22/10/2025
Matashi ya ƙwaƙule wa ƙanwarsa idanu a Bauchi don yin tsafi.
Rundunar ‘yansanda a jihar Bauchi ta tabbatar da k**a wani matashi da ake zargi da ƙwaƙule wa ƙanwarsa idanu biyu don yin tsafin neman kuɗi a ƙaramar hukumar Ganjuwa ta jihar.
Majiyoyi sun ce lamarin ya faru ne a gari Wailo, inda wanda ake zargin, Auwalu Muhammad, ya ɗauki ƙanwarsa mai shekara bakwai, Rukayya Muhammad, zuwa daji, ya yi mata duka, sannan ya ƙwaƙule idanunta biyun.
A cewar mahaifinsu, yaran biyu dukkansu uwa ɗaya uba ɗaya suke, kuma Rukayya na fama da matsanancin rauni sak**akon mummunan abin da ya same ta.
Tuni daia aka garzaya da yaribyar zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) da ke Bauchi, inda likitoci s**a tabbatar da cewa ta rasa idanunta gaba ɗaya.
Likitan da ya duba ta, Dr. Shahir Umar Bello, ƙwararre a fannin kula da ido, ya bayyana cewar “Idanunta duka biyu sun lalace gaba ɗaya, kuma ba za ta iya gani ba har abada.”
Rahotanni sun ce an k**a wanda ake zargin, kuma jami’an tsaro na ci gaba da gudanar da bincike domin tattara cikakken bayani kan wannan danyen aiki da kuma wadanda s**a haɗa kai da shi.