Accuracy News 24

Accuracy News 24 Media And News Compny

Zawiyyar Alheri Ta Gwangwaje Kungiyoyin Kwallon Kafa Na Shiyyar Funtua Da Rigunan Yan Wasa Da KwalloZawiyyar Tsohon Saka...
27/09/2022

Zawiyyar Alheri Ta Gwangwaje Kungiyoyin Kwallon Kafa Na Shiyyar Funtua Da Rigunan Yan Wasa Da Kwallo

Zawiyyar Tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Katsina Dr Mustapha Muhammad Inuwa, ta samar da tallafin Rigunan Sanyawa na Yan Wasa da kuma kwallo ga Kungiyoyin 24 da s**a fito daga Shiyyar Funtua.

Shugaban Zawiyyar Dr.Mustapha Muhammad Inuwa ne ya gabatar da tallafin ga Kungiyoyin da s**a amfana a yayin wani taro da ya gudana a Ofishin Yakin Neman Zaben shi da ke Cikin Birnin Katsina.

Tsohon Sakataren Gwamnatin wanda kuma tsohon mai neman takarar Gwamnan Jihar Katsina ne, ya bukaci Matasa akan su rungumi harkokin Wasanni domin dogaro da kan su, maimakon jiran aikin gwamnati.

A cewar shi, Zawiyyar ta yi kudirin shirya gasar kwallon kafa ne ga Kungiyoyin, to sai dai a sabili da yanayin Matsalar tsaro da Shiyyar ta Funtua ke fama da shi Hakan bai yiwu ba.

A sabili da Haka ne aka yanke shawarar samar da tallafin kayayyakin wasan ga Kungiyoyin kamar yadda aka alkawarta.

Alhaji Mustapha Muhammad Inuwa ya yi amfani da damar wurin sanar da mabiyan shi a harkokin siyasa cewar, su shirya tsaf domin bude wani Sabon babi da zai yi a siyasar shi.

A nashi jawabin, Khalifan Zawiyyar Alhaji Hamisu Hara, ya bayyana cewa Zawiyyar ta Shirya gasar kwallon kafa a shiyyoyin Katsina da Daura, sai dai na Shiyyar Funtua bai samu yiyuwa ba a sabili da yanayin tsaro a Shiyyar.

Ya tabbatar da cewar, zasu cigaba da kasancewa a tare da Dr.Mustapha Inuwa, a duk inda ya nufa a harkokin siyasar shi.

Alhaji Hamisu Hara ya sanar da cewa Zawiyyar ta kashe miliyoyin kudi domin shirya gasar, Wadda ke da nufin tallafawa matasa, tare da kara masu kwarin guiwa akan su rungumi harkar Wasanni domin dogaro da kan su.

Sauran wadanda s**a maganta a lokacin taron sun hada da Shugaban Kwamitin Harkokin Wasanni na Zawiyyar Alheri Aminu Musa, sai wasu daga cikin wakilan Kungiyoyin da s**a amfana.

Gamayyar Kungiyoyin Da Ke Goyon Bayan Takarar Peter Obi A Jihar Katsina Sun Jaddada Aniyar Neman Goyon Bayan Al'umma Ga ...
19/09/2022

Gamayyar Kungiyoyin Da Ke Goyon Bayan Takarar Peter Obi A Jihar Katsina Sun Jaddada Aniyar Neman Goyon Bayan Al'umma Ga Dan Takarar Nasu.

Gamayyar Kungiyoyin Da Ke Neman Zaben Dan Ta Takarar Shugaban Kasa Na Jam'iyyar Labour Party Mr.Peter Obi, sun nanata aniyar su ta cigaba da neman goyon bayan jama'a ga dan takarar nasu a zabe mai zuwa.

Shuwagabannin Kungiyar Sun tabbatar da hakan ne a lokacin wani taro da s**a gudanar a Katsina.

Gamayyar Kungiyar ta yaba da kokarin da sauran kungiyoyi ke cigaba da yi na wayar da kan jama'a akan nagartar dan takarar nasu Mr.Peter Obi.

