Ayzan Multimedia

Ayzan Multimedia Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Ayzan Multimedia, Broadcasting & media production company, Kano.

AYZAN MULTIMEDIA
Gidan jarida ne na zamani da ke kawo Labaran Duniya, Iliman-Tarwa, Ni Shadan-Tarwa, da Tarihi domin faɗakar da zukata, gyara halaye, da gina al’umma bisa gaskiya da ilimi.

Ana fargabar mutane da dama sun nutse sanadiyyar kifewar jirgin ruwa a Neja.
26/07/2025

Ana fargabar mutane da dama sun nutse sanadiyyar kifewar jirgin ruwa a Neja.

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO BaGwamnatin tarayya ta karyata labaran da ake ta yadawa ta kafar sad...
26/07/2025

Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba

Gwamnatin tarayya ta karyata labaran da ake ta yadawa ta kafar sadarwa ta zamani cewar gwamnatin tarayya ta soke jarrabwar WAEC da NECO wadanda aka yi a shekarar 2025 saboda abubuwan da aka yi wadanda s**a sabawa dokokin jarabawar biyu.

A sanarwar da ma’aikatar ilimi ta tarayya ta fitar makon daya gabata wadda kuma dauke da sa hannun darekta na ‘yan jarida da hulda da jama’a, Boriowo Folasade, ya sake ya bayyana rahoton, a matsayin wani abu ne da aka shirya shi, domin a tada hankalin al’umma da s**a hada da dalibai, Iyaye, da jama’a baki daya.

Ma’aikatar ta tabbatar da cewa an kammala jarabawar WAEC ta shekarar 2025 cikin nasara ba tare da wata matsala ba,in da an hadu da wasu matsaloli amma an yi maganinsu da hukumar ita ta yi hakan.

Hakanan ma ta kara yin bayani cewar jarrabawar NECO da ana yin ta ba tare da wata matsala ba, a daidai lokacin da ake shi wannan jawabin babu wta matsalar da aka hadu da ita.

Ma’aikatar ta jaddada bata samu wani labara ba daga wani jami’inta ko rahoto daga hukumomin WAEC, da NECO ko kuma wata hukumar dangane da wani abinda aka yi daya sabwa doka lokacin jarrabawar.

Labarai Masu Nasaba
‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato
An Samu Rarrabuwar Kai Kan Makin Shiga Manyan Makarantu

Don haka nema tayi kira da jama’a kada suyi amfani da shi labarin daya zaman a kanzon kurege da ake ta yadawa,idan wani bayani suke bukata su tuntubi kafa da s**a san ba zata yi zuki ta malle ba,ko kuma jami’an ma’aikatar ilimi ta kafar sadarwarsu ko kuma na, WAEC, da NECO.

“An ja hankalin ma’aikatar ilimi ta tarayya akan wani labara ko rahoton da ya karade kafafen sadarwa na zamani,inda aka yi maganar cewar ban soke jarabawar WAEC ta shekarar 2025 da aka yi saboda an samu laifin aikata magudi lokacin da ake yin ta.

“Ma’aikatar tace don haka tana sanar da jama’a cewa ta yi nesa da kanta,dangane da ita sanarwar ko labarin saboda kuwa ai na kanzon kurege ne inda ta kara jaddada: Jarabawar, WAEC ta shekarar 2025,an kammala ta cikin nasara ba tare da wata matsalar data gagara shawo kai ba,in banda wadansu ‘yan kananan laifukan da s**a auku,wadanda kuma ita hukumar tayi maganinsu.

“Ita kuma jarabawar NECO ana yinta ba tare da wata matsala ba, ya zuwa kuma hali ko lokacin da ake ciki babu wata matsalar da aka fuskanta. Ma’aikatar ilimi ta tarayya bata samu wani sako ba a hukumance daga WAEC ko kuma NECO,ko kuma duk wata hukuma mai shirya jarabawa da ke nuna an samu aikata magudin jarabawa.”

Ma’aikatar har yanzu babu wani abinda daya tada mata hankali wanda ya wuce aikata lamurran da s**a shafi jarabawa cikin gaskiya da rikon amana,da kuma kwanciyar hankali, tana aiki kafada da kafada da su hukumomin jarrabawar,domin a samu inganta yadda ake lura da sa idon dangane da yadda ake gudanar da jarabawar.

