
23/06/2025
A Kano, Matasa Sun Fara Jagorantar Yaki da Wariya ga Masu Bukata
Daga Safiya Usman
Kano, Najeriya – Bashir Ali Haruna, wani matashi da ke fama da larurar kafa ya bayyana yadda rashin tallafi daga gwamnati da tsangwama daga al’umma s**a shafi rayuwarsa. A cewarsa, lokacin da yake karatun diploma, ya sha fama da rashin sauki, amma hakan bai sa ya daina fatan alheri ba.
“Na kammala diploma, amma na dade ina neman aiki kafin na samu wajen wani gidan rediyo mai zaman kansa,” in ji Bashir. Duk da haka, ya sake komawa makaranta domin daukar darasi a matakin HND.
A yau, Bashir ya mayar da karatu tamkar mafita, yana kira ga gwamnati da kungiyoyi masu zaman kansu da su bude damammaki ga masu bukata ta musamman – musamman wajen koyar da sana’o’i da samar da ayyukan yi. “Karatu shine gatan mai bukata. Koda akwai kalubale, kada a karaya,” in ji shi.
A cikin wani yunkuri na fahimtar halin da masu bukata ta musamman ke ciki, rahotanni sun bayyana cewa dubban ‘yan Najeriya masu fama da larura na fuskantar kalubale daga gwamnati da al’umma, lamarin da ke hana su cika muradunsu na yau da kullum.
Wasu daga cikin wadannan kalubale sun hada da rashin samun ilimi mai inganci, kiwon lafiya, damar koyon sana’a da kuma shiga aikin gwamnati – abubuwan da s**a zama ‘yancin kowa a karkashin dokokin kasa da kasa. A mafi yawan lokuta, ana ware su ne ba tare da hakki ba, kuma ba tare da la’akari da irin gudunmuwar da za su iya bayarwa ba.
Yarima Sulaiman Ibrahim, Matashi ne kuma shugaban wata kungiyar farar hula da ke fafutukar kare hakkin masu bukata ta musamman ne aa kano. ya ce shi kansa ya rasa gani a wani lokaci na rayuwarsa, kuma tun daga wannan lokaci yana rayuwa da kalubale.
“Da zarar mutum ya kamu da wata larura, ana jefar da shi kamar babu darajarsa,” in ji shi.
A cewarsa, akwai bukatar gwamnati ta daina nuna halin ko in kula: “Ilimi, lafiya, sana’a – wadannan ba wai taimako ba ne, hakkinsu ne,” ya jaddada. Kungiyarsa na kokari wajen kwatar hakkin masu bukata daga jami’ai, jami’an tsaro da ma’aikatu, duk da cewa hakan na fuskantar turjiya.
Hakkin Masu Bukata ta Musamman da Abinda Doka Ta Tanada
A Najeriya, Dokar Kare Hakkin Masu Bukata ta Musamman ta 2018 (Discrimination Against Persons with Disabilities (Prohibition) Act, 2018) tana da cikakken tsari da manufar kare ‘yancin duk wani dan kasa da ke da larura ta musamman. Wannan doka an kirkiro ta ne domin tabbatar da cewa masu nakasa suna samun adalci da damar rayuwa kamar kowane dan kasa.
Daya daga cikin muhimman abubuwan da dokar ta tanada shi ne haramta nuna wariya ga duk wanda ke da nakasa ko wata larura ta jiki ko ta hankali. Wannan yana nufin cewa ba a yarda a hana mutum wani hakki ko damar rayuwa saboda larurar da yake da ita ba.
Haka kuma, dokar ta bayyana cewa masu nakasa suna da hakkin samun ilimi, lafiya, aikin yi, sufuri da shiga gine-ginen jama’a ba tare da wata tangarda ba. Wannan yana tabbatar da cewa za su iya rayuwa cikin kima da mutunci kamar kowa a cikin al’umma.
