Funtua Zone Reporters

Funtua Zone Reporters Muna Maku Barka da zuwa shafinmu Domin samun labaran Duniya kasance da jaridar Funtua Zone Reporters
(1)

Matashi ya ƙwaƙule wa ƙanwarsa idanu a Bauchi don yin tsafi.Rundunar ‘yansanda a jihar Bauchi ta tabbatar da k**a wani m...
22/10/2025

Matashi ya ƙwaƙule wa ƙanwarsa idanu a Bauchi don yin tsafi.

Rundunar ‘yansanda a jihar Bauchi ta tabbatar da k**a wani matashi da ake zargi da ƙwaƙule wa ƙanwarsa idanu biyu don yin tsafin neman kuɗi a ƙaramar hukumar Ganjuwa ta jihar.

Majiyoyi sun ce lamarin ya faru ne a gari Wailo, inda wanda ake zargin, Auwalu Muhammad, ya ɗauki ƙanwarsa mai shekara bakwai, Rukayya Muhammad, zuwa daji, ya yi mata duka, sannan ya ƙwaƙule idanunta biyun.

A cewar mahaifinsu, yaran biyu dukkansu uwa ɗaya uba ɗaya suke, kuma Rukayya na fama da matsanancin rauni sak**akon mummunan abin da ya same ta.

Tuni daia aka garzaya da yaribyar zuwa asibitin koyarwa na jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) da ke Bauchi, inda likitoci s**a tabbatar da cewa ta rasa idanunta gaba ɗaya.

Likitan da ya duba ta, Dr. Shahir Umar Bello, ƙwararre a fannin kula da ido, ya bayyana cewar “Idanunta duka biyu sun lalace gaba ɗaya, kuma ba za ta iya gani ba har abada.”

Rahotanni sun ce an k**a wanda ake zargin, kuma jami’an tsaro na ci gaba da gudanar da bincike domin tattara cikakken bayani kan wannan danyen aiki da kuma wadanda s**a haɗa kai da shi.

Wannan ita ce Laiyal Jade wadda aka fi sani da Layla, matar Seyi Tunubu. Mahaifiyarta ƴar Najeriya ce, mahaifinta kuma B...
22/10/2025

Wannan ita ce Laiyal Jade wadda aka fi sani da Layla, matar Seyi Tunubu.

Mahaifiyarta ƴar Najeriya ce, mahaifinta kuma Balaraben ƙasar Lebanon. An haifeta a London na ƙasar Birtaniya, sannan ta girma a ƙasar Netherlands da ke tarayyar Turai. Lauya ce, ƴar kasuwa kuma mai hannu da shuni a Najeriya.

Wani fata za ku yi mata ita da mijinta.

Mataimakin shugaban kasar Najeriya Sanata Kashim Shettima ya bude wasu muhimman ayyuka guda biyu da Gwamnan Jihar Katsin...
21/10/2025

Mataimakin shugaban kasar Najeriya Sanata Kashim Shettima ya bude wasu muhimman ayyuka guda biyu da Gwamnan Jihar Katsina ya aiwatar.

A ranar Talata 21/10/2025, mataimakin shugaban kasar ya bude ayyukan guda biyu da Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda ya aiwatar a cikin garin Katsina babban birnin jihar, a wata ziyarar aiki ta yini biyu da mataimakin shugaban kasar ya kawo Jihar Katsina.

Muhimman ayyukan guda biyu da mataimakin shugaban kasar Sanata Kashim Shettima ya bude sun hada da tawayen hanya wadda ta tashi daga bakin round about na Masallacin kofar Soro ta biyo ta kofar marusa, zuwa round about na WTC.

Sai kuma wata cibiya ta koya dabarun noma na zamani, inda akayi mata mazauni, a cikin Sakatariyar Gwamnatin Jihar Katsina, da mai girma Gwamna Malam Dikko Umar Radda ya kirkiro ta ya kuma ginata.

Mataimakin shugaban kasa Sanata Kashim Shettima ya yaba ma Gwamna Malam Dikko Umar Radda akan gina wannan hanya da ta tashi daga bakin masallacin Juma'a na kofar Soro tabi ta kofar marusa zuwa round about na WTC da kuma cibiyar dabarun noma ta zamani.

