Funtua Zone Reporters

Funtua Zone Reporters Muna Maku Barka da zuwa shafinmu Domin samun labaran Duniya kasance da jaridar Funtua Zone Reporters
(1)

08/08/2026

Innalillahi wa inna ilihi Rajiun Allah ya kawo mana zaman lafiya

Da Dumu-Ɗumi:- Dr. Mustapha zai fice daga ADC ya koma APC a katsina Tsohon sakataren gwamnatin jihar Katsina Dr. Mustaph...
08/08/2026

Da Dumu-Ɗumi:- Dr. Mustapha zai fice daga ADC ya koma APC a katsina

Tsohon sakataren gwamnatin jihar Katsina Dr. Mustapha Inuwa zai fice daga ADC ya koma APC da magoya bayansa domin tallata tazarcen Tinubu a zaben 2027 a Katsina

Katsina Reporters ta ruwaito cewa Dr. Mustapha Inuwa yayi kaurin suna wajen s**a da caccakar gwamnatin APC musammam kan matsalar tsaro a Katsina

Mustapha Muhammad Inuwa ya cimma wannan matsayar ne bayan wata ganawa da Tinubu a makon nan.

Ya kuke kallon wannan batu?

28/07/2026

Dalilin Da Ya Sa Na Yanke Wa Saurayina Mazakuta — Maimuna Idris Maigatari

Video 📷 Funtua pots

Za a Fara Gasar Cin Kofin Hon. Ya'u Ahmed NOWA a Dandume Domin Bunƙasa Wasannin MatasaHukumar Ƙwallon Kafa ta Ƙaramar Hu...
23/07/2026

Za a Fara Gasar Cin Kofin Hon. Ya'u Ahmed NOWA a Dandume Domin Bunƙasa Wasannin Matasa

Hukumar Ƙwallon Kafa ta Ƙaramar Hukumar Dandume ta sanar da shirinta na gudanar da Gasar Cin Kofin ɗan takarar kujerar Majalisar Tarayya mai neman wakiltar mazabar Funtua/Dandume a ƙarƙashin jam'iyyar APC, Hon. Ya'u Ahmed NOWA da nufin bunƙasa harkokin wasanni tare da bai wa matasa damar nuna hazaka da basirarsu.

Shugaban Hukumar Ƙwallon Kafa ta Dandume, Alhaji Sulaiman Ibrahim Mairaguna, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis, 23 ga Yulin 2026, yayin wata ganawa da masu ruwa da tsaki a harkar ƙwallon kafa da aka gudanar a gidan kallo na Dan Baba da ke garin Dandume.

Ya bayyana cewa gasar za ta gudana ne bisa tsarin FA (knockout), inda ƙungiyoyi 16 za su fafata domin lashe kofin. Ya ce ƙungiyoyi 11 sun fito daga mazabu 11 na Ƙaramar Hukumar Dandume, yayin da ƙungiyoyi biyar s**a fito daga garin Dandume, kasancewar hedikwatar ƙaramar hukumar ce kuma cibiyar da ke da mafi yawan ƙungiyoyin ƙwallon kafa.

A cewarsa, ƙungiyar da za ta lashe gasar za ta samu babban kofi tare da kyautar Naira 100,000, yayin da wadda ta zo ta biyu za ta karɓi ƙaramin kofi da Naira 50,000. Ita kuwa ƙungiyar da za ta zo ta uku za ta samu Naira 30,000. Haka kuma, kowace ƙungiyar da ta shiga gasar za a ba ta tallafin Naira 10,000 domin ƙarfafa musu gwiwa.

Alhaji Sulaiman Ibrahim Mairaguna ya ce manufar shirya gasar ita ce gano da bunƙasa hazakar matasa, ƙarfafa haɗin kai da zaman lafiya, tare da haɓaka harkokin ƙwallon kafa a matakin ƙananan hukumomi.

Ya ƙara da cewa shirin na nuna irin muhimmancin da Hon. Ya'u Ahmed NOWA ke bai wa matasa ta hanyar samar musu da damar da za su bunƙasa basirarsu. A cewarsa, saka hannun jari a harkokin wasanni na taimakawa wajen rage zaman banza, inganta tarbiyya da kuma buɗe hanyoyin samun ci gaba ga matasa.

Shugaban hukumar ya kuma yi kira ga shugabannin ƙungiyoyi, 'yan wasa da magoya baya da su kiyaye dokoki da ƙa'idojin gasar tare da nuna ruhin wasanni domin tabbatar da cewa an gudanar da gasar cikin lumana da nasara.

