Katsina Trending News

Katsina Trending News Wannan shafi zai rika kawo maku ingantattun labarai da dumi duminsu.

12/01/2025

Duk jihar Katsina babu inda sunan Hamza Sule Wamban Faskari bai kai ba ta fuskar taimakon Al'umma.

Inji Hon. Haruna Abdulrashid Yaro Funtua Darakta Janaral na kungiyar Wamban Faskari Awareness Forum.

Hon. Haruna Abdulrashid Yaro ya fadi haka ne ranar lahadi 12-01-2024 lokacin da yake kaddamar da shugabannin kungiyar Wamban Faskari Political Awareness Forum na shiyya da na kananan hukumomi (11) dake shiyyar Funtua a dakin taro na H&B dake garin Funtua.

Hon. Yaro ya cigaba da bayyana irin taimakon da Hon. Hamza Sule Faskari ke yi ma al'ummar shiyyar Funtua wanda hakan ne ya basu dama na kirkirar wannan kungiya domin cigaba da fadi ma al'umma irin abubuwan da yake yi.

Sannan ya tabbatar ma da al'umma cewa" wannan kungiya bata siyasa ba ce ko wani neman takara, kungiya ce aka kafa domin cigaba da bayyana irin ayyukan alkairin da Hon. Hamza Sule keyi domin al'umma suyi ko yi.

Hon. Haruna Yaro ya mika godiyar sa ga gwamnan jihar Katsina Mal. Dikko Umar Radda bisa kyakkyawan shugabancin sa a jihar Katsina tare da rokon karin zaman lafiya da karuwar arziki a jihar Katsina.

Mutane da dama ne s**a gabatar da jawabai na fatan alkairi tare da tofa albarkacin bakin su akan ayyukan alkairi na Hon. Hamza Sule Faskari a wurin taron.

Bayan kammala jawabai a wurin taron an mika takardun k**a aiki ga shugabannin kungiyar matakin shiyya da kuma kananan hukumomin (11) da s**a fito daga shiyyar ta Funtua, taron ya samu halartar yan siyasa daga ko'ina a fadin shiyyar ta Funtua.

Za a yi koyi da sauran kasashe domin ganin ma’aunin karfin tattalin arziki ya karu, NBS za ta hada da bangarorin badala ...
12/01/2025

Za a yi koyi da sauran kasashe domin ganin ma’aunin karfin tattalin arziki ya karu, NBS za ta hada da bangarorin badala wajen lissafin GDP – Karin bayani a sashen sharhi.

DA DUMIDUMINSA: Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Tsagin Mustapha Inuwa S**a Shigar Kan Zaɓen PDP A Katsina Daga Comr Nura Si...
12/01/2025

DA DUMIDUMINSA: Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Tsagin Mustapha Inuwa S**a Shigar Kan Zaɓen PDP A Katsina

Daga Comr Nura Siniya

Wata babbar kotu a Jihar Katsina ta yi watsi da karar da wasu jiga-jigan jam’iyyar PDP s**a shigar, suna kalubalantar yadda aka gudanar da zabukan shugabannin jam’iyyar a matakan mazabu, kananan hukumomi, da jiha a bara.

Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina, Alhaji Mustafa Inuwa, tare da wasu jiga-jigan jam’iyyar su takwas ne s**a kai shugabannin jam’iyyar kara kotu bisa zargin hana wasu mambobin jam’iyyar samun fom na takarar shugabancin jam’iyyar.

Masu shigar da karar sun bayyana cewa sun kai karar ne a madadin wasu mambobin jam’iyyar 7,905 da s**a nuna rashin jin dadinsu kan yadda aka gudanar da zabukan shugabannin.

Jam’iyyar PDP, ta hannun lauyanta, ta bukaci kotu ta yi watsi da karar, tana mai cewa kotu ba ta da hurumin sauraren irin wannan rikicin.

A yayin yanke hukuncinsa, mai shari’a Abbas Bawale ya yi watsi da karar bisa dalilin cewa kotu ba ta da hurumi kan rikice-rikicen da s**a shafi zaben shugabannin jam’iyya, domin hakan rikici ne na cikin gida.