Kungiyar ta kuma nanata fadada rassan ta a Kananan Hukumomin Jihar Katsina, domin bada sukuni ga Dan Takarar nasu ya samu damar lashe zabe mai zuwa.

A kan haka ne, Gamayyar Kungiyoyin ta kafa wani kwamiti mai dauke da mutane 18 domin neman kudade a nan cikin gida da ma wajen Jihar Katsina, domin ganin an samu nasarar tafiyar da bukatun kungiyoyin yakin neman zaben na Peter Obi a Jihar Katsina.

Mambobin Kwamitin sun kunshi mutum daya daga kowace Kungiya, sai Shugabar Mata da aka zabo daga 20Million Alliance 4Peter Obi.

Ga Kuma Jerin Sunayen Mambobin Kwamitin.

2. Mr.Abdullahi Abubakar - Mamba

3. Mr.Suleiman Abubakar -Mamba

4. Mr.Thomas Ocheme - Mamba

5. Mr.Abubakar Lawal Ala - Mamba

6. Mr.Fred Ugwu - Mamba

7. Mr.Habu Bala - Mamba

8. Mr.Peter Odims - Mamba

9. Mr.Ndubuisi Nweke - Mamba

10.Mr.Jamilu Labour -Mamba

11.Mr.Ogbonna Kelvin C - Mamba

12.Barista Nikolas Edem - Mamba

13.Mr.Victor Daniel - Mamba

14.Madam Ofchonogor - Mamba

Wadannan Kuma Lura Da Mukaman Da Suke Da Su Ya Kasance Dole A Tafi Da Su A Cikin Kwamitin.

15.Mr.Bilyaminu Lado Danjuma - Mamba

16.Mr.Henry Paul - Sakatare

17.Mr.Mahmud Ahmad - Sakataren Kudi

18.Mr.Alex Chigozie - Ma'ajin Kudi

A sa'ilinda yake kira ga mambobin Kwamitin akan su yi aiki tukuru wurin gudanar da aiki, Shugaban Gamayyar Kungiyoyin na Peter Obi, ya kuma shawarce su akan su yi aiki bisa sharudda na aikin da aka gindaya kamar :

1. Samar da Allon Hotunan Tallar Dan Takara na Peter Obi da Datti

2.Gudanar Da Tarurrukan Al'umma a kai a kai

3.Gudanar da gangamin neman goyon bayan dan takarar nasu.

4.Gabatar da shirye-shirye da firarraki kafafen yada labaru

5.Samar da abubuwan da ake bukata a dakin tattara sakamako na magoya bayan Peter Obi a Jihar Katsina.

Kungiyar Yan Jarida Marubuta Harkokin Wasanni Ta Kasa Reshen Jihar Katsina Ta Shirya Gasar Kwallon Teburi Ga Kafafen Yad...
19/09/2022

Kungiyar Yan Jarida Marubuta Harkokin Wasanni Ta Kasa Reshen Jihar Katsina Ta Shirya Gasar Kwallon Teburi Ga Kafafen Yada Labarai

A wani bangare na gudanar da bikin Makon Yan Jarida na wannan shekarar, Kungiyar Yan Jarida Marubuta Harkokin Wasanni Ta Kasa Ta Shirya Gasar Kwallon Teburi ga Kafafen Yada Labaru da ke Jihar.

Bayanin hakan na kunshe ne a cikin wata takardar Manema Labarai mai dauke da sa hannun Shugaban Kungiyar na Jihar Katsina, Kwamarad Nasir Sani Gide.

Gasar mai taken 'Kanwan Katsina Media Table Tennis Competition 2022 a turance, za'a fara ta ne a Ranar 21 ga watan Satumba na wannan shekarar da muke ciki.

Kamar yadda takardar ta bayyana, za'a gudanar da gasar ne a sakatariyar Kungiyar Yan Jarida ta Kasa reshen Jihar Katsina kuma za'a fara ne da misalin karfe 11:00AM na safe.

