06/07/2026
MALAMIN ILMIN TAURARI YA FITAR DA HASASHEN ABUBUWAN DA YA CE ZA SU IYA FARUWA A IRAKI KAFIN ƘARSHEN NUWAMBA 2026
Daga Sokoto, Najeriya.
Wani malamin ilmin taurari, Sheikh Abubakar Malam Umar Maisanda, ya fitar da abin da ya bayyana a matsayin hasashen wasu abubuwan da ya ce za su iya faruwa a ƙasar Iraki tsakanin ranar 6 ga Yuli zuwa 30 ga Nuwamba, 2026.
A cikin sanarwar da ya wallafa a shafinsa, Abubakar Maisanda ya ce hasashen nasa ya samo asali ne daga abin da yace Allah Ya bayyana masa, tare da abin da ya danganta da ƙa'idar ilmin taurari.
Ga abubuwan da ya yi hasashen za su iya faruwa:
1. Jam'iyyar da ke mulki za ta iya fuskantar manyan matsaloli da rikice-rikice a cikin harkokinta.
2. Iraki na iya fuskantar ƙalubalen tsaro da fitintinu, ko dai sak**akon rikicin siyasa ko kuma yaƙi. Haka kuma, ya yi kira ga gwamnatin ƙasar da ta ƙara ƙaimi wajen tsaurara matakan tsaro, yana mai cewa za a samu nasarar k**a wasu da ake zargi da aikata ta'addanci.
3. Ya kuma yi hasashen yiwuwar samun hatsurran jiragen sama, ko dai sak**akon hare-haren ta'addanci ko wasu matsalolin da s**a shafi harkokin sufurin jiragen sama.
4. A cewarsa, kafin ranar 30 ga Nuwamba, 2026, ana iya samun sauyin gwamnati ta hanyar juyin mulki ko kuma a k**a shugaban ƙasar. Ya buƙaci hukumomin Iraki su ƙara taka-tsantsan tare da ɗaukar matakan da s**a dace domin tabbatar da zaman lafiya.
5. Haka kuma, ya ce wasu baƙi daga wata ƙasa za su shiga Iraki, lamarin da ya yi iƙirarin cewa na iya haifar da tashin hankali da asarar rayuka. Saboda haka, ya shawarci hukumomi su ƙara sa ido kan masu shiga ƙasar.
6. Maisanda ya kuma yi hasashen cewa wasu 'yan ƙasar za su yi hijira sak**akon matsalolin da ka iya tasowa, yayin da ake iya korar wasu baƙi da ba 'yan ƙasar ba.
7. Ya ƙara da cewa ana iya gudanar da bincike kan wasu manyan mutane a ƙasar, inda za a ƙwace wasu kadarori da kuɗaɗe tare da tsare wasu daga cikinsu.
8. A ƙarshe, ya yi hasashen cewa za a iya samun zanga-zanga a wasu sassan Iraki kafin ƙarshen watan Nuwamba, 2026.
A Lura: Wannan hasashe ra'ayi ne da iƙirarin wanda ya fitar da shi, kuma ba hujja ce da ke tabbatar da cewa abubuwan da aka ambata za su faru ba.
Wane fata kuke yi wa ƙasar Iraki da al'ummarta?