Ana sa ran gasar za ta haɗa matasa daga sassa daban-daban na Ƙaramar Hukumar Dandume, yayin da za a sanar da ranar fara wasannin bayan kammala dukkan shirye-shiryen gudanar da gasar.

Funtua Zone Reporters

Hukumar CDP Ta Gudanar da Taron Tattara Bukatun Al'umma a Mazabar Magaji Wando A, DandumeHukumar Community Development P...
19/07/2026

Hukumar CDP Ta Gudanar da Taron Tattara Bukatun Al'umma a Mazabar Magaji Wando A, Dandume

Hukumar Community Development Programme (CDP) ta gudanar da taron tattara bukatun al'umma da sauraron korafe-korafe a Mazabar Magaji Wando A da ke Ƙaramar Hukumar Dandume, domin tattara bayanan da za a yi amfani da su wajen tsara kasafin kuɗin Jihar Katsina na shekarar 2027.

An gudanar da taron ne a ranar Asabar, 18 ga Yuli, 2026, ƙarƙashin jagorancin shugaban CDP na gundumar, Hamisu Sha'aibu.

A yayin taron, wakilan al'umma daga rumfunan zaɓe daban-daban na mazabar sun gabatar da muhimman bukatu da ƙalubalen da ke fuskantarsu, tare da yin kira ga gwamnati da ta sanya su cikin abubuwan da za a aiwatar a kasafin kuɗin shekarar 2027.

Shugabannin Hukumar CDP sun karɓi waɗannan buƙatu tare da bayyana cewa za a tattara su domin miƙa su ga hukumomin da abin ya shafa, da nufin a yi la'akari da su wajen tsara kasafin kuɗin jihar.

Taron ya samu halartar tsohon ɗan Majalisar Dokokin Jihar Katsina mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Dandume, Hon. Haruna Goma, da Kansilan da ke wakiltar gundumar, Hon. Auwal Mohammed Bilyamu, da Supervisory Councillor, Hon. Zaharadini Albasu, tare da sauran shugabannin al'umma da masu ruwa da tsaki.

A Ƙalla Manoma 5,000 Za Su Amfana Yayin da Tafidan Ɗandume Ya Ƙaddamar da Shirin Tallafa wa Manoma a Jihar KatsinaKamfan...
11/07/2026

A Ƙalla Manoma 5,000 Za Su Amfana Yayin da Tafidan Ɗandume Ya Ƙaddamar da Shirin Tallafa wa Manoma a Jihar Katsina

Kamfanin SHIAGRO NIGERIA LIMITED, mallakin Alhaji Ibrahim Shu'aibu, wanda aka fi sani da Tafidan Ɗandume, ya ƙaddamar da shirin rabon kayan noma ga manoma a Ƙaramar Hukumar Ɗandume ta Jihar Katsina.

An ƙaddamar da shirin ne a ranar Asabar, 11 ga Yuli, 2026, a ƙarƙashin Renewed Hope Smallholder Farmers Support and Value Chain Programme, wanda ake aiwatarwa tare da haɗin gwiwar Bankin Noma na Najeriya (BOA).

A cewar Shugaban Kamfanin SHIAGRO NIGERIA LIMITED, Alhaji Ibrahim Shu'aibu (Tafidan Ɗandume), kamfaninsa na cikin kamfanoni 20 da Gwamnatin Tarayya ta zaɓa domin aiwatar da wannan shiri a sassa daban-daban na ƙasar.

Ya bayyana cewa a kalla manoma 5,000 ne ake sa ran za su amfana da shirin, inda za a raba musu ingantattun iri, taki da magungunan kashe kwari domin ƙara yawan amfanin gona da bunƙasa harkar noma a Jihar Katsina.

Sai dai ya jaddada cewa kayan noman ba tallafi ne kai tsaye ba, domin za a ba manoman su ne a matsayin bashi, wanda za su mayar bayan sun girbe amfanin gonarsu.

Ya kuma bayyana cewa an tanadi tsarin da zai bai wa manoma damar sayar da ragowar amfanin gonarsu a farashin da ya dace idan s**a buƙata, domin tabbatar da samun riba mai kyau.

