Funtua Zone Reporters

Funtua Zone Reporters Muna Maku Barka da zuwa shafinmu Domin samun labaran Duniya kasance da jaridar Funtua Zone Reporters

An Karrama Tsohon Baturen ’Yan Sanda da Marigayi ASP Sale Ya’u a DandumeA ranar Alhamis, 31 ga Yuli, 2052, an gudanar da...
31/07/2025

An Karrama Tsohon Baturen ’Yan Sanda da Marigayi ASP Sale Ya’u a Dandume

A ranar Alhamis, 31 ga Yuli, 2052, an gudanar da bikin karrama tsohon Baturen ’yan sanda na karamar hukumar Dandume, CSP Emmanuel Zangina, da marigayi ASP Sale Ya’u, tsohon jami’in hulda da jama’a na rundunar ’yan sanda a yankin.

Bikin ya gudana ne a harabar sakatariyar karamar hukumar Dandume, karkashin jagorancin shugaban karamar hukumar, Hon. Bashir Sabi’u Musa (Gyazama), tare da hadin gwiwar kwamitin tsaron garin Dandume.

An karrama CSP Emmanuel Zangina ne bisa jajircewarsa da kwarewa a aiki, da kuma karin girma da aka yi masa tare da sauya masa wurin aiki zuwa Shaidam a jihar Filato.

A yayin taron, mahalarta sun bayyana CSP Zangina da marigayi ASP Sale Ya’u a matsayin jaruman da s**a nuna kwazo da sadaukarwa a lokacin da suke bakin aiki, musamman wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Shugaban karamar hukumar, Hon. Bashir Sabi’u Musa, ya ce tun bayan tafiyar CSP Zangina, an nada CSP Muhammad Haruna Uba a matsayin sabon baturen ’yan sanda a Dandume. Ya ce sabon baturen ya riga ya fara daukar matakai na gyaran motocin sintiri da karfafa tsaro domin tunkarar hare-haren ’yan bindiga a yankin.

Ya kuma bukaci kwamitin tsaron gari da ya fadada ayyukansa zuwa dukkan gundumomi 11 da ke cikin karamar hukumar domin tabbatar da tsaro mai dorewa.

Mai martaba Hakimin Dandume, Alhaji Ja’afar Ibrahim Sambo, wanda ya samu wakilcin Alhaji Shamsuddeen Ja’afar Ibrahim, ya yaba da aikin CSP Zangina tare da kiraye-kirayen da sabon baturen ya ci gaba da jajircewa wajen kare lafiyar al’umma.

Kwamitin tsaron Dandume ya yi amfani da damar wajen bayyana wasu daga cikin nasarorin da s**a samu da kalubalen da suke fuskanta, tare da roƙon gwamnatin da al’umma da su ci gaba da bayar da goyon baya ga jami’an tsaro.

Abokan aikin marigayi ASP Sale Ya’u da wasu daga cikin al’ummar Dandume sun bayyana irin kishin kasa da sadaukarwar da ya nuna, tare da cewa ya rasu ne yayin da yake kokarin dakile harin ’yan bindiga a kan hanyar Magaji Wando a bara.

Taron ya samu halartar manyan baki da s**a hada da sarakuna, shugabannin al’umma, ’yan kasuwa, wakilan kungiyoyi, mata, matasa, da ’yan uwa da abokan arziki. An rufe taron da addu’o’in zaman lafiya da fatan alheri ga yankin karamar hukumar Dandume.

An Karrama Tsohon Baturen ’Yan Sanda da Marigayi ASP Sale Ya’u a DandumeA ranar Alhamis, 31 ga Yuli, 2052, an gudanar da...
31/07/2025

An Karrama Tsohon Baturen ’Yan Sanda da Marigayi ASP Sale Ya’u a Dandume

A ranar Alhamis, 31 ga Yuli, 2052, an gudanar da bikin karrama tsohon Baturen ’yan sanda na karamar hukumar Dandume, CSP Emmanuel Zangina, da marigayi ASP Sale Ya’u, tsohon jami’in hulda da jama’a na rundunar ’yan sanda a yankin.

