Funtua Post News

Funtua Post News Funtua Post
Dandalin kawo ingantattun labarai daga Funtua da sauran sassan Najeriya. Muna tabbatar da gaskiya tare da sahihanci a kowanne labari.

WhatsApp=08166055055

Matashi Mai Kwazo Ya Zo Muku Da Ingantaccen POS Machine na MoniepointUMAR SANI AMURO COMMUNICATION CENTRE Unguwar Dallat...
31/07/2025

Matashi Mai Kwazo Ya Zo Muku Da Ingantaccen POS Machine na Moniepoint

UMAR SANI AMURO COMMUNICATION CENTRE
Unguwar Dallatu Area, Opp. Investment Ruwan Doruwa Plaza, Gusau
📞 07032778028

Muna siyar da POS a farashi mai sauƙi — ₦25,000 kacal

Wannan na'ura ba ta da matsalar network kuma tana aiki da sauri da inganci.

Kar ka bari a baka labari Ka zo yau kaima ka mallaki naka!

PDP Ta Shiga Tsaka Mai Wuya a Katsina — Manyan Jiga-Jiganta Sun Sauya Sheƙa Zuwa ADCA ranar Alhamis, 31 ga Yuli, 2025, a...
31/07/2025

PDP Ta Shiga Tsaka Mai Wuya a Katsina — Manyan Jiga-Jiganta Sun Sauya Sheƙa Zuwa ADC

A ranar Alhamis, 31 ga Yuli, 2025, aka gudanar da ziyara a garin Tsiga wanda ya tarbi shugabannin siyasa daga sassa daban-daban. Ziyara ya zama dandalin bayyana sabuwar tafiya da kuma irin tasirin da jam’iyyar ADC ke karɓa a matakin karamar hukumar Bakori.

Inda hon. Abubakar Tsoho ya jagorancin tawagar sa ta karamar hukumar Bakori da Danja.

Karkashin jagorancin.

Dr. Mustapha Muhammad Inuwa

Sanata Ahmad Babba Kaita

Brig. General Maharazu Ismail Tsiga

Hon. Babangida Ibrahim Talau

Hon. Ibrahim Tukur (Wazirin Bakori)

Ziyarar ta duba matsalolin da s**a dabaibaye siyasa a yankin, da matakan da ya dace a ɗauka don sake farfado da siyasa mai inganci da nagarta. An kuma tattauna hanyoyin ƙarfafa jam’iyyar ADC da shirye-shiryen da ke tafe gabanin zaben 2027.

Bayan kammala taron, mahalarta sun gudanar da ziyara ga dattijai da marasa lafiya a garin Tsiga, a wani mataki na nuna damuwa da halin da al’umma ke ciki da kuma ɗora sabuwar tafiyar akan tsarin tausayi da kishin kasa.

Sanarwa daga Amb. Lukman Tsiga.

Tsohon Sanatan Kogi ta Yamma, Sanata Dino Melaye, ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP), i...
31/07/2025

Tsohon Sanatan Kogi ta Yamma, Sanata Dino Melaye, ya sanar da ficewarsa daga jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP), inda ya bayyana komawarsa zuwa jam’iyyar haɗaka ta African Democratic Congress (ADC) a yau Alhamis.

Melaye, wanda ya shahara da salon siyasa mai jan hankali da kuma fitowa fili da ra’ayinsa, ya bayyana wannan sauyin mataki a wata sanarwa da ya fitar. Ya ce wannan mataki ya biyo bayan “zaburar da shi da kuma bukatar sake fasalin siyasa domin samar da sabon salo na shugabanci a Najeriya.”

Sanatan na tsohon ɗan Majalisar Dattawa ya taɓa zama ɗaya daga cikin manyan jiga-jigan jam’iyyar PDP, musamman a lokacin da ya tsaya takarar gwamnan jihar Kogi a ƙarƙashin jam’iyyar a 2023.

Matsalar Tsaro:-Yanzu-Yanzu: Zanga-Zangar Neman Tsaro a Zamfara!Rahotanni daga jihar Zamfara na bayyana cewa ɗaruruwan m...
31/07/2025

Matsalar Tsaro:-Yanzu-Yanzu: Zanga-Zangar Neman Tsaro a Zamfara!

Rahotanni daga jihar Zamfara na bayyana cewa ɗaruruwan mazauna Jimrawa da ke ƙaramar hukumar Ƙauran Namoda – ciki har da mata, matasa da dattawa – sun sauka a birnin Gusau, fadar gwamnatin jihar, suna gudanar da zanga-zanga domin neman mafita daga matsalolin tsaro da ke damun yankinsu.

