nan.

Idan ka kalli abubuwan kawo ci gaba da yake ta kwararowa al'ummar sa ba kakkautawa ka san lallai wannan shugaba ne mai sanin ya kamata. Kuma Jagora ne mai iya fahimtar bukatun al'ummar da su ka tura shi wakilci a Abuja. Ba wai ba inke!

Anwar tsohon Babban Sakataren Yada Labarai ne na tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje CON, za kuma a iya samun sa a [email protected]
28 ga Watan Mayu, 2025

Kungiyar Albinism Association of Nigeria (AAN) Ta Gudanar da Taron Wuni Daya a Kano, Tare da Kira ga Gwamnati kan Kula d...
15/05/2025

Kungiyar Albinism Association of Nigeria (AAN) Ta Gudanar da Taron Wuni Daya a Kano, Tare da Kira ga Gwamnati kan Kula da Masu larurar Zabiya

Daga Safiya Usman

Kungiyar Albinism Association of Nigeria (AAN) ta shirya wani taron wuni daya a jihar Kano domin duba matsalolin da masu fama da cutar Zabiya ke fuskanta, tare da bukatar a hada su cikin tsare-tsaren yau da kullum na gwamnati.

Mataimakiyar shugabar kungiyar, Hajiya Mariya Isiyaka, ta bayyana cewa taron ya biyo bayan wani taron fadakarwa da s**a halarta a kasar Jamus, wanda ya mayar da hankali kan inganta fannin lafiyar masu albinism, iliminsu, da kuma samun kulawa ta musamman daga gwamnati da al’umma. Ta jaddada cewa wannan rukunin na fuskantar tsangwama a cikin al'umma, lamarin da ya kara dagula musu rayuwa.

A jawabin da ya gabatar a wajen taron, Kwamishinan yada labarai na jihar Kano, Hon. Ibrahim A. Waiya, ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar na daukar duk wani mataki da ya dace domin tallafa wa masu bukata ta musamman, ciki har da masu fama da albinism. Ya bayyana cewa suna da mahimmanci a cikin al’umma duba da gudunmawar da suke bayarwa a fannoni daban-daban. Kwamishinan ya kara da cewa, nan bada jimawa ba, gwamnati za ta kaddamar da hukumar da za ta kula da bukatun masu fama da albinism da sauran masu bukata ta musamman, kamar yadda doka ta tanada.

Wakiliyarmu Safiya Muhammad Usman, wadda ta halarci taron, ta ruwaito cewa shugaban kungiyar AAN na kasa, Dr. Bisi Bamishe, ya bayyana cewa taron ya mayar da hankali kan hanyoyin da za a bi domin kawar da wariya da nuna bambanci ga masu albinism, musamman a Kano da Najeriya baki daya.

Kungiyar Society Forum ta Kai Ziyarar Taya Murna ga Daraktar Masu Bukata ta Musamman, Dr. Binta BalaDaga Safiya Muhammad...
13/05/2025

Kungiyar Society Forum ta Kai Ziyarar Taya Murna ga Daraktar Masu Bukata ta Musamman, Dr. Binta Bala

Daga Safiya Muhammad Usman

Kungiyar Society Forum ta kai ziyarar taya murna ga Daraktar Ma’aikatar Mata, Kanana Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Dr. Binta Bala, biyo bayan nadin da aka yi mata a matsayinta na jagorar bangaren masu bukata ta musamman.

Shugaban kungiyar, Yarima Ibrahima, ya bayyana cewa ziyarar na da nufin mika gaisuwar taya murna da kuma gabatar da kudirin kungiyar wajen tallafa wa masu bukata ta musamman ta fannoni da dama, musamman ilimi, lafiya da koyar da sana’o’in hannu domin su samu damar dogaro da kansu.

Yarima ya ce, “Mun kawo wannan ziyara ne saboda Dr. Binta tana daya daga cikin masu bukata ta musamman, kuma muna jinjinawa Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, wanda ya ga dacewar nada ta a wannan mukami domin kare muradun masu bukata ta musamman.”

A nata bangaren, Dr. Binta Bala ta nuna farin ciki bisa wannan ziyara da kungiyar ta kawo. Ta bayyana cewa za ta yi duk mai yiwuwa wajen ganin rayuwar masu bukata ta musamman ta inganta. Ta kara da cewa daga cikin manyan kudirorinta na farko har da samar da kayan karatu ga masu nakasar gani da kuma ba su tallafin sana’o’in dogaro da kai.

Haka zalika, shugabar kungiyar Kilishi Development Foundation, Zubaida Rabiu, ta ce suna aiki tukuru wajen zagaye kananan hukumomi da sassan birnin Kano domin tantance bukatun masu bukata ta musamman da kuma tallafa musu. Ta ce sun zo ne don hada kai da gwamnati da sauran kungiyoyi domin ceto rayuwar wannan rukuni na al’umma.

Ziyarar ta nuna jajircewar kungiyoyin daidaiku wajen hada kai da gwamnati domin samar da mafita ga masu bukata ta musamman a Jihar Kano.

Kungiyoyi Masu Zaman Kansu da Gwamnatin Kano sun hada kai don yaki da zaizayar Ƙasa A wani taron tattaunawa da aka gudan...
07/05/2025

Kungiyoyi Masu Zaman Kansu da Gwamnatin Kano sun hada kai don yaki da zaizayar Ƙasa

A wani taron tattaunawa da aka gudanar a ofishin Gidauniyar Dr Aminu Magashi Garba (AMG), an bayyana bukatar karfafa hadin gwiwa tsakanin kungiyoyi masu zaman kansu da gwamnatin jihar Kano domin magance matsalar zaizayar kasa da kuma inganta tsaftar muhalli a fadin jihar.

Da yake jawabi a wajen taron, Dr Aminu Magashi Garba ya jaddada muhimmancin ganin gwamnati ta duba kungiyoyi masu zaman kansu a matsayin abokan hulda wajen tsara da kuma aiwatar da shirye-shiryen cigaban lafiya da muhallin al'umma.

Ya ce "Wajibi ne gwamnati ta ba kungiyoyi masu zaman kansu damarmaki na tattaunawa da hadin kai, domin hakan na da muhimmanci wajen kyautata lafiyar jama'a da samun dorewar ci gaba a Kano."

A nasa bangaren, Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi na jihar Kano, Dahiru Muhammad Hashim, ya yaba da kokarin da Gidauniyar Dr Aminu Magashi Garba ke yi. Ya bayyana cewa gwamnatin Kano ta shirya kaddamar da shirin dashen bishiyoyi har guda miliyan biyar a fadin jihar, domin samar da ingantaccen yanayi da kariya ga muhallin jihar.
"Wannan shiri na dashen bishiyoyi zai taimaka wajen rage zaizayar kasa, inganta tsaftar iska da kuma kawo sauyi mai kyau ga muhallinmu," in ji kwamishinan.

Wakiliyarmu, ta rawaito cewa kwamishinan ya bukaci kungiyoyi masu zaman kansu da daukacin al’ummar Kano da su fito su bayar da gudunmawa a wannan gagarumin shiri, domin tabbatar da cewa jihar ta samu sabuwar rayuwa ta fuskar muhalli da tsabtace iska.

Taron ya kasance wata hanya ta kara fahimtar juna tsakanin gwamnati da kungiyoyi masu zaman kansu wajen aiki tare don amfanin al'umma da ci gaban jihar.

Address

Nasarawa GRA
Kano
23471

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Prime Time News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Prime Time News Hausa:

Share