Kamar yadda sanarwar ta bayyana, Kungiyar yan jaridu ta kasa reshen Jihar Katsina hadin gwiwa da kungiyar Yan Jarida Marubuta wasanni ta Najeriya (SWAN) reshen jihar Katsina, su ne s**a shirya gasar.

Sanarwar ta bayyana cewa , za'a buga gasar ne tsakanin kafafen Yada Labarai da s**a hada Gidan Talabijin na Jihar Katsina KTTV, sai gidan Radiyo na Jihar Katsina da Ma’aikatar Yada Labaru da kuma reshen Kungiyar Yan Jaridu ta Najeriya masu aikewa da rohotonni reshen jihar Katsina.

Sauran sun hada Gidan Talabijin na Kasa da ke Katsina NTA da Gidan Rediyo na Alfijir da ke Katsina gami da Gidan rediyo na Vision FM da ke Katsina tare da Gidan Rediyo na (Companion FM) da kuma Gidan Rediyo na Martaba da ke Funtua.

Turkashi.....Rikakken Ɗan Ta'addan Nan BelloTurji, Wanda Ya Addabi Al'ummar Yankin Arewa Maso Yamma Yake A Bakin Aiki Ci...
19/09/2022

Turkashi.....

Rikakken Ɗan Ta'addan Nan BelloTurji, Wanda Ya Addabi Al'ummar Yankin Arewa Maso Yamma Yake A Bakin Aiki Cikin Shirin Ko Ta Kwana Kamar Wani Hukumar Kayan Sarki.

Mambobin Zawiyyar Dr.Mustapha Muhammad Inuwa Sun Jaddada Mubaya'ar Su Ga Jagoran NasuMambobin Ƙungiyar Zawiyya Alheri su...
18/09/2022

Mambobin Zawiyyar Dr.Mustapha Muhammad Inuwa Sun Jaddada Mubaya'ar Su Ga Jagoran Nasu

Mambobin Ƙungiyar Zawiyya Alheri sun kara jaddada goyon bayan su ga Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Jihar Katsina kuma jagoran siyasar su Dr.Mustapha Muhammad Inuwa.

Mambobin Kungiyar sun jaddada mubaya'ar su ne a lokacin da s**a ziyarci jagoran nasu a Ofishin yakin neman zaben shi da ke katsina.

Ƙungiyar a ƙarƙashin jagorancin Alhaji Hamisu Hara tare da daukacin mambobin ta na Kananan Hukumomi 34 na Jihar Katsina sun ce suna tare da jagoran nasu a duk inda ya dosa a harkokin siyasar shi.

Da yake magantawa a lokacin taron, Tsohon mai neman takarar Gwamnan Dr. Mustapha Muhammad Inuwa, ya tabbatar da cewa, tuni ya dauki rashin nasarar shi a zaben fidda gwani a matsayin mukaddari daga Allah SWT.

Shehin Zawiyyar yace nan bada jimawa zai sanar da matsayar sa akan inda zai koma da ɗumbin magoya bayan sa, da Ɗan Takarar da zai marawa baya, kasancewar tuni Majalisar ƙolin sa ta ɗauki matsaya akan haka.

Alhaji Mustapha Inuwa yace duk matakin da zai ɗauka, zai yishi ne domin tsare mutuncin kan sa da magoya bayan sa, sai ya buƙaci masoyan sa da su cigaba da addu'a akan Allah ya haska abinda yafi nasara ga Al'ummar Jihar Katsina.

Ya yi jawabi mai tsawo akan ƙoƙarin da yayi na samun tsaro a Jihar Katsina, da kuma sharrin da akayi mashi na sanya hannu a ta'addanci, sai ya buƙaci Al'umma dasu dogon nazari kasancewar ba Katsina kaɗai ake ta'addanci ba.

Khalifan Zawiyyar Alhaji Hamisu Hara yace sun shirya gangamin taron domin jaddada mubayi'ar su ga Alhaji Mustapha Muhammad Inuwa, da kuma tabbatar masa da cewa duk inda ya koma da siyasar sa zasu bishi.

