Prime Time News Hausa

Prime Time News Hausa Hausa reliable online Newspapers

Gidauniyar Dr. Magashi Garba da Ma’aikatar Jinkai Sun Gudanar da Taron Kwana Daya Akan Samar da Asusun Agajin Gaggawa a ...
25/08/2025

Gidauniyar Dr. Magashi Garba da Ma’aikatar Jinkai Sun Gudanar da Taron Kwana Daya Akan Samar da Asusun Agajin Gaggawa a Kano

Gidauniyar AMG karkashin jagorancin Dr. Aminu Magashi Garba tare da haɗin gwiwar Ma’aikatan Jinkai na Jihar Kano sun gudanar da taron kwana ɗaya da ya mayar da hankali kan yadda za a samar da Asusun Agajin Gaggawa domin inganta bangaren lafiya da ilimi a jihar.

A jawabin sa, shugaban gidauniyar AMG, Dr. Aminu Magashi Garba, ya bayyana cewa an shirya taron ne domin tattauna matsalolin da al’umma ke fuskanta a fannoni daban-daban. Ya ce lafiya da ilimi su ne ginshiƙan ci gaban kowace al’umma, saboda haka akwai buƙatar gwamnati ta dauki ƙarin matakai na musamman domin samar da asusun da zai tallafa wa lafiyar al’ummar Kano baki ɗaya.

A nasa jawabin, shugaban Ma’aikatan Jinkai na Kano, Hon. Adamu Aliyu Kibiya, ya jaddada bukatar haɗin kai tsakanin gwamnati, kungiyoyi masu zaman kansu da sauran masu ruwa da tsaki wajen ciyar da jihar gaba. Ya ce idan aka samar da wannan asusu, zai taka muhimmiyar rawa wajen rage radadi da matsalolin da al’ummar Kano ke fuskanta, musamman a lokacin bala’o’i da rashin lafiya.

Wakiliyar Prime Time News Hausa ta rawaito cewa mahalarta taron sun bukaci gwamnatin tarayya da ta jiha da kuma ‘yan kasuwa su haɗa hannu wajen kafa Asusun Agajin Gaggawa domin kare rayukan jama’a a lokutan hadari da kuma inganta walwalar al’umma.

Kwamishinan Yada Labarai ya Jaddada Bukatar Gogewa da Kwarewa a Aikin JaridaDaga Safiya Usman Aikin jarida na bukatar go...
14/08/2025

Kwamishinan Yada Labarai ya Jaddada Bukatar Gogewa da Kwarewa a Aikin Jarida

Daga Safiya Usman

Aikin jarida na bukatar gogewa da kwarewa a aikace domin yada labarai masu inganci, a cewar Kwamishinan Yada Labarai da Ayyukan Cikin Gida na Jihar Kano, Comrade Abdullahi Ibrahim Waiya.

Waiya ya bayyana haka ne a yayin wani taro da Kungiyar ‘Yan Jarida ta Kasa (NUJ) reshen Kano ta shirya tare da hadin gwiwar ma’aikatarsa, wanda aka gudanar a Kano, bisa sahalewar Gwamnan Jihar, Injiniya Abba Kabir Yusuf.

Ya ce taron ya mayar da hankali ne kan tattauna hanyoyin bunkasa aikin jarida a jihar, tare da kara baiwa ‘yan jarida masu tasowa horo da shawarwari domin inganta basirarsu a fagen aikin jarida.

“Gwamnatin Jihar Kano ta shirya tsaf domin cigaba da baiwa ‘yan jarida masu tasowa horo, ganin ido da kuma samar da damar kwarewa a aikin jarida,” inji Waiya.

A nasa jawabin, Shugaban NUJ na kasa, Comrade Alhassan Yahaya, ya nuna farin cikinsa kan wannan taro da ya gudana a Kano, inda ya ce yana da nufin inganta albashin ‘yan jarida da ci gaba da bai musu horo domin inganta aikin jarida.

Ya kuma yi kira ga mambobin NUJ a Kano da su ziyarci asibitoci domin yin inshora don kare lafiyarsu da ta iyalansu.

A nasa bangaren, daya daga cikin gogaggun ‘yan jarida a Kano, Ahmad Aminu, ya ce taron ya kunshi tattaunawa kan hanyoyin da za su kawo ci gaba a aikin jarida tare da samar da tsare-tsaren horo ga ‘yan jarida.

Taron ya samu halartar manyan ‘yan jarida da tsofaffin kwamishinoni na Ma’aikatar Yada Labarai da Ayyukan Cikin Gida, ciki har da Baba Haliru Dantiye, Farfesa Umar Faruk Jibrin, da sauran mahalarta taron.

‎‎Yadda Sauyin Yanayi Ke Jefa Mata Masu Juna Biyu Cikin Hadari"‎‎‎Daga Safiya Usman ‎‎A wani bincike na musamman da aka ...
29/07/2025


‎Yadda Sauyin Yanayi Ke Jefa Mata Masu Juna Biyu Cikin Hadari"



Daga Safiya Usman


‎A wani bincike na musamman da aka gudanar, an gano cewa sauyin yanayi, musamman lokacin zafi, na haddasa matsaloli masu tarin yawa ga mata masu juna biyu, inda hakan ke jefa su cikin hadurran lafiya da ke bukatar kulawa ta musamman.

‎A cikin hirar da muka yi da Hajiya Fatima, wata gogaggiya a fannin kiwon lafiya da wayar da kai kan batutuwan sauyin yanayi, ta bayyana cewa mata da yawa ba su da isasshen ilimi dangane da yadda sauyin yanayi ke shafar lafiyar su, musamman lokacin da suke dauke da ciki.

