Prime Time News Hausa

Prime Time News Hausa Hausa reliable online Newspapers

Al’ummar Sheka Sun kuduri aniyar  Kawar Da Fadan Daba Da Shaye-shaye Tsakanin MatasaDaga Aisha Abubakar Mai AgogoA wani ...
01/06/2025

Al’ummar Sheka Sun kuduri aniyar Kawar Da Fadan Daba Da Shaye-shaye Tsakanin Matasa

Daga Aisha Abubakar Mai Agogo

A wani yunƙuri na tabbatar da zaman lafiya da daidaita rayuwar matasa a yankin, al’ummar Sheka da ke cikin karamar hukumar Kumbotso a Jihar Kano, sun gudanar da taro na musamman a safiyar yau domin tattauna hanyoyin da za su magance matsalolin fadan daba da shaye-shaye da ke addabar matasa.

Taron, wanda aka gudanar a filin makarantar firamare ta Sheka, ya samu halartar manyan baki daga sassa daban-daban ciki har da masu rike da sarautar gargajiya, malamai na addini da na boko, da kuma wakilan kungiyoyi masu zaman kansu.

A jawabin sa, Dagacin Sheka, Alhaji Abubakar Musa Zakari Sheka, ya bayyana cewa kafa kungiyar da aka yi na da nufin samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin al’ummar. Ya ce, "Wannan kungiya za ta zama wata kafa ta kawo sauyi mai kyau a tsakanin matasa, ta hanyar ba su shawarwari da tallafi domin su canza rayuwarsu."

Shi ma da yake bayani, Shugaban Karamar Hukumar Kumbotso, Hon. Abdullahi Ghali BASAF, ya jaddada cewa matasa za su gyaru ne idan aka rungume su da kulawa da fahimta. “Idan har za a rinka jin matsalolin matasa, ana ba su tallafi ta hanyoyi daban-daban, babu shakka za a samu nagartattun matasa a gaba,” in ji shi.

Kungiyar Muryar Mutanen Sheka, wacce ta shirya taron, ta bayyana kudirinta na samar da ayyukan yi ga matasa, da kuma ba wasu jari domin su fara sana’o’i, yayin da wasu za a mayar da su makaranta don samun ilimi da tarbiyya.

Al’ummar Sheka sun bayyana wannan taro a matsayin sabon babi na fatan dorewar zaman lafiya da ci gaban yankin, tare da bukatar hadin kan kowa da kowa domin cimma nasara.

Mutumin da ya ƙirƙiro maganin zubar da ciki ya mutuDaga Aisha Abubakar Mai Agogo Ƙwararren mai binciken kimiyya wanda ya...
31/05/2025

Mutumin da ya ƙirƙiro maganin zubar da ciki ya mutu

Daga Aisha Abubakar Mai Agogo

Ƙwararren mai binciken kimiyya wanda ya ƙirƙiri maganin zubar da ciki, Étienne-Émile Baulieu ya mutu yana da shekara 98 a duniya.

Dr Baulieu ya ƙirƙiro maganin zubar da cikin ne a shekarar 1984.

Bayan ƙirƙiro shi, maganin mifepristone ya kawo sauyi a tsarin haihuwa a duniya kamar yadda kafar yada labarai da BBC ta ruwaito.

TINUBU SHEKARU BIYU A MULKI: Gwamnati na Fama da Kalubale Duk da Yunkurin SauyiDaga Aisha Abubakar Mai AgogoYau Alhamis,...
29/05/2025

TINUBU SHEKARU BIYU A MULKI: Gwamnati na Fama da Kalubale Duk da Yunkurin Sauyi

Daga Aisha Abubakar Mai Agogo

Yau Alhamis, 29 ga watan Mayu, 2025, Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya cika shekaru biyu da zama a kujerar shugabancin ƙasar. Wannan lokaci mai ɗan gajeren zango ya kasance cike da muhimman sauye-sauye da s**a shafi fannonin rayuwa na yau da kullum – daga batun man fetur, tattalin arziki, walwalar jama’a, zuwa batun tsaro.

Tun daga ranar farko da ya hau mulki, shugaban ya ɗauki mataki na cire tallafin man fetur – wata doka da ta janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a da masana. Gwamnati ta bayyana wannan mataki a matsayin hanya ta dakile asarar kuɗi da magance zambar da ta dabaibaye tsarin tallafin. Sai dai sakamakon hakan ya jefa talakawa cikin mawuyacin hali, inda hauhawar farashin kaya da faduwar darajar Naira s**a tsananta.