Bikin ya gudana ne a harabar sakatariyar karamar hukumar Dandume, karkashin jagorancin shugaban karamar hukumar, Hon. Bashir Sabi’u Musa (Gyazama), tare da hadin gwiwar kwamitin tsaron garin Dandume.

An karrama CSP Emmanuel Zangina ne bisa jajircewarsa da kwarewa a aiki, da kuma karin girma da aka yi masa tare da sauya masa wurin aiki zuwa Shaidam a jihar Filato.

A yayin taron, mahalarta sun bayyana CSP Zangina da marigayi ASP Sale Ya’u a matsayin jaruman da s**a nuna kwazo da sadaukarwa a lokacin da suke bakin aiki, musamman wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Shugaban karamar hukumar, Hon. Bashir Sabi’u Musa, ya ce tun bayan tafiyar CSP Zangina, an nada CSP Muhammad Haruna Uba a matsayin sabon baturen ’yan sanda a Dandume. Ya ce sabon baturen ya riga ya fara daukar matakai na gyaran motocin sintiri da karfafa tsaro domin tunkarar hare-haren ’yan bindiga a yankin.

Ya kuma bukaci kwamitin tsaron gari da ya fadada ayyukansa zuwa dukkan gundumomi 11 da ke cikin karamar hukumar domin tabbatar da tsaro mai dorewa.

Mai martaba Hakimin Dandume, Alhaji Ja’afar Ibrahim Sambo, wanda ya samu wakilcin Alhaji Shamsuddeen Ja’afar Ibrahim, ya yaba da aikin CSP Zangina tare da kiraye-kirayen da sabon baturen ya ci gaba da jajircewa wajen kare lafiyar al’umma.

Kwamitin tsaron Dandume ya yi amfani da damar wajen bayyana wasu daga cikin nasarorin da s**a samu da kalubalen da suke fuskanta, tare da roƙon gwamnatin da al’umma da su ci gaba da bayar da goyon baya ga jami’an tsaro.

Abokan aikin marigayi ASP Sale Ya’u da wasu daga cikin al’ummar Dandume sun bayyana irin kishin kasa da sadaukarwar da ya nuna, tare da cewa ya rasu ne yayin da yake kokarin dakile harin ’yan bindiga a kan hanyar Magaji Wando a bara.

Taron ya samu halartar manyan baki da s**a hada da sarakuna, shugabannin al’umma, ’yan kasuwa, wakilan kungiyoyi, mata, matasa, da ’yan uwa da abokan arziki. An rufe taron da addu’o’in zaman lafiya da fatan alheri ga yankin karamar hukumar Dandume.

Funtua zone Reporters

YAN BINDIGA SUN KAI HARI HAYIN DAN BINNI A YANKIN GOYA DAKE FUNTUA A Daren jiya laraba kafin wayewar yau alhamis rahotan...
31/07/2025

YAN BINDIGA SUN KAI HARI HAYIN DAN BINNI A YANKIN GOYA DAKE FUNTUA

A Daren jiya laraba kafin wayewar yau alhamis rahotanni s**a zo mana yan bindiga sun kai hari Unguwar Hayin Danbinni dake shiyyar Goya karkashin karamar hukumar Funtua. Majiyar mu ta shaida mana yan bindigar sun kashe wani mutum mai suna Isiya Halliru tare da ɗauke babban limamin juma'a na garin s**a tafi dashi.

Zuwa hada wannan rahoton babu wata sanarwa daga hukumomin tsaro. Amma ko a cikin makon nan jami'an yansanda a jihar Katsina sun samu nasarar kubutar da wasu mutane 28 da dabbobi a yankin karamar hukumar Sabuwa bayan hare hare da dama da yan bindigar s**a kai a sassa daban daban na yankunan kudancin Katsina wato shiyyar Funtua.

