Prime News Hausa

Prime News Hausa Prime News Hausa – inda gaskiya ke magana.

Tinubu Ya Sa A Binciki Google, Meta da X Kan Zargin Amfani da Labaran Nijeriya Ba Tare da Izini BaShugaban Ƙasa, Bola Ah...
06/07/2026

Tinubu Ya Sa A Binciki Google, Meta da X Kan Zargin Amfani da Labaran Nijeriya Ba Tare da Izini Ba
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ba da umarni ga Federal Competition and Consumer Protection Commission (FCCPC) da ta gudanar da cikakken bincike kan manyan kamfanonin fasaha na duniya, ciki har da Google, Meta, X da wasu kamfanonin AI.
Ana zargin kamfanonin da amfani da labarai da sauran ayyukan jarida na kafafen yaɗa labarai na Nijeriya wajen gudanar da harkokinsu ba tare da izini ko biyan haƙƙin masu wallafa ba. Wannan mataki ya biyo bayan ƙorafin haɗin gwiwa da ƙungiyoyin kafafen yaɗa labarai s**a kai wa fadar shugaban ƙasa.
Ƙungiyoyin da s**a gabatar da ƙorafin sun haɗa da Newspaper Proprietors' Association of Nigeria (NPAN), Nigeria Union of Journalists (NUJ), Broadcasting Organisations of Nigeria (BON) da Guild of Corporate Online Publishers (GOCOP).
An bayyana cewa umarnin ya isa FCCPC ne ta hannun Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, inda aka buƙaci hukumar ta binciki ko an karya dokokin gasa, haƙƙin mallakar fasaha da kuma haƙƙin masu wallafa labarai.

SANARWABabbar Hukumar Zaɓe ta Ƙasa ta sake ƙara wa'adin yin sabon katin zaɓe ga waɗanda ba su taɓa yin rajista ba.A yanz...
03/07/2026

SANARWA

Babbar Hukumar Zaɓe ta Ƙasa ta sake ƙara wa'adin yin sabon katin zaɓe ga waɗanda ba su taɓa yin rajista ba.

A yanzu, za a ci gaba da yin rajistar katin zaɓe har zuwa 24 ga watan Yuli, 2026.

Idan har yanzu ba ka yi rajistar katin zaɓenka ba, ka yi amfani da wannan damar kafin wa'adin ya cika.

Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Hukuncin Dauri Ga ’Yan Ta’adda 1,721 Tun Daga 2017 – ONSAOfishin Mai Bai wa Shugaban Ƙ...
02/07/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Samu Nasarar Hukuncin Dauri Ga ’Yan Ta’adda 1,721 Tun Daga 2017 – ONSA

Ofishin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Harkokin Tsaro (ONSA) ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta samu nasarar tabbatar da laifin ta’addanci ga mutum 1,721 tun bayan fara shirin shari’a kan masu laifukan ta’addanci a watan Oktoban shekarar 2017.

Daraktan Harkokin Shari’a na ONSA, Zakari Mijinyawa, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis yayin taron haɗin gwiwa na masu magana da yawun hukumomin tsaro, soji da jami’an tabbatar da doka da oda a Abuja.

Ya ce shirin, wanda ONSA ke jagoranta tare da Ma’aikatar Shari’a ta Tarayya, bangaren shari’a da hukumomin tsaro, ya kammala matakai goma na gudanar da shari’o’in ta’addanci.

A cewarsa, an kuma sallami ko wanke waɗanda ba a samu isassun hujjojin da za su tabbatar da laifinsu ba, domin mutunta ƙa’idodin adalci da damar samun shari’a ta gaskiya.

Mijinyawa ya ce matakai uku na farko da aka gudanar tsakanin 2017 zuwa 2018 sun samar da hukunci kan mutum 366, an sallami mutum 882, an wanke mutum biyar, yayin da aka ɗage shari’ar mutum 61.

Ya ƙara da cewa matakai na huɗu zuwa na takwas, da aka gudanar tsakanin 2023 zuwa 2025, sun haifar da hukunci 490, ciki har da laifukan tallafa wa ta’addanci, manyan laifukan ƙasa da ƙasa da kuma laifukan cin zarafin mata da yara.

Hakazalika, matakai na tara da na goma da aka gudanar a shekarar 2026 sun samar da hukunci 865, adadin da ya zarce rabin dukkan hukuncin da aka samu tun bayan fara shirin.

Ya bayyana cewa wannan adadi na shekarar 2026 ya fi jimillar hukuncin 856 da aka samu a cikin shekaru tara da s**a gabata.

Mijinyawa ya jaddada kudirin gwamnatin tarayya na tabbatar da hukunta masu aikata laifukan ta’addanci tare da kiyaye kundin tsarin mulki da bin doka da oda.

