GAZE TV HAUSA

GAZE TV HAUSA Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from GAZE TV HAUSA, TV Channel, Kano.

Muna sake taya Ambassador Aliyu Binn Abbas murnar fitowarsa a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar Action Dem...
30/05/2026

Muna sake taya Ambassador Aliyu Binn Abbas murnar fitowarsa a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar Action Democratic Party (ADP), tare da tabbatar masa da cikakken goyon bayanmu yayin da yake ci gaba da fafutukar ci gaban ƙasa da shigar da matasa cikin harkokin mulki.
Allah Ya sanya wannan nasara ta zama mafarin sabon babi na fata, ci gaba da ɗaukakar Najeriya.labarin GAZE TV NEWS HAUSA

ASSALAMUALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUHU YAN UWA  DA ABOKAN  ARZIQI  INAIWA KOWA BARKA DA SALLAH ALLAH YA KARBA  MANA...
27/05/2026

ASSALAMUALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUHU YAN UWA DA ABOKAN ARZIQI INAIWA KOWA BARKA DA SALLAH
ALLAH YA KARBA MANA IBADUNMU.data GAZE TV NEWS HAUSA

Lamine Yamal ya jawo muhawara sosai bayan ya daga tutar Palestine yayin bikin lashe kofin La Liga da FC Barcelona ta yi ...
15/05/2026

Lamine Yamal ya jawo muhawara sosai bayan ya daga tutar Palestine yayin bikin lashe kofin La Liga da FC Barcelona ta yi bayan doke Real Madrid. Hotunan da aka yada daga faretin kungiyar sun bazu sosai a intanet, inda wani rubutu a Instagram ya samu miliyoyin martani tare da sake tada muhawara kan nuna ra’ayin siyasa a harkar kwallon kafa.
Tsohon kocin Barcelona, Pep Guardiola, ya kare matashin ɗan wasan inda ya ce:
“Lamine ya kamata ya yi alfahari da abin da ya yi.”
Guardiola ya kara da cewa ‘yan kwallon kafa mutane ne da suke zama abin koyi ga jama’a, kuma suna da babbar dama ta isar da ra’ayoyinsu idan ya zama dole.
Kocin Barcelona na yanzu, Hansi Flick, ya ce bai goyi bayan haɗa siyasa da kwallon kafa ba, amma ya amince cewa Yamal ya isa girman da zai iya yanke shawarar kansa.labarin GAZE TV NEWS HAUSA

Innalillahi Wa'inna ilaihi Raji'un!!! Allah ya yiwa Tahir Muhammad Egu Rasuwa Fatan Allah yaji kansa da Rahama 😭🙏Ameen y...
05/05/2026

Innalillahi Wa'inna ilaihi Raji'un!!!
Allah ya yiwa Tahir Muhammad Egu Rasuwa Fatan Allah yaji kansa da Rahama 😭🙏
Ameen ya Hayyu ya Qayyum labarin GAZE TV NEWS HAUSA

Matasa Su Tashi Domin  Dimokuraɗiyyar Najeriya  NYA Ta Yi Kira Najeriya na cikin mawuyacin hali Sanata Gumba ya yaba da ...
05/04/2026

Matasa Su Tashi Domin Dimokuraɗiyyar Najeriya NYA Ta Yi Kira
Najeriya na cikin mawuyacin hali Sanata Gumba ya yaba da kishin ƙasa na NYA
Bauchi, Najeriya — 5 ga Afrilu, 2026
Shugaban National Youth Alliance (NYA), Ambasada Aliyu Bin Abbas, ya yi kira ga matasan Najeriya da su tashi tsaye da jarumtaka, haɗin kai, da kyakkyawan buri domin kare dimokuraɗiyyar ƙasa da makomarta.
An yi wannan kira ne a yayin taron karawa juna sani na NYA mai taken “Haifar da Sabuwar Najeriya”, tare da rantsar da masu kula da ƙananan hukumomi 112 na shiyyar Arewa maso Gabas, wanda aka gudanar a Jihar Bauchi.
A cikin jawabinsa, Ambasada Abbas ya bukaci matasa su kasance masu ladabi, gaskiya, da sadaukarwa ga aikin ƙasa, yana mai jaddada cewa alhakin sake gina da farfaɗo da Najeriya yana hannun matasa.
Ya ce: “Najeriya na cikin wani mawuyacin lokaci. Dole ne mu tashi tsaye da ƙuduri da hangen nesa guda domin ceton ƙasarmu da kuma mayar da ita kan turbar da ta dace.”
Ya kuma jaddada muhimmancin shigar matasa cikin shugabanci da harkokin mulki, yana mai cewa lokaci ya yi da sabon ƙarni zai ɗauki nauyin kare dimokuraɗiyya da kuma ci gaba da sadaukarwar jaruman ƙasa na baya.
Baƙon mai jawabi, Sanata Adamu Ibrahim Gumba, ya yaba wa NYA bisa hangen nesa da kishin ƙasa da take nunawa wajen sauya fasalin Najeriya. Ya kuma ƙarfafa gwiwar mambobi da su shiga harkokin siyasa tare da aiki a cikin ingantattun tsare-tsare domin samar da sauyi mai ɗorewa.
Haka zalika, Kwamishinar Jinƙai ta Jihar Bauchi, Hajara Yakubu Wanka, ta bayyana fata mai kyau kan rawar da matasa za su taka wajen gina ƙasa, tana mai cewa haɗin kai, jajircewa, da hangen nesa na matasa za su kai Najeriya ga ci gaba mai dorewa.
Wannan taro ya zama wani babban mataki a ƙoƙarin NYA na haɗa kai, ƙarfafa gwiwa, da kuma bai wa matasan Najeriya dama domin gina ƙasa mai cike da adalci, ci gaba, da dimokuraɗiyya mai ƙarfi.labarin GAZE TV NEWS HAUSA

