13/09/2026
Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a taron shugabannin BRICS karo na 18, wanda ake gudanarwa a birnin New Delhi na ƙasar India. Shettima ya isa India ne domin wakiltar Najeriya a taron da ke haɗa manyan ƙasashe masu tasowa...
A yayin taron, Shettima ya gana da Firaministan India, Narendra Modi, yayin da shugabannin ƙasashe daban-daban s**a hallara a Bharat Mandapam, wurin da ake gudanar da taron...
Taron na bana ya mayar da hankali kan ƙarfafa haɗin gwiwar tattalin arziki, kasuwanci, fasaha, makamashi, kiwon lafiya da ci gaba mai ɗorewa, tare da tattauna matsalolin da ke addabar duniya a halin yanzu...
Najeriya na ƙoƙarin amfani da kasancewarta cikin tsarin BRICS wajen ƙara samun damar zuba jari, kasuwanci, fasaha da haɗin gwiwar tattalin arziki da ƙasashe membobin kungiyar...
Firaministan India Narendra Modi ya kuma jaddada muhimmancin ƙarfafa haɗin kan ƙasashen Global South, tare da yin kira da a gyara tsarin hukumomin duniya domin ƙasashe masu tasowa su samu ƙarin tasiri wajen yanke shawarar da ta shafi duniya...
A ranar ƙarshe ta taron, Modi ya gana da shugabanni daga wasu ƙasashe, ciki har da wakilin Najeriya, yayin da taron ya ci gaba da tattauna batutuwan tattalin arziki, tsaro da siyasar duniya...
Muftahu Yahaya Mai Dandarani