A cikin wadannan shekaru biyu, matsin rayuwa ya ƙaru – daga tsadar kayayyaki, karancin albashi, zuwa ƙarancin aikin yi. Jama’a a kasuwanni da gidajen mai na ci gaba da fuskantar kalubale, yayin da gwamnati ke jaddada cewa tana kan tafarkin gyara, duk da cewa hakan na zuwa a hankali.

A bangaren tsaro kuwa, gwamnatin Tinubu na fuskantar manyan ƙalubale, musamman a arewacin ƙasar, inda hare-haren 'yan bindiga, satar mutane, da rikice-rikicen ƙabilanci da addini ke ci gaba da addabar al'umma. Duk da ɗaukar sabbin dabaru da ƙaddamar da ayyuka na yaki da ta'addanci, tsoro da rashin kwanciyar hankali har yanzu na addabar jama’a.

Duk da cewa an samu cigaba a wasu fannonin, da dama daga cikin 'yan ƙasa na ganin cewa tsadar rayuwa da matsalolin tsaro har yanzu na barazana ga jin daɗin rayuwa da kwanciyar hankali. Yayin da Tinubu ke shirin shiga shekara ta uku a ofis, idanu na ƙasar na karkata wajen ganin ko mulkinsa zai iya cika alkawurran da ya ɗauka.

Jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Kabo : Manuniya Kan Kyawun Alaka Tsakanin Shugaba Tinubu da Sanata BarauDaga Abba Anwar Da ...
28/05/2025

Jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Kabo : Manuniya Kan Kyawun Alaka Tsakanin Shugaba Tinubu da Sanata Barau

Daga Abba Anwar

Da farko ya zama dole a yabawa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu saboda mayar da Babbar Makarantar Kimiyya da Fasaha ta Gwamnatin Tarayya ta Kabo zuwa ga Jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Kabo. Abinda kamar yadda a ka ce, ba a taba samun wani shugaba ya yi haka cikin kankanin lokaci ba.

Bayan hobbasa da kokarin gaske da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa ta Kasa, Sanata Barau Jibrin CON, ya yi wajen samar da wannan Babbar Makarantar, a shiyyar Kano ta Arewa, canza sunan Babbar makarantar da ba ta matsayin Jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Gwamnatin Tarayya, wata manuniya ce ta kyakkyawar alakar da ke tsakanin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da kuma Sanata Barau.

Tun yanzu tun ba a je ko ina ba, shugaban kasa Tinubu ya na nuni da cewar alakarsa da Sanata Barau mai kyau ce kuma zartacciya. Wacce yanayi ya nuna za su iya aiki tare dan ci gaban kasar nan. A dukkan matsayin da mai karatu zai iya tunani.

Kamar dai yadda Sanatan da kansa ya nuna, a cikin shekaru biyu kacal Shugaba Tinubu ya samar da manyan makarantu guda biyu ga jihar Kano. Bayan daga likkafar babbar Kwalejin Ilimi ta Gwamnatin Tarayya ta Kano, zuwa ga matsayin Jami'a. Wacce a da an taba mayar da ita Jami'a amma wasu dalilai na siyasa su ka sa a ka soke hakan. Amman Tinubu ya dawo da waccan daga martabar da a ka soke. Duk bisa kokarin Sanata Barau da abokan aikin sa 'yan majalisa.

Tare da kuma canza mata suna zuwa ga Jami'ar Ilimi ta Yusuf Maitama Sule. Dan tunawa da mazan jiya tare da rike sunan sa a cikin al'umma saboda irin gudummawar da ya bayar wajen ci gaban Arewa da kuma kasa gaba daya.

Sai kuma ita Jami'ar Fasaha da Kimiyya ta Kabo ga kuma Kwalejin Tarayya ta Kimiyya da Fasaha ta Rano. "Wannan ba karamin kyakkyawan baya shugaban kasa ya kafa ba a wannan jihar ta mu ta Kano, " in ji Sanata Barau.

Kalli dai irin babban kokarin da Sanata Barau ya yi fa tun daga matakin Majalisa zuwa ga sahalewar da shugaban kasa ya bayar na mayar da Babbar Makarantar Fasaha da Kimiyya ta Kabo zuwa Jami'ar Fasaha da Kimiyya.

Shi da kan sa Sanatan ya ce "A cikin wata biyu da su ka wuce na gabatar da kudurin neman a mayar da Babbar Makarantar Tarayya ta Fasaha da Kimiyya ta Kabo zuwa Jami'ar Tarayya ta Fasaha da Kimiyya ta Kabo. Wanda ina godewa majalisun mu na Dattawa da na Wakilai. Wanda a cikin wata biyu kacal su ka yarda da wannan kundin kudurin.