Daga jaridar: Fitila Hausa News

Jagoran 'yan bindiga da aka fi sani da Kachalla Maha ya yi ikirarin cewa yana da ƙarfin da zai iya ƙaddamar da hari kan ...
30/06/2026

Jagoran 'yan bindiga da aka fi sani da Kachalla Maha ya yi ikirarin cewa yana da ƙarfin da zai iya ƙaddamar da hari kan kowane gwamna a Najeriya idan ya ga dama.
A cewarsa, wasu jami'an tsaro da ake tura wa domin kai farmaki a kansa suna ba shi bayanan sirri tun kafin a fara gudanar da hare-haren, lamarin da ya ce yana ba shi damar kauce wa jami'an tsaro.
Ya kuma yi ikirarin cewa har bayanai kan wasu muhimman tarukan tsaro da s**a shafi Shugaban Ƙasa na isa gare shi kafin a aiwatar da wasu matakai, yana mai cewa hakan na ba shi damar sanin shirye-shiryen gwamnati a kansa.

Sai dai, waɗannan kalamai ikirari ne da Kachalla Maha ya yi, kuma har zuwa yanzu babu wata hujja mai zaman kanta ko wata sanarwa daga hukumomin tsaro da ta tabbatar da sahihancinsu.

An Gudanar da Muhimmin Ganawa Tsakanin Mataimaki na Musamman na Gwamnan Jihar Katsina da Kakakin Majalisar DokokiMataima...
29/06/2026

An Gudanar da Muhimmin Ganawa Tsakanin Mataimaki na Musamman na Gwamnan Jihar Katsina da Kakakin Majalisar Dokoki
Mataimaki na Musamman ga Gwamnan Jihar Katsina kan Harkokin Ƙananan Yara, Faruq Lema, ya kai ziyarar girmamawa ga Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Katsina, Honarabul Nasiru Yahaya Daura, a ofishinsa.
Ziyarar ta kasance wata dama ta ƙarfafa haɗin gwiwa da musayar ra'ayoyi kan batutuwan da s**a shafi ci gaban al'umma, musamman harkokin da s**a shafi walwala da makomar ƙananan yara a jihar.

YANZU-YANZU: Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram sun kai hari makarantar Government Day Secondary School da ke garin L...
29/06/2026

YANZU-YANZU: Wasu da ake zargin mayaƙan Boko Haram sun kai hari makarantar Government Day Secondary School da ke garin Lassa, Ƙaramar Hukumar Askira/Uba ta Jihar Borno.
Rahotanni sun ce harin ya faru ne da safiyar yau yayin da ɗalibai ke gudanar da jarabawar NECO/SSCE. Maharan, waɗanda ake zargin sun yi shigar sojoji da jami'an Forest Guard, sun samu damar shiga harabar makarantar kafin su aiwatar da harin.
A cewar majiyoyi, an yi garkuwa da wani malami tare da wasu ɗalibai, sai dai har yanzu ba a tabbatar da adadin waɗanda aka sace ba.
Jami'an tsaro sun fara ɗaukar matakan gaggawa domin ceto waɗanda abin ya shafa, yayin da ake ci gaba da jiran cikakkiyar sanarwa daga hukumomin da abin ya shafa.
Allah Ya kare Najeriya, Ya kuɓutar da duk waɗanda aka sace lafiya. 🤲🏽

25/06/2026

thank you for 4k follwers.

MARTANI: 'Ýan Arewa Sune Màțšalar Nijeriya, Domin Sune Yañ Bindigà, Sune Mabarata Sannan Kuma Sune Baŕayin Daji, Inji Ve...
24/06/2026

MARTANI: 'Ýan Arewa Sune Màțšalar Nijeriya, Domin Sune Yañ Bindigà, Sune Mabarata Sannan Kuma Sune Baŕayin Daji, Inji VeŕyDarkMan
..Yunƙurin Faɗin Gaskiya Bazaisa Ya zagi Duk Iyayenmu, Muyi shiru ba...........


Na kalli wani sashe na bidiyon ɗan gwagwarmayar Kudancin Najeriya, wato verydarkman, inda yace 'yan Arewa sune suke mayar da Najeriya baya, yayi maganganu masu kaushi, dakuma sosa zuciya, amma idan za'ayi adalci akwai ƙamshin gaskiya akan abinda ya faɗa, akwai kuma inda yayi kuskure dayawa wanda Zamuyi masa gyara.
Inda yayi kuskure shine, daya hade Hausawa gaba ɗaya, kuma ya ware ƙabilar Hausawa ya ɗora mata laifi, ya manta cewa a kowacce ƙabila akwai nagari kuma akwai ɓata gari.