Sanata Muntari Dandutse Ya Aika da Tallafi Ga 'Yan Gudun Hijira a BakoriSanatan da ke wakiltar Shiyyar Funtua a Majalisa...
29/07/2025

Sanata Muntari Dandutse Ya Aika da Tallafi Ga 'Yan Gudun Hijira a Bakori

Sanatan da ke wakiltar Shiyyar Funtua a Majalisar Dattawa, Sanata Muntari Mohammad Dandutse, ya aika da kayan tallafi ga ‘yan gudun hijira da ke zaune a ƙaramar hukumar Bakori.

Kayan tallafin sun haɗa da buhunan masara masu nauyin kilo 50 guda 30, ledojin ruwan sha guda 300 da kuma kuɗin cefane naira 300,000.

An isar da kayan ne ta hannun wakilan Sanatan a ƙaramar hukumar, ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban ƙaramar hukumar Bakori, Hon. Abubakar Shuaibu Solo.

Yayin da yake isar da tallafin, Hon. Solo ya ce Sanata Dandutse na cikin damuwa kan halin da al'umma ke ciki, musamman yadda matsalar tsaro ke ƙara tsananta a yankin.

Ya ƙara da cewa Sanatan zai ci gaba da ɗaukar matakai domin tallafa wa al’umma da kuma tabbatar da zaman lafiya mai ɗorewa a Shiyyar Funtua.

Shugaban kwamitin kula da ‘yan gudun hijira a Bakori, Alhaji Kabir Mamman, ya bayyana godiya a madadin al’umma da shugabannin ƙaramar hukumar, tare da tabbatar da cewa za a raba tallafin yadda ya dace.

Wannan na daga cikin matakan da Sanata Dandutse ke ɗauka domin rage raɗaɗin da al’umma ke fuskanta a sassan Shiyyar Funtua.

Rahoto: Jamilu Garkuwan Dandutse Media Reporters, Shiyyar Funtua

TIRƘASHI: Bayan caccakar da Kwankwaso ya yi: Gwamnatin Tinubu ta kira taro a Kaduna na kwanaki Biyu domin kowane minista...
29/07/2025

TIRƘASHI: Bayan caccakar da Kwankwaso ya yi: Gwamnatin Tinubu ta kira taro a Kaduna na kwanaki Biyu domin kowane minista ya fito ya yi bayanin a gaban dattawa da masu ruwa da tsaki irin ayyukan da Gwamnatin tarayya ke yi wa yankin Arewa a ma’aikatar sa,

Wannan dai na zuwa ne bayan da madugun yan adawa Rabi'u Musa Kwankwaso ya soki Gwamnatin Tinubu da cewa ta fifita yankin Kudu tana watsi da shiyyar Arewa a wajen ayyukan cigaba

Wane aiki Gwamnatin Tinubu ke yi a yankin ku?

Hon. Yahaya Nuhu Mahuta Ya Halarci Taron Rufe Gasar Premier League a DandumeA ranar Lahadi, 27 ga Yuli, 2025, dan majali...
28/07/2025

Hon. Yahaya Nuhu Mahuta Ya Halarci Taron Rufe Gasar Premier League a Dandume

A ranar Lahadi, 27 ga Yuli, 2025, dan majalisar jiha mai wakiltar karamar hukumar Dandume, Hon. Yahaya Nuhu Mahuta, ya halarci bikin rufe gasar Premier League da aka gudanar a babban filin wasa na Scorpion da ke cikin garin Dandume.

Taron, wanda ya samu halartar dimbin masoya kwallon kafa daga sassa daban-daban na karamar hukumar, ya kasance wani babban mataki na karrama kungiyoyin da s**a nuna bajinta a gasar da ta gudana cikin kwanciyar hankali da girmama juna.

