Funtua Zone Reporters

Funtua Zone Reporters Muna Maku Barka da zuwa shafinmu Domin samun labaran Duniya kasance da jaridar Funtua Zone Reporters
(1)

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara ta kâshe shugaban ’yan bindiga, ta k**a mutum uku tare da kwato mak**ai da babura.A w...
11/06/2026

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara ta kâshe shugaban ’yan bindiga, ta k**a mutum uku tare da kwato mak**ai da babura.

A wani samame da jami’an Sashen Yaki da Manyan Laifuka (VCRU) s**a kai a yankin Birisawa da ke Karamar Hukumar Gummi bayan samun sahihan bayanan sirri, sun yi artabu da ’yan bindiga. A yayin musayar wuta, an kashe shugaban kungiyar ’yan bindigar, an k**a mutum uku, yayin da wasu s**a tsere da raunukan harbi.

Jami’an sun kuma lalata sansanin ’yan bindigar tare da kwato bindigogi uku da babura biyar. Rundunar ta ce tana ci gaba da farautar sauran wadanda s**a tsere domin tabbatar da tsaro a jihar.

Iran Ta Kaddamar Da Hare-haren Ramuwar Gayya Kan Sansanonin Amurka a Gabas ta TsakiyaRahotanni sun ce rundunar kare juyi...
10/06/2026

Iran Ta Kaddamar Da Hare-haren Ramuwar Gayya Kan Sansanonin Amurka a Gabas ta Tsakiya

Rahotanni sun ce rundunar kare juyin juya halin Musulunci ta Iran (IRGC) ta harba mak**ai masu linzami da jirage marasa matuƙa domin kai hare-hare kan wasu sansanonin sojojin Amurka da ke ƙasashen Bahrain, Kuwait da Jordan.

Hare-haren na zuwa ne a matsayin martani ga hare-haren da Amurka ta kai kan wasu wuraren soji a Iran a baya-bayan nan.

Daga cikin wuraren da aka ce an kai wa hari akwai hedikwatar rundunar ruwa ta biyar ta Amurka da ke Bahrain, sansanin sojin saman Ali Al Salem da ke Kuwait, da kuma sansanin sojin saman Al-Azraq da ke Jordan.

Bayan hare-haren, ƙasashen da abin ya shafa sun kunna tsarin kariyar sararin samaniyarsu, yayin da aka samu rahotannin katsewa da jinkirin zirga-zirgar jiragen sama a wasu yankuna.

Rahotannin farko sun nuna cewa yawancin mak**an da Iran ta harba an dakile su, kuma babu rahoton asarar rayuka ko wata babbar barna da ta auku a sansanonin sojin Amurka da aka kai wa hari.

Masu sa ido na ganin cewa wannan na daga cikin manyan hare-haren kai tsaye da Iran ta kai kan sansanonin sojin Amurka a yankin cikin 'yan shekarun nan, lamarin da ke ƙara tayar da hankalin al'umma kan yiwuwar ƙarin rikici a Gabas ta Tsakiya.

*Domin samun sabbin labarai daga Gabas ta Tsakiya da sauran sassan duniya, ku ci gaba da bibiyar shafin Sisinbaki Communication.*

An gudanar da Sallar Ga'ib ga Dattijo Hon. Yusuf, wanda ya rasu a hannun 'yan bindiga An gudanar da Sallar Jana’iza ta G...
10/06/2026

An gudanar da Sallar Ga'ib ga Dattijo Hon. Yusuf, wanda ya rasu a hannun 'yan bindiga

An gudanar da Sallar Jana’iza ta Ga'ib (Sallar Mamacin da ke nesa) ga shugaban ƙungiyar Izala (JIBWIS) reshen ƙaramar hukumar Koko-Besse ta jihar Kebbi, Marigayi Hon. Yahaya Tanko Besse, da Yammacin ranar Talata a garin Besse.

Marigayin ya rasu ne bayan da wasu ‘yan bindiga s**a yi garkuwa da shi tun ranar 18 ga watan Mayun 2026, inda labarin rasuwarsa ya karade kafafen yaɗa labarai a yau.

