KTG Hausa News

KTG Hausa News Ingantattun Labarai wanda s**a inganta na gaskiya.

Karin Harajin Mai Na 5% Ba Sabon Haraji Ba Ne, Kuma Ba Za a Aiwatar Da Shi Yanzu Ba – Gwamnatin TarayyaKwamitin Shugaban...
08/09/2025

Karin Harajin Mai Na 5% Ba Sabon Haraji Ba Ne, Kuma Ba Za a Aiwatar Da Shi Yanzu Ba – Gwamnatin Tarayya

Kwamitin Shugaban Kasa kan Tsarin Haraji da Sauye-sauyen Haraji ya ce karin kashi 5% a kan farashin mai ba sabon haraji ba ne da gwamnatin Tinubu ta kawo.

A cewar kwamitin, wannan kudiri daman akwai shi a cikin dokar Federal Roads Maintenance Agency (FERMA) ta 2007, sai dai an sake saka shi a sabuwar dokar haraji ne domin samar da daidaito da kuma gaskiya.

Kwamitin ya ce karin ba zai fara aiki nan take ba har sai Ministan Kuɗi ya fitar da oda ta musamman a cikin sanarwar gwamnati.

Haka kuma, an bayyana cewa karin ba zai shafi dukkan kayan da ake saku daga man fetur ba, musamman wanda ake amfani da su a gidaje kamar gas ɗin girki (LPG), Kalanzir, da CNG, domin tallafawa burin Najeriya na wanzar da makamashi mai tsafta.

Kwamitin ya ce an samar da karin kuɗin ne domin samar da kuɗaɗen ginawa da gyaran manyan hanyoyi. Ya ce idan an aiwatar da shi yadda ya kamata, zai rage yawaitar aukuwar haɗari a hanya, zai sauƙaƙawa matafiya, da kuma rage kuɗin sufuri.

𝐃𝐚 𝐃𝐮𝐦𝐢-𝐃𝐮𝐦𝐢: Kansila a Kaduna ya naɗa masu ba shi shawara 18Kansilan da ke wakiltar Kinkiba Ward a ƙaramar hukumar Soba...
08/09/2025

𝐃𝐚 𝐃𝐮𝐦𝐢-𝐃𝐮𝐦𝐢: Kansila a Kaduna ya naɗa masu ba shi shawara 18

Kansilan da ke wakiltar Kinkiba Ward a ƙaramar hukumar Soba ta jihar Kaduna, Hon. Sunusi Hashim, ya naɗa masu ba shi shawara 18 domin ƙarfafa shugabancinsa a matakin ƙaramar hukuma.

Hashim ya bayyana cewa ya dauki wannan mataki ne domin baiwa matasa dama, da kuma tabbatar da cewa kowane fanni na rayuwa a mazabar Kinkiba ya samu wakilci.

A cewarsa:
“A matsayina na kansila, ina da burin ganin mazabar mu ta ci gaba. Wannan naɗi ba wai don nuna mulki ba ne, illa don baiwa jama’ar Kinkiba damar bada shawarwari kai tsaye wajen yanke hukunci da aiwatar da ayyuka.”

Sai dai wannan naɗi ya jawo cece-kuce a tsakanin mazauna yankin. Wasu sun yaba da shi a matsayin hanyar baiwa matasa dama da kuma tunkarar matsalolin al’umma, yayin da wasu kuma ke ganin yawan masu ba da shawara na iya zama abin ban mamaki ga matsayi irin na kansila.

KTG Hausa News

DA DUMI-DUMI: El-Rufai Ya Kai Ƙarar Kwamishinan ‘Yan Sanda Na Kaduna Gaban Hukumar PSC Kan Zarge-Zargen Rashin Da’a Da C...
08/09/2025

DA DUMI-DUMI: El-Rufai Ya Kai Ƙarar Kwamishinan ‘Yan Sanda Na Kaduna Gaban Hukumar PSC Kan Zarge-Zargen Rashin Da’a Da Cin Zarafi

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufai, ya shigar da ƙara gaban Hukumar Kula da Ayyukan ‘Yan Sanda ta Ƙasa (PSC) kan wasu jami’an rundunar ‘yan sanda na jihar Kaduna.