Wadannan Ma'auratan Sun Yi Shekaru 25 Da Yin Aure.Allah Ya Kara Dankon Soyayya Ya Kuma Yi Wa Zuri'a Albarka.
18/09/2022

Wadannan Ma'auratan Sun Yi Shekaru 25 Da Yin Aure.

Allah Ya Kara Dankon Soyayya Ya Kuma Yi Wa Zuri'a Albarka.

Ina Tsoron Kada EFCC Ta Kame Ni Idan Pi-Network Ta Fashe - Cewar Wani Dan Pi
18/09/2022

Ina Tsoron Kada EFCC Ta Kame Ni Idan Pi-Network Ta Fashe - Cewar Wani Dan Pi

Ba Dare Daya Za'a Shawo Kan Matsalar Layukan Waya Da Basu Da Rajista Ba A Najeriya, Matsala Ce Da Ke Bukatar Zurfin Ilim...
18/09/2022

Ba Dare Daya Za'a Shawo Kan Matsalar Layukan Waya Da Basu Da Rajista Ba A Najeriya, Matsala Ce Da Ke Bukatar Zurfin Ilimi Da Jajircewa - Cewar Ministan Sadarwa Da Tattalin Arziki Na Zamani.

18/09/2022

Taron Kaddamar Da Aza Harsashen Gina Katafariyar Asibiti A Filin Canada Da Ke Yankin Sabuwar Unguwa A Nan Cikin Birnin Katsina.

Aikin Dai Dan Takarar Kujerar Dan Majalissar Tarayya Mai Wakiltar Mazabar Katsina Ta Tsakiya Na Jam'iyyar APC Honorabul Sani Aliyu Danlami Ne Ya Samo Shi Kuma Ya Kaddamar Da Shi.

Mai Raba Alkairi Ya Kaddamar Da Gina Katafariyar Asibiti A Cikin Birnin KatsinaDan Takarar Kujerar Dan Majalissar Tarayy...
17/09/2022

Mai Raba Alkairi Ya Kaddamar Da Gina Katafariyar Asibiti A Cikin Birnin Katsina

Dan Takarar Kujerar Dan Majalissar Tarayya mai wakiltar mazabar Katsina ta Tsakiya Honorabul Sani Aliyu Danlami, ya kaddamar da aikin gina katafariyar cibiyar kula da kiwon lafiya a Cikin Filin Kanada da ke Sabuwar Unguwa a cikin Birnin Katsina.

Katafariyar Asibitin mai dauke da gadaje 20 na kwantar da marasa lafiya, ta kuma kunshi dakin Gwaje-Gwaje da Dakin Karbar Haihuwa gami da Gidajen Ma'aikatan Asibitin.

A cewar Honorabul Danlami, a bisa yunkurin shi na kawo cigaba ga al'ummar Mazabar ne ya sanya ya yi ruwa da tsaki domin nemo aikin asibitin daga Birnin Tarayya Abuja.

Alhaji Sani Aliyu Danlami ya tabbatar da cewa, ya nemo aikin ne a Hukumar Kula Da Tattara Kudin Shiga ta Gwamnatin Tarayya, wato(Federal Inland Revenue Service)a turance.

Dan Takarar ya nanata kudirin shi na cigaba da aiwatar da ayyukan cigaban jama'a, musamman ma taimakon Marayu da masu karamin karfi, domin su san cewa an kula da su.

Garkuwan Arewan na Katsina ya kuma bukaci jama'a akan su taya shi da addu'a akan Allah SWT ya kara mashi kwarin gwuiwar tausaya wa Marayu da mabukata.

Daga nan sai ya tabbatar da cewa da izinin Allah aikin ba zai dauki dogon lokaci ba ana gudanar da shi.

Sauran wadanda s**a maganta a lokacin taron sun yaba wa Garkuwan Arewan akan fafutukar shi ta kawo cigaba ga al'umma.