A nashi jawabin, mai girma Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda ya bayyana cewa" hanyar mai nisan kilomita uku da rabi an faɗaɗa daga hanya mai hannu daya zuwa tagwayen hanyoyi, da hanyoyin ruwa hagu da dama, da fitilun hanya masu amfani da hasken rana, wanda hanyar lakume kudi sama da miliyan dubu hudu.

Gwamnan ya kara da cewa" hanyar tana cikin hanyoyi guda goma da ake sabuntawa zuwa na zamani a cikin garin Katsina babban birnin jihar, wanda aka bada kwangilar su sama da miliyan dubu saba'in da hudu, aikin hanyoyin zai taik**a ka wajen rage cunkoson ababen hawa, sannan kuma zai bunkasa harkokin kasuwanci da tattalin arziki.

Taron ya samu halartar mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Hon. Faruk Lawal Jobe, Kakakin majalisar dokoki ta Jihar Katsina Rt. Hon. Nasir Yahaya Daura,tsoffin Gwamnonin Jihar Katsina, Rt. Hon. Aminu Bello Masari, da Barr. Ibrahim Shehu Shema.

Tsohon Gwamnan Jihar Borno na mulkin soja Kanal Abdulmuminu Amin mai ritaya, mai martaba Sarkin Daura Alhaji Umar Faruk Umar, wakilin Sarkin Katsina Kauran Katsina Alhaji Aminu Nuhu Abdulkadir, Alhaji Dahiru Bara'u Mangal wanda ya samu Hon. Bala Saulawa.

Yan majalisar dokoki ta Jihar Katsina, yan majalisar zartarwa ta Jihar Katsina, Alhaji Usman Sarki, Alhaji Ladan Wapa, shugaban taro kwamishinan ma'aikatar ayyuka ta Jihar Katsina Engr. Hon. Sani Magaji Ingawa. Da dai sauransu.

DA DUMI-DUMI: Ana Zargin Wani Tsohon Gwamna Da Daukar Nauyin Sojojin Najeriya dlDomin Yiwa Tinubu Juyin Mulki A Ranar 25...
20/10/2025

DA DUMI-DUMI: Ana Zargin Wani Tsohon Gwamna Da Daukar Nauyin Sojojin Najeriya dlDomin Yiwa Tinubu Juyin Mulki A Ranar 25 Ga Wannan Watan Na October

An k**a wasu karin hafsoshin soji kan zargin kifar da Gwamnatin Shugaba Tinubu da tallafin wani tsohon gwamna kuma tsohon babban jami'in gwamnati a bangaren man fetur, k**ar yadda jaridar Aminiya ta ruwaito.

Hukumar Leƙen Asirin Soji ta Najeriya (DIA) tana gudanar da bincike kan wani tsohon gwamna bisa zargin sa da daukar nauyin sojoji da nufin yi wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu juyin mulki.

Majiyoyin Aminiya sun bayyana cewa akwai zargi mai karfi cewa tsohon gwamnan, wanda ɗan asalin yankin Kudu ne kuma tsohon babban jami’in gwamnati a ɓangaren albarkatun mai da iskar gas ne, ya ɗauki nauyin yunƙurin juyin mulkin, wanda da aka shirya aiwatarwa a ranar 25 ga watan Oktoban nan da muke ciki.

A ƙarshen mako ne kafofin watsa labarai na Shahara Reporters da Premium Times s**a ruwaito cewa wasu hafsoshin soji 16, —waɗanda Hedikwatar Tsaro ta Najeriya ta ce sun shiga hannu saboda aikata abubuwan da saɓa ƙa’idar aiki— an tsare su ne saboda zargin su da yunƙurin kifar da Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Daga cikin sojojin da aka k**a akwai wani mai muƙamin Birgediya-Janar da wani Kanar da wasu na ƙasa da su da ke Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Sha’anin Tsaro (NSA).

Majiyar Aminiya ta tabbatar da cewa akwai ƙamshin gaskiya a rahoton zargin yunƙurin juyin mulkin.

Majiyar ta ce, “Gaskiya ne. Akwai hannun fararen hula, ciki har da wani tsohon gwamna, kuma ana bincike domin gano irin rawar da s**a taka a ciki. A halin yanzu, sojoji 16 da ake zargi suna tsare.

