Muryar Arewa Reporters

Muryar Arewa Reporters Muryar Arewa Reporters Shafi ne na samo labarai masu muhimmanci dake faruwa a sassan Duniya

Iran ta inganta mak**ai masu linzaminta zuwa mataki na ban mamakitun bayan Gwabza yaƙin tsakanin Iran da Isra’ila na Tsa...
24/01/2026

Iran ta inganta mak**ai masu linzaminta zuwa mataki na ban mamaki
tun bayan Gwabza yaƙin tsakanin Iran da Isra’ila na Tsawon kwanaki 12.

Kakakin ma’aikatar tsaron Iran ya ce ƙasar tana da mak**an roƙa masu inganci da ƙarfi fiye da waɗanda aka yi amfani da su a lokacin yakin kwanaki 12

Brigadier Janar Reza Talaei-Nik ya magantu a ranar Asabar cewa Iran ta kuma ƙara yawan mak**an roƙanta.

Uku daga cikin yarjejeniyoyin da Abba Kabir Yusuf yarattabawa hannu a fadar shugaban kasa su ne .   Na 1 zai koma jam'iy...
18/01/2026

Uku daga cikin yarjejeniyoyin da Abba Kabir Yusuf yarattabawa hannu a fadar shugaban kasa su ne .

Na 1 zai koma jam'iyyar APC a karshen wata na uku da shigar sa ofis.

Na 2 ba zai taba masarauta ba tun da ba kuri'a ce ta shigar da shi ofis ba alfarma ce ta shugaban kasa.

Na 3 zai karkade littafin tuhumar da ake yi wa uban gidan sa na dibar kudaden kananan hukumomi har Naira miliyan 70-70 wadan da yakwashe yaje yayi takarar shugaban kasa da su a jihar Lagos.

Awa biyu da rattaba hannun sa a cikin dare fadar shugaban kasa ta umarci alkalan kotun koli ta tabbatar da Abba a matsayin gwamnan kano.

In kun tuna jama'a a lokacin da aka je kotuna 2 tuni har jami'an gwamnatin Abba sun yi nisa wajen cefanar da kayan gwamnatin kano a ma'aikatun su da nufin gafiya ta tsira da na bakin ta.

Don haka masu tunanin cewa wai Abba in ya koma cikin jam'iyyar APC zai dawo da mai martaba sarkin kan Alhaji Aminu Adamu Abdullahi Bayero su daina.

Ba don komai ba sai don saba alkawarin da Abba yayi tun da farko. Don haka yanda kotun koli ta tabbatar da Abba wanda yakawo karshen shari'ar sa da jam'iyyar APC.

Bayanan sirri sun tabbatar da cewa kotun koli za a baiwa umarni ta dawo da mai martaba sarkin kano Alhaji Aminu Adamu Abdullahi Bayero.

In ta dawo da shi shi ke nan sunusin kano ya tafi ke nan har gaban abada.

Amma in Abba ne yadawo da shi, to sunusi yana da iko da kuma damar ci gaba da shari'a.

Kowa ya kwantar da hankalin sa da yardar ALLAH wannan shi ne abin da zai faru.

Matar Bahaushe Ta Fi Kowace Mace Gata A nahiyarmu ta Africa Amma Ita Ce tafi Gasa Wa Namiji Aya A Hannu Matar Malam Baha...
18/01/2026

Matar Bahaushe Ta Fi Kowace Mace Gata A nahiyarmu ta Africa Amma Ita Ce tafi Gasa Wa Namiji Aya A Hannu

Matar Malam Bahaushe tana da gata sosai sama da sauran matan kabilunmu, domin Malam Bahaushe bai yarda ya ga matarsa ta fita tana aikin karfi ko wahala ba.

Shi duk talaucin sa ya fi son matar sa ta zauna a gida shi ya fita ya yi aikin karfin ko wahalar domin ya nemo musu abin da za su ci shi da ita da yaransu.

Ada da wuya ka ga matar Malam Bahaushe tana zuwa Daukan ruwan da zasu sha koh nemo abin da zasu ci, ko daukar nauyin karatunta ko daukar nauyin gidanta da na yaranta koh da kuwa mai hali ce

Malam Bahaushe idan mai hali ne
hatta girki da wanki koh wanke-wanke ya haramtawa matarsa sai dai ya dauko masu yi mata hidima... Ita sai dai ta kwanta ta ci ta sha tayi ibada sai kuma kula da tarbiyyar yaransu kawai... Ko Unguwa za ta akwai direba idan ba mota a ba ta kudin keke napep.

Amma wallahi abin takaici da haushi sai kaji Malam Bahaushe kullum yana kuka da matarsa... Sam ba ta bashi had'in kai kullum cikin neman tashin hankali k**ar America
Da yawa daga cikin ire iren wadannan matsalolin ne kan sa wani namiji dake da hali karin aure ko Allah zai sa ya dace koh kuma yayi tunanin tsallakawa ya Auro wata kabilar ta daban wacce yake tunanin zai samu zaman lafiya da ita.

Wai kuwa matanmu na kasar hausa suna lura da yadda matan wasu kabilun ke fama da aikin karfi domin daukar nauyin mazansu da yaransu?
Ta dalilin aikin karfin da suke yi har jikinsu ya murde ya zama irin na maza

Kuma duk da haka suna girmama mazajensu duk da irin yadda suke gallaza musu kuwa?

