Muryar Arewa Reporters

Muryar Arewa Reporters Muryar Arewa Reporters Shafi ne na samo labarai masu muhimmanci dake faruwa a sassan Duniya

17/06/2025

Some Important Facts Nigerians Should Understand About Iran 🇮🇷 and Israel 🇮🇱

- Iran 🇮🇷 is not an Arab country; it is predominantly Persian.
- Israel 🇮🇱 is not a Christian nation; it is predominantly Jewish.
- The Jewish people practice Judaism, not Christianity ✝.
- In Israel 🇮🇱, both Christianity and Islam are minority religions, but there are more Muslims than Christians.
- Iran 🇮🇷 actually has a larger Christian population than Israel.
- There are more Arabs in Israel 🇮🇱 than there are Christians ✝.
- Preaching Christianity is easier in the United Kingdom 🇬🇧 than it is in Israel.
- Iranians 🇮🇷 speak Persian (Farsi), and only a small minority speak Arabic.
- Iran is the leading Shia Muslim nation and often at odds with Sunni Islamic doctrine, which is led by Saudi Arabia.

If the only reason you support Israel is because it is mentioned in the Bible or you believe it is a Christian country...

If the only reason you support Iran is because you think it is an Arab nation or simply because it is predominantly Muslim...

If your support is not based on who is right or wrong, who breaks international laws, or who upholds justice and fairness; but is instead based solely on religious sentiment...

Then you are not standing for truth, fairness, or humanity. You are simply acting out of religious bias.

Let us stand for truth, justice, and human dignity; no matter who is involved.
COPIED

17/06/2025

Shin kasan irin yawa, girma da ƙarfin ƴan fashin hanyar da Missiles ɗin Iran suke haɗuwa da su kafin su isa Israel ?

***Duk lokacin da Iran ta harba Ballistic Missiles daga Isfahan zuwa lsra'ilá, waɗannan Missiles za su fuskanci taɗiya kala-kala kafin su isa ga inda aka aika su. K**a tun daga kan matattarar Sojojin Amurka da ke iraƙi, ƙananun Jiragen yaƙi na Faransa da ke UAE (wanda Sa'udiyya ta ba da damar a yi amfani sararin samaniyar ta), da Manyan Jiragen Ruwa da ake kira USS Carl Vincent da suke ɗauke da ƙananun Jiragen kaɗe Missiles wanda suke kula da shige da fice a yankin Tekun Persia.

Idan Missiles ɗin Iran s**a tsallake dukkan waɗannan kayan yaƙin kaɗo Missiles da ke jibge (a hanyar su ta zuwa Isra'ila) za su ƙara cin karo da jirgin Air Force Typhoon mallakin masarautar ƙasar Ingila, da F-35 fighter Jet mallakin ƙasar Cyprus da suke a sararin samaniyar ƙasar Jordan (suna jiran isowar su).

Idan waɗannan Missiles na ƙasar Iran duk sun tsallake waɗannan wurare, Arrow-3 Air Defence system na ƙasar lsra'ilá yana jiran isowar su don kaɓar da su tun daga nisan Kilomita dubu biyu, Idan Arrow-3 ya gaza ɓarar da waɗannan Missiles, akwai Arrow-2 shi ma yana jiran matsowar waɗannan missiles daga nisan kilomita 1500 zuwa Kilomita 500.

Bayan haka, akwai David's Sling Defense System (a ƙasar ta Isra'ila) shi ma yana jiran ƙarasowar waɗannan Missiles daga nisan Kilomita 300 zuwa 40.

(Duk da haka) idan waɗannan Missiles ɗin s**a tsallake dukkan waɗannan hare-hare, a ƙarshe, akwai Iron Dome, wanda shi ma aikin kaɗar da Missiles yake yi daga nisan kilomita 70 zuwa Kilomita 4.

Shin ko akwai wani Missiles a Duniya da zai iya tsallake dukkan waɗannan tuɓatuɓai ya isa ga inda aka tura shi? Waɗannan Missiles da Iran ta yi amfani da su, Missiles ne na cikin gida, a yayin da waɗancan kayan aiki da suke ta ƙoƙarin ɓaro waɗannan Missiles an ƙirƙire su a ƙasashen da s**a fi ko ina cigaba a Duniya.