Funtua Zone Reportes

Labari da duminsa;Yanzun haka shugaban karamar hukumar Faskari Hon Surajo Aliyu Daudawa ya shiga daji da kansa har wajen...
19/10/2025

Labari da duminsa;

Yanzun haka shugaban karamar hukumar Faskari Hon Surajo Aliyu Daudawa ya shiga daji da kansa har wajen Fulanin da aka yi sasanci da su, inda ya amso mutum 26 da yan bindiga s**a yi garkuwa da su a yankin Tafoki

Isiya Kwashen Garwa shi ne ya jagoranci bayar da wa'adan aka s**a saki a yau

A yayin ceto mutanen, shugaban karamar hukumar Faskari, da shi Isya Kwashen Garwa sun yi maganganu masu muhimmanci da yak**ata kowa ya ji

Bidiyon na nan tafe

Hedkwatar Tsaro Ta Karyata Jita-jitar Yunkurin Juyin Mulki, Ta Bayyana Dalilin Soke Bikin Cika Shekaru 65 Da Ƙasar Najer...
18/10/2025

Hedkwatar Tsaro Ta Karyata Jita-jitar Yunkurin Juyin Mulki, Ta Bayyana Dalilin Soke Bikin Cika Shekaru 65 Da Ƙasar Najeriya Ta Samu ’Yanci

Katsina Times

Hedkwatar Tsaron Ƙasa (DHQ) ta musanta wani rahoton da wani shafin intanet ya wallafa, wanda ke ikirarin cewa soke bikin cika shekaru 65 da Najeriya ta samu ’yanci yana da nasaba da wani yunkurin juyin mulki.

A cikin wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labaran Tsaro, Birgediya Janar Tukur Gusau, ya fitar a ranar Asabar, 18 ga Oktoba, 2025, DHQ ta bayyana rahoton a matsayin ƙarya, mai cike da mugunta da kuma nufin tada hankalin jama’a da zubar da amincewa tsakanin al’umma.

Sanarwar ta ce an soke bikin ne domin bai wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu damar halartar wani muhimmin taron haɗin gwiwa a ƙasashen waje, tare da bai wa dakarun Najeriya damar ci gaba da mayar da hankali kan yaƙi da ta’addanci, rikicin ’yan tawaye da ’yan fashi da makami a faɗin ƙasar.

DHQ ta kuma bayyana cewa k**a wasu jami’an soja 16 da ake bincike a kansu, ba shi da alaƙa da jita-jitar juyin mulki da ake yaɗawa, illa dai wani bincike ne na cikin gida da aka saba gudanarwa don tabbatar da ɗa’a da ƙwarewa a cikin rundunar soja. Ta ce an kafa kwamitin bincike kuma za a bayyana sak**akonsa bayan kammala aiki.

“Hedkwatar Tsaron Ƙasa tana nan daram bisa biyayya ga Kundin Tsarin Mulkin Ƙasa da kuma gwamnatin tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa kuma Babban Kwamandan Rundunar Sojin Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, GCFR,” in ji sanarwar.

DHQ ta roƙi ’yan Najeriya da su yi watsi da rahoton ƙarya, tare da ci gaba da ba da goyon baya ga jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya, ci gaba, da haɗin kai a cikin ƙasa.

Hedkwatar Tsaro, Abuja

Juyin Mulki a Shirye?  Rahotanni Sun Bayyana Cewa Sojoji 16 Sun Shirya Cire Tinubu Daga Mulki! 🇳🇬Rahotanni daga Sahara R...
18/10/2025

Juyin Mulki a Shirye?

Rahotanni Sun Bayyana Cewa Sojoji 16 Sun Shirya Cire Tinubu Daga Mulki! 🇳🇬

Rahotanni daga Sahara Reporters sun bayyana cewa akalla manyan jami’an soja 16 daga rundunar sojin Najeriya an tsare su bisa zargin shirya juyin mulki domin kifar da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

A cewar majiyoyi, waɗannan jami’an — daga mukamin Captain zuwa Brigadier General — sun fara gudanar da tarurrukan asiri domin kifar da gwamnati, suna zargin cewa “’yan siyasa masu son kai” sun lalata kasar.

Sai dai rundunar sojin Najeriya ta fito da wata sanarwa tana cewa an k**a jami’an ne saboda rashin ladabi da gazawa a jarrabawar karin girma, amma majiyoyin cikin gida sun tabbatar cewa tsare su ya shafi shirin juyin mulki ne.

