31/10/2025
Hukumar Cigaban Arewa maso Yamma (NWDC) da raya kogunan Hadejia-Jama’are sun kulla yarjejeniyar hadin gwiwa domin inganta harkar noma a yankin Arewa maso Yamma.
An kulla yarjejeniyar ne yayin ziyarar da Shugaban Hukumar NWDC, Farfesa Shehu Abdullahi Ma’aji, ya kai hedkwatar hukumar Koda ke Kano a ranar Laraba.
Farfesa Ma’aji da tawagarsa sun samu tarba daga Manajan Darakta na hukumar kogunan Hadejia-Jama'are, Injiniya Rabiu Suleiman Bichi da Daraktan Kudi, Musa Ilyasu Kwankwaso da wasu jami’an hukumar.
A lokacin ziyarar, Farfesa Ma’aji ya yi bayani kan manufar hukumar NWDC tare da neman izinin amfani da filayen noma domin jawo hankalin masu zuba jari a harkar noma da bunkasa tattalin arziki a yankin.
Da yake magana, Injiniya Bichi ya nuna farin ciki da hadin gwiwar, inda ya jaddada cewa jihohin Kano da Jigawa kadai suna da tanadin ruwa sama da cubic metres miliyan 2.4 da kuma filayen noma sama da hektar miliyan 2.1, yayin da hukumar HJRBDA ke kula da hektar 22,000 kai tsaye.
Ya bayyana wasu shirye-shirye da ake aiwatarwa, ciki har da horas da matasa sama da 1,000 kan noman greenhouse, tura ma’aikatan gona 500 a matsayin masu ba da shawara da kuma samar tuƙa-tuƙa, tsarin ban ruwa na rani da sabbin fasahohin noma na zamani.
Dukkanin hukumomin biyu sun amince da kafa tsarin hadin kai na dindindin domin karfafa zuba jari, musayar fasaha, da ci gaban noma mai dorewa a yankin Arewa maso Yamma.