Sun yi mashi addu'ar samun nasara a dukkan lamurran shi na siyasa, sai s**a yi kira ga sauran yan siyasa akan su yi koyi da shi.

An Yaye Yan Sintiri 600 Da Aka Baiwa Horon Sarrafa Makaman Zamani Da Dubarun Yaki A Jihar KatsinaA wani mataki na tunkar...
17/09/2022

An Yaye Yan Sintiri 600 Da Aka Baiwa Horon Sarrafa Makaman Zamani Da Dubarun Yaki A Jihar Katsina

A wani mataki na tunkarar yan ta'adda masu tada kayar baya a Jihar Katsina, Gwamnatin Masari ta dauki dawainiyar bayar da horo ga yan sintiri su 600 domin ganin an shawo kan matsalar.

An dai bada horon ne ga yan sintirin akan dabarun sarrafa makamai na zamani da sauran dabarun yaki, ta yadda zasu taimakawa sauran jami'an tsaro, don ganin an samu damar kakkabe yan ta'adda da s**a hana zaune tsaye a Jihar Katsina.

Idan dai masu Bibiyar Shafin Accuracy News 24 basu manta ba, wadanda aka baiwa horon sun fito ne daga Kananan Hukumomi 34 na Jihar Katsina.

Jami'an Hukumar Kula Da Tsaron Lafiyar Yan Kasa wato Civil Defence, su ne s**a bayar da horon ga yan sintirin, a farfajiyar Kwalejin Hukumar da ke kan hanyar Katsina zuwa Batsari.

Da yake magantawa a wurin taron, Gwamnan Jihar Katsina Alhaji Aminu Bello Masari, ya bayyana cewa bayar da horon na daga cikin yunkurin da Gwamnatin shi ke yi na ganin an kakkabe masu aikata laifukan ta'addanci kwata-kwata a Jihar Katsina.

Alhaji Aminu Bello Masari wanda Sakataren Gwamnatin Jiha Alhaji Muntari Lawal ya wakilta, ya nanata kudirin Gwamnatin shi na bayar da dukkan goyon bayan da ya dace ga jami'an tsaro domin basu sukunin ganin an shawo kan matsalolin tsaro a Jihar Katsina.

Ya bukaci jama'a akan kada su gajiya wurin bayar da bayanan sirri ga jami'an tsaro, domin taimaka masu wurin fuskantar duk wasu masu son zaluntar jama'a.

A nashi jawabin, Mai Bada Shawara Akan Harkokin Tsaro Alhaji Ibrahim Ahmad Katsina, ya yi tuni da cewar a baya ma Gwamna Masari ya dauki dawainiyar bayar da irin wannan horo ga yan sintiri kusan 500.

Ya bukaci wadanda aka horas din akan koda yaushe su rika aiki da jami'an tsaro daban-daban da suke a yankunan su.

Sauran wadanda s**a maganta sun hada da Wakilin Mai Martaba Sarkin Katsina Alhaji Abdulmuminu Kabir Usman, da Shugaba Kwalejin Bayar Da Horo Ta Civil Defence Babangida Abdullahi tare da Kwamandan Sintiri Yan Sintiri na Jihar Katsina Rabo Kurfi.

Sun Jinjina wa Gwamna Aminu Bello Masari akan yadda suke fadi tashi don ganin an kakkabe yan ta'adda a Jihar Katsina.

APC Ta Dakatar Da Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Kurfi A Jihar KatsinaJam'iyyar APC A Karamar Hukumar Kurfi A Jihar...
16/09/2022

APC Ta Dakatar Da Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Kurfi A Jihar Katsina

Jam'iyyar APC A Karamar Hukumar Kurfi A Jihar Katsina Ta Dakatar Da Mataimakin Shugaban Karamar Hukumar Kurfi Malam Nazifi Bisa Zargin Yi Wa Jam'iyyar APC Zagon Kasa Kuma An Kafa Kwamitin Da Zai Yi Kwakkwaran Bincike Kan Zarge-zargen Da Ake Yi Masa.