An ce ma wannan dalilin ne ya sa aka soke bikin tunawa da samun ’yancin kai na ranar 1 ga Oktoba, domin rahotanni sun nuna cewa an shirya aiwatar da juyin mulkin ne a wurin bikin.

Tuni jami’an tsaro s**a fara bincike mai zurfi, yayin da ake ci gaba da tsare jami’an a shelkwatar Defence Intelligence Agency (DIA).

Tun bayan samun ’yancin kai a 1960, Najeriya ta sha juyin mulki guda biyar da s**a canja tafarkin gwamnati.

Sojojin Najeriya sun ce sun ceto mutane 21 da aka yi garkuwa da su a jihohin Kwara da Kogi, ciki har da jariri da 'yan k...
18/10/2025

Sojojin Najeriya sun ce sun ceto mutane 21 da aka yi garkuwa da su a jihohin Kwara da Kogi, ciki har da jariri da 'yan kasar China hudu.

A cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce dakarun 2 Division/Sector 3 Operation FANSAN YAMA ne s**a gudanar da aikin ceto a ranar 17 ga Oktoba, tare da hadin gwiwar 12 Brigade Lokoja da 22 Armoured Brigade Ilorin.

Mutanen da aka ceto sun hada da maza 14, mata 5, jariri daya, da kuma 'yan China hudu. Rundunar ta ce an sace su daga wurare daban-daban a cikin jihohin Kwara da Kogi, kuma wasu daga cikinsu sun shafe fiye da watanni hudu a hannun masu garkuwa da su.

Sanarwar ta ce bayan sojoji sun kara kaimi a farmakin da suke yi, masu garkuwa da mutanen sun tilasta sakin wadanda s**a sace.

Babban Kwamandan 2 Division, Manjo Janar CR Nnebeife, ya ce an ba wadanda aka ceto taimakon gaggawa da abubuwan jin kai don taimaka musu su murmure daga wahalar da s**a sha.

Ya ce rundunar za ta ci gaba da kai farmaki kan masu aikata laifi, tare da tabbatar da cewa ba za a bar wani wuri da 'yan ta'adda za su boye ba a yankin da rundunar ke da alhakin tsaro.

An kai wadanda aka ceto zuwa cibiyar lafiya ta sojoji don samun kulawar likita, inda yawancin su ke samun sauki daga gajiya da s**a sha.

Manjo Janar Nnebeife ya gode wa Rundunar Sojin Sama ta Najeriya bisa goyon bayan da ta bayar a lokacin aikin, tare da yabawa sauran hukumomin tsaro bisa hadin kai da s**a nuna.

Ya kuma jinjinawa dakarun da s**a gudanar da aikin, tare da umartar su da su ci gaba da kaimi don dawo da zaman lafiya a yankunan da ke karkashin 2 Division.

Funtuua zone Reporter

Labari da Dumi-DumiZa a Nada Hon. Murtala Adam Dan Maigora a Matsayin Sarkin Waya na Karamar Hukumar DandumeKaramar huku...
18/10/2025

Labari da Dumi-Dumi

Za a Nada Hon. Murtala Adam Dan Maigora a Matsayin Sarkin Waya na Karamar Hukumar Dandume

Karamar hukumar Dandume na shirin shaida sabon babi a tarihin shugabancin sana’ar sayar da wayoyi, yayin da aka bayyana cewa Hon. Murtala Adam Dan Maigora zai karɓi mukami a matsayin Sarkin Waya na Masu sana'ar sayar da wayoyi na ƙaramar hukumar.

Bayan nasarar da ya samu a matsayin Chairman na Ƙungiyar Masu Sana’ar Sayar da Wayoyi, rahotanni daga cikin gida sun tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba za a nada shi a matsayin shugaban gaba ɗaya na sana’ar waya a matakin gargajiya da na al’umma.

Wannan nadin na zuwa ne bayan shafe lokaci yana jagorantar ƙungiyar cikin nasara, inda ya taka rawar gani wajen haɗa kan masu sana’a, ƙarfafa haɗin gwiwa, da kawo sauye-sauye masu ma’ana a harkar kasuwanci da tsaro.