Da yake jawabi a wajen taron, Hon. Yahaya Mahuta ya bayyana jin daɗinsa kan yadda aka gudanar da gasar, yana mai cewa hakan ya nuna irin hazaka da kwazon da matasan yankin ke da shi. Ya bayyana gasar a matsayin wata dama ta haɗa kan matasa da kuma inganta harkar wasanni a Dandume.

Ya ce A matsayina na wakilin al’umma, zan ci gaba da jajircewa wajen ganin an samar da sabon filin wasa a Dandume domin ƙarfafa sha’awar matasa da kuma bunkasa baiwarsu ta kwallon kafa."

Hon. Mahuta ya kuma bai wa hukumar shirya gasar tallafin kudi har naira dubu dari (₦100,000) domin ƙara ƙarfafa ayyukanta, tare da bayyana niyyarsa ta ɗaukar nauyin shirya wata sabuwar gasa ta matasa a nan gaba.

A nasa jawabin, shugaban hukumar kwallon kafa ta karamar hukumar Dandume, Alhaji Sulaiman Ibrahim Mairaguna, ya nuna godiya ga Hon. Mahuta bisa goyon bayan da yake bai wa harkar wasanni da ci gaban matasa. Ya kuma bukaci dan majalisar da ya taimaka wajen samar da babban filin wasa a yankin, yana mai jaddada cewa:

Matasan Dandume na da hazaka da kwazo, kuma suna da kishin ci gaba a fannin kwallon kafa. Taimakon gwamnati zai taimaka matuka wajen gina makomar wasanni a nan gaba."

Bikin rufe gasar ya gudana cikin nishadi da farin ciki, inda al’umma s**a nuna gamsuwa da nasarar gasar da kuma irin kulawar da wakilan su ke nuna.

Taron ya samu halartar wasu daga cikin kansilolin karamar hukumar Dandume, ciki har da Hon. Alhaji Magaji Ba Kauye, da Hon. Barista Abubakar Mohammed Gardi, wanda ya samu wakilcin Malam Anwarudeen Balada da sauransu.

zone Media Reporters

Yan binsiga sun kashe mutane talatiin da takwas bayan sun biya kuɗin fansa naira milyan hansunDaga Muhammad Kwairi Wazir...
28/07/2025

Yan binsiga sun kashe mutane talatiin da takwas bayan sun biya kuɗin fansa naira milyan hansun

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Rahotanni sun tabbatar da cewa wasu ‘yan bìñdiga sun ķàšhe mutane 38 da s**a yi garkuwa da su a jihar Zamfara, duk da cewa an biya su kuɗin fansa har naira miliyan 50 domin a sako su

Wannan mummunan al’amari ya faru ne a wani yankin Banga dake ƙaramar hukumar Kaura Namoda a jihar, inda bayan biyan kuɗin, maharan s**a ki sakin mutanen kuma s**a kashe su duka

Wani ɗan majalisa daga jihar ya bayyana matuƙar bakin cikinsa tare da neman afuwar jama’a kan abin da ya faru. Ya ce gwamnati na ci gaba da ƙoƙarin shawo kan matsalar tsaro a yankin

YANZU YANZU: An kwantar da Piraministan Izraila Benjamin Natanyahu yanzu haka a Asibitin Kula da Masu Ciwo Mai Tsanani (...
28/07/2025

YANZU YANZU: An kwantar da Piraministan Izraila Benjamin Natanyahu yanzu haka a Asibitin Kula da Masu Ciwo Mai Tsanani (Intensive Care Unit). WANE FATA KUKE MASA?

27/07/2025
Hon. Auwal Bilyaminu Ya Kaddamar da Aikin Gyaran Makarantar Islamiyya a Magaji WandoA wani mataki na inganta ilimin addi...
26/07/2025

Hon. Auwal Bilyaminu Ya Kaddamar da Aikin Gyaran Makarantar Islamiyya a Magaji Wando

A wani mataki na inganta ilimin addini da walwalar al’umma, Kansila mai wakiltar Mazabar Magaji Wando (A), Hon. Auwal Bilyaminu, ya kaddamar da aikin gyaran makarantar Islamiyya da ke cikin yankin.

