Ayzan Multimedia

Ayzan Multimedia Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Ayzan Multimedia, Broadcasting & media production company, Kano.

AYZAN MULTIMEDIA
Gidan jarida ne na zamani da ke kawo Labaran Duniya, Iliman-Tarwa, Ni Shadan-Tarwa, da Tarihi domin faɗakar da zukata, gyara halaye, da gina al’umma bisa gaskiya da ilimi.

Fadar shugaban kasa ta tabbatar wa ’yan Najeriya cewa hauhawar farashin kaya (inflation) a kasar zai ci gaba da sauka, h...
16/09/2025

Fadar shugaban kasa ta tabbatar wa ’yan Najeriya cewa hauhawar farashin kaya (inflation) a kasar zai ci gaba da sauka, har ya kai zuwa kasa da kaso goma cikin dari wato single digit.

Mai ba Shugaban Kasa shawara kan harkokin tattalin arziki, Tope Fasua, ne ya bayyana haka a shirin The Morning Brief na Channels TV a ranar Talata.

Fasua ya ce saukar da aka samu a adadin hauhawar farashin kaya ya riga ya fara tasiri a kan farashin kayan abinci, wanda ya fara sauka a kasuwanni.

Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ta fitar da sabbin alkaluma a ranar Litinin, inda ta nuna cewa hauhawar farashin kaya ya sauka zuwa 20.12% a watan Agusta 2025, idan aka kwatanta da kashi 21.88% a watan Yuli 2025.

Ƙungiyar Shugabannin Hukumomin Jin Dadin Alhazai ta Jihohin Nijeriya ta bukaci hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya (...
16/09/2025

Ƙungiyar Shugabannin Hukumomin Jin Dadin Alhazai ta Jihohin Nijeriya ta bukaci hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya (NAHCON) da ta gaggauta kammala daidaita bayanan kuɗaɗen da aka kashe Hajjin 2025 kafin ta shiga cikakken shirin na 2026.

A cikin wata wasiƙa da Shugaban ƙungiyar, Ahmed Idris Al-Makura, da Sakataren ƙungiyar, Abubakar Salihu, s**a sanya hannu, sun yaba da yadda NAHCON ke haɗa jihohi a shirin hajji, amma sun nuna damuwa game da jinkirin maidawa mahajjata kuɗaɗensu da kuma wasu hakkoki.

Ƙungiyar ta ce akwai mahajjata da s**a daɗe sama da shekaru biyu ana riƙe musu kuɗi, abin da zai iya kawo cikas wajen haɗa waɗanda aka jinkirta zuwa tsarin Hajjin 2026.

“Ba daidai ba ne a buɗe lissafin hajjin 2026 ba tare da rufe na 2025 ba. Wannan na iya haifar da ruɗani da wahalar aiki,” in ji ƙungiyar.

Kotu ta daure wani dan Nijeriya a Amurka bisa samunsa da laifin zambar kudin gado Dala milyan 6
16/09/2025

Kotu ta daure wani dan Nijeriya a Amurka bisa samunsa da laifin zambar kudin gado Dala milyan 6

Gwamnatin jihar Katsina ta umurci da a fitar da buhunan hatsi 90,000 don yakar tamowa a fadin jiharGwamnan jihar Malam D...
15/09/2025

Gwamnatin jihar Katsina ta umurci da a fitar da buhunan hatsi 90,000 don yakar tamowa a fadin jihar

Gwamnan jihar Malam Dikko Radda ya ce za a raba wannan kayan abinci ne ga iyalan da yaransu ke fama da tamowa.

Yanzu yanzu: Ƙasar Spain ta sanar da soke kwangilar sayen makamai na Euro miliyan 700 daga Isra'ila saboda hare-haren da...
15/09/2025

Yanzu yanzu: Ƙasar Spain ta sanar da soke kwangilar sayen makamai na Euro miliyan 700 daga Isra'ila saboda hare-haren da take ci gaba da kaiwa a zirin Gaza.