Daga karshe ma’aikatar ta kara jaddada ta sha alwashin yadda ake gudanar da jarabawar yayi daidai kamar yadda dokokin hukumar s**a bayyana, na samun gaskiya kan duk wata jarabawar da ake yi a Nijeriya,don haka su hukumomin jarrabawar jarabawar abokan huldar ta ne da kuma aiki tare.

Jami'ar Fatakol Ta Ba Wa Gwamnan Jihar Adamawa Digirin Girmamawa Jami’ar birnin Fatakol da ke Jihar Rivers, ta karrama g...
26/07/2025

Jami'ar Fatakol Ta Ba Wa Gwamnan Jihar Adamawa Digirin Girmamawa

Jami’ar birnin Fatakol da ke Jihar Rivers, ta karrama gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri da digirin girmamawa ta zama "Dakta A Fannin Kimiyyar Aikin Gwamnati", domin yaba wa da gudunmawar da yake bayarwa a fannin shugabanci da aikin gwamnati.

Bayan zartarwar majalissar gudanarwar Jami’ar, rijistara, sakataren majalissar, Dakta, Gloria Chindah, ta tabbatar da cewa za a miƙa wa gwamnan lambar a yayin bikin yaye ɗaliban Jami'ar karo na 35 da zai gudana a ranar 26 ga Yuli, 2025, kamar yadda Dokin Ƙarfe TV ta ruwaito.

"Cikin girmamawa da ƙanƙan da kai, nake bayyana karɓan lambar yabo ta matsayin Dakta a fannin kimiyyar aikin gwamnati da Jami’ar Fatakol ta ba ni. Wannan karramawa ta tabbatar da ƙoƙarin da nake kan harkokin shugabanci da aikin gwamnati. Ina miƙa saƙon godiyata ga majalissar ƙoli da majalissar zartarwar Jami’ar bisa wannan girmamawa gare ni. Ina alfahari da kasancewarta ɗaya daga cikin mutanen da suke ba da gudunmawa ga rayuwar al’umma. Ina mai tabbatar da cewa zan ci gaba da kasancewa mai daraja da nagarta da aiki tuƙuru da sadaukarwar da wannan karramawa ta wakilta. Wannan zai ƙarfafa mun gwiwar ci gaba da aikin da nake kan gina Jihar Adamawa da Najeriya. Kuma zan halarci wajen ba da lambar a hukumance". Cewar gwamna Fintiri.

Hotuna: Yadda Jami’ar North West da ke Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai tare da karrama wasu fitattun mutane da s**...
26/07/2025

Hotuna: Yadda Jami’ar North West da ke Kano ta gudanar da bikin yaye ɗalibai tare da karrama wasu fitattun mutane da s**a taka rawar gani a fannoni daban-daban.

Cikin waɗanda Jami’ar ta karrama har da tsohon Gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, da fitaccen ɗan kasuwa marigayi Alhaji Aminu Dantata, da wasu da dama.

Umarni ya biyo bayan fushin da jama’a, s**a yi bayan ɓullar sunan Kwamishinan Sufuri, Alhaji Ibrahim Namadi Dala, da aka...
26/07/2025

Umarni ya biyo bayan fushin da jama’a, s**a yi bayan ɓullar sunan Kwamishinan Sufuri, Alhaji Ibrahim Namadi Dala, da aka gani a takardar neman belin wanda ya shahara da zargin safarar miyagun kwayoyi, Sulaiman Aminu Ɗanwawu.

Tuni Gwamna Yusuf, ya kafa kwamiti na musamman s ƙarƙashin jagorancin Aminu Hussain, Mai ba shi shawara na musamman kan harkokin Shari’a, don zurfafa bincike kan lamarin da kuma bayar da shawarwari kan matakan da ya kamata a ɗauka cikin gaggawa.

Attajirin Afirka, Alhaji Aliko Dangote, ya ajiye kujerarsa a matsayin shugaban hukumar gudanarwar kamfanin Dangote Cemen...
26/07/2025

Attajirin Afirka, Alhaji Aliko Dangote, ya ajiye kujerarsa a matsayin shugaban hukumar gudanarwar kamfanin Dangote Cement Plc, daga ranar 25 ga Yuli, 2025.