El-Rufai ya bayyana kansa a matsayin ɗan ƙasa da kuma tsohon gwamna wanda ya ba da gudummawa ga ci gaban jihar Kaduna tsawon shekaru takwas, tare da yin aiki a matakai daban-daban na ƙasa. Ya ce ƙarar da ya shigar ya samo asali ne daga kishin ƙasa da kuma damuwarsa kan makomar rundunar ‘yan sanda wadda, duk da ƙalubale, ita ce ginshiƙin tsaro da kare doka a ƙasar nan.

Ya ƙara da cewa dole ne kowane ɗan ƙasa ya tallafa wa rundunar ‘yan sanda ba kawai ta hanyar goyon baya ba, har ma da tabbatar da cewa PSC ta yi amfani da ikon da doka ta ba ta wajen tabbatar da da’a da ɗabi’a a tsakanin jami’an rundunar.

KBC Hausa

𝐃𝐚 𝐃𝐮𝐦𝐢-𝐃𝐮𝐦𝐢: Wata Kungiya a Arewa ta bukaci a tsige manyan hafsoshin tsaroKungiyar Northern Ethnic National Forum ta bu...
08/09/2025

𝐃𝐚 𝐃𝐮𝐦𝐢-𝐃𝐮𝐦𝐢: Wata Kungiya a Arewa ta bukaci a tsige manyan hafsoshin tsaro

Kungiyar Northern Ethnic National Forum ta bukaci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya ayyana dokar ta-baci kan harkar tsaro a ƙasar, tare da gaggauta tsige shugabannin rundunonin tsaro na ƙasa.

Kungiyar ta bayyana cewa matsalar tsaro a yankin Arewa ta kai wani matsayi mai tsanani, inda al’ummar ƙauyuka da birane ke fama da hare-haren ’yan bindiga, garkuwa da mutane, da satar shanu.

A cikin sanarwar da ta fitar, kungiyar ta ce rashin tsari da gazawar shugabancin manyan hafsoshin tsaro sun haddasa tabarbarewar lamarin, abin da ya sa rayuka da dukiyoyin jama’a ke ci gaba da salwanta a kullum.

Shugaban kungiyar ya ce:
“Mun gaji da ta’addanci da kashe-kashe a Arewa. Shugaban Ƙasa ya kamata ya ɗauki matakin gaggawa ta hanyar tsige shugabannin tsaro domin ba wa rundunonin tsaro sabon salo da sabuwar jajircewa.”

Kungiyar ta kuma yi kira ga gwamnati da ta sanya albarkatu masu yawa a fannin tsaro, ta bunkasa aikin leken asiri da kuma samar da kayan aiki na zamani domin yaƙi da ’yan ta’adda.

Lamarin dai ya jawo cece-kuce, inda wasu ’yan Arewa ke goyon bayan kiran kungiyar, yayin da wasu ke ganin sauya shugabannin tsaro kawai ba zai wadatar ba sai an yi cikakken garambawul a tsarin tsaro gaba ɗaya.

KTG Hausa News

Yanzu haka Wata yayi Khusufi a jihar Sokoto. Kufa a jihohin ku?
07/09/2025

Yanzu haka Wata yayi Khusufi a jihar Sokoto.
Kufa a jihohin ku?

𝐃𝐚 𝐃𝐮𝐦𝐢-𝐃𝐮𝐦𝐢: Gwamnatin Jihar Bauchi ta amince da N6.5bn domin gina titin Misau mai layi biyuGwamnatin jihar Bauchi ta a...
07/09/2025

𝐃𝐚 𝐃𝐮𝐦𝐢-𝐃𝐮𝐦𝐢: Gwamnatin Jihar Bauchi ta amince da N6.5bn domin gina titin Misau mai layi biyu

Gwamnatin jihar Bauchi ta amince da kashe sama da naira biliyan 6.5 domin yin titin cikin gari mai tsawon kilomita 7.5 da zai ratsa garin Misau, a ƙaramar hukumar Misau.

