09/06/2026
Hukumar Sadarwa ta Najeriya, Nigerian Communications Commission, ta bayyana cewa kamfanonin sadarwa sun biya fiye da masu amfani da layukan waya miliyan 75 diyya saboda matsalolin rashin ingancin sadarwa, a wani mataki da aka bayyana a matsayin daya daga cikin manyan shirye-shiryen kare hakkin masu amfani da waya a Afirka.
hukumar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar bayan taron kwamitin gudanarwarta na 109 da aka gudanar a ranar 25 ga Mayu, 2026, inda ta ce an samu gagarumin ci gaba wajen tabbatar da kamfanonin sadarwa sun cika ka’idojin ingancin ayyukan da ake bukata daga gare su.
Jaridar punch ta Rawaito Hukumar ta tuna cewa a ranar 29 ga Maris, 2026, ta umarci kamfanonin sadarwa su biya diyya ga masu amfani da layi da s**a fuskanci matsalolin sadarwa. A karkashin wannan umarni, kamfanonin sun rika tura katin waya kai tsaye ga wadanda abin ya shafa bisa la’akari da yadda suke kashe kudi a wuraren da aka samu gazawar sadarwa.
A cewar sanarwar, an samu cikakken bin umarnin daga kamfanonin sadarwa, lamarin da ya sa aka biya fiye da masu amfani da layi miliyan 75 diyya. Sai dai NCC ta ce har yanzu tana gudanar da bincike mai zaman kansa domin tabbatar da cewa an hada dukkan wadanda s**a cancanci karbar diyya a cikin tsarin.
Hukumar ta kuma bayyana cewa tana ci gaba da sa ido kan yadda masu samar da kayayyakin sadarwa, musamman kamfanonin hasumiyoyin sadarwa, ke amfani da kudaden tarar da aka kakaba musu wajen inganta cibiyoyin sadarwa, domin kara ingancin ayyukan sadarwa da rage matsalolin da masu amfani da layi ke fuskanta a fadin Najeriya.