Zanga-zangar da ke gudana a yanzu haka ta samo asali ne daga gajiya da tsoron da mazauna ke ciki sak**akon hare-haren ‘yan bindiga da ke hana su samun bacci da kwanciyar hankali a gidajensu.

Masu zanga-zangar na ɗauke da alluna da rubuce-rubuce masu kira ga gwamnati da jami’an tsaro da su ɗauki mataki na gaggawa kafin lamarin ya fi karfinsu.

Za mu ci gaba da kawo muku cikakken bayani kai-tsaye daga Gusau…




'a

Barista Mustapha Mahuta, ɗan asalin Ɗandume a Jihar Katsina, ya samu sabon matsayi a matsayin Mataimakin Mai Ba Jam’iyya...
30/07/2025

Barista Mustapha Mahuta, ɗan asalin Ɗandume a Jihar Katsina, ya samu sabon matsayi a matsayin Mataimakin Mai Ba Jam’iyyar ADC Shawara kan Harkokin Shari’a a matakin ƙasa.

Gwamna Dikko Radda Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta Kafar Zoom Daga Abuja — An Amince Da Ayyuka Masu Ƙima Sama d...
30/07/2025

Gwamna Dikko Radda Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta Kafar Zoom Daga Abuja — An Amince Da Ayyuka Masu Ƙima Sama da Naira Biliyan 19 a Katsina

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, ya jagoranci zaman majalisar zartarwar jihar ta kafar Zoom daga inda yake, inda aka amince da muhimman ayyuka guda biyu da za su ƙarfafa ci gaban al’umma.

A yayin zaman, majalisar ta amince da gina wata hanya daga Rafin Iwa zuwa Tashar Bawa a Karamar Hukumar Sabuwa, da za ta ci kuɗi kimanin naira biliyan 18 da miliyan 500.

Haka kuma, an ɗaga darajar Asibitin Mai’adua zuwa Babbar Asibiti, akan kuɗi naira biliyan ɗaya da miliyan ɗari ɗaya.

Hamshakin Ɗan Kasuwa Alhaji Dahiru Mangal Ya Halarci Jami'ar Bristol Dake Kasar Burtaniya, Domin Halartar Bikin Kammala ...
30/07/2025

Hamshakin Ɗan Kasuwa Alhaji Dahiru Mangal Ya Halarci Jami'ar Bristol Dake Kasar Burtaniya, Domin Halartar Bikin Kammala Karatun Ƴa'yansa

Hamshakin ɗan kasuwa na Najeriya, Alhaji Dahiru Mangal, ya halarci bikin kammala karatu na ‘ya’yansa biyu — Alhaji Mohammed Dahiru Mangal da Alhaji Rabi’u Dahiru Mangal — a Jami’ar Bristol, dake ƙasar Burta

Hotunan Bikin Yaye Ɗalibai Daga Makarantar Police Children School, Funtua📸 Hotuna daga Bashir Garba
30/07/2025

Hotunan Bikin Yaye Ɗalibai Daga Makarantar Police Children School, Funtua

📸 Hotuna daga Bashir Garba

Babbar Kotun Jihar Katsina mai lamba 9, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a I.I. Mashi, ta yanke hukuncin kisa ta hanyar ra...
30/07/2025

Babbar Kotun Jihar Katsina mai lamba 9, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a I.I. Mashi, ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga mutum biyu – Shamsu Lawal, tsohon mai gadi, da Tasi’u Rabi’u, mai girki – bayan ta tabbatar da cewa su ne s**a kashe tsohon Kwamishinan Kimiyya da Fasaha na Jihar Katsina, Hon. Rabe Nasir, a shekarar 2021.

Wannan hukunci ya zo ne bayan shekara huɗu da faruwar lamarin da ya tayar da hankali a fadin jihar da ma ƙasar baki ɗaya.

Tarihin Marigayin:
Hon. Rabe Nasir ya kasance ɗaya daga cikin manyan 'yan siyasa da s**a taka rawa a jihar Katsina. Ya taba rike mukamin Kwamishinan Kimiyya da Fasaha, sannan ya yi aiki a hukumar tsaro ta DSS kafin daga bisani ya shiga siyasa.

Yadda Aka Kashe Shi:
Binciken asibiti da na rundunar ‘yan sanda ya tabbatar da cewa mutanen biyu – wadanda s**a kasance ma’aikatan gidan marigayin – sun haɗa guba da abinci s**a ba shi, wanda hakan ya raunata shi matuƙa. Daga bisani, s**a caccaka masa wuka har lahira.