Dandazon al’umma da s**a haɗa da malamai, shugabannin addini, jami’an gwamnati, da mazauna yankin ne s**a halarci jana’izar domin yi wa marigayin addu’ar samun rahama.

SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR FUNTUA YA SAKE RABA MOTOCI GA KANSILOLI DOMIN INGANTA AYYUKAN GUDANARDA OFFICE.A yau Litinin, 8...
08/06/2026

SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR FUNTUA YA SAKE RABA MOTOCI GA KANSILOLI DOMIN INGANTA AYYUKAN GUDANARDA OFFICE.

A yau Litinin, 8 ga Yuni, 2026, Shugaban Karamar Hukumar Funtua, Hon. Alhaji Abdulmutallab Jibrin Sulaiman Goya, ya sake nuna jajircewarsa wajen tallafa wa abokan aikinsa da inganta ayyukan gudanarwa, inda ya mika sabbin motoci guda uku ga wasu kansiloli uku na karamar hukumar.

Wannan na zuwa ne bayan da a kwanakin baya ya raba wasu motoci guda uku ga wasu kansiloli, wanda hakan ya kawo adadin kansilolin da s**a amfana da motocin zuwa mutum shida cikin kansiloli goma sha ɗaya na Karamar Hukumar Funtua.

Kansilolin da s**a amfana da wannan kashi na biyu sun hada da:

- Hon. Abdullahi Mai Turare, Kakakin Majalisar Karamar Hukumar Funtua kuma Kansilan Sabon Gari Ward.
- Hon. Surajo Goya, Kansilan Mazabar Goya Ward.
- Hon. Nasiru Poly, Kansilan Mazabar Dandutse Ward.

Wannan mataki na daga cikin manufofin Shugaban Karamar Hukumar na sauke nauyin da ke kan abokan aikinsa tare da samar musu da hanyoyin gudanar da ayyukansu cikin sauki da inganci, domin su ci gaba da yi wa al'ummar mazabunsu hidima yadda ya k**ata.

Haka kuma, wannan kokari ya yi daidai da manufar gwamnatin Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umar Radda, wadda ta mayar da hankali kan samar da ingantattun kayan aiki ga shugabanni a matakai daban-daban domin inganta ayyukan gwamnati da kusantar da ci gaba ga al'umma.

~Umar Musa Sheme
Motocin da aka raba sun kasance masu kyau da inganci, inda guda biyar daga cikinsu suke kirar Peugeot 307, yayin da motar da aka bai wa Kakakin Majalisar ita ce kirar Toyota Corolla LE 2013, wadda ke cikin kyakkyawan yanayi kuma mai nagartaccen aiki.

Al'ummar Karamar Hukumar Funtua na ci gaba da yaba wa wannan gagarumin kokari na Shugaban Karamar Hukumar, wanda ke nuna kishin ci gaban yankinsa da kuma kulawa da walwalar abokan aikinsa domin samun ingantaccen shugabanci a matakin karamar hukuma.

DA ƊUMI-ƊUMINSA: Ɗan Majalisar Tarayya na Funtua da Ɗandume Ya Fice Daga APC Zuwa PDPƊan Majalisar Wakilai mai wakiltar ...
06/06/2026

DA ƊUMI-ƊUMINSA: Ɗan Majalisar Tarayya na Funtua da Ɗandume Ya Fice Daga APC Zuwa PDP

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar ƙananan hukumomin Funtua da Ɗandume a Majalisar Tarayya, Abubakar Mohammad Gardi, ya fice daga jam’iyyar APC tare da sauya sheƙa zuwa jam’iyyar PDP.

Sauya sheƙar tasa na zuwa ne a daidai lokacin da harkokin siyasar zaɓen shekarar 2027 ke ƙara ɗaukar zafi a jihar Katsina da ma faɗin ƙasar nan.