Kwamishinan yada labarai na jihar, ya bayyana cewa aikin zai haɗa da faɗaɗa titin zuwa layi biyu, gina sabbin gadar mota da hanyar ruwa, da kuma sanya fitilun zamani domin inganta tsaro da kyawun gari.

Ya kara da cewa manufar gwamnatin Sanata Bala Mohammed ita ce sauƙaƙa zirga-zirga, bunƙasa kasuwanci, da kuma samar da ayyukan yi ga matasa a lokacin gudanar da aikin.

A cewarsa:
“Wannan aiki ba wai kawai zai sauƙaƙa sufuri ba ne, har ma zai taimaka wajen bunƙasa tattalin arzikin al’umma da rage cunkoso a cikin garin Misau. Gwamnati za ta tabbatar da cewa aikin ya gudana yadda ya kamata kuma cikin inganci.”

Al’umma a garin Misau sun bayyana jin daɗin wannan mataki, inda wasu ke ganin zai kawo ci gaba mai ɗorewa, yayin da wasu kuma ke kira da a tabbatar da cewa an kammala aikin cikin lokaci ba tare da tangarda ba.

KTG Hausa News

𝐃𝐚 D𝐮𝐦𝐢-D𝐮𝐦𝐢: NNPP ta soke korar da ta yiwa Abdulmumin Jibrin, ta ce har yanzu cikakken ɗan jam’iyya neJam’iyyar New Nig...
07/09/2025

𝐃𝐚 D𝐮𝐦𝐢-D𝐮𝐦𝐢: NNPP ta soke korar da ta yiwa Abdulmumin Jibrin, ta ce har yanzu cikakken ɗan jam’iyya ne

Jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) ta bayyana cewa ba ta amince da rahoton da ke cewa an kori tsohon ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Kiru/Bebeji a Jihar Kano, Hon. Abdulmumin Jibrin, daga jam’iyyar ba.

A wata sanarwa da ta fitar a Kano, jam’iyyar ta ce matakin da wasu s**a ɗauka na bayyana cewa an yi wa Jibrin kora daga NNPP “ba shi da tushe, b***e makama.” Ta ƙara da cewa har yanzu Jibrin yana cikin jam’iyyar a matsayin cikakken ɗan ƙasa mai daraja wanda ya taka rawa sosai wajen gina NNPP tun daga tushe.

Jagororin jam’iyyar sun jaddada cewa ba kowanne ɓangare na jam’iyya ne ke da ikon yanke irin wannan hukunci ba sai dai tsarin jam’iyya ta ƙasa baki ɗaya. Sun yi kira ga magoya baya da jama’a da kada su bari rikice-rikicen cikin gida su dusashe martabar jam’iyyar a idon jama’a.

> “Babu wani hukunci na ƙarshe da ya tabbatar da korar Abdulmumin Jibrin. Har yanzu yana ɗaya daga cikin muhimman jigon jam’iyyar, kuma muna ganin yana da rawar da zai taka wajen inganta NNPP a matakin jiha da ƙasa baki ɗaya,” in ji sanarwar.

Wannan mataki na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun ƙarin tashin hankali da rarrabuwar kawuna a cikin jam’iyyar musamman a Kano, inda rikicin shugabanci da na matsayi s**a rura wutar sabani tsakanin ’ya’yan jam’iyyar.

Wasu magoya bayan NNPP a Kano sun yi maraba da wannan mataki na soke korar, suna mai cewa zai hana jam’iyyar ta rabu gida biyu. A cewarsu, Jibrin jigo ne wanda ya yi rawar gani wajen tallata jam’iyyar a zaɓen 2023, don haka bai kamata a yi gaggawar kawar da shi ba.

Sai dai wasu masu sharhi sun bayyana damuwa cewa irin waɗannan rikice-rikicen na iya raunana jam’iyyar musamman ganin cewa NNPP ta samu gagarumar nasara a Kano a bara. A cewarsu, idan ba a shawo kan sabanin cikin gida da wuri ba, zai iya zama cikas ga makomar jam’iyyar a zaɓukan gaba.