Yadda manyan mutane masu rike da mukamai a Nijeriya 'yan asalin jihar Katsina s**a hadu domin nemo mafitar rashin tsrao ...
15/09/2025

Yadda manyan mutane masu rike da mukamai a Nijeriya 'yan asalin jihar Katsina s**a hadu domin nemo mafitar rashin tsrao da bunkasa ilimi a Katsina

Sakataren gwamnatin Najeriya George Akume ya baiyana cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta yi himma wurin magance matsalar...
15/09/2025

Sakataren gwamnatin Najeriya George Akume ya baiyana cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta yi himma wurin magance matsalar rashin aikin yi da inganta rayuwar ‘yan Nijeriya.

Akume, a lokacin da sabbin shugabannin kungiyar matasa ta Nijeriya NYC, ƙarƙashin jagorancin Kwamared Jethro Annum s**a kai masa ziyara a Abuja ya jaddada cewa shugaban kasa ya ƙaddamar da manufofi da tsare-tsaren da za su rage radadin rayuwa tare da samar da damar ci gaba ga matasa.

Da Dumi-DumiMatatar mai ta Dangote ta ƙaddamar da motocin CNG don rarraba man fetur a faɗin Nijeriya a Litinin ɗinnan.Wa...
15/09/2025

Da Dumi-Dumi

Matatar mai ta Dangote ta ƙaddamar da motocin CNG don rarraba man fetur a faɗin Nijeriya a Litinin ɗinnan.

Wannan shiri zai rage tsadar jigilar mai tare da taimaka wa ƙananan masana’antu da kamfanoni sama da miliyan 42 wajen rage kuɗin gudanarwa, inji matatar.

YANZU-YANZU: Shugaban Kasar IRAN Ya Sauka a Doha Babban birnin Qatar don halartar wani taron gaggawa na shugabannin kasa...
15/09/2025

YANZU-YANZU: Shugaban Kasar IRAN Ya Sauka a Doha Babban birnin Qatar don halartar wani taron gaggawa na shugabannin kasashen Musulmi da Larabawa, wanda aka shirya don tattauna harin da Isra’ila ta kai kan Qatar.

Kasashe 50 Zuwa 57 Ake Saran Zasu Halarci Wannan Taron Da Za a Gudanar Yau Litinin. Babban manufarsa ta zuwa taron Shi ne kare matsayin Iran da nuna goyon baya ga Qatar kan wannan harin na Ise-ra-ila.

Da kuma Ankarar da Shugabannin kasashen Musulmai su ɗauki matakai na haɗin kai da kuma tsayawa kai da fata wajen adawa da irin waɗannan hare-hare. Yace lokaci ya yi da magana ba ta wadatar wa, Sai anyi aiki wajen kare hakkokin ƙasashen musulmi.

Shugaban Amurka Donald Trump ya sake jaddada goyon bayansa ga Qatar, bayan harin saman da Isra’ila ta kai kan wasu shuga...
15/09/2025

Shugaban Amurka Donald Trump ya sake jaddada goyon bayansa ga Qatar, bayan harin saman da Isra’ila ta kai kan wasu shugabannin Hamas a birnin Doha makon da ya gabata.

A yayin da yake magana da manema labarai, Trump ya ce:
"Qatar ta kasance babbar abokiyar hulɗa gare mu. Isra’ila da kowa baki ɗaya, dole mu yi taka-tsantsan. Idan za mu kai hari kan wani.

"Wasu mutane da dama ba su fahimci Qatar sosai ba. Qatar babban abokiyar harkokin mu ne, kuma suna rayuwa cikin ƙalubale ne sosai, saboda suna tsakiyar ƙasashe masu rikice-rikice."

Trump ya ce zai sake kakabawa kasar China haraji kashi 100 idan ta cigaba da sayen man ƙasar Rasha.
15/09/2025

Trump ya ce zai sake kakabawa kasar China haraji kashi 100 idan ta cigaba da sayen man ƙasar Rasha.

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya ce cire tallafin man fetur da Gwamnatin Tarayya ta yi shi ne mafi alheri ga Najeriya....
15/09/2025

Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II ya ce cire tallafin man fetur da Gwamnatin Tarayya ta yi shi ne mafi alheri ga Najeriya.
Amma ya ce yawan ciwo bashin da take yi, da kuma yadda take facaka da kuɗaɗen zai jefa ƙasar cikin matsalar tattalin arziki na tsawon shekaru.

Mene ne ra'ayinku?

Address

Kano

Telephone

+2349042713230

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Ayzan Multimedia posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share