Abinda ya rage mana shine samun sahalewar shugaban kasa kan ya sa hannu a mayar da abin ya zama doka. Kafin ma majalisa ta kai masa wannan kudurin na samu shugaban kasa na yi masa bayanin muhimmancin mayar da makarantar ta zama Jami'a.

Bayan ya yi alkawarin zai sa hannu bisa hakan. Da kai masa kuduri ba tare da bata wani lokaci ba, ya rattaba hannu a kai. Kamar yadda ya yi alkawari."

Sanatan ya ci gaba da cewa," Na nunawa shugaban kasa muhimmancin samar da ilimin kimiyya da fasaha ga matasan mu. Wanda Kano ce ta fi kowace jiha yawan matasa a kasar nan. Saboda haka ya zama wajibi da kodayaushe a tallafawa neman ilimin su.

Ba fa wannan ne kawai abubuwan dubawa ba a wannan babban kokari da Sanata Barau ya yi na mayar da wannan makaranta zuwa Jami'ar Kimiyya da Fasaha ba, akwai maganar an samar da wani yalwataccen bigire na samarwa da jama'a aikin yi. A halin da a ke ciki na rashin ayyukan yi ga matasa.

Sannan kuma irin kwasa-kwasan da za a karanta a wannan makaranta na bagarorin kimiyya da fasaha, wanda abinda zamani ke nema kenan ruwa a jallo, su ma su na nuni ga yadda al'umma za su amfana matuka da gaske.

Hatta kayan aiki da samar da yanayi mai kyau ga wannan jami'a dan cimma babban burin kafa ta, Sanatan ya yi alkawarin ci gaba da jajircewa wajen ganin ta mike sosai ta amsa sunan ta na jami'a.

Ya ce zai ci gaba da bibiyar ganin an samar da malamai da kuma yanayi mai kyau na koyo da koyarwa. Hatta ci gaba da gine-gine dan samun gamsassun wurare da kuma bangarori na yin karatu cikin kwanciyar hankali da nutsuwa a cikin zuciyar malamai da dalibai da kuma ma'aikatan wannan jami'a.

Irin hangen nesan da Sanata Barau ke nunawa wajen tafiyar da wannan ofis na sa na dan majalisar dattawa mai wakiltar Kano ta Arewa, da kuma babban mukamin da yake rike da shi na Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, kullum ya na kara haska mana waye Sanatan. Wakili na gari, wanda yake amfani da ilimi wajen tafiyar da harkokin sa na wakilci. Ga kuma dattako da sanin ya kamata.

Bayan yabawa da Sanatan ya yi ga shugaban kasa wajen wannan abin alheri na mayar da makarantar zuwa jami'a, ya ci gaba da cewa, "Kamar yadda kowa ya sani ne cewar su fa matasa sune kashin bayan ci gaban kowace irin al'umma.

Saboda haka kokarin da mu ka yi na mayar da wannan makaranta zuwa jami'a abu ne da ya dace da bukatun zamani na harkokin ci gaban al'umma. Ya zama dole mu yi duk mai yiwuwa wajen ganin mun ba matasan mu goyon baya da dukkan tallafin da ya kamata na su bayar da ta su gudummawar na ci gaban kasa. Dan mu gudu tare mu tsira tare."

Ga dukkan mai lura da al'amuran yau da kullum zai fahimci cewar Sanata Barau ya na da tsahon da zai iya yi wa jama'arsa aiki a ko ina ne cikin fadin kasar nan.

Idan ka kalli abubuwan kawo ci gaba da yake ta kwararowa al'ummar sa ba kakkautawa ka san lallai wannan shugaba ne mai sanin ya kamata. Kuma Jagora ne mai iya fahimtar bukatun al'ummar da su ka tura shi wakilci a Abuja. Ba wai ba inke!

Anwar tsohon Babban Sakataren Yada Labarai ne na tsohon Gwamnan Jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje CON, za kuma a iya samun sa a [email protected]
28 ga Watan Mayu, 2025

Kungiyar Albinism Association of Nigeria (AAN) Ta Gudanar da Taron Wuni Daya a Kano, Tare da Kira ga Gwamnati kan Kula d...
15/05/2025

Kungiyar Albinism Association of Nigeria (AAN) Ta Gudanar da Taron Wuni Daya a Kano, Tare da Kira ga Gwamnati kan Kula da Masu larurar Zabiya

Daga Safiya Usman

Kungiyar Albinism Association of Nigeria (AAN) ta shirya wani taron wuni daya a jihar Kano domin duba matsalolin da masu fama da cutar Zabiya ke fuskanta, tare da bukatar a hada su cikin tsare-tsaren yau da kullum na gwamnati.