Dakatarwa Ta Fara Aiki Daga Yau Juma'a Har Sai An Kammala Binciken.

Yan Sanda Sun Bindige Wani Mutum Da Ake Zargin Dan Fashi Da Makami Ne A Jihar KatsinaJami'an Rundunar Yan Sanda Ta Jihar...
16/09/2022

Yan Sanda Sun Bindige Wani Mutum Da Ake Zargin Dan Fashi Da Makami Ne A Jihar Katsina

Jami'an Rundunar Yan Sanda Ta Jihar Katsina, sun samu nasarar bindige wani mutum da ake zargin cewa Dan Fashi Da Makami ne akan hanyar Daura zuwa Mai'adua.

Wanda aka bindige din yana daga cikin Yan Fashi Da Makami su 3 da ake zargin sun sato wata mota kirar Toyota Jeep daga Birnin Tarayya Abuja.

Kakakin Rundunar Yan Sanda ta Jihar Katsina S.P Gambo Isah ne ya gabatar da gawar dan fashin a sa'ilin da yake jawabi ga Manema Labaru akan nasarorin da Rundunar ta samu.

A cewar shi, an hallaka dan fashin ne akan hanyar su ta zuwa Jamhuriyar Nijar, a iyakar Karamar Hukumar Mai'adua.

Haka zalika, sauran wadanda suke tare da su a motar sun tsira da harbin bindiga na yan sanda a jikin su.

Kakakin Rundunar ya bayyana cewa, wadanda ake zargin suna amfani ne da wata na'ura da ke dauke sabis din na'urar gano inda aka nufa da abin hawa da Jami'an Yan Sanda ke amfani da ita daga Abuja domin gano inda motar ta nufa.

A sabili da rohoton sirri da aka samu, jami'an Rundunar Yan Sanda ta Jihar Katsina sun samu nasarar gano motar kuma aka hallaka daya daga cikin wadanda ake zargin sun sato motar.

Hoto: Gidan Talabijin Na Jihar Katsina KTTV

Duk Abunda Za Ka Yi Ka Da Ka Kuskura Ka Shiga Hakkin Iyayenka, Biyayya Ga Iyaye Tana Daga Darajar Mutum Duk Kaskancinsa,...
16/09/2022

Duk Abunda Za Ka Yi Ka Da Ka Kuskura Ka Shiga Hakkin Iyayenka, Biyayya Ga Iyaye Tana Daga Darajar Mutum Duk Kaskancinsa, Haka Nan Bijire Wa Iyaye Yana Kaskantar Da mutum Duk Girman Darajarsa.

Allah Ka Karawa Iyayenmu Lafiya Da Nisan Kwana, Waɗanda S**a Rasu Allah Ya Jiƙansu!

Cewar Jarumin Fina-finan Kannywood, Abdul Sahir

Hotunan Tsaunin Bilat Da Ke Cikin Jihar Agadez Ta Jamhuriyar Nijar, Yana Da Fadin Mita 1600.
16/09/2022

Hotunan Tsaunin Bilat Da Ke Cikin Jihar Agadez Ta Jamhuriyar Nijar, Yana Da Fadin Mita 1600.

Marigayiya Sarauniyar Ingila A Cikin Shigar Kayan Kwallo Na Yan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Da Ke Kasar Ingila.
16/09/2022

Marigayiya Sarauniyar Ingila A Cikin Shigar Kayan Kwallo Na Yan Kungiyar Kwallon Kafa Ta Arsenal Da Ke Kasar Ingila.

MALAMAI MAGADA ANNABAWATakaitaccen Tarihin Babban Malamin Addinin Islama A Jihar Katsina Sheikh Imam AbateCikakken sunan...
16/09/2022

MALAMAI MAGADA ANNABAWA

Takaitaccen Tarihin Babban Malamin Addinin Islama A Jihar Katsina Sheikh Imam Abate

Cikakken sunan Shehin Malamin Shi ne, Malam Muhamud Abdulbaqi Muhamud (Abbate).