Wasu matan kabilun fa su fita kiwon dabbobi ko yin itacen girki, wasu suyi aikin kafinta ko daukar bulo ko gini koh kankare wasu da ciki ko goyo suke wannan aikin kuma su samo kudin su dawo gida su girka abinci su ci su da mazajensu da yaransu... Ke kuma matar Malam Bahaushe mai ki ka sani game da irin wadannan aiyukan wahalar

Ni dai wallahi na kasa fahimtar me yake damun wasu daga cikin matan hausawa yak**ata ku chanza tunani

17/01/2026

Allah ya shiga tsakanin nagari da mugu
Gawarwakin mutanen da aka shikenan a unguwar dorayi

17/01/2026

Gwamnatin Kano Ta Musanta Wani Rahoto

Gwamnatin Jihar Kano ta musanta wani rahoto da wata kafar yaɗa labarai ta wallafa, wanda ke zargin cewa umarnin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayar na dakatar da tura takardu zuwa ofishinsa ya janyo tsaiko ko durƙushewar harkokin gudanarwa a jihar.

A cikin wata sanarwa da Sakataren Gwamnatin Jihar, Umar F. Ibrahim, ya sanya wa hannu, gwamnatin ta bayyana rahoton a matsayin ƙarya marar tushe, tana mai cewa ba ya da hujjar doka ko gaskiya.

Sanarwar ta bayyana cewa an bayar da umarnin ne a ƙarshen watan Disamba, bayan karewar aikin kasafin kuɗin shekarar da ta gabata, yayin da sabon kasafin ke gaban Majalisar Dokoki.

Gwamnatin ta jaddada cewa manufar umarnin ba ta tsaya kan tsaida ayyukan mulki ba, sai dai ƙarfafa da’a da tsari a harkokin kuɗi, domin hana kashe kuɗaɗe ba tare da izini ba da kuma kare jihar daga matsalolin binciken kuɗi da shari’o’i a gaba.

Ta kuma tabbatar wa al’umma cewa ayyukan gwamnati, musamman a fannonin tsaro, lafiya, ilimi da tsafta, sun ci gaba da gudana yadda ya k**ata bisa tanade-tanaden doka.

16/01/2026
16/01/2026

16/01/2026

Akwai Wani Abu, idan akan same shi ana murna, idan aka rabu dashi ma murna ake, menene shi?

Yadda Al’ummar garin Tidibale Dake Karamar Hukumar Isa A Jihar Sokoto Suke Kaura Bayan Wa'adin Da Bello Țùŕji Ýa Ba Šu Ñ...
16/01/2026

Yadda Al’ummar garin Tidibale Dake Karamar Hukumar Isa A Jihar Sokoto Suke Kaura Bayan Wa'adin Da Bello Țùŕji Ýa Ba Šu Ña Barin Garin

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Manjo Donatus Okafor Wanda (a ramuwar gayya) sojojin Arewa s**a bunne shi da ransaManjo Donatus Okafor shi ne sojan da y...
16/01/2026

Manjo Donatus Okafor Wanda (a ramuwar gayya) sojojin Arewa s**a bunne shi da ransa

Manjo Donatus Okafor shi ne sojan da ya bai wa Tafawa Balewa giya nau'in burkutu da taba sigari, ya tilasta masa cewa sai ya kwankwada, ya ce masa idan ya sha za su kyale shi. Da sauran cin zarafi da s**a rika yi wa manyan Arewa a lokacin da s**a k**a su kafin su karkashe su, kisan wulakanci da tozartawa.

Tafawa Balewa yaki shan bukatun ya ki shan sigarin, yace addinin sa ya hana, kafin su kashe shi Tafawa Balewa yace: Inyamuri inyamuri kai da da mulkin Najeriya har abada da yardar Allah.

A matsayinsa na kwamandan rundunar da ke kula da tsaron Firayim Minista Abubakar Tafawa Balewa, Okafor saboda cin amana, ya yi amfani da saninsa da Firayim Minista don shirya dabarar yadda za a halaka shi.

An gano Okafor a matsayin daya daga cikin masu shirya makirci kashe Tafawa Balewa tare da su Manjo Emmanuel Ifeajuna da Kyaftin Ogbo Oji, waɗanda s**a fara shirin juyin mulkin tun daga watan Agusta na 1965.

A daren juyin mulkin, Okafor ya jagoranci sojoji zuwa gidan Birgediya Zakariya Maimalari, wanda daga ƙarshe s**a kashe shi. Duk da cewa bayanai sun bambanta game da hannun da ya ke da shi kai tsaye game da kisan Firayim Minista, wasu rahotanni sun ce shi da Ifeajuna sun sace Firayim Minista s**a harbe shi.

Bayan gazawar juyin mulkin da kuma kwace iko da Janar Aguiyi-Ironsi ya yi, an tsare Okafor a gidan yarin Abeokuta.

Mutuwar Manjo Donatus Okafor batayi kyau ba.

A lokacin juyin mulkin ramuwar gayya da aka yi a watan Yulin 1966, sojojin arewa sun kutsa cikin gidan yarin in da aka tsare Donatus Okafor don neman ɗaukar fansa kan mutuwar shugabannin arewa, in da s**a k**ashi s**ayi masa dukkan kawo wuka, s**a binne shi da ransa.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Muryar Arewa Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Muryar Arewa Reporters:

Share