Mataimakiyar shugabar kungiyar, Hajiya Mariya Isiyaka, ta bayyana cewa taron ya biyo bayan wani taron fadakarwa da s**a halarta a kasar Jamus, wanda ya mayar da hankali kan inganta fannin lafiyar masu albinism, iliminsu, da kuma samun kulawa ta musamman daga gwamnati da al’umma. Ta jaddada cewa wannan rukunin na fuskantar tsangwama a cikin al'umma, lamarin da ya kara dagula musu rayuwa.

A jawabin da ya gabatar a wajen taron, Kwamishinan yada labarai na jihar Kano, Hon. Ibrahim A. Waiya, ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar na daukar duk wani mataki da ya dace domin tallafa wa masu bukata ta musamman, ciki har da masu fama da albinism. Ya bayyana cewa suna da mahimmanci a cikin al’umma duba da gudunmawar da suke bayarwa a fannoni daban-daban. Kwamishinan ya kara da cewa, nan bada jimawa ba, gwamnati za ta kaddamar da hukumar da za ta kula da bukatun masu fama da albinism da sauran masu bukata ta musamman, kamar yadda doka ta tanada.

Wakiliyarmu Safiya Muhammad Usman, wadda ta halarci taron, ta ruwaito cewa shugaban kungiyar AAN na kasa, Dr. Bisi Bamishe, ya bayyana cewa taron ya mayar da hankali kan hanyoyin da za a bi domin kawar da wariya da nuna bambanci ga masu albinism, musamman a Kano da Najeriya baki daya.

Kungiyar Society Forum ta Kai Ziyarar Taya Murna ga Daraktar Masu Bukata ta Musamman, Dr. Binta BalaDaga Safiya Muhammad...
13/05/2025

Kungiyar Society Forum ta Kai Ziyarar Taya Murna ga Daraktar Masu Bukata ta Musamman, Dr. Binta Bala

Daga Safiya Muhammad Usman

Kungiyar Society Forum ta kai ziyarar taya murna ga Daraktar Ma’aikatar Mata, Kanana Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Dr. Binta Bala, biyo bayan nadin da aka yi mata a matsayinta na jagorar bangaren masu bukata ta musamman.

Shugaban kungiyar, Yarima Ibrahima, ya bayyana cewa ziyarar na da nufin mika gaisuwar taya murna da kuma gabatar da kudirin kungiyar wajen tallafa wa masu bukata ta musamman ta fannoni da dama, musamman ilimi, lafiya da koyar da sana’o’in hannu domin su samu damar dogaro da kansu.

Yarima ya ce, “Mun kawo wannan ziyara ne saboda Dr. Binta tana daya daga cikin masu bukata ta musamman, kuma muna jinjinawa Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, wanda ya ga dacewar nada ta a wannan mukami domin kare muradun masu bukata ta musamman.”

A nata bangaren, Dr. Binta Bala ta nuna farin ciki bisa wannan ziyara da kungiyar ta kawo. Ta bayyana cewa za ta yi duk mai yiwuwa wajen ganin rayuwar masu bukata ta musamman ta inganta. Ta kara da cewa daga cikin manyan kudirorinta na farko har da samar da kayan karatu ga masu nakasar gani da kuma ba su tallafin sana’o’in dogaro da kai.

Haka zalika, shugabar kungiyar Kilishi Development Foundation, Zubaida Rabiu, ta ce suna aiki tukuru wajen zagaye kananan hukumomi da sassan birnin Kano domin tantance bukatun masu bukata ta musamman da kuma tallafa musu. Ta ce sun zo ne don hada kai da gwamnati da sauran kungiyoyi domin ceto rayuwar wannan rukuni na al’umma.

Ziyarar ta nuna jajircewar kungiyoyin daidaiku wajen hada kai da gwamnati domin samar da mafita ga masu bukata ta musamman a Jihar Kano.

Kungiyoyi Masu Zaman Kansu da Gwamnatin Kano sun hada kai don yaki da zaizayar Ƙasa A wani taron tattaunawa da aka gudan...
07/05/2025

Kungiyoyi Masu Zaman Kansu da Gwamnatin Kano sun hada kai don yaki da zaizayar Ƙasa

A wani taron tattaunawa da aka gudanar a ofishin Gidauniyar Dr Aminu Magashi Garba (AMG), an bayyana bukatar karfafa hadin gwiwa tsakanin kungiyoyi masu zaman kansu da gwamnatin jihar Kano domin magance matsalar zaizayar kasa da kuma inganta tsaftar muhalli a fadin jihar.

Da yake jawabi a wajen taron, Dr Aminu Magashi Garba ya jaddada muhimmancin ganin gwamnati ta duba kungiyoyi masu zaman kansu a matsayin abokan hulda wajen tsara da kuma aiwatar da shirye-shiryen cigaban lafiya da muhallin al'umma.

