11/07/2026
A Ƙalla Manoma 5,000 Za Su Amfana Yayin da Tafidan Ɗandume Ya Ƙaddamar da Shirin Tallafa wa Manoma a Jihar Katsina
Kamfanin SHIAGRO NIGERIA LIMITED, mallakin Alhaji Ibrahim Shu'aibu, wanda aka fi sani da Tafidan Ɗandume, ya ƙaddamar da shirin rabon kayan noma ga manoma a Ƙaramar Hukumar Ɗandume ta Jihar Katsina.
An ƙaddamar da shirin ne a ranar Asabar, 11 ga Yuli, 2026, a ƙarƙashin Renewed Hope Smallholder Farmers Support and Value Chain Programme, wanda ake aiwatarwa tare da haɗin gwiwar Bankin Noma na Najeriya (BOA).
A cewar Shugaban Kamfanin SHIAGRO NIGERIA LIMITED, Alhaji Ibrahim Shu'aibu (Tafidan Ɗandume), kamfaninsa na cikin kamfanoni 20 da Gwamnatin Tarayya ta zaɓa domin aiwatar da wannan shiri a sassa daban-daban na ƙasar.
Ya bayyana cewa a kalla manoma 5,000 ne ake sa ran za su amfana da shirin, inda za a raba musu ingantattun iri, taki da magungunan kashe kwari domin ƙara yawan amfanin gona da bunƙasa harkar noma a Jihar Katsina.
Sai dai ya jaddada cewa kayan noman ba tallafi ne kai tsaye ba, domin za a ba manoman su ne a matsayin bashi, wanda za su mayar bayan sun girbe amfanin gonarsu.
Ya kuma bayyana cewa an tanadi tsarin da zai bai wa manoma damar sayar da ragowar amfanin gonarsu a farashin da ya dace idan s**a buƙata, domin tabbatar da samun riba mai kyau.
Alhaji Ibrahim Shu'aibu ya buƙaci waɗanda za su ci gajiyar shirin da su kiyaye dukkan sharuɗɗan da aka gindaya, musamman mayar da abin da aka ba su a kan lokaci, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen faɗaɗa shirin domin ƙarin manoma su ci gajiyarsa a nan gaba.
Da yake jawabi a wajen taron, Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Ɗandume kuma wakilin Shugaban Ƙaramar Hukumar, Alhaji Basiru Musa, ya ce shirin zai taimaka matuƙa wajen bunƙasa harkar noma da inganta rayuwar manoma a Ɗandume da sauran sassan Jihar Katsina.
Taron ya samu halartar wakilin Shugaban Ƙaramar Hukumar Funtua, Babangida Ibrahim Mailayu, Farfesa Muhammad Yusuf, Alhaji Bello Bashir Ɗanmaliki, wakilin Hakimin Ɗandume, da sauran manyan baƙi.
11 ga Yuli, 2026