Rahotanni sun nuna cewa matakin da Hon. Gardi ya ɗauka na iya sauya yanayin siyasa a yankin Funtua da Ɗandume, musamman ganin irin tasirin da yake da shi a tsakanin magoya bayansa.

Sai dai zuwa yanzu, ɗan majalisar bai fito fili ya bayyana cikakken dalilin da ya sa ya bar APC ba, yayin da jam’iyyun biyu ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.

Masu sa ido kan harkokin siyasa na ci gaba da bibiyar wannan sauyi, wanda ake ganin na iya yin tasiri ga shirye-shiryen jam’iyyu gabanin babban zaɓen shekarar 2027.

WANNAN ABIN KUNYA NE: Tsohon kakakin rundinar Sojin Nigeria General Rabe Abubakar da matarsa wanda barayin daji s**ayi g...
06/06/2026

WANNAN ABIN KUNYA NE: Tsohon kakakin rundinar Sojin Nigeria General Rabe Abubakar da matarsa wanda barayin daji s**ayi garkuwa dasu, suna rokon a ceto su

Gaskiya wannan babban abin kunya ne, kuma abin tsoro, ace General na Soja yana hannun barayin daji da suke a cikin Kasar Gwamnati mai cikakken iko

Ya k**ata a sake lissafi gaskiya, bai k**ata haka yana faruwa ba, kuma babu uzuri akan lamarin tsaro, ayi abinda ya dace kawai

Allah Ka kawo mana karshen wannan masifa!

Daga Datti Assalafiy

Innalillahii Wa Inna Ilaihir Raji'un 😭Wannan ba magana bace ta siyasa, ba magana bace ta ƴan Kwankwasiyya ko Atiku, ko k...
05/06/2026

Innalillahii Wa Inna Ilaihir Raji'un 😭

Wannan ba magana bace ta siyasa, ba magana bace ta ƴan Kwankwasiyya ko Atiku, ko kuma ta wani ɓangare na Addini ko ƙabila. Magana ce ta kishin al'ummar mu da ahalinmu.

Wallahi Tallahi babu wani yanki na Nijeriya da za'ai musu wannan cin kashin kajin a zauna lafiya. Walau Bayarabe ko Inyamuri. Yankin Arewa ne kaɗai za'ai musu wannan cin kashin kajin kaji tsit.

Wannan cin mutunci ne, keta alfarma ce. Bayan an yi garkuwa da ahalinku, a kuma dinga binsu ɗaya bayan ɗaya ana musu fyaɗe. Hasbunallahu Wa Ni'imal Wakili 😭

Wannan cin mutunci ne. Wannan wulaƙanci ne kuma keta alfarmar duk wani ɗan Arewa ne.

Shin bamu da gwamnati ne?
Bamu da jami'an tsaro ne?
Bamu da wakilai ne?

Wane irin bala'i ne muke ciki haka.

Ba maganar ni Kwankwasiyya nike ko Gandujiyya ba. Magana ce ta tsaro. Tsaron al'ummar mu, mutanen mu, kuma ahalin mu.

Idan yau ta faru da wani, kaima zata iya faruwa da kai. Ko da ƙanwar ka, ko gyatumar ka ko wani dangin ka.

Idan yau ta faru a Zamfara, zata iya faruwa a Katsina, Kano, Jigawa, Taraba ko kuma wani yanki da ke tare da mu.

Idan har muka yadda muryoyin mu sun dakushe, to wannan cin mutuncin zai ci gaba ne.

Allah Ubangiji ka tarwatsa farincikin duk wanda yake da hannu ko masaniya a cikin wannan iskancin dake faruwa 🙏

Allah ya isa. Ba mu yafe ba 😭😭

Mailafiya.