Alhaji Ibrahim Shu'aibu ya buƙaci waɗanda za su ci gajiyar shirin da su kiyaye dukkan sharuɗɗan da aka gindaya, musamman mayar da abin da aka ba su a kan lokaci, yana mai cewa hakan zai taimaka wajen faɗaɗa shirin domin ƙarin manoma su ci gajiyarsa a nan gaba.

Da yake jawabi a wajen taron, Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Ɗandume kuma wakilin Shugaban Ƙaramar Hukumar, Alhaji Basiru Musa, ya ce shirin zai taimaka matuƙa wajen bunƙasa harkar noma da inganta rayuwar manoma a Ɗandume da sauran sassan Jihar Katsina.

Taron ya samu halartar wakilin Shugaban Ƙaramar Hukumar Funtua, Babangida Ibrahim Mailayu, Farfesa Muhammad Yusuf, Alhaji Bello Bashir Ɗanmaliki, wakilin Hakimin Ɗandume, da sauran manyan baƙi.

11 ga Yuli, 2026

11/07/2026
Gidauniyar Marafa Danmumini Foundation za ta raba littattafai da kayan rubutu ga ɗaliban DandumeRanar Asabar, 4 ga Yuli,...
04/07/2026

Gidauniyar Marafa Danmumini Foundation za ta raba littattafai da kayan rubutu ga ɗaliban Dandume

Ranar Asabar, 4 ga Yuli, 2026, Gidauniyar Marafa Danmumini Foundation, ƙarƙashin jagorancin Hon. Lawal Ibrahim Danmumini, ta sanar da shirinta na raba littattafan karatu da kayan rubutu ga ɗaliban makarantu a faɗin Ƙaramar Hukumar Dandume ta Jihar Katsina.

A cikin wata sanarwa da gidauniyar ta fitar, ta ce shirin na da nufin tallafa wa ɗalibai da iyayensu tare da ƙarfafa gwiwar matasa wajen neman ilimi.

Sanarwar ta bayyana cewa shirin wani ɓangare ne na ayyukan jin ƙai da gidauniyar ke gudanarwa domin bunƙasa ilimi da kuma tallafa wa ci gaban al'umma.

Gidauniyar ta kuma ce shirin ya yi daidai da ƙoƙarin gwamnatin Jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Malam Dikko Umaru Radda na inganta harkokin ilimi da samar da ingantacciyar makoma ga matasan jihar.

Baya ga rabon littattafai da kayan rubutu, sanarwar ta ce gidauniyar za ta ƙaddamar da rabon riguna da huluna masu ɗauke da hoton da tambarin gwamnan jihar, a matsayin wani ɓangare na shirinta na wayar da kai da nuna goyon baya ga manufofin ci gaban gwamnatin jihar.

Shugaban gidauniyar, Hon. Lawal Ibrahim Danmumini, ya ce za su ci gaba da gudanar da ayyukan jin ƙai da tallafa wa al'umma ta hanyoyin da s**a dace da doka, domin inganta rayuwar jama'a da ƙarfafa ci gaban ilimi a yankin.

Ya kuma yi addu'ar Allah Ya ci gaba da ba Jihar Katsina zaman lafiya da ci gaba, tare da bai wa Gwamna Dikko Umaru Radda lafiya da hikimar ci gaba da gudanar da ayyukan raya jihar.

Hon. Bishir Sani Funtua Zai Wakilci Matasan Funtua a Majalisar Matasa ta Jihar KatsinaƊaya daga cikin fitattun matasan m...
30/06/2026

Hon. Bishir Sani Funtua Zai Wakilci Matasan Funtua a Majalisar Matasa ta Jihar Katsina

Ɗaya daga cikin fitattun matasan masu gwagwarmaya a tafiyar Mai Girma Sanata Muntari Mohammed Dandutse, Hon. Bishir Sani Funtua, na daga cikin waɗanda za su wakilci matasan Ƙaramar Hukumar Funtua a sabuwar Majalisar Matasa ta Jihar Katsina, wadda Gwamna Malam Dr. Dikko Umaru Radda ya amince da kafawa.

Hon. Bishir Sani Funtua ya nemi addu'a da goyon bayan matasan Funtua da kewaye, yana mai cewa zai yi iya ƙoƙarinsa wajen samar da wakilci nagari, haɗa kan matasa, da kare martabarsu.

Ya kuma gode wa dukkan waɗanda s**a nuna masa goyon baya, tare da addu'ar Allah Ya saka wa kowa da alheri.

Address

Katsina Ala

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Funtua Zone Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Funtua Zone Reporters:

Shortcuts

Share