Trump ya bayyana shirinsa na tura manyan jami'an ƙasar Amurka zuwa birnin Tehran domin tattaunawa da hukumomin Iran a ga...
17/06/2025

Trump ya bayyana shirinsa na tura manyan jami'an ƙasar Amurka zuwa birnin Tehran domin tattaunawa da hukumomin Iran a game da lamarin

DA ƊUMI ƊUMI: Shugaban riƙon ƙwarya na Burkina Faso, Ibrahim Traoré, ya karɓi fasfo na farko na gamayyar kasashe uku na ...
30/01/2025

DA ƊUMI ƊUMI: Shugaban riƙon ƙwarya na Burkina Faso, Ibrahim Traoré, ya karɓi fasfo na farko na gamayyar kasashe uku na (AES)

Shugaban riƙon ƙwarya na Burkina Faso, Kaftin Ibrahim Traoré, ya karɓi fasfo na farko na zahiri daga ƙungiyar Haɗin Kan Ƙasashen Sahel (AES) a birnin Ouagadougou.

Ƙungiyar AES, wacce ƙasashen Burkina Faso, Mali da Nijar s**a kafa, ta ƙaddamar da sabuwar takardar fasfo ta bai ɗaya, bayan ficewarsu daga ƙungiyar ECOWAS.

Ficewar su daga ECOWAS ta fara aiki ne a hukumance a ranar Laraba, 29 ga Janairu.

17/07/2024

Shout out to my newest followers! Excited to have you onboard! Dahiru B Danbagudu, Muftahu Idrismusa, Yusuf Bin Salisu, Muso Annabi, Mustapha Yusuf Maitama, Fatima Mohd, Hajara Ibrahim, Salisu Idris Bakori, Journalist Sulaiman Ahmad Sulaiman, Nasa Adu Isah, Babangiad U Mlf, Zakaria Ibrahim, Abubakar Muhammad Yandadi, Sa'adatu Yusuf Gele, Lukman Umar, Murtada Sulaiman, Habibu Abdulrahaman Aliyu, Sanusi Dan Kano, Suleiman Mohammed Takuti, Malan Umar, Ammar Garo, Harunà ALi, Umar Abdul, Muhammed Dalhat Muhameed Dalhat, Abibakar Aja, Basiru Dan Baba

WATA SABUWA: Akwai yiyuwar Sarki Aminu Ado Bayero zai gabatar da yawan Salla.Sarki Alhaji Aminu Ado Bayero, ya umarci ha...
11/06/2024

WATA SABUWA: Akwai yiyuwar Sarki Aminu Ado Bayero zai gabatar da yawan Salla.

Sarki Alhaji Aminu Ado Bayero, ya umarci hakimai a jihar Kano da su shigo cikin birnin na Kano domin fara shirin hawan sallah babba.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwa da galadiman Kano Alhaji Abba Sunusi ya sanyawa hannu.

Sanarwar ta kuma buƙaci hakiman da su shigo cikin Kano da dagatansu, mahaya da kuma dawakansu. Mene ne ra'ayinku?

Wani magidanci ne da matarsa kullum ce-ce-ku-ce ya yi yawa tsakaninsu. Kullum cikin zarginta yake da hada husuma a cikin...
10/06/2024

Wani magidanci ne da matarsa kullum ce-ce-ku-ce ya yi yawa tsakaninsu.

Kullum cikin zarginta yake da hada husuma a cikin gidansa, har da tsakanin danginsa.

Wata rana ya shigo gida, sai ya tarar tana barci sai ya ce:

"Fitina barci take".

Sai ta juyo ta ce masa:

"Allah ya tsine wa wanda ya tasheta".

Wani malami mai hikima yana zaune tare da wasu mutane, sai zancen mata da kuma aure ya fado.Sai daya daga cikinsu ya ce:...
10/06/2024

Wani malami mai hikima yana zaune tare da wasu mutane, sai zancen mata da kuma aure ya fado.

Sai daya daga cikinsu ya ce: Ai mace k**ar takalmi ne, namiji zai iya gwadawa ya canja, ya gwada ya canja har sai ya sami wanda ya yi daidai da kafarsa.

Sai mahalarta s**a dubi wannan malamin s**a tambaye shi: Mene ne ra’ayinka a kan abin da ya fada?