Cikin maganarsa yace Bahaushe yana tasowa ne, dan ya koyi sana'ar barace-barace, sai sana'ar gadi, wankin takalmi, suya dakuma shayi, naji taƙaicin wannan kalaman, amma a wannan ɓangaren yanada hujja, domin sune irin mutanen da yafi gani a can kudancin Najeriya, duk da cewa munada manyan malamai, yan kasuwa dakuma fitattun mutane a duniya. Wannan ya faru ne saboda sakacin na shugabannin Arewa das**a kasa tsayawa wajen gina wannan yankin namu, sai shegiyar sata, anan Arewa ne fa mutum ɗaya fa ake zargin ya sace 210 Tiriliyan, wannan kuɗin ya isa magance 60% na matsalolin Arewa.

Muna goyon Bayan faɗin Gaskiya, amma bazamu bari a fake da haka a zagemu ba, yan Arewa sunada ilmi, sunada daraja, Hausawa sunada ƙima, kuma sunada ilmi, laifi kuma ba'a alaƙantashi da wata ƙabila guda ɗaya.

Ga wasu abubuwa dashi verydarkman ya Manta:

•Ya manta cewa wanda yafi kowa kuɗi a Afrika Bahaushe ne kuma ɗan Arewa.

•Ya Manta cewa kaso 75 na 'yan ta'adda ba Hausawa bane, Fulani ne.

•Ya manta cewa Kaso 75 na B©ko H@ram Kanuri ne Ba Hausawa bane.

•Ya manta cewa a kudancin Najeriya jihar sa ta edo, tana cikin jihohi marasa zaman lafiya, dan haka ba Hausawa ne matsalar NAJERIYA ba, ba wata ƙabila da za'a ɗorawa laifi, tsari ne yazo da haka, dakuma rashin kyakkyawan shugabanci.

Idan ka Yarda Da duk Abinda Ya Faɗa Ga abinda Hakan Yake nufi;

•Kenan duk Hausawa, malamai Iyayenmu, da mutanen kirki cikinmu jahilai ne kamar yadda ya faɗa?

•Yace Hausawa na haihuwar yara domin su zubar dasu, wanda Ni dakai duk Bama cikinsu.

•Yace Hausawa basu iya komai ba, sai gadi, da goge takalmi, alhalin munada dukkanin rukunin mutane masu basira, a fadin Duniya.

Laifi bana ƙabila ɗaya bane, na mutane ne, wanda cikin kowacce ƙabila akwai wanda yake s**an abinda suke aikatawa.

Zanso kalamansa su Zaburar da shugabannin Arewa, dakuma 'yan Arewa wajen gina yankin mu, dakuma rage masu barace-barace, hakan zai ragewa irinsu samun damar zaginmu.

Allah Ya raya mana Arewa, Allah Ya bamu tsaro mai ɗorewa.

Daga: Abubakar Shehu Dokoki

An Fara Tantance Wadanda Aka Zaba A Aikin CDCFIB A KatsinaHukumar CDCFIB ta fara tantance gwajin lafiya ga wadanda aka z...
24/06/2026

An Fara Tantance Wadanda Aka Zaba A Aikin CDCFIB A Katsina

Hukumar CDCFIB ta fara tantance gwajin lafiya ga wadanda aka zaba a aikin daukar ma'aikata na shekarar 2024/2025 a Kwalejin Peace and Disaster Management da ke Babbar Riga, kan titin Batsari a Jihar Katsina.
Jami'an hukumar sun jaddada cewa aikin daukar ma'aikatan kyauta ne gaba daya, tare da gargadin masu neman aikin da su guji masu damfara ko duk wanda ke neman kudi da sunan taimaka musu samun aikin.
Hukumar ta kuma tabbatar da cewa za a yi tantancewar ne cikin gaskiya, adalci da kuma bisa cancanta, inda wadanda s**a cika sharudda ne kawai za su samu nasara.
Allah Ya ba wa matasanmu sa'a. 🤲

YANZU-YANZU: Kotu Ta Sanya Ranar 30 Ga Yuni Don Yanke Hukunci Kan Buƙatar Sowore Ta Dawo Masa Da BeliBabbar Kotun Tarayy...
24/06/2026

YANZU-YANZU: Kotu Ta Sanya Ranar 30 Ga Yuni Don Yanke Hukunci Kan Buƙatar Sowore Ta Dawo Masa Da Beli
Babbar Kotun Tarayya ta ɗage yanke hukunci kan buƙatar da ɗan gwagwarmaya Omoyele Sowore ya shigar na neman a dawo masa da belinsa.
Bayan sauraron hujjojin ɓangarorin biyu, kotun ta ce za ta yanke hukunci a ranar 30 ga Yuni, 2026.
Ana zargin Sowore da karya wasu sharuddan beli sakamakon kalaman da ya yi, lamarin da ya sa aka janye belin nasa. Yanzu dai ana jiran hukuncin kotu domin sanin ko za a dawo masa da 'yancinsa kafin ƙarshen shari'ar.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Prime News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share