Karamchi

Karamchi Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Karamchi, Newspaper, No. 305 world gate shopping complex, one man village, Karu Nassarawa, Karu.

Jaridan karamchi gidan labarai kamfani ne mai zaman kansa dake farautar labarai lungu da sako wanda s**a hada da siyasa, tattalin arziki, noma da kiwo, matsalar tsaro da suk wani nau’in labari na take hakkin dan adam daga masu ganin sunfi karfin doka/oda.

Ministan Tsaro Ya Kai Ziyarar Ban Kwana Ga Shugaba Tinubu a Addis AbabaMinistan Tsaro na Najeriya, Mai Girma Mohammed Ba...
18/02/2025

Ministan Tsaro Ya Kai Ziyarar Ban Kwana Ga Shugaba Tinubu a Addis Ababa

Ministan Tsaro na Najeriya, Mai Girma Mohammed Badaru Abubakar CON mni, a ranar Litinin 17/02/2025, ya kai ziyarar ban kwana ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu CGFR a birnin Addis Ababa na ƙasar Habasha, jim kaɗan kafin shugaban ya baro ƙasar zuwa Najeriya.

Shugaba Tinubu yana Habasha ne domin halartar taron koli na Ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU) karo na 38, wanda aka gudanar a Addis Ababa.

Sojojin Nijeriya sun ceto mutane 59 da aka yi garkuwa da su daga maboyar 'yan bindiga
18/02/2025

Sojojin Nijeriya sun ceto mutane 59 da aka yi garkuwa da su daga maboyar 'yan bindiga

Kamfanin Airtel ya kara farashin data a Nijeriya Kamfanin sadarwa na Airtel a Nijeriya, wands shi ne na biyu mafi girma ...
18/02/2025

Kamfanin Airtel ya kara farashin data a Nijeriya

Kamfanin sadarwa na Airtel a Nijeriya, wands shi ne na biyu mafi girma a kasar ya yi ƙare-ƙare sosai ga tsarin farashin data.

Wani bincike da Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa ya yi, ya nuna cewa duk wanda ya yi amfani da lambar *312 # da kuma a shafin yanar gizon Airtel zai ga cewa an yi ƙarin farashin na data.

A cewar shafin yanar gizo na kamfanin, ƙarin wanda ya shafi nau'ikan adadin daga daban-daban, na da nufin rage tasirin hauhawar farashin datar a kamfanin, musamman duba da yanayin ƙalubale na tattalin arziki.

Tsare-tsaren bayanan da aka sabunta, wanda aka buga a sahfin yanar gizonsa, sun haɗa da tsare-tsaren yau da kullun: N50 akan 40MB na tsawon kwana 1, 100MB akan Naira 100 (kwana 1), 200MB akan. 200 (na kwanaki 3), da kuma 1GB akan Naira 350.

A gefe guda kuma, tsare-tsaren data na mako-mako sun koma 350MB akan N350, 750MB akan N500 tare da 1GB na kallon YouTube da tsakar dare ta amfani da 200MB YouTube Music/Spotify tsawon kwanaki 7.

Sai kuma tsarin 1GB akan N500 da 1GB na kallon YouTube tsakar dare da kuma 50MB na shiga shafukan sada zumunta shima akan N500 tsawon kwanaki 7 da dai sauran su.

Zargin Da Jami’in Kamfanin Binance Ya Yi Kan Ribaɗu Zuƙi Ta Malle Ce - Jaafar JaafarShugaban sashen kula da laifuffukan ...
18/02/2025

Zargin Da Jami’in Kamfanin Binance Ya Yi Kan Ribaɗu Zuƙi Ta Malle Ce - Jaafar Jaafar

Shugaban sashen kula da laifuffukan kuɗaɗe na kamfanin hada-hadar kuɗaɗen kirifto (Binance), Tigran Gambaryan ya yi zargin cewa mai ba wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribaɗu ya nemi biliyoyin kuɗaɗe daga gare shi a matsayin cin-hancin biya masa buƙatarsa ta siyasa nan gaba. Duk da cewa bai gabatar da wata ƙwaƙƙwarar hujja ba.

