FMA News

FMA News Ku turo mana saƙon abinda ke faruwa a yankunanku ta Whatsapp a kan: 08107929320

An samar da wannan kafar ta FMA ne domin kawo mu ku sahihan labarai na abinda ke faruwa a Najeriya da ma sassan duniya ba tare da tauye bayanai, yin ƙage, ko wariya ba.

24/11/2025

Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima Yana Wakiltar Shugaba Tinubu a Taron AU–EU a Angola

Kashim Shettima yana halartar Taron Kolin AU–EU karo na 7 a New Protocol Hall da ke birnin Luanda na ƙasar Angola.

Wannan muhimmin taro na manyan shugabannin Afirka da Turai, wanda gwamnatin Angola ta dauki nauyinsa,zai gudana ne tsawon kwanaki biyu inda za a tattauna manyan batutuwa na ƙasa da ƙasa, mai taken Inganta Zaman Lafiya da Ci Gaba ta Hanyar Gaskiya da Haɗin Kai a Duniya.

Shugabannin ƙasashe suna musayar ra’ayoyi domin haɓaka dangantaka da haɗin gwiwa tsakanin nahiyoyin Afirka da Turai.

12/11/2025

Haɗuwar Kwankwaso da Ganduje a wajen ta’aziyyar rasuwar mahaifiyar tsohon gwamnan jihar Bauchi, Ahmad Adamu Mu’azu.

07/11/2025

Sanata Barau ya musanta zargin da ake yi masa cewa yana ƙoƙarin hana tabbatar Engr. Abdullahi Garba Ramat a matsayin shugaban hukumar kula da wutar lantarki ta ƙasa NERC.

Mai magana da yawun sanatan, Sh*tu Madaki Ƙunci ne ya musanta hakan a wani taron manema labarai yau Juma'a.

04/11/2025

Cacar baki tsakanin shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio da mataimakinsa, Barau Jibrin akan batun barazanar Trump ga Najeriya.

Marubuciya Fauziyya D Sulaiman ce ta tabbatar da rasuwar tasa a shafinta na Facebook.
02/11/2025

Marubuciya Fauziyya D Sulaiman ce ta tabbatar da rasuwar tasa a shafinta na Facebook.

Shugaba Tinubu zai gana da Trump ba da jimawa ba, in ji Daniel Bwala
02/11/2025

Shugaba Tinubu zai gana da Trump ba da jimawa ba, in ji Daniel Bwala

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar daukar matakin soji akan Najeriya, yana mai zargin gwamnatin kasar da kyale...
02/11/2025

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar daukar matakin soji akan Najeriya, yana mai zargin gwamnatin kasar da kyalewa ana kashe kiristoci.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Mista Trump ya ce Washington na iya shiga Najeriya da ƙarfin soji don kakkaɓe abin da ya kira ƴanta'adda masu kishin Islama da ke aikata ta'asa.

Ya kuma yi barazanar dakatar da duk wani taimakon Amurka ga Najeriya.

Yadda aka yi bikin bankwana da tsohon babban hafsan sojin Najeriya, Janar Christopher Musa bayan shugaban ƙasa Bola Ahme...
31/10/2025

Yadda aka yi bikin bankwana da tsohon babban hafsan sojin Najeriya, Janar Christopher Musa bayan shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ritayarsa.

Musa ya cika shekaru 38 yana aikin soja.

Hukumar Cigaban Arewa maso Yamma (NWDC) da raya kogunan Hadejia-Jama’are sun kulla yarjejeniyar hadin gwiwa domin ingant...
31/10/2025

Hukumar Cigaban Arewa maso Yamma (NWDC) da raya kogunan Hadejia-Jama’are sun kulla yarjejeniyar hadin gwiwa domin inganta harkar noma a yankin Arewa maso Yamma.

An kulla yarjejeniyar ne yayin ziyarar da Shugaban Hukumar NWDC, Farfesa Shehu Abdullahi Ma’aji, ya kai hedkwatar hukumar Koda ke Kano a ranar Laraba.

Farfesa Ma’aji da tawagarsa sun samu tarba daga Manajan Darakta na hukumar kogunan Hadejia-Jama'are, Injiniya Rabiu Suleiman Bichi da Daraktan Kudi, Musa Ilyasu Kwankwaso da wasu jami’an hukumar.