Wasu daga cikin mambobin ƙungiyar sun bayyana cewa Hon. Murtala ya cancanci wannan matsayi bisa jajircewarsa, gaskiya, da hangen nesa da ya nuna a lokacin da yake shugabanci. Sun ce nadin nasa a matsayin Sarkin Waya zai ƙarfafa martabar sana’ar da kuma kawo daidaito a harkokin kasuwanci da al’umma.

Ana sa ran cewa da zarar an kammala shirye-shiryen da s**a dace, za a sanar da ranar nadin a hukumance, tare da gudanar da bikin da zai samu halartar manyan baki daga sassa daban-daban na jihar Katsina da ma ƙasar baki ɗaya.

Wannan nadin na Hon. Murtala Adam Dan Maigora a matsayin Sarkin Waya na Dandume na nuni da yadda al’umma ke daraja shugabanci mai nagarta, da kuma yadda sana’ar waya ke ƙara samun matsayi a cikin tsarin rayuwar yau da kullum.

Rahoto daga Funtua Zone Reporters

Gwamnatin jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa PhD ta sake yaye sabbin jami’an tsaron cikin ...
15/10/2025

Gwamnatin jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Gwamna Malam Dikko Umar Raɗɗa PhD ta sake yaye sabbin jami’an tsaron cikin gida, wato Katsina Community Watch Corps, a karo na uku.

An gudanar da bikin yaye jami’an ne a ranar Laraba, 15 ga Oktoba 2025, a sansanin horas da jami’an tsaro na farin kaya da ke kan hanyar Batsari, cikin garin Katsina, inda mutum 200 s**a kammala horo kuma aka ba su kayan aiki.

Da yake jawabi yayin bikin, Gwamna Dikko Raɗɗa ya fara da gode wa Allah bisa damar da aka samu ta gudanar da bikin yaye jami’an karo na uku. Ya bayyana cewa gwamnatin jihar na ci gaba da samun nasarori a fannin tsaro tun bayan kafa rundunar Katsina Community Watch Corps, musamman a yankunan da ake fama da matsalar tsaro.

Gwamnan ya kuma tabbatar da cewa gwamnati ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da zaman lafiya a duk fadin jihar.

Raɗɗa ya nuna jin dadinsa kan yadda al’ummomi ke ƙoƙarin sasanta da ‘yan bindiga a wasu yankuna, wanda ya ce hakan ya haifar da ci gaba a ƙananan hukumomin Jibia, Batsari, Musawa, Matazu, Faskari, Dandume da wasu wurare.

A ƙarshe, gwamnan ya bukaci sabbin jami’an da su jajirce wajen gudanar da aikinsu cikin gaskiya da aminci, tare da yin addu’a ga waɗanda s**a rasa rayukansu yayin gudanar da wannan aiki, yana roƙon Allah ya jikansu ya gafarta musu.

A nasa jawabin, kwamishinan ma’aikatar harkokin tsaro na jihar Katsina, Hon. Nasir Mu’azu Danmusa, ya yaba wa gwamnatin jihar bisa himmar da take nunawa wajen inganta tsaro.

Shi ma shugaban horas da jami’an, Manjo Janar Junaid Bindawa (Rtd), ya bayyana godiyarsa ga gwamnan bisa wannan gagarumin ƙoƙari.

Taron ya samu halartar kakakin majalisar dokokin jihar Katsina, wanda mataimakinsa Hon. Abduljalal Haruna R***a ya wakilta, tare da wasu kwamishinoni, shugabannin tsaro, sarakunan gargajiya, ‘yan majalisa, da shugabannin kananan hukumomi.

Jamilu Garkuwan Dandutse Dandume

15/10/2025

Da alama Gwamna Dikko Radda ba ya son daukar shawara a mulkin jihar Katsina - Zargin Dr. Mustapha Inuwa

Matashi me suna Abdullahi dan jihar Katsina da ya yi ridda ya koma Kirista ya fito ya godewa Allah inda yace da yana han...
15/10/2025

Matashi me suna Abdullahi dan jihar Katsina da ya yi ridda ya koma Kirista ya fito ya godewa Allah inda yace da yana hanyar bata Amma yanzu Allah ya nuna masa hanyar gaskiya
Trending Videos

Address

Katsina Ala

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Funtua Zone Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Funtua Zone Reporters:

Share