La’alla Ribaɗu ya ɓata wa wasu, ko wasu ba za su iya yafe masa ba, amma magagana ta gaskiya shi ba mazambaci ba ne, ba ya karɓan cin-hanci. Ya nuna tsantsar nagarta a lokacin da ya ƙi karɓan Dala Biliyan 15 kuɗin toshiyar baki daga tsohon gwamnan Jihar Delta, James Ibori. A watan Satumbar shekarar 2013, Ribaɗu ya bayyana a gaban wata babbar kotu da ke birnin Landan na ƙasar Ingila (Crown Court), inda ya tabbatar da cewa Ibori ya ba shi kuɗaɗen a hannu. An yarda da bayaninsa sannan kuma an k**a Ibori da laifi.

Fagen siyasar Najeriya k**ar daji yake, inda kowace irin dabba ke rayuwa. Idan kana son shiga fagen siyasa, ka shirya mu’amala da kowane irin nau’i na mutane. Nagari da wanda ba na gari ba. Duk Jam’iyyun siyasa ɗaya ne, har yanzu idan kana son ka samu nasarar lashe zaɓe a Jihar Delta, sai ka k**a ƙafa da James Ibori, k**ar yadda Jolly Nyame da Joshua Dariye suke da wannan tasirin a Jihohin Taraba da Filato.

A gefe guda, ina kallon Ribaɗu a matsayin wani mutum mai tsarki a ruhin (APC), duba da irin abubuwan da wasu shugabannin ke yi a jam’iyya mai mulki. Ribaɗu ya ƙi yarda da baragadar Wike. Cakwaikwaiwar ministan da ke ƙalubalantar gwamna Fabura a Jihar Rivers. Da ace babu Ribaɗu a jam’iyyar (APC), da tuni jam’iyyar ta ƙwace iko da Jihohin Kano, Bauchi, da kuma Filato, da sauransu a kotu. Ya tsaye wa gwamnonin jam’iyyun adawa a daidai lokacin da kurayen jam’iyyarsa ke amfani da matsayinsu domin farautar nasara a kotun ƙoli.

Abin da kowa yake tunani shi ne duk wani ɗan Najeriya mazambaci ne da ke karɓa da ba da cin hanci da rashawa. Lallai ya k**ata Gambaryan ya sani cewa, ko da jam’iyyar ƴan N**i da ta haifar da mutane irin su Adolf Hi**er, Heinrich Himmler, Hermann Goring da Joseph Goebbels, tana kuma da wani nagartaccen mutum, Oskar Schindler.

An yi garkuwa da ma'aikaci Asibitin koyarwa na jami'ar Modibbo Adama da ke Yola a jihar Adamawa da wasu mutane 3 -  Rund...
18/02/2025

An yi garkuwa da ma'aikaci Asibitin koyarwa na jami'ar Modibbo Adama da ke Yola a jihar Adamawa da wasu mutane 3 - Rundunar 'yan sandan jihar

DA DUMI DUMINSA: Ya k**ata Ace kayan masarufi Sunyi Tashin Gwauron Zabi zuwa yanzu, Munayin Asara Sosai Sabida faduwar k...
18/02/2025

DA DUMI DUMINSA: Ya k**ata Ace kayan masarufi Sunyi Tashin Gwauron Zabi zuwa yanzu, Munayin Asara Sosai Sabida faduwar kayan masarufi, ƙungiyar Masu Siyar kayan masarufi ta koka game da Faɗuwar farashin kayan masarufi a Najeriya inda ta bayyana cewa Suna yin Asara Sosai.