Lamarin ya faru ne a gidansa da ke unguwar Fatima Shema a birnin Katsina a ranar 3 ga Disamba, 2021. Bayan kisan, ‘yan sanda sun k**a wadanda ake zargi, kuma daga bisani s**a gurfana a gaban kotu inda aka gabatar da hujjoji da shaidu masu ƙarfi da s**a tabbatar da laifin nasu.

Hukuncin Kotu:
Bayan dogon shari’a da shaidu na kwarara, kotu ta tabbatar da laifin kisan kai, ta kuma yanke musu hukuncin kisa ta hanyar rataya.

Masu fashin baki na ganin cewa wannan hukunci zai zama izina ga wasu da ke da niyyar aikata laifi mak**ancin haka a nan gaba, kuma hakan na daga cikin ƙoƙarin tabbatar da doka da oda a cikin al’umma.

|Katsina Times.

Halin Da Titin Abdullahi Aminchi Road Ke Ciki Ya Tabbatar da Bukatar Gaggauta Gyara A ci gaba da bibiyar matsalolin titu...
30/07/2025

Halin Da Titin Abdullahi Aminchi Road Ke Ciki Ya Tabbatar da Bukatar Gaggauta Gyara

A ci gaba da bibiyar matsalolin tituna a garin Funtua, mun sami korafi daga mazauna unguwar Abdullahi Aminchi Road kan yadda layin ya lalace matuka, har ya gagara kasancewa titin da ya dace da zirga-zirgar jama’a.

"A shekarun baya, lokacin da Sanata Muntari Dandutse yake matsayin dan Majalisar Tarayya mai wakiltar Funtua/Dandume, ya gabatar da aikin wasu tituna guda uku k**ar yadda ke a kwamitin aikin da aka sanya a hoton da ke kasa. Daga cikin wadancan tituna akwai wannan layin na Abdullahi Aminchi Road.

"Sai dai abin takaici, yayin da sauran titunan biyu s**a samu aiwatar da aikin, wannan layi ya kasance an tsallake shi – kuma har zuwa yau ba a waiwayi gyaransa ba. Wannan tsallakewar ne ya hana aikin titin lokacin da Hon. Lawal Abbas ke aikin titin Tudun/Iya, da kuma lokacin da Sanata Yakubu Lado ke gyaran wasu tituna a yankin.

Layin Abdullahi Aminchi Road yana da akwatunan zabe guda takwas, kuma a halin yanzu yana cikin matsin lamba saboda rushewar kwalbati da tabo da ke hana kowane irin sauki wajen tafiya da motoci ko kafa.

Saboda haka, muna yin kira ga wakilanmu – musamman dan Majalisa mai wakiltar Funtua Alhaji Abubakar Muhammad Gardi – da ya dauki wannan korafi da mahimmanci, a tabbatar da cewa aikin wannan layi ya fara kafin lokacin kamfen ko zabe, domin jin dadin al’ummar da ke cikin yankin.

Daga Aminu S. Uthman |

Ni dan jihar Katsina ne mai kishin cigaban al’umma da makomar kananan yara. Ina amfani da wannan damar domin na roki Mai...
30/07/2025

Ni dan jihar Katsina ne mai kishin cigaban al’umma da makomar kananan yara. Ina amfani da wannan damar domin na roki Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, da ya dubi yiwuwar kirkiro da hukuma ko shiri na musamman da zai dakile yawan yara da ke yawon bara a jihar Katsina.

Yana matukar tayar da hankali da bacin rai ganin yara ‘yan kasa da shekaru 5 zuwa 7 na yawo a manyan tituna suna bara, wasu ma har zuwa karfe 10 na dare, suna cikin hadarin fadawa hannun miyagu, hatsarin hanya, ko kuma fadawa cikin muguwar rayuwa. Abin takaici shi ne, da yawa daga cikin wadannan yaran ba almajirai ba ne; iyayensu na raye, amma sakacin iyaye da rashin kula ne ya jefa su cikin wannan hali.

Ina rokon Gwamna da ya duba wannan batu da idon rahama da tausayi, ya kirkiro wata hukuma ko tsarin da zai:

Tattara wadannan yara daga tituna,

Mayar da su makaranta ko cibiyoyin tarbiyya,

Koyar da iyaye hakkin da ke kansu wajen kula da tarbiyyar ‘ya’yansu,

Daukar mataki akan iyayen da s**a gaza cika nauyin da ya rataya a kansu.

Wannan mataki zai taimaka gaya wajen kare makomar yaranmu, rage zaman banza da aikata laifi a nan gaba, da kuma gina rayuwar al’umma mai inganci a jihar Katsina.

Allah ya taimaka, ya ba Gwamna ikon yin adalci ga al’ummar jihar Katsina.

— Amb Bashir Bala Funtua

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Funtua Post News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Funtua Post News:

Share