24/06/2026
MARTANI: 'Ýan Arewa Sune Màțšalar Nijeriya, Domin Sune Yañ Bindigà, Sune Mabarata Sannan Kuma Sune Baŕayin Daji, Inji VeŕyDarkMan
..Yunƙurin Faɗin Gaskiya Bazaisa Ya zagi Duk Iyayenmu, Muyi shiru ba...........
Na kalli wani sashe na bidiyon ɗan gwagwarmayar Kudancin Najeriya, wato verydarkman, inda yace 'yan Arewa sune suke mayar da Najeriya baya, yayi maganganu masu kaushi, dakuma sosa zuciya, amma idan za'ayi adalci akwai ƙamshin gaskiya akan abinda ya faɗa, akwai kuma inda yayi kuskure dayawa wanda Zamuyi masa gyara.
Inda yayi kuskure shine, daya hade Hausawa gaba ɗaya, kuma ya ware ƙabilar Hausawa ya ɗora mata laifi, ya manta cewa a kowacce ƙabila akwai nagari kuma akwai ɓata gari.
Cikin maganarsa yace Bahaushe yana tasowa ne, dan ya koyi sana'ar barace-barace, sai sana'ar gadi, wankin takalmi, suya dakuma shayi, naji taƙaicin wannan kalaman, amma a wannan ɓangaren yanada hujja, domin sune irin mutanen da yafi gani a can kudancin Najeriya, duk da cewa munada manyan malamai, yan kasuwa dakuma fitattun mutane a duniya. Wannan ya faru ne saboda sakacin na shugabannin Arewa das**a kasa tsayawa wajen gina wannan yankin namu, sai shegiyar sata, anan Arewa ne fa mutum ɗaya fa ake zargin ya sace 210 Tiriliyan, wannan kuɗin ya isa magance 60% na matsalolin Arewa.
Muna goyon Bayan faɗin Gaskiya, amma bazamu bari a fake da haka a zagemu ba, yan Arewa sunada ilmi, sunada daraja, Hausawa sunada ƙima, kuma sunada ilmi, laifi kuma ba'a alaƙantashi da wata ƙabila guda ɗaya.
Ga wasu abubuwa dashi verydarkman ya Manta:
•Ya manta cewa wanda yafi kowa kuɗi a Afrika Bahaushe ne kuma ɗan Arewa.
•Ya Manta cewa kaso 75 na 'yan ta'adda ba Hausawa bane, Fulani ne.
•Ya manta cewa Kaso 75 na B©ko H@ram Kanuri ne Ba Hausawa bane.
•Ya manta cewa a kudancin Najeriya jihar sa ta edo, tana cikin jihohi marasa zaman lafiya, dan haka ba Hausawa ne matsalar NAJERIYA ba, ba wata ƙabila da za'a ɗorawa laifi, tsari ne yazo da haka, dakuma rashin kyakkyawan shugabanci.
Idan ka Yarda Da duk Abinda Ya Faɗa Ga abinda Hakan Yake nufi;
•Kenan duk Hausawa, malamai Iyayenmu, da mutanen kirki cikinmu jahilai ne kamar yadda ya faɗa?
•Yace Hausawa na haihuwar yara domin su zubar dasu, wanda Ni dakai duk Bama cikinsu.
•Yace Hausawa basu iya komai ba, sai gadi, da goge takalmi, alhalin munada dukkanin rukunin mutane masu basira, a fadin Duniya.
Laifi bana ƙabila ɗaya bane, na mutane ne, wanda cikin kowacce ƙabila akwai wanda yake s**an abinda suke aikatawa.
Zanso kalamansa su Zaburar da shugabannin Arewa, dakuma 'yan Arewa wajen gina yankin mu, dakuma rage masu barace-barace, hakan zai ragewa irinsu samun damar zaginmu.
Allah Ya raya mana Arewa, Allah Ya bamu tsaro mai ɗorewa.
Daga: Abubakar Shehu Dokoki