Cikin Masu Siyen Kayan Abinci Suna Boyewa Idan Ya Yi Tsada Su Fito Da Shi Suna Siyarwa, Ya Duri Ruwa, Inda Wani Da Ya Sayi Buhunun Masara Akan Naira Dunu 75 Ya Fito Zai Siyar Aka Ki Saye A Naira Dubu Hamsin

Me za ku ce?

Jagora a yankin Neja-Delta, Edwin Clark ya mutu yana da shekaru 97Edwin Clark, tsohon kwamishinan tarayya na yada labara...
18/02/2025

Jagora a yankin Neja-Delta, Edwin Clark ya mutu yana da shekaru 97

Edwin Clark, tsohon kwamishinan tarayya na yada labarai kuma fitaccen jagoran kabilar Ijaw a yankin Kudu-maso-Kudu ya mutu.

Daily Trust ta rawaito cewa a wata sanarwa, iyalan Clark-Fuludu Bekederemo na garin Kiagbodo, Jihar Delta, sun bayyana cewa tsohon sanatan ya rasu a ranar Litinin, 17 ga Fabrairu.

Ya rasu yana da shekaru 97.

Kafin rasuwarsa, Clark shi ne jagora kabilar Ijaw

Gwamnatin Zamfara ta hana taron siyasa a jihar Gwamnatin jihar Zamfara ta haramta duk wani taruka da gangamin siyasa a  ...
18/02/2025

Gwamnatin Zamfara ta hana taron siyasa a jihar

Gwamnatin jihar Zamfara ta haramta duk wani taruka da gangamin siyasa a jihar.

A cewar gwamnatin, haramcin, wanda ya shafi dukkanin jam’iyyun siyasa, kuma ya fara aiki nan take, an yi shi ne domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

Daily Trust ta rawaito cewa da ya ke magana a wata hira da sashen Hausa na BBC, babban mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Zamfara kan harkokin yada labarai da hulda da jama’a, Mustapha Jafaru Kaura, ya ce matakin ya biyo bayan rikicin siyasa da ya ɓarke a karamar hukumar Maru ta jihar.

Ya ce, “Daga yanzu, an hana duk wani tarukan siyasa da gangamin da zai iya haifar da tarzoma. Gwamnati na alhinin faruwar lamarin da ya faru a karamar hukumar Maru wanda ya yi sanadin kona dukiyoyi.”

Ya kara da cewa, haramcin na wucin-gadi ne da nufin hana tashin hankali a jihar da ke fama da tashe-tashen hankula bisa aiyukan ƴan ta'adda.

Kotu ta aikewa Abdullahi Abbas da Faizu Alfindiki sammaci bisa zargin ɓatanci ga gwamnan Kano Babbar Kotun Shari'ar Musu...
18/02/2025

Kotu ta aikewa Abdullahi Abbas da Faizu Alfindiki sammaci bisa zargin ɓatanci ga gwamnan Kano

Babbar Kotun Shari'ar Musulunci da ke kasuwa, ƙarƙashin Mai Shari'a Abdu Abdullahi Waiya, ta aike da sammaci ga shugaban jam'iyyar APC na Kano, Abdullahi Abbas, da Faizu Alfindiki, ɗan APC bisa zargin yin batanci ga gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf.

Freedom Radio ta rawaito cewa, wasu hadiman gwamnan, Amir Abdullahi da Ishaq Abdul ne su ka shigar da ƙarar, inda su ke zargin Abbas da Faizu da batanci ga gwamnan Yusuf ta hanyar WhatsApp da facebook.

A zaman kotun na yau, lauyan masu ƙara, Shazali Muhammad Ashiru, ya shaidawa Freedom Radio cewa sun shigar da karar ne bisa kalaman da wadanda ake ƙarar ke yi.

A cewar sa, "kalaman sun yi muni kuma za su iya haifar da tunzuri daga al'ummar jihar Kano masoya gwamna da ma halin mai girma Gwamna.