A lokacin ziyarar, Farfesa Ma’aji ya yi bayani kan manufar hukumar NWDC tare da neman izinin amfani da filayen noma domin jawo hankalin masu zuba jari a harkar noma da bunkasa tattalin arziki a yankin.

Da yake magana, Injiniya Bichi ya nuna farin ciki da hadin gwiwar, inda ya jaddada cewa jihohin Kano da Jigawa kadai suna da tanadin ruwa sama da cubic metres miliyan 2.4 da kuma filayen noma sama da hektar miliyan 2.1, yayin da hukumar HJRBDA ke kula da hektar 22,000 kai tsaye.

Ya bayyana wasu shirye-shirye da ake aiwatarwa, ciki har da horas da matasa sama da 1,000 kan noman greenhouse, tura ma’aikatan gona 500 a matsayin masu ba da shawara da kuma samar tuƙa-tuƙa, tsarin ban ruwa na rani da sabbin fasahohin noma na zamani.

Dukkanin hukumomin biyu sun amince da kafa tsarin hadin kai na dindindin domin karfafa zuba jari, musayar fasaha, da ci gaban noma mai dorewa a yankin Arewa maso Yamma.

Shugaban kwamitin tsaron cikin gida na majalisar wakilai, Garba Muhammad Ɗiso, ya ce sun samu barazana daga yan ta’adda ...
28/10/2025

Shugaban kwamitin tsaron cikin gida na majalisar wakilai, Garba Muhammad Ɗiso, ya ce sun samu barazana daga yan ta’adda cewa za su kai hari da bama-bamai a ginin majalisar.

Ya bayyana hakan ne a yayin zaman sauraron ra’ayoyin jama’a kan kudirin dokar kafa hukumar tsaron majalisar dokoki wadda ke da nufin inganta tsarin tsaro da kare yan majalisa, ma’aikata da baki da ke zuwa majalisar.

A cewarsa, majalisar ta dade tana fama da matsalolin tsaro da s**a hada da satar motoci da babura, lalata kayan gwamnati, yin amfani da katin karya da kuma shigowar baki marasa rajista cikin harabar majalisar.

Dan majalisar ya ce akwai gaggawar bukatar karfafa tsaron majalisar don hana faruwar abin da ka iya haifar da matsala ga tsarin dimokuradiyya.

Jam’iyyar PDP ta mayar da martani ga tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, kan barazanarsa na kai jam’iyyar kara kot...
28/10/2025

Jam’iyyar PDP ta mayar da martani ga tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, kan barazanarsa na kai jam’iyyar kara kotu bisa zargin hana shi fom shiga takarar shugabancinta.

Mataimakin mai magana da yawun jam’iyyar na kasa Ibrahim Abdullahi ne ya bayyana haka an Abuja.

Ya ce Sule Lamido ya je Wadata Plaza wato shalkwatar jam’iyyar maimakon Legacy House, inda ake sayar da fom din a hukumance, kuma ya yi kokarin kirkirar hayaniya ce kawai don jawo hankalin jama’a.

Jami’in ya kuma ce, jam’iyyar na da niyyar ci gaba da gyara matsalolinta duk da kokarin da wasu ke yi na kawo cikas.

Ya kara da cewa, PDP ba za ta bari wasu masu neman rigima su kawo tangarda ga shirye-shiryen gudanar da babban taron jam’iyyar da aka shirya gudanarwa a Ibadan dake jihar Oyo ba, cikin watan Nuwambar 2025.

A makon da ya gabata ne dai gwamnonin PDP s**a nuna goyon bayansu ga tsohon ministan ayyuka na musamman, Kabiru Turaki a matsayin dan takarar shugaban jam’iyyar da suke marawa baya.

Abind ya sa Abdullahi ya bayyana cewa zaɓen Tanimu Turaki a matsayin ɗan takarar maslaha na shugabancin jam’iyyar, ya biyo bayan tsarin tarihi da PDP ke bi, inda gwamnoni da manyan jiga-jigan jam’iyya ke yanke hukunci tare.

A ranar Litinin ne dai, tsohon gwamnan Sule Lamido, ya yi barazanar ne bayan an ki sayar masa da fom din takarar kujerar shugaban jam’iyyar na kasa.

28/10/2025

Sanata Barau Jibrin ya gana da sabbin jami’an ƴansanda da ya samarwa aiki.

Address

Kano
KANO

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when FMA News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share