Funtua Zone Reporters

Funtua Zone Reporters Muna Maku Barka da zuwa shafinmu Domin samun labaran Duniya kasance da jaridar Funtua Zone Reporters
(1)

20/09/2025

---

📷 Bidiyo
Jawabin Jagoran ’Yan Bindiga a Zaman Sulhu Kacalla dawa

A Ƙananan Hukumomin Dandume da Sabuwa Sun Gudanar da Zaman Sulhu da ’Yan Bindiga

A yau, Ƙananan Hukumomin Dandume da Sabuwa sun gudanar da zaman sulhu tare da ’yan bindigar daji domin tabbatar da zaman lafiya da tsaro a fadin yankin.

Wannan zaman sulhu ya kasance wani muhimmin mataki na ƙoƙarin kawo ƙarshen matsalar tsaro da kuma tabbatar da kwanciyar hankali ga mazauna yankunan, tare da dakatar da hare-haren da s**a addabi al’umma a baya-bayan nan.

Jagoran ’yan bindigar da ya halarci taron ya yi jawabi inda ya bayyana aniyar su ta sauke makamai da kuma shiga sahun zaman lafiya tare da sauran al’umma, idan aka cika musu wasu muhimman sharudda na tsaro da walwala.

Rahotanni sun bayyana cewa shugabannin al’umma, dattawa, sarakunan gargajiya da jami’an tsaro duk sun halarci zaman tare da fatan samun ingantaccen sakamako ga kowa da kowa.

Labari da duminsa; Yan bindiga karkashin jagorancin Jelani dake yankin Farin Dutse kan hanyar Maigora zuwa Faskari, suma...
17/09/2025

Labari da duminsa; Yan bindiga karkashin jagorancin Jelani dake yankin Farin Dutse kan hanyar Maigora zuwa Faskari, suma sun sako karin wasu mata uku yan garin Kadisau da s**a yi garkuwa da su a kwanakin baya

Cikakken labari mai hade da bidiyo na nan tafe

Yan Bindiga a ƙaramar Hukumar Faskari ta Jihar Katsina Sanadiyyar Sasanci Sun saki Mutane 28 da suke Garkuwa Dasu Ƙarƙas...
17/09/2025

Yan Bindiga a ƙaramar Hukumar Faskari ta Jihar Katsina Sanadiyyar Sasanci Sun saki Mutane 28 da suke Garkuwa Dasu Ƙarƙashin Jagoran ɗan bindiga Isiya kwashen Garwa,

Allah kiyaye Gaba ya kuɓutar Mana da Sauran yan Uwan Mu Dake Hannun Su ya kawo Mana ƙarshen Su da Masu Ɗaukar Nauyin Su a yankunan Mu da ƙasa Baki ɗaya Amen,

Karamar hukumar a Faskari, Jihar Katsina tabi sahun kananan hukumomin Jihar wajen yin sulhu da yan bindiga masu tada kay...
14/09/2025

Karamar hukumar a Faskari, Jihar Katsina tabi sahun kananan hukumomin Jihar wajen yin sulhu da yan bindiga masu tada kayar baya a Jihar.

Rahotanni daga ƙaramar hukumar Faskari, a Jihar Katsina, sun tabbatar da cewa an cimma yarjejeniyar sasanci tsakanin al’ummar yankin da wasu daga cikin ƴan bindiga da ke addabar yankin tsawon lokaci.

Majiyar mu ta Katsina Daily News ta ruwaito cewa wannan yarjejeniya ta samo asali ne a yayin wani zama na musamman da aka gudanar, inda aka cimma matsayar cewa ƴan bindigar za su daina kai hare-hare da cutar da al’umma, sai dai za su rika shigowa gari cikin lumana domin gudanar da rayuwar su ta yau da kullum.

A yayin taron, jagoran ƴan bindigar da aka fi sani da Ado Aleru ya yi alƙawarin cewa: “Daga yanzun kowa ya je gonarsa hankalinsa kwance, ba abin da zai ƙara faruwa da shi ko zullumin harin ƴan bindiga ko’ina a fadin ƙaramar hukumar Faskari.”

Matakin dai ya zo ne bayan dogon lokaci na tashin hankali da kashe-kashe, garkuwa da mutane tare da kuma tilasta wa wasu mazauna yankin barin muhallansu.

Sai dai ra’ayoyin jama’a sun bambanta kan wannan mataki; yayin da wasu ke ganin shi a matsayin nasara da ci gaba wajen dawo da zaman lafiya, wasu kuma na nuna damuwa kan amincewa da ƴan bindiga su ci gaba da shigowa gari ba tare da an hukunta su ba.

Ana sa ran hukumomi za su ci gaba da sanya idanu kan yarjejeniyar tare da ɗaukar matakan da s**a dace domin tabbatar da dorewar zaman lafiya a yankin.