"Don haka sai mu ka ga cewa doka ta bada damar duk wanda ya ga ana wani abu da zai iya haifar da rashin kwanciyar hankali zai iya garzayawa zuwa kotu ya shigar da kara domin wanzar da zaman lafiya.

"Kalaman da Abdullahi Abbas da Faizu Alfindiki sun yi muni ga muhibbar mai girma Gwamnan Kano kuma ko waye aka fadawa haka zai iya zuwa kotu ya nemi hakkin sa," in ji lauyan.

Kotun ta kuma sanya 24 ga watan Fabrairu domin dawowa gaban kotun.

Ƴan kasuwa a Kano sun yaba wa Tinubu kan faɗuwar farashin abinci
18/02/2025

Ƴan kasuwa a Kano sun yaba wa Tinubu kan faɗuwar farashin abinci

Da Malamai ya k**ata ayi koyi wajen hadin kan al umma ba ‘yan siyasa ba. Sule Lamido ya yiwa Malamai shagube yayin ziyar...
18/02/2025

Da Malamai ya k**ata ayi koyi wajen hadin kan al umma ba ‘yan siyasa ba.

Sule Lamido ya yiwa Malamai shagube yayin ziyarar ta’aziyyar rasuwar dan sheikh Sambo Rigachikun.

Bayan kammala gaisuwar, Shehin ya bukaci tsohon gwamnan Jigawa Sule Lamido da su hada Kai domin ganin yankin nasu ya cigaba, sai dai nan take dan siyasar ya maida martani cikin Hikima inda yace, Malamai ne yafi dacewa su hada Kai kafin yan siyasa su biyo baya.

Lamido ya shawarci malaman dasu dena aibata juna da zagin juna kawai saboda sabanin fahimta dake tsakaninsu.

Abin jira a gani yanzu shi ne ko malaman zasu dena zagin juna su rungumi zaman lafiya da dena aibata juna ko a’ah.

Lokaci Alkali.:

Saudiyya ta ba Nijeriya tallafin ton 100 na dabino
18/02/2025

Saudiyya ta ba Nijeriya tallafin ton 100 na dabino

Yanzu haka Farashin kayan masàrufi daga kasuwar Garin Hardawa dake karamar hukumar Misau a Jihar Bauchi.Price Update:   ...
17/02/2025

Yanzu haka Farashin kayan masàrufi daga kasuwar Garin Hardawa dake karamar hukumar Misau a Jihar Bauchi.

Price Update: 16 February, 2025.
HARDAWA Local Market Prices: Grains and Legumes.

Farashin Kaya Daga Kasuwar Buhu dake cikin garin HARDAWA, Karamar Hukumar Misau, Jihar Bauchi.

Farin Wake #90,000 .
Jar Dawa 50,000
Farar Dawa 48,000 - 45,000.
Masara 55,000.
Gero 52,000
Gyada Mai Bayo.40,000 -48,000 Yanayin Ingancinta.

Mal.Musa Ahmed Hardawa.
Magatakardar Kungiyar Wayar da Kan Matasa akan Harkokin Siyasa.

Tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato, Sanata Aminu Waziri Tambuwal, ya yi watsi da sauya sheka da ke faruwa a yankin Arewa maso...
17/02/2025

Tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato, Sanata Aminu Waziri Tambuwal, ya yi watsi da sauya sheka da ke faruwa a yankin Arewa maso Yamma, yana mai cewa ana yin hakan ne saboda son rai ba don amfanin al’umma ba.

Da yake zantawa da manema labarai bayan taron farko na Majalisar Zartarwa ta Yankin Arewa maso Yamma na jam’iyyar PDP a Kaduna a ranar Asabar, Tambuwal ya soki masu sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki, yana mai cewa manufarsu ba ta da alaka da kishin jama’a.