04/06/2026

Innalillahi wa inna ilihi Rajiun

Hon. Murtala Muhammad Malamiyya Ya Mika Godiya Ga Alhaji Abdullahi Abubakar Albasu Bisa Kyautar MotaTsohon ɗan takarar k...
04/06/2026

Hon. Murtala Muhammad Malamiyya Ya Mika Godiya Ga Alhaji Abdullahi Abubakar Albasu Bisa Kyautar Mota

Tsohon ɗan takarar kujerar Majalisar Dokokin Jihar Katsina a ƙarƙashin Jam’iyyar APC mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Funtua, Hon. Murtala Muhammad Malamiyya, ya bayyana matuƙar farin cikinsa tare da miƙa saƙon godiya ga Shugaban Rukunin Kamfanonin A A Albasu Nigerian Limited, Alhaji Abdullahi Abubakar Albasu, bisa kyautar mota kirar Toyota Corolla S da ya yi masa.

Hon. Malamiyya ya ce wannan karamci da Jagora Alhaji Abdullahi Abubakar Albasu ya nuna masa ya ƙara tabbatar da irin halayen taimako, tausayi da kulawar da yake bai wa al’umma da abokan hulɗarsa.

Ya bayyana cewa kalmomi ba za su isa su bayyana irin godiya da jin daɗin da yake yi ba kan wannan kyauta mai daraja, wadda ya ce ta zo a lokacin da take da matuƙar muhimmanci a gare shi.

An miƙa motar ne ta hannun Manajan Darakta (M.D) na kamfanin A A Albasu Nigerian Limited, Alhaji Lawal Yaro Funtua, tare da Alhaji Auwalu Gwaigwaye, a wani taro da aka gudanar a gaban Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙaramar Hukumar Funtua, Malam Sani, tare da B.B Oil, kansilolin Ƙaramar Hukumar Funtua da sauran masu ruwa da tsaki na wannan gida mai albarka, ciki har da Alhaji Nuhu Shu’aibu (Mai Masara).

A cikin saƙon godiyarsa, Hon. Murtala Muhammad Malamiyya ya yabawa Alhaji Abdullahi Abubakar Albasu bisa irin gudunmawar da yake bayarwa wajen tallafa wa al’umma da inganta rayuwar jama’a.

Ya ce" Ina miƙa godiyata ta musamman ga Jagora Alhaji Abdullahi Abubakar Albasu bisa wannan kyauta mai daraja. Hakika na ji daɗi matuƙa, kuma ba zan manta da wannan karamci ba. Allah Ya saka masa da alheri, Ya ƙara masa lafiya, arziki, ɗaukaka da nisan kwana.”

Ya kuma yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya sanya albarka a cikin wannan kyauta, Ya bunƙasa harkokinsa, Ya ci gaba da ba shi ikon taimakon al’umma da gudanar da ayyukan alheri.

Masu halartar taron sun bayyana wannan kyauta a matsayin wata alama ta kyakkyawar dangantaka, girmamawa da karamci da ke tsakanin Jagora Alhaji Abdullahi Abubakar Albasu da waɗanda yake hulɗa da su.

Taron ya gudana cikin yanayi na farin ciki da fatan alheri, inda mahalarta s**a yi addu’o’in samun ƙarin nasara da ci gaba ga Jagora Alhaji Abdullahi Abubakar Albasu da kuma Hon. Murtala Muhammad Malamiyya.

Funtua zone Reporter

Zaɓen 2027, Arewa za ta yi wa Tinubu sakayya da kuri'u masu yawa — MatawalleKaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya ...
01/06/2026

Zaɓen 2027, Arewa za ta yi wa Tinubu sakayya da kuri'u masu yawa — Matawalle

Karamin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya bayyana cewa yana da yakinin al'ummar Arewacin Najeriya za su mara wa Bola Ahmed Tinubu baya sosai a zaben shekarar 2027.

Matawalle ya ce wannan goyon baya zai kasance ne a matsayin nuna godiya ga ayyukan ci gaba da gwamnatin Tinubu ta aiwatar a yankin Arewa tun bayan hawanta mulki.

Jaridar Daily Nigerian ta ambato shi ya ce, yankin ya amfana da muhimman ayyukan more rayuwa da sauran shirye-shiryen ci gaba da gwamnatin tarayya ke gudanarwa.

Address

Katsina Ala

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Funtua Zone Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Funtua Zone Reporters:

Share