An haifi Mallam Abbate ne a cikin Birnin Katsian, a Unguwar Yanshuni, a Shekara ta 1930.

Ya fara Karatun Tsangaya (Makarantar Allo) a wajan Mahaifinsa Mallam Abdulbaki, wanda kwararran Malami ne ta fannoni da dama da rubuce-rubuce da s**a shafi Ilimin Addinin Islama.

Ana kiran Mallam Mahmud Abdulbaki da Abbate ne saboda sunan kakan shi ke gareshi, wato Mallam Mudi.

Malam Abbate ya cigaba da sauran karance karancen shi ne a wurin Mahaifin shi, kuma bayan Allah ya yi wa Mahaifin nashi rasuwa Shekara 60 da ta wuce, ya kara dukufa a wurin neman Ilimi wurin Malamai daban-daban a nan cikin Birnin Katsina, Domin fadada karatun shi, musamman yadda yazama halifan Mahaifinsa.

Ya yi karatu a wurin Malamai fiye da 1, a Katsina, wanda s**a hada da Malam Aala Tsohuwar kasuwa da Malam Falalu Darma da Malam Gambo da Malam Yusif da Malam Hamisu Galadanci da Mallam Muhammadu Bahillace da sauran su.

Daga cikin Abokan Karatunsa Kuma akwai Limamin Katsina Malam Liman Malam Lawal da Malam Babangida Abbas, Limamin Garin Rimi, Limamin Jibiya da Shehu Mallam Namadi da sauran su.

Imam Malam Abbate ya gaji Makarantar Gidan su tun yana Dan Shekara 30, wadda yake jagora har yanzu.

Yana da tsarin koyarwa Wanda yake Yi kamar haka:

*Ranar Assabar TAFSIRIN AL QUR'ANI
*Ranar Lahadi da Litinin Fiqihu da lugga da Nahawu
*Talata da Laraba HADISI

Ana Fara zaman koyar da karatu tun daga karfe 7:00 Na safe har zuwa karfe 1:30 na Rana, sannan Kuma yana gudanar da karatun Azumi a kowace Shekara Sau Hudu da safe, TAMBIHUL GAFILINA A Masallacin gidan su na Yanshuni.

Bayan Sallah Azahar Asshifa'i a Masallacin cikin Unguwar Alkali.

Bayan Sallar La'asar, Tafsiri a Masallacin Gidan Sarkin Fadan Katsina sai Kuma bayan anagama Sallah Tarawuhi Tafsiri a Masallacin Dan Fili Unguwar Alkali.

Sheikh Malam Abate ya jagoranci Alahzai da dama zuwa aikin Hajji tun lokacin Katsina na a karkashin Tsohuwar Jihar Kaduna, har zuwa lokacin da ita ma Katsina ta samu jiha.

A cikin Shekara ta 2006 ne Mai Martaba Sarkin Katsina Alh Dr Muhammadu Kabir Usman, ya nada Mallam Liman Abbate a matsayin Babban Limamin Masallacin juma'a na Unguwar Tayoyi da ke nan cikin Birnin Katsina, Wanda aka fi sani da Masallacin Mangal.

Allah ya sa a gama da duniya lafiya.

Daga Karshe Dan Daudu Abdullahi Umar Ya Sha Bulala Arba'inKotu ta yi wa wani dan daudu da aka ga hoton bidiyon shi na ya...
16/09/2022

Daga Karshe Dan Daudu Abdullahi Umar Ya Sha Bulala Arba'in

Kotu ta yi wa wani dan daudu da aka ga hoton bidiyon shi na yawo a kafafen sada zumunta na zamani a kan kabarin wata mamaciya yana danna mata ashar bulala 40.

An dai bulale dan daudun ne bayan da kotun ta same shi dumu-dumu da laifin zuwa makabarta yana zagin wata mata da ke kwance cikin kabarinta a Jihar Kano.

Address

Shagari Lowcost
Katsina
0000

Telephone

+2347033444156

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Accuracy News 24 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Accuracy News 24:

Videos

Share