Sai ya ce: Lallai abin da wannan mutum ya fada gaskiya ne cif-da-cif. Mace k**ar takalmi take a idon wanda ya dauki kansa kafa (kaskantacce),
Amma ita kambin sarauta ce ga wanda yake ganin kansa kai (shugaba).

Saboda haka kada ku zargi mai magana, amma dai ku fahimci yaya ya dauki kansa.

AN KARA ZUBAR DA KIMA DA MUTUNCIN NIGERIA A IDON DUNIYAKowa dai yana sane da abinda ya faru kwanaki kadan da s**a wuce t...
07/05/2024

AN KARA ZUBAR DA KIMA DA MUTUNCIN NIGERIA A IDON DUNIYA

Kowa dai yana sane da abinda ya faru kwanaki kadan da s**a wuce tsakanin mahukuntan Nigeria da kamfanin Binance wanda ake hada-hadar kudin Crypto a cikinsa

A wani yunkuri na borin kunya daga mahukuntan Nigeria sunce wai Binance ne ya haddasa hauhawar farashin Dala, don haka s**a dauki mataki kan Binance, s**a dakatar da P2P garemu 'yan Nigeria da muke mu'amala da Binance Exchanger

Daga bisani Mahukuntan Nigeria sun k**a ma'aikatan Binance guda biyu, amma ance wai daya daga cikinsu ya tsere ba tare da anyi bayanin hanyar da yabi yatsere ba

Kwatsam yau kuma sai Shugaban gudanarwan kamfanin Binance ya saki labari cewa wasu daga cikin mukarraban Gwamnatin Nigeria sun bukaci kamfanin Binance ya basu cin hanci na kudi Dalar Amurka Miliyan 150, kusan Naira Biliyan 200 kenan a kudin Nigeria wai zasu gyara matsalar dake tsakanin Binance da Gwamnatin Nigeria

Amma Binance sunki yadda su bada cin hancin, s**ace suna so a warware matsalar ta hanyar doka, yanzu wannan labarin shine yake trending a duniya
Kunga an kara zubar mana da kima da mutuncin Kasarmu Nigeria a idon duniya

Mun fahimci cewa dama an nemi daukar mataki kan Binance ne don wasu tsirarun mukarraban Gwamnati su samu kudi amma hakarsu bata cimma ruwa ba, tonon asiri ya biyo baya

To da wannan muke kira ga Maigirma Mai bawa shugaban Kasa shawara akan tsaro Malam Nuhu Ribado akan ya binciki wadanda s**a nemi Binance su bada cin hanci, ayi gaggawan rabasu da Gwamnatin Tinubu, inda hali a dauki matakin da ya dace a kansu

Allah Ya sauwake

Dalili nafarko dayasa maza basason auren female soja shine akullun tunanunsu ana lalata dasu bayankuma ba hakabane ako.i...
07/05/2024

Dalili nafarko dayasa maza basason auren female soja shine akullun tunanunsu ana lalata dasu bayankuma ba hakabane ako.ina akasamu na banza dole asamu na kirki Amma se anamusu kudin goro gaskiya yak**ata adena haka

SABON HARAJI DAGA BABBAN BANKIN NIGERIACBN Ta Umurci Bankuna Da Su Cire Kashi 0.5% A Duk Wata Transifa Da Aka Yi A Banki...
07/05/2024

SABON HARAJI DAGA BABBAN BANKIN NIGERIA

CBN Ta Umurci Bankuna Da Su Cire Kashi 0.5% A Duk Wata Transifa Da Aka Yi A Banki Saboda Gudanar Da Tsaron Yanar Gizo. duka Lokacinda zaka tura kudin 10,000 za'a dauki 500 Naira charges

Haka zalika Idan zaka sanya kudi a asusun Bankinka Da s**a kai adadin 500k za'a chaje ka 2% wato duk ,500k zaka bayarda 10,000 idan kuma zaka sanya 1,000,000 zaka bayarda 20,000

Sai kuma masu amfani da Corporate account zasu bayarda 3% idan zasu ajiye 3,000,0000 a cikin asusun Bankinsu wato kowace 3M zaka bayarda 90,000

Bari mugani ko akwai masu Halifax irin na shugabanin mu
07/05/2024

Bari mugani ko akwai masu Halifax irin na shugabanin mu

Address

Kano

Telephone

+2348104172563

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muryar Arewa Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Muryar Arewa Reporters:

Share