Wata sanarwa da kakakin kamfanin, Anthony Chiejina, ya fitar, ta bayyana cewa Dangote zai mayar da hankali sosai kan matatar mai, masana’antar sinadarai, takin zamani da kuma hulda da gwamnati, domin kara hanzarta ci gaban kasuwancin kamfaninsa cikin shekaru biyar masu zuwa.

Biyo bayan hakan, kamfanin ya sanar da Emmanuel Ikazoboh a matsayin sabon Shugaban Hukumar Gudanarwar kamfanin.
Ikazoboh na daya daga cikin manyan daraktoci masu zaman kansu a hukumar.

Hakazalika, Mariya Aliko Dangote ta samu shiga cikin Hukumar Gudanarwar kamfanin, yayin da Farfesa Dorothy Ufot ta yi murabus.

Duk Da Kasancewa Ta Shugabar Ƙasa Har Yanzu Ina Yi Wa Miji Na Wanki Da Girki, Inji Shugabar Ƙasar TanzaniyaShugabar ƙasa...
26/07/2025

Duk Da Kasancewa Ta Shugabar Ƙasa Har Yanzu Ina Yi Wa Miji Na Wanki Da Girki, Inji Shugabar Ƙasar Tanzaniya

Shugabar ƙasar Tanzaniya, Samia Saluhu Hassan, ta ce har yanzu tana girki da wanki na kayan mijinta, duk da kasancewarta shugabar ƙasa, matar aure, kuma uwa hakan bai sa ta bjire wa kyautata wa mijinta ba saboda kwaɗayin samun rahmar Ubangiji.

Me zaku ce?

Rundunar Sojin Sama ta ƙasar Qatar ta soke babban atisayen jiragen sama da aka shirya yi tare da Rundunar Sojin Sama ta ...
26/07/2025

Rundunar Sojin Sama ta ƙasar Qatar ta soke babban atisayen jiragen sama da aka shirya yi tare da Rundunar Sojin Sama ta Indiya — musamman da matukan jiragen Rafale — ba tare da bayyana dalili ba.

Lamarin ya bar tambayoyi masu yawa a zukatan masu sharhi kan harkokin tsaro.

🚨 LABARI YANZU-YANZU ⚡️ |Ƙasar Yemen ta sanar da kaddamar da manyan hare-hare guda huɗu (4) na soja da s**a nufi muhimma...
26/07/2025

🚨 LABARI YANZU-YANZU ⚡️ |
Ƙasar Yemen ta sanar da kaddamar da manyan hare-hare guda huɗu (4) na soja da s**a nufi muhimman wurare masu tsananin mahimmanci a cikin ƙasar Isra’ila.

Alamu na nuna rikicin na kara tsananta a Gabas ta Tsakiya.

Shugaba Putin ya gargadi ƙasar Jamus da kada ta tallafa wa Ukraine a yakin ta da Rasha.Sai dai Jamus ta ƙi karɓar wannan...
26/07/2025

Shugaba Putin ya gargadi ƙasar Jamus da kada ta tallafa wa Ukraine a yakin ta da Rasha.
Sai dai Jamus ta ƙi karɓar wannan gargadi, tana mai tabbatar da cewar za ta ci gaba da ba Ukraine cikakken goyon baya.

Rikicin ya ci gaba da ɗaukar sabon salo!

Netanyahu: Muna nazarin zaɓuɓɓuka daban-daban tare da haɗin gwiwar Amurkawa domin dawo da fursunoninmu da kuma kawo ƙars...
25/07/2025

Netanyahu: Muna nazarin zaɓuɓɓuka daban-daban tare da haɗin gwiwar Amurkawa domin dawo da fursunoninmu da kuma kawo ƙarshen mulkin Hamas.

Tun kafin aje ko'ina 'yan Kwankwasiyya sun ƙaryata zargin da Dan Bello ya yiwa gwamnatin Kwankwasiyya ta Abba Gida-Gida ...
25/07/2025

Tun kafin aje ko'ina 'yan Kwankwasiyya sun ƙaryata zargin da Dan Bello ya yiwa gwamnatin Kwankwasiyya ta Abba Gida-Gida da hujjoji cikin hotuna da bidiyoyi.

Address

Kano

Telephone

+2349042713230

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ayzan Multimedia posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share