Mai shari’a Bawale ya ambaci wasu hukuncin kotuna daban-daban da kuma tanade-tanaden dokar zabe ta 2022, wadanda s**a nuna cewa hurumin kotu ya takaita ne kan rikicin fidda gwani na jam’iyyun siyasa.

Game da ikirarin lauyan PDP cewa masu shigar da karar ba su kai koken nasu ga shugabancin jam’iyyar na kasa ba, mai shari’a Abbas Bawale ya ce kotu ta gamsu da cewa masu karar sun yi amfani da duk hanyoyin cikin gida wajen neman sulhu kafin su garzaya kotu.

Bayan hukuncin, lauyan masu shigar da karar, Barista Mustafa Sh*tu Mahuta, ya bayyana rashin gamsuwarsa da hukuncin kotu, tare da yin alkawarin daukaka kara a madadin wadanda yake karewa.

Jagoran ‘Yan Adawa na Borno Attom Magira Ya Sauya sheka daga NNPP Zuwa SDP.Tsohon dan takarar kujerar Sanata na jam’iyya...
12/01/2025

Jagoran ‘Yan Adawa na Borno Attom Magira Ya Sauya sheka daga NNPP Zuwa SDP.

Tsohon dan takarar kujerar Sanata na jam’iyyar NNPP a jihar Borno Atom Magira ya fice daga jam’iyyar New Nigeria People Party zuwa jam’iyyar Social Democratic Party.

Magira wanda tsohon dan takarar gwamna ne a karkashin jam’iyyar All Progressives Congress, babban dan adawa ne wanda a baya-bayan nan aka k**a shi kuma aka tsare shi a gidan yari saboda kiran da ya yi na neman ‘yan siyasa da su yi hadaka (Maja) a jam’iyyar adawa daya a jihar da kuma zarginsa da s**ar Gwamna Babagana Umara Zulum.

Masu sharhi sun shaida wa wakilinmu cewa an tsare Mista Magira ne a kan wani allo da magoya bayan kungiyar “YES TO MRGER” s**a dauki nauyinsa, inda s**a bukaci a hade dukkanin jam’iyyun siyasar jihar. Wasu da ba a san ko su waye ba ne s**a lalata allon tallan mai dauke da hoton Mr Magira mai dauke da rubutun “Say Yes To Merger”.
Daga baya an gurfanar da shi tare da bayar da belinsa bayan kwana 9 a hannun ‘yan sanda.

A wata sanarwa da mai taimaka masa Muhammad Yahaya ya fitar, Magira ya bayyana matakinsa na komawa jam’iyyar Social Democratic Party.

“Tafiyar siyasar Magira tana da ban sha’awa, tun daga kasancewarsa Jagoran jam’iyyar NNPP na jahar Borno , kuma dan takarar Sanatan Borno ta tsakiya a zaben 2023 zuwa mai neman tsayawa takarar gwamna a jam’iyyar APC 2019, kuma dan takarar mataimakin shugaban jam’iyyar APC shiyyar Arewa maso Gabas a 2022, ya ci gaba da nuna jagoranci mai hangen nesa. , ya kuma kasance mai fafutukar tabbatar kudurin "Not Too Young to Run", wanda ke jan hankalin matasan Najeriya su shiga harkokin shugabanci a kasar.

Kungiyar SERAP mai fafutukar yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya ta maka gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da gwamnonin ...
12/01/2025

Kungiyar SERAP mai fafutukar yaki da cin hanci da rashawa a Najeriya ta maka gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da gwamnonin kasar a gaban kotun ECOWAS.

Mahadin da ya bayyana a Taraban zai Gudanar da Maulidn Shehu Inyass.Sako daga Tawagar Mahadi Suna Mai cewa Muna isar wa ...
12/01/2025

Mahadin da ya bayyana a Taraban zai Gudanar da Maulidn Shehu Inyass.

Sako daga Tawagar Mahadi Suna Mai cewa Muna isar wa duk duniya da sako
Cewa Imamu mahdi ya bayyana a mambilla domin Gaskiya daya ce haka Kuma Allah baya Shawara domin Gudanar da lamarin sa.

Daliban Mahadi Suna Mai Kafa Hujja da cewa Allah na bayyana baiwar sa a duk inda ya so domin shi Mai iKo ne Kuma Babu Wanda zai iya ja da iKon sa. ballanta ya hana Allah yin aikin sa kuma Babu Wanda ya isa ya karyata gaskiya.

