Prime Time News Hausa

Prime Time News Hausa Hausa reliable online Newspapers based in Kano

Bayan gudanar da zaman tattaunawa tsakanin 'yan takarar gwamna biyu, Ibrahim Al'amin Little da Mallam Ibrahim Khalil, an...
09/06/2026

Bayan gudanar da zaman tattaunawa tsakanin 'yan takarar gwamna biyu, Ibrahim Al'amin Little da Mallam Ibrahim Khalil, an samu matsaya cewa duk hukuncin da uwar jam'iyyar ADC ta yanke a gobe Laraba 'yan takarar za su karɓa.

Rahotanni sun bayyana cewa a zaman da aka yi yau, kowa ya yarda da duk hukuncin da jamiyya za ta ɗauka kuma za ta sanar a gobe zai yi biyayya.

Hakan na ƙunshe a cikin wani sakon mai taimakawa Ibrahim Al'amin Little kan kafafen sada zumunta, Adnan Mukhtar Tudunwada ya fitar a shafinsa na Facebook.

Allah Ya yi wa fitaccen ɗan gwagwarmayar siyasa a Jihar Kano,kuma guda cikin masu magana akafafen yaɗa labarai Dattijo A...
09/06/2026

Allah Ya yi wa fitaccen ɗan gwagwarmayar siyasa a Jihar Kano,kuma guda cikin masu magana akafafen yaɗa labarai Dattijo Alhaji Musa Magaji Gausu rasuwa.

Muna miƙa ta’aziyyarmu ga iyalansa, abokansa da daukacin al’ummar Jihar Kano. Allah Ya jikansa da rahama, Ya gafarta masa kurakuransa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa.

Hukumar Sadarwa ta Najeriya, Nigerian Communications Commission, ta bayyana cewa kamfanonin sadarwa sun biya fiye da mas...
09/06/2026

Hukumar Sadarwa ta Najeriya, Nigerian Communications Commission, ta bayyana cewa kamfanonin sadarwa sun biya fiye da masu amfani da layukan waya miliyan 75 diyya saboda matsalolin rashin ingancin sadarwa, a wani mataki da aka bayyana a matsayin daya daga cikin manyan shirye-shiryen kare hakkin masu amfani da waya a Afirka.

hukumar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar bayan taron kwamitin gudanarwarta na 109 da aka gudanar a ranar 25 ga Mayu, 2026, inda ta ce an samu gagarumin ci gaba wajen tabbatar da kamfanonin sadarwa sun cika ka’idojin ingancin ayyukan da ake bukata daga gare su.

Jaridar punch ta Rawaito Hukumar ta tuna cewa a ranar 29 ga Maris, 2026, ta umarci kamfanonin sadarwa su biya diyya ga masu amfani da layi da s**a fuskanci matsalolin sadarwa. A karkashin wannan umarni, kamfanonin sun rika tura katin waya kai tsaye ga wadanda abin ya shafa bisa la’akari da yadda suke kashe kudi a wuraren da aka samu gazawar sadarwa.

A cewar sanarwar, an samu cikakken bin umarnin daga kamfanonin sadarwa, lamarin da ya sa aka biya fiye da masu amfani da layi miliyan 75 diyya. Sai dai NCC ta ce har yanzu tana gudanar da bincike mai zaman kansa domin tabbatar da cewa an hada dukkan wadanda s**a cancanci karbar diyya a cikin tsarin.

Hukumar ta kuma bayyana cewa tana ci gaba da sa ido kan yadda masu samar da kayayyakin sadarwa, musamman kamfanonin hasumiyoyin sadarwa, ke amfani da kudaden tarar da aka kakaba musu wajen inganta cibiyoyin sadarwa, domin kara ingancin ayyukan sadarwa da rage matsalolin da masu amfani da layi ke fuskanta a fadin Najeriya.

Kano, Tarayyar Turai da UNICEF sun kaddamar da shirin ilimi na shekaru 10 domin magance matsalar koyo Gwamnatin Jihar Ka...
09/06/2026

Kano, Tarayyar Turai da UNICEF sun kaddamar da shirin ilimi na shekaru 10 domin magance matsalar koyo

Gwamnatin Jihar Kano, hadin gwiwar da Tarayyar Turai (EU) da kuma Asusun Tallafawa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) sun fara tsara shirin ilimi na shekaru 10.

Majalisar Wakilai ta gayyaci shugabannin hukumomin tsaro da kuma Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro, Nuhu Ribadu...
09/06/2026

Majalisar Wakilai ta gayyaci shugabannin hukumomin tsaro da kuma Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro, Nuhu Ribadu, domin su bayyana a gabanta kan yadda matsalar rashin tsaro ke ƙara ta'azzara a ƙasar nan.

Matakin ya biyo bayan amincewa da wani ƙuduri da ɗan majalisar mai wakiltar mazaɓar Gummi/Bukkuyum ta Jihar Zamfara, Sulaiman Gumi, ya gabatar.

Majalisar ta nuna damuwa kan yawaitar hare-haren 'yan bindiga da masu tayar da ƙayar baya da ke kashewa tare da sace jama'a a sassan ƙasar, yayin da ake ci gaba da kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya sake duba shugabancin hukumomin tsaro.