Dokar ta umarci gwamnatin tarayya, jihohi da kananan hukumomi da su samar da muhallin da ya dace da masu larura, wanda zai ba su damar shiga makarantu, asibitoci, kasuwanni da sauran wuraren aiki cikin sauki.
An bai wa gwamnati shekaru biyar (daga 2019 zuwa 2024) domin ganin cewa dukkan gine-gine da motocin sufuri da ake amfani da su a kasar nan sun dace da bukatun masu bukata ta musamman. Wannan tanadi yana da matukar muhimmanci wajen rage wariya da kara musu damar rayuwa mai inganci.
Matakin Kasa (Gwamnatin Tarayya)
A shekarar 2024, Gwamnatin Tarayya ta karawa Hukumar Kare Hakkin Masu Bukata ta Musamman (NCPWD) kudin kasafinta da kashi 500% fiye da shekarar 2023. Wannan karin ya nuna irin jajircewar da Shugaba Bola Tinubu ke nunawa wajen ganin an aiwatar da dokokin da s**a shafi samun damar shiga gine-gine da rayuwa cikin kima.
Domin shekarar 2025, an tsara cewa hukumar NCPWD za ta samu kusan naira biliyan 2.1, domin aiwatar da shirin karfafa tattalin arzikin masu bukata, da kuma shirye-shiryen da s**a shafi mata masu nakasa da ci gaban su.
Sai dai kungiyoyin farar hula kamar CISLAC na ci gaba da kira da a kara kasafin kudi a cikin kasafin kudin karin gaggawa na 2024, tare da tabbatar da cewa an biya bukatun masu nakasa a kowane mataki.
Matakin Jihar Kano
A cikin kasafin kudin 2023, Gwamnatin Kano ta ware naira miliyan 100 ga Asusun Tallafa wa Masu Larura (Disability Trust Fund) da kuma Hukumar Kula da Mutanen da ke da Bukata ta Musamman, karkashin Ma’aikatar Harkokin Musamman.
A shekarar 2024, an kara kasafin wannan asusu zuwa naira miliyan 197.3, domin ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen tallafi, musamman wajen samar da horo da ayyukan yi ga masu larura a jihar.
A wani rahoto, an bayyana cewa jihar Kano ta ware kusan naira miliyan 158 don shirye-shirye na tallafi da karfafa gwiwar masu bukata ta musamman, ciki har da ayyuka na musamman da horar da sana’o’i.
Baya ga hakan, gwamnatin jihar na shirin kafa Hukumar Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, domin kula da aiwatar da tsare-tsaren da s**a shafi walwalar masu nakasa.
Shawarwarin Masana
Dr. Nasir Yakubu Malami daga Jami’ar Bayero, Kano, ya ce lokaci yayi da gwamnati za ta tsara gine-ginen jama’a da su dace da masu larura.
“Asibitoci, makarantu, kasuwanni – ya kamata su kasance wurare masu saukin shiga da fita ga dukkan nau’in nakasa,” in ji shi.
Ya kuma jaddada cewa akwai bukatar tsare-tsare daban-daban na lafiya, ilimi da walwala da s**a dace da bangarorin larura – na gani, ji, motsi da sauransu.
Dr. Binta Bala, daraktar ayyukan jinkai a jihar Kano, ta ce babbar matsala ita ce rashin wakilcin masu bukata ta musamman a cikin manyan kujeru na gwamnati. “Ana basu mukamai na SA ko PA kawai, ba a basu dama su zamo cikin masu yanke shawara ba,” ta bayyana.
Ta kuma bukaci gwamnati da ta tabbatar da aiwatar da dokokin da aka tsara domin kare rayuwar masu bukata ta musamman da hukunta duk wanda ya ci zarafinsu.
A yayin da kalubale ke ci gaba da bayyana, matasa da kungiyoyin masu fafutuka suna nuna cewa lokaci ya yi — ba na tausayi ba, sai na adalci. Masu bukata ta musamman ba za su tsaya a gefe ba har abada.