Ya ce "Wajibi ne gwamnati ta ba kungiyoyi masu zaman kansu damarmaki na tattaunawa da hadin kai, domin hakan na da muhimmanci wajen kyautata lafiyar jama'a da samun dorewar ci gaba a Kano."

A nasa bangaren, Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi na jihar Kano, Dahiru Muhammad Hashim, ya yaba da kokarin da Gidauniyar Dr Aminu Magashi Garba ke yi. Ya bayyana cewa gwamnatin Kano ta shirya kaddamar da shirin dashen bishiyoyi har guda miliyan biyar a fadin jihar, domin samar da ingantaccen yanayi da kariya ga muhallin jihar.
"Wannan shiri na dashen bishiyoyi zai taimaka wajen rage zaizayar kasa, inganta tsaftar iska da kuma kawo sauyi mai kyau ga muhallinmu," in ji kwamishinan.

Wakiliyarmu, ta rawaito cewa kwamishinan ya bukaci kungiyoyi masu zaman kansu da daukacin al’ummar Kano da su fito su bayar da gudunmawa a wannan gagarumin shiri, domin tabbatar da cewa jihar ta samu sabuwar rayuwa ta fuskar muhalli da tsabtace iska.

Taron ya kasance wata hanya ta kara fahimtar juna tsakanin gwamnati da kungiyoyi masu zaman kansu wajen aiki tare don amfanin al'umma da ci gaban jihar.

Kungiyar The Scoop Storytelling Initiative Ta Shirya Bita Ga 'Yan Jarida a KanoKungiyar The Scoop Storytelling Initiativ...
02/05/2025

Kungiyar The Scoop Storytelling Initiative Ta Shirya Bita Ga 'Yan Jarida a Kano

Kungiyar The Scoop Storytelling Initiative ta shirya bita na kwana biyu ga matasa 'yan jarida a jihar Kano, domin bunkasa kwarewarsu a aikin jarida tare da amfani da ilimi wajen isar da sahihan rahotanni.

Wannan shiri na daya daga cikin kokarin kungiyar na tallafa wa matasa su zama masu tasiri a harkar yada labarai a Najeriya da ma duniya baki daya.

A yayin bude taron, Daraktar kungiyar, Hajiya Zainab Bala, ta bayyana cewa akwai dimbin rahotanni a Najeriya da ke bukatar ingantaccen tsari da ilimi wajen isar da su. Ta ce yaduwar kafafen sadarwa ya haifar da karuwar labaran karya da ba su da tushe, musamman daga wasu matasa mata da ke yada su ba tare da kulawa da ka'idojin aikin jarida ba.

Ta kara da cewa wannan bita na Kano na daga cikin jerin shirye-shiryen da s**a faro a jihohi domin horar da matasa 'yan jarida su rika yin aiki da gaskiya, kwarewa, da kishin kasa.

Ana sa ran wannan bita zai taimaka wa matasa ‘yan jarida wajen fahimtar rawar da za su taka wajen yaki da labaran karya da bunkasa sahihan labarai da s**a danganci rayuwar al’umma.

Gwamnatin Kano Ta Bude Tenda Don Gudanar da Muhimman Ayyuka Guda UkuGwamnatin Jihar Kano ta bude tenda domin gudanar da ...
29/04/2025

Gwamnatin Kano Ta Bude Tenda Don Gudanar da Muhimman Ayyuka Guda Uku

Gwamnatin Jihar Kano ta bude tenda domin gudanar da manyan ayyuka guda uku da nufin inganta hanyoyin sufuri a fadin jihar. Ayyukan sun haɗa da fadada titin Katsina daga shataletalen Baban Gwari zuwa Mile Tara, da titin Dakata zuwa Yada Kunya har zuwa Bela a karamar hukumar Nasarawa, da kuma kammala aikin titin daga Jaba zuwa Gayawa a karamar hukumar Ungogo.

Da yake jawabi a wajen bude tender ɗin, kwamishinan ayyuka da gidaje na jihar Kano, Injiniya Marwan Ahmad, wanda Babban Darakta na Mulki da Kuɗi a ma'aikatar, Alhaji Tukur Abdullahi, ya wakilta, ya bukaci 'yan kwangila da za su samu aikin da su tabbatar sun yi aiki mai inganci domin jin daɗin al’ummar jihar.

A nata bangaren, Babbar Sakatariya a ma'aikatar ayyuka da gidaje, wacce Engr. Lawan Datti ya wakilta, ta bayyana cewa gwamnati ta tanadi isassun kuɗaɗe don gudanar da wadannan muhimman ayyuka. Ta ce matakin zai taimaka gaya wajen sauƙaƙa zirga-zirga a tsakanin al'ummar jihar.