‎ “Akwai lokacin da mace ke samun canje-canje na jiki saboda juna biyu. Sauyin yanayi, musamman zafi, na kara tsananta lamarin. Mafi yawan matan da ba su da ilimi kan hakan kan fada cikin mawuyacin hali,” in ji Hajiya Fatima.



‎Zafin Rana Da Hayakin Gawayi Na Kara Dagula Lamura

‎A cewar Hajiya Fatima, zafi mai tsanani na hana mata masu juna biyu sukuni, kuma hakan na iya janyo hauhawar jini, bugun zuciya da ma faduwar gwiwa. Ta kara da cewa amfani da gawayi wajen dafa abinci, duk da cewa yana saukaka kashe kudi, na iya jefa lafiyar mata cikin hadari.

‎ “Hayakin gawayi yana da illa ga huhu, musamman ga masu ciki. Sannan wahalar hurawa da saurin konewar sa na kara wahalar da mace mai juna biyu,” ta ce.



‎Ta yi kira ga mazaje da su dinga bai wa matansu kulawa ta musamman, ta hanyar tanadar musu da wuri mai iska, da amfani da hasken rana (solar) domin saukaka zafin daki da kare lafiyar uwargida da jinjirin da ke cikin ta.

‎Bitar Rayuwar Mata Masu Sana’ar Gurasa a Kwanar Dala

‎A wani bangare na wannan bincike, Hajiya Fatima ta kai ziyara unguwar Kwanar Dala a Kano, inda ta gana da wasu mata da ke gudanar da sana’ar gurasa. Ta yaba da kokarinsu na jurewa kalubalen sauyin yanayi da hayakin wuta da ke barazana ga lafiyarsu.

‎“Matan suna yin gurasa ba dare ba rana. Ko da ruwa ya sauka, su kan ci gaba da aiki. Wannan jajircewa ta burge ni matuka,” in ji ta.



‎Matan sun bayyana cewa suna fuskantar zafin wuta da hayaki, amma babu wata mafita ta zamani da za ta taimaka musu wajen gudanar da sana’ar cikin sauki da kariya ga lafiyarsu.

‎Shirin Muryarta Raya Muhalli Ya Taimaka

‎Hajiya Fatima ta bayyana irin rawar da shirin “Muryarta Raya Muhalli” ke takawa wajen wayar da kai kan illolin sauyin yanayi da hanyoyin da za a bi don kare kai. Ta ce ta koyi darussa masu yawa daga shirin, wanda hakan ne ya karfafa mata gwiwar ci gaba da ilimantar da mata a unguwanni daban-daban.

‎Kira Ga Gwamnati Da Kungiyoyi Masu Zaman Kansu

‎A karshe, Hajiya Fatima ta bukaci Gwamnatin Jihar Kano da kungiyoyin ci gaban al’umma da su rika kai dauki ga mata masu sana’ar gurasa da sauran al’umma da ke fama da matsin rayuwa sakamakon sauyin yanayi.

‎"Tallafa wa wadannan mata zai ba su damar amfani da hanyoyin zamani wajen sana’ar su, sannan hakan zai rage hadurran lafiyar da suke fuskanta,” ta jaddada.



Gidauniyar AMG Ta Kaddamar Da Shirin Tallafawa Marasa Lafiya a KanoDaga Safiya Usman Gidauniyar AMG ta bayyana cewa kula...
26/07/2025

Gidauniyar AMG Ta Kaddamar Da Shirin Tallafawa Marasa Lafiya a Kano

Daga Safiya Usman

Gidauniyar AMG ta bayyana cewa kula da lafiyar al’umma, musamman marasa ƙarfi da masu fama da cututtuka daban-daban, na daga cikin muhimman abubuwa da s**a kamata a mayar da hankali a kansu domin inganta rayuwar jama’a a fadin Jihar Kano.

Wannan bayani ya fito ne daga Shugaban Gidauniyar, Dr. Aminu Magashi Garba, yayin wata tattaunawa da aka gudanar a shelkwatar gidauniyar tare da haɗin gwiwar ma’aikatar lafiya da taimakekeniya ta jihar Kano.

A cewar Dr. Aminu Magashi, babban burin taron shi ne kara wayar da kai da kuma tallafa wa marasa ƙarfi ta hanyar yi musu rijista a asibitoci daban-daban, samar musu da magunguna kyauta da kuma kula da lafiyarsu ba tare da wata wahala ba.

"Za mu ware sama da naira miliyan biyu (₦2,000,000) a wannan shekarar domin ci gaba da wannan aikin alheri, musamman a kananan hukumomi daban-daban na jihar Kano," inji Dr. Aminu.

A nasa bangaren, wani daga cikin mahalarta taron, Malam Salisu Umar Durumin Iya, ya bayyana cewa lokaci ya yi da masu hannu da shuni za su fito su tallafa wa marayu da marasa ƙarfi domin samun lada da kuma taimakawa wajen rage radadin rayuwa da suke fuskanta.

Ya ce kwamitin da gidauniyar ta kafa zai gudanar da aikin zakulo mabukata cikin tsari domin yi musu rijista kyauta a asibitoci.

A ƙarshe, Alhaji Sha’ibu Ahmed Indabawa, ɗaya daga cikin mahalarta taron, ya yaba da ƙoƙarin Gidauniyar AMG wajen tallafa wa mabukata. Ya kuma yi kira ga sauran masu hali da su shiga cikin irin wannan aiki domin taimakawa rage mace-mace da barace-barace da ke yawaita a fadin jihar Kano.

Taron ya ƙare da ƙudurin ci gaba da irin wannan aikin alheri don tabbatar da ingantacciyar rayuwa ga kowa da kowa.

Address

Nasarawa GRA
Kano
23471

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Prime Time News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Prime Time News Hausa:

Share