A halin da ake ciki, Abdulmumin Jibrin dai bai fitar da wata sanarwa kai tsaye ba game da lamarin, amma wasu daga cikin magoya bayansa sun bayyana a kafafen sada zumunta cewa sun ji daɗin matsayin jam’iyyar na tabbatar da shi a matsayin cikakken ɗan NNPP.

KTG Hausa News

06/09/2025

Mu shakata da wannan amma banda dariya da yawa kada cikin mutum yayi ciwo nima bara naci gaba da tawa🤣😂😂🤣🤣😂😂

YANZU-YANZU: Tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa Alh Atiku Abubakar Ya Dawo Najeriya Bayan kwashe Kwanaki da yayi Yana Hutu ...
06/09/2025

YANZU-YANZU: Tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa Alh Atiku Abubakar Ya Dawo Najeriya Bayan kwashe Kwanaki da yayi Yana Hutu a ƙasar Dubai.

Wanne fata kuke masa

HOTO MAI MAGANA Tsohon Gwamnan jihar Bauchi Mallam Isah Yuguda tare da tsohon dan takarar Gwamnan jihar na Bauchi a zabe...
06/09/2025

HOTO MAI MAGANA

Tsohon Gwamnan jihar Bauchi Mallam Isah Yuguda tare da tsohon dan takarar Gwamnan jihar na Bauchi a zaben 2023 Air Marshal Sadique Baba Abubakar.

Koh wani irin tasiri Air Marshal zai yi a zaben 2027?

Mabiyin addinin Kirista mai suna Daure David daga jihar Bauchi, Cikin farin kaya yayin da ya fito zaga Garin Maulidi da ...
06/09/2025

Mabiyin addinin Kirista mai suna Daure David daga jihar Bauchi, Cikin farin kaya yayin da ya fito zaga Garin Maulidi da aka Gudanar Yau A Bauchi.

Wanne fata kuke masa.?

Gwamna Uba Sani ya gargadi ‘yan adawa kan batun tsaroGwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya gargadi wasu ’yan adawa da su da...
06/09/2025

Gwamna Uba Sani ya gargadi ‘yan adawa kan batun tsaro

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya gargadi wasu ’yan adawa da su daina amfani da matsalar tsaro a matsayin makamin siyasa, yana mai cewa tsaro lamari ne da ya shafi rayuwar al’umma gaba ɗaya, ba batun nuna banbancin ra’ayi ba.

A wata jawabi da ya yi a Kaduna ranar Asabar, gwamnan ya ce:

“Ba za mu iya warware matsalar tsaro ta hanyar carpet-bombing kawai akan ’yan ta’adda ba. Tsaro na bukatar tsari, dabaru, da haɗin kai tsakanin gwamnati da al’umma.”

Masanin harkokin tsaro, Dr. Kabiru Adamu, ya bayyana cewa gargadin Gwamna Sani ya yi daidai da bukatar ƙara zurfafa haɗin kai. A cewarsa, tsaro “ba aikin soja kaɗai ba ne, aikin al’umma baki ɗaya ne.”

Shi ma wani tsohon jami’in tsaro, Col. Hassan Umar (rtd.), ya ce siyasantar da matsalar tsaro na iya lalata ƙoƙarin da ake yi wajen samun zaman lafiya. “Idan aka rika amfani da tsaro a matsayin makamin siyasa, ana rage wa jami’an tsaro ƙarfin guiwa, kuma hakan na iya jawo matsala fiye da mafita,” in ji shi.

Gwamnan ya ƙara da cewa akwai buƙatar a haɗa kai tsakanin gwamnati, shugabannin gargajiya, da malaman addini wajen yaƙar matsalar rashin tsaro. Ya kuma yi kira ga matasa da su guji shiga harkokin da ka iya jefa rayuwarsu cikin haɗari.

KTG Hausa News

Address

Kano, Road Azare, Bauchi, State
Katagum
08160438660

Telephone

+2347067658337

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KTG Hausa News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to KTG Hausa News:

Share