Wakiliyar mu, Safiya Muhammad Usman, ta rawaito cewa taron ya samu halartar wakilai daga kamfanonin gina tituna da sauran daraktoci daga ma'aikatun gwamnati na jihar Kano.

Hukumomi Sun Bayyana Matakan Kula da Lafiyar Tsofofi a Jihar KanoDaga Safiya Usman A wani taron tattaunawa da ya gudana ...
24/04/2025

Hukumomi Sun Bayyana Matakan Kula da Lafiyar Tsofofi a Jihar Kano

Daga Safiya Usman

A wani taron tattaunawa da ya gudana a Kano, an bayyana sabbin hanyoyi da za a bi domin kula da lafiyar tsofofi da kuma koya musu sana’o’in hannu, domin inganta rayuwarsu da rage dogaro da wasu. Wannan bayani ya fito ne daga bakin Hajiya Rabi Yusuf Gezawa, MON, wacce ita ce mataimakiya a bangaren kula da lafiya da motsa jiki na tsofofi a kungiyar Stakeholders Consultative on Ageing.

A cewar Hajiya Rabi, tun a shekarar 2017 ne Hukumar kula da Dattijai ta gwamnatin tarayya ta kaddamar da wata doka da nufin kare tsofaffi daga cin zarafi da tauye musu hakki. Ta ce saboda haka ne s**a ga dacewar mika wannan doka ga gwamnatin jihar Kano domin kare tsofaffi daga cin zarafi da nuna musu bambanci. Ta kara da cewa, "Suma tsofaffi suna da hakki a gwamnati da kuma cikin al’umma baki daya."

Mallam Umar Abdula'aziz, mataimaki mai kula da harkokin hulda da cigaban tsofaffi, ya bayyana cewa a yayin taron, an hadu da likitoci domin duba lafiyar tsofaffi tare da koya musu hanyoyin motsa jiki domin kara lafiyar jikinsu da walwala. “Mun gudanar da wannan taro ne domin kara wayar da kai tare da ba su damammaki da s**a dace da su,” in ji shi.

Wasu daga cikin tsofaffin da s**a ci gajiyar shirin sun nuna matukar farin cikinsu, inda s**a gode wa hukumomin da s**a shirya wannan shiri da ya ba su damar yin gwaje-gwaje da samun magunguna kyauta.

A karshe, Hajiya Rabi ta yi kira ga duk masu ruwa da tsaki da su hada kai da kungiyarsu domin tabbatar da ingantacciyar kulawa ga tsofaffi a jihar Kano, tana mai cewa wannan aiki ba na gwamnati kadai ba ne, ya shafi kowa da kowa a cikin al’umma.

Matakin Gwamnatin Nijar Na Maye Gurbin Harshen Faransa Da Hausa: Mahimmanci Ga Ci Gaban Ƙasa Da Tasiri A Yammacin Afirka...
16/04/2025

Matakin Gwamnatin Nijar Na Maye Gurbin Harshen Faransa Da Hausa: Mahimmanci Ga Ci Gaban Ƙasa Da Tasiri A Yammacin Afirka

Daga: Adamu S Ladan

A ‘yan kwanakin nan, hukumomin kasar Nijar sun dauki mataki mai tarihi na dakatar da amfani da harshen Faransa a matsayin harshen gwamnati, tare da maye gurbinsa da harshen Hausa – daya daga cikin manyan harsunan ‘yan asalin kasar.

Wannan mataki ba kawai sauyi ne na harshen sadarwa ba, har ila yau wata alama ce ta fafutukar dawo da martabar al’ada, tarihi da yancin kai na al’umma.

Mahimmancin Wannan Mataki Ga Ci Gaban Nijar ba ya misaltuwa musamman wajen Karfafa Al’adu da Asalin Ƙasa. Harshen Hausa na da dogon tarihi da alaka da rayuwar yau da kullum ta Hausawan Nijar. Mayar da shi harshen gwamnati na nufin dawo da al’ummar ƙasar da asalin su, tare da tabbatar da cewa al’adun su da harshensu sun samu girmamawa a matakin kasa. Wannan zai kara jin dadin jama’a da sha’awar shiga harkokin mulki da ci gaba. Don an kauda wariya da amfani da bakon harshen turanci ya jefa da dama mutanen kasar da ba sa iya amfani da shi duk kuwa da dimbin basira da hikima da Allah Ya ba su.

Saboda haka, amfanin harshen gida watau, Hausa zai kara saukaka huldar gwamnati da jama'a.Yawancin ‘yan Nijar ba su da cikakkiyar fahimta ko iya magana da harshen Faransa, wanda ke zama cikas ga samun saukin fahimtar manufofin gwamnati. Aikin gwamnati da hulɗar jama’a da harshen da suke fahimta zai kara tasiri, yarda da kuma ingancin aiwatar da tsare-tsare.