Jam'iyyar NDC ta bayyana cewa ba za ta kakaba wa jihar Kano ko wata jiha 'yan takara ba, tana mai jaddada aniyarta na ta...
09/06/2026

Jam'iyyar NDC ta bayyana cewa ba za ta kakaba wa jihar Kano ko wata jiha 'yan takara ba, tana mai jaddada aniyarta na tabbatar da dimokuraɗiyya da adalci a cikin harkokin jam'iyyar.

a wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na ƙasa na jam'iyyar, Osa Director, ya fitar cewa shugabannin NDC ƙarƙashin jagorancin Sanata Henry Seriake Dickson sun gana da tawaga daga shugabancin ƙungiyar Kwankwasiyya ta ƙasa domin tattauna matsalolin da s**a taso a Kano.

Sanarwar ta ce shugabannin jam'iyyar na shiga tsakani ne domin warware saɓanin da ke tsakanin ƙungiyar Kwankwasiyya da tsofaffin shugabannin NDC a Kano, tare da tabbatar da cewa an bai wa kowane mamba damar shiga harkokin jam'iyyar ba tare da wariya ba.

Jam'iyyar ta kuma ce har yanzu ba ta fitar da sakamakon zaɓen fidda gwani a kowace jiha ba, saboda haka ta bukaci jama'a da mambobinta su yi watsi da duk wata jerin sunayen da ake yaɗawa a matsayin sakamakon zaɓen fidda gwani.

Me za ku ce?

Kungiyar Kwankwasiyya ta bayyana cewa babu kamshin gaskiya a rahotannin da ke yawo cewa jagoranta kuma ɗan takarar matai...
09/06/2026

Kungiyar Kwankwasiyya ta bayyana cewa babu kamshin gaskiya a rahotannin da ke yawo cewa jagoranta kuma ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar Najeriya Democratic Congress (NDC), Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi barazanar ficewa daga jam’iyyar.

Mai magana da yawun kungiyar, Habibu Sale Mohammed, ya ce rahotannin da ke ikirarin cewa Kwankwaso ko kungiyar Kwankwasiyya na nuna rashin jin daɗi kan sauya wasu daga cikin sunayen ’yan takarar da aka gabatar, ba su da tushe.

A cewarsa, Kwankwaso ya bayyana irin waɗannan rahotanni a matsayin jita-jita kawai, yana mai jaddada cewa kungiyar Kwankwasiyya ba ta da wata ƙorafi a halin yanzu.

Tun da farko dai wasu kafafen yaɗa labarai sun ruwaito cewa kungiyar za ta iya daukar matakin ficewa daga NDC bayan an sauya wasu daga cikin ’yan takarar da aka ce magoya bayan kungiyar ne s**a gabatar.

Sai dai Habibu Sale Mohammed ya musanta waɗannan zarge-zarge, yana mai cewa babu wata matsala tsakanin kungiyar da jam’iyyar, kuma rahotannin da ake yadawa ba su da ingantaccen tushe.

Hon Umar Yusuf Usman Shinge, Tsohon Dan Takarar Majalisar Jiha Mai Wakiltar karamar hukumar Karaye bayan ficewar sa daga...
09/06/2026

Hon Umar Yusuf Usman Shinge, Tsohon Dan Takarar Majalisar Jiha Mai Wakiltar karamar hukumar Karaye bayan ficewar sa daga Jam'Iyar NDC ya samu takarar majalisa jaha a jam'iyyar PDP .

Bayan Samun Tikitin Takarar Majalisar jaha Mai Wakiltar Kananan Hukumomin Karaye da Rogo A Jam'Iyar PDP A zaben 2027 Dake Tafe.

Hon umar shinge yayi Kira Ga Al'ummar Mazabar sa tab Karaye da Rogo, Na Jam'Iyun APC, ADC, NDC , PDP, Dama Sauran Jam'iyu, Musamman Matasa Da Iyaye dasu , Hadakai Domin Ciyar Da Yankin Gaba Domin Kawo Sauyi.

Kwankwaso Ya Karɓi 'Yan Takarar NDC na Jihar Kogi a AbujaTsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyyar NDC, Rabiu Mus...
09/06/2026

Kwankwaso Ya Karɓi 'Yan Takarar NDC na Jihar Kogi a Abuja

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyyar NDC, Rabiu Musa Kwankwaso, ya karɓi baƙuncin 'yan takarar jam'iyyar NDC na jihar Kogi a gidansa da ke Maitama, Abuja.

A yayin ganawar, Kwankwaso ya tarbi tawagar 'yan takarar tare da tattauna muhimman batutuwan siyasa da s**a shafi ci gaban jam'iyyar NDC da kuma shirye-shiryen tunkarar zaɓuɓɓuka masu zuwa.

Ba ni ne na rabu da Abba ba, Har yanzu ina sonsa don ba ni ne nace ya tafi ba.Inji KwankwasoKwankwaso ya bayyana haka ne...
09/06/2026

Ba ni ne na rabu da Abba ba, Har yanzu ina sonsa don ba ni ne nace ya tafi ba.Inji Kwankwaso

Kwankwaso ya bayyana haka ne yayin zantawarsa da kaffar yaɗa labarai ta BBC.

Me za ku ce ?

Address

Nasarawa GRA
Kano
23471

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Prime Time News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Prime Time News Hausa:

Share