Aikin gyaran ya haɗa da sabunta bangon makarantar, sake rufe ginin da kuma sanya sabbin ƙofofi da tagogi. Wannan mataki na ɗaya daga cikin shirye-shiryen Hon. Auwal Bilyaminu na bunkasa fannin ilimin addini da samar da kyakkyawan yanayi ga dalibai da malamai.

Yayin da yake jawabi a wajen kaddamar da aikin, Hon. Auwal Bilyaminu ya ce:

Ilimin addini ginshiƙi ne na tarbiyya da ci gaban al’umma. Wannan aikin na daga cikin ayyukan da na kuduri niyyar aiwatarwa domin amfani ga al’umma.”

Ya ƙara da cewa yana da muhimmanci shugabanni su riƙa ɗaukar nauyin tallafa wa cibiyoyin koyar da addini domin ciyar da al’umma gaba.

Wasu daga cikin mazauna yankin sun nuna farin ciki da wannan mataki, inda s**a yaba da jajircewar kansilan wajen duba bukatun al’umma, musamman a fannin ilimi. Sun bayyana cewa aikin zai ƙarfafa gwiwar iyaye wajen tura 'ya'yansu makaranta, da kuma ƙarfafa koyar da darussan addinin Musulunci a yankin.

Ana sa ran cewa aikin zai ƙare cikin ƙanƙanin lokaci tare da kawo sauyi mai amfani ga makarantar da al’ummar yankin gaba ɗaya.

Al’ummar Bakori Ta Kudu Sun Rufe Hanyoyi Saboda Matsalar TsaroA yau Asabar, 26 ga Yuli, 2025, da misalin ƙarfe 11 na saf...
26/07/2025

Al’ummar Bakori Ta Kudu Sun Rufe Hanyoyi Saboda Matsalar Tsaro

A yau Asabar, 26 ga Yuli, 2025, da misalin ƙarfe 11 na safe, al’ummar yankin Bakori ta Kudu da ke ƙaramar hukumar Bakori a jihar Katsina sun ɗauki matakin rufe dukkan hanyoyin da ke haɗa yankinsu da sauran sassan gari.

Yankunan da abin ya shafa sun haɗa da garuruwan Kakumi, Guga da wasu kauyuka na kusa, inda mutane da dama s**a fito s**a toshe hanyoyin shiga da fita daga yankin, ciki har da hanyar Funtuwa, Malumfashi, Katsina da ta Kano.

Wakilinmu da ya kai ziyara yankin ya iske gungun motoci da fasinjoji a tsaye, yayin da babu wata hanya da za a iya bi domin shiga ko fita daga Bakori zuwa wasu garuruwa.

Wasu daga cikin mazauna yankin da s**a nemi a ɓoye sunayensu sun bayyana cewa sun ɗauki wannan mataki ne saboda yadda 'yan ta’adda ke kai hari a yankinsu babu kakkautawa, suna kashe mutane, raunata su, da kuma kwashe dukiya ba tare da wata tsangwama ba. Sun bayyana cewa sun yi ta kai ƙorafi ga hukumomi amma ba su ji wani amsa ko ɗaukar mataki ba, don haka s**a ɗauki matakin kare kansu da kansu.

Wakilinmu ya yi ƙoƙarin jin ta bakin shugaban ƙaramar hukumar Bakori, Alhaji Musa Abubakar Barde, sai dai wayar sa ba ta shiga ba har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

Ko da yake gwamnatin jihar Katsina na ci gaba da ƙoƙarin yaki da 'yan ta’adda a yankin, amma alamu na nuna cewa matsalar tsaro na kara ta’azzara, musamman a kananan hukumomin Faskari, Bakori, Kankara, Funtuwa, Dandume, Sabuwa da wasu yankuna na jihar da kuma makwabtan jihohi.

Address

Katsina Ala

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Funtua Zone Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Funtua Zone Reporters:

Share

Category