18/02/2025
Zargin Da Jami’in Kamfanin Binance Ya Yi Kan Ribaɗu Zuƙi Ta Malle Ce - Jaafar Jaafar
Shugaban sashen kula da laifuffukan kuɗaɗe na kamfanin hada-hadar kuɗaɗen kirifto (Binance), Tigran Gambaryan ya yi zargin cewa mai ba wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribaɗu ya nemi biliyoyin kuɗaɗe daga gare shi a matsayin cin-hancin biya masa buƙatarsa ta siyasa nan gaba. Duk da cewa bai gabatar da wata ƙwaƙƙwarar hujja ba.
La’alla Ribaɗu ya ɓata wa wasu, ko wasu ba za su iya yafe masa ba, amma magagana ta gaskiya shi ba mazambaci ba ne, ba ya karɓan cin-hanci. Ya nuna tsantsar nagarta a lokacin da ya ƙi karɓan Dala Biliyan 15 kuɗin toshiyar baki daga tsohon gwamnan Jihar Delta, James Ibori. A watan Satumbar shekarar 2013, Ribaɗu ya bayyana a gaban wata babbar kotu da ke birnin Landan na ƙasar Ingila (Crown Court), inda ya tabbatar da cewa Ibori ya ba shi kuɗaɗen a hannu. An yarda da bayaninsa sannan kuma an k**a Ibori da laifi.
Fagen siyasar Najeriya k**ar daji yake, inda kowace irin dabba ke rayuwa. Idan kana son shiga fagen siyasa, ka shirya mu’amala da kowane irin nau’i na mutane. Nagari da wanda ba na gari ba. Duk Jam’iyyun siyasa ɗaya ne, har yanzu idan kana son ka samu nasarar lashe zaɓe a Jihar Delta, sai ka k**a ƙafa da James Ibori, k**ar yadda Jolly Nyame da Joshua Dariye suke da wannan tasirin a Jihohin Taraba da Filato.
A gefe guda, ina kallon Ribaɗu a matsayin wani mutum mai tsarki a ruhin (APC), duba da irin abubuwan da wasu shugabannin ke yi a jam’iyya mai mulki. Ribaɗu ya ƙi yarda da baragadar Wike. Cakwaikwaiwar ministan da ke ƙalubalantar gwamna Fabura a Jihar Rivers. Da ace babu Ribaɗu a jam’iyyar (APC), da tuni jam’iyyar ta ƙwace iko da Jihohin Kano, Bauchi, da kuma Filato, da sauransu a kotu. Ya tsaye wa gwamnonin jam’iyyun adawa a daidai lokacin da kurayen jam’iyyarsa ke amfani da matsayinsu domin farautar nasara a kotun ƙoli.
Abin da kowa yake tunani shi ne duk wani ɗan Najeriya mazambaci ne da ke karɓa da ba da cin hanci da rashawa. Lallai ya k**ata Gambaryan ya sani cewa, ko da jam’iyyar ƴan N**i da ta haifar da mutane irin su Adolf Hi**er, Heinrich Himmler, Hermann Goring da Joseph Goebbels, tana kuma da wani nagartaccen mutum, Oskar Schindler.