Wannan mataki kuma ya kara jaddada gwagwarmayar Kawar da dabarar mulkin mallaka da 'yan mulaka'u ke amfani da ita wajen tabbatar da dakushe cigaban Afuruka. Amfani da harshen Faransa tsawon shekaru kamar yadda turancin Ingilishi ya ke a Najeriya ya kasance wani nau’i na ci gaba da tasirin mulkin mallaka. Wannan sauyi lalle wata hanya ce ta nuna cikakken ‘yancin kai da kokarin gina kasa bisa ginshikin ƙasaitar al’ummar ta.

Wannan mataki zai karfafa matsayin harshen Hausa ba kawai a Nijar ba, har da Najeriya, Ghana, da Kamaru, da Chadi da sauran kasashe da Hausawa ke rayuwa. Yana da yiyuwar hakan zai sa kasashen makwabta su fara duba yiwuwar amfani da harshen Hausa a wasu fannoni na gwamnati ko hulda da jama’a.

Haka ma matakin zai iya kawo hadin Gwiwa tsakanin Hausawan yanki Afuruka ta yamma. Yayin da harshen Hausa ke kara samun karbuwa a matakin gwamnati a Nijar, hakan zai karfafa zumunci, hulda da fahimtar juna tsakanin Hausawan kasashen da ke makwabta. Wannan na da tasiri sosai wajen inganta harkokin kasuwanci, ilimi, da hadin kan al’umma.

Wannan mataki wata dama ce ta bunkasa Ilimi da harshen. Harshen Hausa da ke da dimbin adabi, tarihi da hikima zai kara samun karbuwa a matsayin harshe na ilimi. Makarantu, kafafen yada labarai, da cibiyoyin kimiyya za su fara duba mahimmancin Hausa wajen yada ilimi da bayanai. Musamman a Arewacin Najeriya da rashin amfani da harshen gida a jawo koma baya gaya a harkar ilmi.

To, wane mataki ya kamata hausawan sauran kasashen afrika ta yamma za su dauka don cimma burin maida harshen Hausa a matsayin harshen hulda a gwamnatance musamman yankin arewacin Najeriya da Ghana da Kamaru da Chadi da ke amfani da harshen wajen huldodin yau da kulum?

Wannan tambaya na da matukar muhimmanci, domin tana tabo wata babbar dama da Hausawa da masu jin Hausa ke da ita wajen karfafa matsayin harshensu a matsayin harshe na hulda a matakin gwamnati a yankin Yammacin Afirka. Ga wasu matakai da za a iya dauka don cimma wannan buri, musamman a Arewacin Najeriya, da Ghana da Kamaru.