04/04/2026

YANZU-YANZU: Mutum sama da miliyan 3 ne s**a fita domin taro gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf a yau asabar. Rahotanni sun ce ba a taɓa taron siyasa a Kano wanda ya tara miliyoyin mutane irin na yau ba. Kano ba masaka tsinke ko'ina ka shiga mutane ne birjik kai ka ce akwai aljanu a taron.

Anya kuwa akwai ɗan siyasa mai tarin masoya a Kano kamar Abba Gida-gida.labarin GAZE TV NEWS HAUSA

YANZU-YANZU: Mutum sama da miliyan 3 ne s**a fita domin taro gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf a yau asabar. Rahotanni sun c...
04/04/2026

YANZU-YANZU: Mutum sama da miliyan 3 ne s**a fita domin taro gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf a yau asabar. Rahotanni sun ce ba a taɓa taron siyasa a Kano wanda ya tara miliyoyin mutane irin na yau ba. Kano ba masaka tsinke ko'ina ka shiga mutane ne birjik kai ka ce akwai aljanu a taron.

Anya kuwa akwai ɗan siyasa mai tarin masoya a Kano kamar Abba Gida-gida.labarin GAZE TV NEWS HAUSA

Alhamdulillah! Yau rana ce ta farin ciki da murna ƙwarai.Ina miƙa godiya ta musamman ga al’ummar Nassarawa Local Governm...
28/03/2026

Alhamdulillah! Yau rana ce ta farin ciki da murna ƙwarai.
Ina miƙa godiya ta musamman ga al’ummar Nassarawa Local Government da kuma Jihar Kano baki ɗaya bisa irin ƙauna, girmamawa, da tarbar da kuka yi mini—tun daga filin jirgin sama har zuwa gidana—bayan dawowata daga aikin Umrah a ƙasar Saudiyya.
Yawan fitowar dubban magoya baya ya nuna a fili cewa al’ummata suna tare da ni tsayin daka. Wannan haɗin kai da goyon baya yana da matuƙar muhimmanci a gare ni, kuma ba zan taɓa ɗaukar sa da wasa ba.
Haka kuma, ya bayyana cewa kuna tsayawa kai da fata tare da Mai Girma Gwamna Abba Kabir Yusuf, da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, tare da jam’iyyarmu mai girma ta All Progressives Congress (APC).
Allah Maɗaukakin Sarki Ya ci gaba da saka muku da alheri mai yawa. Tare za mu ci gaba da aiki domin haɗin kai, zaman lafiya, da cigaban al’ummarmu.
Na gode ƙwarai 🤝
Amb. Yusuf Imam Oganboye
Shugaban Ƙaramar Hukumar Nassarawa
Mataimakin ALGON Kano Central.labarin GAZE TV NEWS HAUSA

Barka da Sallah (Eid Mubarak)Ya Allah ka maimaita mana wannan rana cikin alheri, arziki da albarkaAllah ya karɓa mana az...
20/03/2026

Barka da Sallah (Eid Mubarak)
Ya Allah ka maimaita mana wannan rana cikin alheri, arziki da albarka
Allah ya karɓa mana azumi, tsayuwar dare da dukkan ayyukan alheri
Muna roƙon Allah ya sake maimaita mana da ku cikin lafiya, farin ciki da wadata daga.GAZE TV NEWS HAUSA

Ebrahim Zolfaghari, mai magana da yawun hedikwatar sojojin Khatam al-Anbiya Central Headquarters ta Iran, ya ce kasancew...
16/03/2026

Ebrahim Zolfaghari, mai magana da yawun hedikwatar sojojin Khatam al-Anbiya Central Headquarters ta Iran, ya ce kasancewar jirgin ruwan yaki na Amurka USS Gerald R. Ford a cikin Red Sea ana kallonsa a matsayin barazana ga Iran.
A cewarsa, duk cibiyoyin tallafi da ayyukan sabis da ke taimaka wa wannan jirgin ruwan yaki na Amurka za su iya zama wurin da Iran za ta kai hari idan rikicin ya ci gaba. Wannan bayanin ya fito ne ta hanyar kamfanin dillancin labarai na Iran Fars News Agency.
The Current
Wannan magana na zuwa ne a lokacin da rikicin tsakanin Iran, Amurka da Isra’ila ke kara tsananta a yankin Gabas ta Tsakiya, yayin da jiragen ruwan yaki na Amurka s**a fara shiga yankin domin nuna karfin soja.labarin GAZE TV NEWS hAUSA

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when GAZE TV HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category