Don haka mahdi ya zo domin ya shiryar da duniya ne wato Alkhairi ne a gareku ku zo kuyi mubayu'a tun da wuri.

Don haka ba 'a ja da Ikon Allah.

Bayan haka Daliban Mahadi Suna Gayyatar shehunnai za zakirai almajirai har da Shugabannin Nageriya zuwa matakin duniya wato maulidin sheikhu Ibrahima nyass a gidan imamu mahdi Daiba Gembu a ranar 22/1/2025 Allah ka nuna mana wannan rana Mai dauke da darajoji Mai albarka ameen Neman Karin bayani kira ko WhatsApp +2349161111375 ko +2349022233916

INEC ta buƙaci naira biliyan 126 a kasafin kuɗinta na 2025
12/01/2025

INEC ta buƙaci naira biliyan 126 a kasafin kuɗinta na 2025

Mai Shari'a Juan Merchan ya faɗa wa kotun cewa ya fahimci sallamar Trump ita ce "hukunci ɗaya kacal da ya dace da doka b...
12/01/2025

Mai Shari'a Juan Merchan ya faɗa wa kotun cewa ya fahimci sallamar Trump ita ce "hukunci ɗaya kacal da ya dace da doka ba tare da an ci mutuncin ofis mafi girma ba

Gwamnatin jihar Borno ta ƙaddamar da wata katafariyar Ruga da ta samar ga makiyayan jihar, a wani mataki na bunƙasa hark...
12/01/2025

Gwamnatin jihar Borno ta ƙaddamar da wata katafariyar Ruga da ta samar ga makiyayan jihar, a wani mataki na bunƙasa harkar kiwo, da kuma kawo ƙarshen rikici tsakanin makiyaya da manoma.

An yi gine-gine na wajen zaman makiyaya, da samar da wajen kiwo da na noman ciyawa.

Mutune 16, ciki har da ƴan bijilanti sun mutu a harin sama na soji a ZamfaraAkalla mutane16 ake fargabar sun rasa rayuka...
12/01/2025

Mutune 16, ciki har da ƴan bijilanti sun mutu a harin sama na soji a Zamfara

Akalla mutane16 ake fargabar sun rasa rayukansu bayan wani harin sama da sojoji s**a kai a garin Tungar Kara, karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara.

Jaridar TheCable ta samo rahoto daga Zagazola Mak**a, wani masani mai kawo rahotanni kan yaki da ta'addanci a yankin tafkin Chadi, cewa majiyoyin sirri sun bayyana cewa wadanda abin ya shafa sun hada da mambobin Kungiyar Tsaro ta Al’umma ta Zamfara (ZCPG), ƴan sa kai, da mazauna yankin da aka kira don tunkarar harin da ‘yan bindiga s**a kai.

“Sojojin sun zaci ƴan bijilanti din su ne yan bindigars, bayan yan bindigan sun tsere daga wurin,” in ji rahoton.

“a halin yanzu an gano gawarwaki 16, amma adadin wadanda s**a mutu baki daya bai bayyana ba.”

Olusola Akinboyewa, daraktan hulda da jama’a da labarai na hedkwatar Sojojin Sama na Najeriya (NAF), bai maida martani kan tambayoyin TheCable game da lamarin ba.

Jami'an lafiya a birnin Los Angeles na Amurka sun ce adadin mutanen da s**a mutu sak**akon gobarar da ke ci gaba da ruru...
12/01/2025

Jami'an lafiya a birnin Los Angeles na Amurka sun ce adadin mutanen da s**a mutu sak**akon gobarar da ke ci gaba da ruruwa a yankin ya kai 16.

Ga wasu bayanai dangane da gobarar ta Amurka.

Hukumar Gudanarwar Jami'ar Ahmadu Bello Dake Zaria Ta Amince Da Baiwa Babban Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Sharif Ib...
12/01/2025

Hukumar Gudanarwar Jami'ar Ahmadu Bello Dake Zaria Ta Amince Da Baiwa Babban Malamin Addinin Musulunci, Sheikh Sharif Ibrahim Saleh Digirin Girmamawa A Taron Yaye Daliban Karo Na 44

Daga Jamilu Dabawa

Address

Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Trending News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share