"Mutane na barin jam’iyyarsu saboda dalilai daban-daban. Amma abin da na lura da shi shi ne, ba a yin sauya sheka bisa bukatun jama’a, sai don amfanin kai, wanda ake kiransa a turance ‘infrastructure na ciki’.”

"Idan kai ɗan siyasa ne mai hankali, ba za ka shiga APC ba duba da halin matsin tattalin arziki da kuma gazawar gwamnatin Tinubu,” in ji Tambuwal.

Jigon na PDP ya zargi gwamnatin APC da rashin jagoranci mai kyau, tausayi, da kuma sanin mak**ar aiki.

Ya yi kira ga ‘yan adawa da su haɗa kai tare da tsara dabaru don tunkarar zaɓen 2027, domin samar da wata madogara ga ‘yan Najeriya.

"Babu wani abin jan hankali a APC sai dai son kai. Mu da muke da kishin kasa da kuma hidima ga jama’a dole ne mu haɗa kai domin tabbatar da cewa a 2027 mun kawar da wannan gwamnati da ta gaza wa ‘yan Najeriya,” in ji shi.

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Wadannan 'Yan Mata Biyu Zubaidat Kariyo Da Umma Jagindi Gari Sun Rasu Sak**akon Çiź...
17/02/2025

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Wadannan 'Yan Mata Biyu Zubaidat Kariyo Da Umma Jagindi Gari Sun Rasu Sak**akon Çiźon Maçijì

Ita Umma aurenta ya rage saura makonni biyu kafin rai ya yi halinsa.

Allah Ya gafarta musu?

Na yaba da irin gudunmuwar gina Nijeriya da El-Rufa'i yake badawa - Sakon Kwankwaso a bikin cikar  tsohon Gwamnan jihar ...
17/02/2025

Na yaba da irin gudunmuwar gina Nijeriya da El-Rufa'i yake badawa - Sakon Kwankwaso a bikin cikar tsohon Gwamnan jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufa'i shekaru 65

Wannan wani shahararren makarancin Alƙur'ani Mai Tsarki ne. Ku faɗa mana cikakken sunan sa.
17/02/2025

Wannan wani shahararren makarancin Alƙur'ani Mai Tsarki ne. Ku faɗa mana cikakken sunan sa.

A sakon taya murnar cika shekaru 63, Tinubu ya jinjinawa El-Rufai kan bada gudunmawa ga cigaban dimokuraɗiyyaShugaban ka...
17/02/2025

A sakon taya murnar cika shekaru 63, Tinubu ya jinjinawa El-Rufai kan bada gudunmawa ga cigaban dimokuraɗiyya

Shugaban kasa Bola Tinubu ya taya tsohon gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai murnar cika shekaru 65 a duniya, inda ya bayyana shi a matsayin “shugaba, malami, kuma dan siyasa” wanda ya yi shura akan “ƙwazo da hazaka.”

A cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Lahadi, Tinubu ya yaba da rawar da El-Rufai ya taka a matsayin wanda ya bada gudunmawa wajen kafa jam’iyyar APC da kuma gudunmawar da ya bayar wajen samun nasarar jam’iyyar a zabuka uku a jere.

Bayo Onanuga, mai baiwa shugaban kasa shawara na musamman kan Bayanai da Dabaru ne ya fitar da sanarwar a yau Lahadi.

“Shugaban kasa ya yaba da rawar da Mallam El-Rufai ya taka fafutukar da aka yi kafin kafa jam’iyyar APC da kuma gudunmawar da ya bayar wajen samun nasarar jam’iyyar a zabuka uku a jere na 2015, 2019, da 2023,” in ji sanarwar.

Tinubu ya kuma yabawa “kokarin da tsohon ministan ya yi na tabbatar da dimokradiyya; kyakkyawar hidimarsa ga al’umma, da nasiha ga matasa masu tasowa.”

Address

No. 305 World Gate Shopping Complex, One Man Village, Karu Nassarawa
Karu

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Karamchi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category