1. Inganta Hausa a Ilimi da Makarantu
• Rike wa da koyar da Hausa a makarantu, musamman tun daga matakin farko (primary) har zuwa gaba da sakandire. Idan yara sun tashi da Hausa a matsayin harshe na koyarwa, hakan zai sa su girma da jin dadin amfani da shi a rayuwar yau da kullum. Sabanin halin da ake ciki yanzu inda yaran su batan- baka-tantan ba su iya turancin ba sun kuma saki Hausa.
• Kafa cibiyoyin bincike da koyar da Hausa a jami’o’i na gida da kasashen waje domin zurfafa ilimi da adabin Hausa.
• A Najeriya, ana bukatar karfafa amfani da Hausa a fannin ilimi da kwasa-kwasai na musamman a jami'o'in Arewacin Najeriya.
2. Tallafa wa Kafafen Yada Labarai da Littattafan Hausa
• Gwamnatoci da kungiyoyi masu zaman kansu su rika daukar nauyin shirye-shiryen Hausa a kafafen yada labarai na kasa da kasa kamar NTA, Radio Nigeria, GTV (Ghana), CRTV (Kamaru) da sauransu.
• Wallafa littattafai da mujallu da jaridu a Hausa, wanda zai kara bunƙasa karatu da fahimtar harshen a cikin al’umma.
• A samar da manhajojin wayar salula da na kwamfuta da ke amfani da Hausa domin amfani a makarantu da ma’aikatun gwamnati.
3. Kafa Kungiyoyi da Harsashen Hausa A Matsayin Agenda
• Hausawa a kasashe daban-daban su kafa kungiyoyin kare da bunkasa Hausa, masu hada kai da gwamnati da jama'a, domin su rika matsa lamba da gabatar da bukatu ga gwamnati.
• Kungiyoyin irin su Hausa Language Promotion Council ko Hausa Cultural Renaissance Forum na iya zama cibiyoyi na hadin kai da tsara dabaru.
4. Shiga Siyasa da Tuntuba da Shugabanni
• Hausawa a bangarori daban-daban su rika tuntubar ‘yan siyasa da masu rike da madafun iko domin su fahimci bukatar amfani da Hausa a matsayin harshe na hulda a hukumomi, musamman a yankunan da Hausawa ke rinjaye.
• ‘Yan majalisa, ‘yan kwamitin ilimi da yada labarai a kasashe irin su Najeriya, da Ghana, da Kamaru za su iya bayar da gudunmawa wajen kawo sauyi a dokokin gwamnati.
5. Haɗin Gwiwar Yankin Yammacin Afirka
• A gina hadin gwiwa tsakanin kasashen da Hausa ke yawo kamar Najeriya, Nijar, Ghana, da Kamaru, da Chadi domin samar da tsarin hadaka kan harshen Hausa – kamar su shirya tarukan harshe, ilimi da al’adu.
• Wannan na iya taimaka wajen karɓar Hausa a matsayin harshe na yanki kamar yadda ECOWAS ke da yunkurin yare iri-iri.
Kammalawa:
Matakin da Nijar ta dauka wata kafa ce ta kirkire-kirkire da martaba al’umma. Yana wakiltar sabuwar hanya ta gina kasa bisa harshe, al’ada da tsari na cikin gida. Harshe yana da matukar muhimmanci wajen gina tunani, kawo hadin kai da tabbatar da yanci. Nijar ta bude sabuwar kofa ga sauran kasashen Afirka don tunani mai zurfi kan rawar da harsunan gida za su taka wajen ciyar da kasashen gaba. Wannan mataki na da karfi sosai wajen karfafa al’ummar Hausa da ba su wani sabon mataki na fahimta da girmamawa a matakin yanki da duniya baki daya.

Harshen Hausa na da dimbin tarihi, yawan masu amfani, da kuma ƙwarewa a bangaren sadarwa. Wannan shi ya sa kasashen da ke da'awar cigaba su rungumi harshen wajen amfani da shi a kafafen yada labarai don cimma burin su na siyasa da tattalin arziki. Abin da ya rage ma Hausawa shi ne tura karfi da haɗin kai daga gwamnati, jama’a, da masu ruwa da tsaki, domin karfafa matsayin Hausa ba kawai a huldar yau da kullum ba, har a doka da tsarin mulki. Tsarin mulki a Najeriya musamman ya bada dama da ayi amfani da harshen gida a majalisun tarayya, hadda ma koyar wa a matakin farko na makarantu.
Yanzu da Nijar ta fara jagoranci, lokaci ya yi da sauran kasashen da Hausawa ke da rinjaye su bi sahu, domin a gina yare a matsayin tushen ci gaban al’umma da yancin kai.

Adamu S Ladan.

Ramadan: Gwamnan Jihar Kano ya baiwa wasu kungiyoyin Yan jaridu tallafin  shinkafa buhu 450Gwamnan Jihar Kano ya baiwa w...
10/03/2025

Ramadan: Gwamnan Jihar Kano ya baiwa wasu kungiyoyin Yan jaridu tallafin shinkafa buhu 450

Gwamnan Jihar Kano ya baiwa wasu daga cikin kungiyoyin Yan jaridu tallafin shinkafa buhu 450

Alfijir labarai ta ruwaito wannan na ƙunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamna Abba Kabir Sanusi Bature D-Tofa ya Sanyawa hannu.

Bature yace kungiyoyin da s**a amfana sun hada da kugiyar ƴan jaridu ta ƙasa reshen jihar (NUJ) da kugiyar Jami'an hulɗa da jama'a ta ƙasa reshen jihar Kano (NIPR) da kugiyar mata ƴan jaridu (NAWOJ) da kugiyar maruba labarin wasanni reshen jihar Kano (SWAN) sauran sun haɗa da kugiyar ma.'akatan radio da talavijin da wasan kwaikwayo da kirkira (RATTAWU) da kugiyar shugabannin kafafen ƴaɗa labarai da kuma ASSOMEG kungiyar yan jaridu ta yanar gizo.

Raban ya gudana a cibiyar ƴan jaridu dake Farm Center dake jihar Kano ƙarƙashin jagorancin kwamishinan yaɗa labarai na jihar Kano Comr Ibrahim Abdullahi Waiya da mai magana da yawun Gwamnan Sanusi Bature D-Tofa da wakilan kafafen ƴaɗa labarai da Kuma kungiyoyin.

Address

Nasarawa GRA
Kano
23471

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Prime Time News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Prime Time News Hausa:

Share