Yanzu Yanzu Rahotanni daga garin Bilbils da ke cikin karamar hukumar Faskari, Sun Tabbatar da cewa Ana can ana gudanar d...
14/09/2025

Yanzu Yanzu Rahotanni daga garin Bilbils da ke cikin karamar hukumar Faskari, Sun Tabbatar da cewa Ana can ana gudanar da taron sassanci da Yan bindiga masu garkuwa da mutane. Allah yasa wannan mataki ya zama alkhairi ga kasa baki ɗaya, tare da kawo sauƙi da zaman lafiya a yankin.

"Ba kowa ne ke da karfin zuciyar kare soyayya ba. Amma wannan matar — ta tsaya tsayin daka, ta fuskanci al’umma, ta kare...
10/09/2025

"Ba kowa ne ke da karfin zuciyar kare soyayya ba. Amma wannan matar — ta tsaya tsayin daka, ta fuskanci al’umma, ta kare mijinta a fili, kuma ta zamo abar koyi ga mata da yawa a Arewacin Najeriya.

Ga cikakken tarihin Hajiya Hafsatu, matar farko ta Marigayi Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto:

Hajiya Hafsatu ta fito daga gidan sarautar Sokoto. Ita 'yar Waziri Abdulkadir Maccido ne, wanda ya fito daga dangin Gidadawa — dangin da s**a taka muhimmiyar rawa wajen kafuwar Daular Usmaniyya ta Sokoto. [1]

Ta kasance matar farko ga Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto. A matsayinta na matar shugaba, ta kasance ginshiki a rayuwarsa, tana goyon bayansa a dukkan al'amuransa na siyasa da rayuwar sa

A ranar 15 ga Janairu, 1966, lokacin juyin mulkin soja na farko a Najeriya, Hajiya Hafsatu ta rasa rayuwarta tare da mijinta, Sir Ahmadu Bello, lokacin da sojoji s**a kai hari gidansu a Kaduna. Wannan harin ya yi sanadiyyar mutuwar su duka. [2]

Hajiya Hafsatu ta bar tarihi mai cike da sadaukarwa, biyayya, da kishin kasa. Rayuwarta ta zama abin koyi ga matan Najeriya, musamman wajen nuna goyon baya jajircewa da kuma tsayawa tare da mazajensu a lokutan da suke fuskantar kalubale.

Asalin Hoto A Comment Section 👇





08/09/2025
Harin ’Yan Bindiga a Garin Magaji Wando na Ƙaramar Hukumar DandumeA daren Juma’a zuwa Asabar, 5 zuwa 6 ga Satumba 2025, ...
06/09/2025

Harin ’Yan Bindiga a Garin Magaji Wando na Ƙaramar Hukumar Dandume

A daren Juma’a zuwa Asabar, 5 zuwa 6 ga Satumba 2025, ’yan bindiga sun kai hari a garin Magaji Wando da ke ƙaramar hukumar Dandume, Jihar Katsina.

Rahotanni daga mazauna yankin sun ce maharan sun kashe mutum bakwai, sun raunata akalla takwas, sannan s**a yi awon gaba da mutane uku mata biyu da yaro ɗaya.

Wani mazaunin garin ya shaida wa majiyar Funtua zone Reporter cewa maharan sun yi musayar wuta da al’ummar garin da s**a yi ƙoƙarin ceto mutanen da aka sace. A yayin hakan ne aka kashe mutum biyar nan take tare da harbin wasu biyu.

Daga baya, jami’an tsaro da ke aikin sintiri a yankin sun shiga domin tallafa wa al’umma, inda s**a kwashe waɗanda s**a jikkata zuwa asibiti. Sai dai a kan hanyarsu ta dawowa, ’yan bindigar sun yi musu kwanton bauna, inda s**a sake kashe wasu mutane biyu tare da jikkata takwas, sannan s**a ƙona motar jami’an tsaron.

Mutum biyar na kwance a Babbar Asibitin Funtua, yayin da aka tura mutum uku zuwa babban asibitin Katsina saboda munin raunukan da s**a samu.

A cewar mazauna yankin, mace guda daga cikin waɗanda aka yi garkuwa da su ta samu damar tserewa.

Masu magana da yawun al’ummar yankin sun bukaci jami’an tsaro da su ɗauki matakan gaggawa tare da amfani da motocin sulke da aka kawo domin taimakawa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Funtua zone Reporter

03/09/2025

Daga zawiyyar Sheikh Abdullahi Dandume, al’ummar Musulmi daga sassa daban-daban na jihar Katsina da wajenta suna taruwa domin gudanar da Maulidi. Wannan wuri ya kasance cibiyar taro da ake gudanar da addu’o’i, karatun Alkur’ani da wa’azi, tare da tunawa da haihuwar Annabi Muhammad (SAW).”

Address

Katsina Ala

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Funtua Zone Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Funtua Zone Reporters:

Share

Category