Moppan dakin kara

Moppan dakin kara Page of hospitality

Hajiya Binta Kofar Soro: Shahararriyar mai wasan Hausa 'Yar Kanywood a garin Katsina Yau tacika shekara 4 da rasuwa Uban...
23/03/2023

Hajiya Binta Kofar Soro: Shahararriyar mai wasan Hausa 'Yar Kanywood a garin Katsina

Yau tacika shekara 4 da rasuwa Ubangiji ya jaddada rahama a kabarinta

Me Ya Sa Hukumar Kidaya Ba Ta Tantance Wadanda S**a Nemi Aikin Kidaya Na Yankin Wakilin Arewa 'B' A Karamar Hukumar Kats...
11/02/2023

Me Ya Sa Hukumar Kidaya Ba Ta Tantance Wadanda S**a Nemi Aikin Kidaya Na Yankin Wakilin Arewa 'B' A Karamar Hukumar Katsina Ba?

Daga Mohammad A. Isa

Korafe-korafe sun yawaita daga al'ummar da s**a fito daga yankin Wakilin Arewa 'B' a karamar hukumar Katsina, kan yadda hukumar kidaya ta jiha ta tsallake tantance mutanen yankin wadanda s**a nemi aikin wucin gadi wanda hukumar za ta gudanar a shekarar nan ta 2023, alhali a cewarsu sun cike duk sharuddan da ake nema na tantancewar, har ma an saki sunayensu tare da lika sunayen nasu su kimanin 285 a ofishin Hedikwatar hukumar Kidayar ta Jiha domin tantancewa.

Al'ummar sun bayyana mani cewa, hukumar ta saki jadawalin ranakun tantance kowane rukunin al'umma na yankunan karamar hukumar ta Katsina (Wards) a ofishin hikimar, inda a jadawalin, hukumar ta sanya ranar Lahadi 5 ga watan Fabrairun 2023 a matsayin ranar da za ta tantance mutanen da s**a fito daga yankin na Wakilin Arewa 'B', sai dai da mutanen yankin s**a halarci Hedikwatar tancewar a ranar da aka ayyana masu, tun da sanyi Safiya har zuwa Yammaci ba su ga keyar ko mutum daya daga cikin ma'aikatan tantancewar ba tsawon yin, daga bisani ne ma s**a sami sakon cewa ma'aikatan sun ce ranar ba za su yi aikin tantancewar ba, sai dai su dawo kashegari (Litinin 6 ga Fabrairu).

Al'ummar sun ci gaba da bayyana mani cewa, kashegari da s**a sake dawowa k**ar yadda aka umurce su, shi ma tun da sanyin safiya har rana ta yake ba su ga keyar kowa ba, sai ma wani sako marar dadi da s**a samu daga ma'aikatan cewa a fadawa mutane cewa su fa sun riga da sun rufe tantancewar tun a ranar Lahadi, don haka kowa ya k**a gabansa.

Bayan gama jin korafe-korafen al'ummar yankin, na garzaya zuwa ofishin shugaban riko na yanki da al'ummar Wakilin Arewa 'B' din s**a fito wato Galadiman Arewa. A tattaunawar da na yi da Galadiman Arewan, ya bayyana mani cewa; duk da yake su ne Sarakunan jama'a, amma hukumar kidayar ba ta saka su a cikin sha'anin aikin ba, b***e su san abin da yake zuwa yana dawowa a cikinsa. Don haka kawai kowa ya hakura da aikin tun da an ce an rufe.

Haka kuma, na yi tattaki zuwa Hedikwatar hukumar don jin ta bakinsu a kan korafe-korafen da jama'ar ke yi a kansu dangane da rashin tantance su, amma dai magana daya tilo ce amsar, "an rufe tantancewar tun ranar Lahadi."

Wasu mutane sun tsegunta mani cewa, duk da an ce an rufe tantancewar, amma suna lura da wasu mutane na gittayya a hukumar, suna kai Sunayen da Lambobin rajistarsu na aikin Kidayar, wanda suke zargin kila masu uwa a bakin murhu ne za a tantance su ta bayan gida.

"Meye matsayinmu a yanzu da ba a tantance mu ba? A matsayinmu na 'yan k'asa da muka cika sharuddan zama 'yan kasa kuma muka cika sharuddan yin aikin a matakin farko (domin har sunayensu ya fito saura tantancewar), shin yanzu an soke mu ne a cikin tsarin aikin, ko kuwa? Idan an soke mu ne, meye dalilin sokewar, kuma me ya sa ba a yi mana bayani don mu san matsayinmu ba?" Tambayoyin da al'ummar na Arewa 'B' ke yi kenan.

Yankin Wakilin Arewa 'B' dai yanki ne da ke cikin birnin katsina tsamo-tsamo, wanda yake da dubban al'ummma da s**a hada da 'yan Boko, Ma'aikatan gwamnati, 'yan Kasuwa, Dalibai, da wadanda s**a kammala Karatu a Manyan makarantu da sauransu.

An rantsar da Zababbun Shuwagabannin MOPPAN na jihar Katsina.Daga Zaharaddeen Ishaq AbubakarA ranar Lahadi 4 ga watan Sa...
05/09/2022

An rantsar da Zababbun Shuwagabannin MOPPAN na jihar Katsina.

Daga Zaharaddeen Ishaq Abubakar

A ranar Lahadi 4 ga watan Satumba ne aka rantsar da zababbun shuwagabannin haddiyar kungiyar masu harkar Fina-finai ta kasa reshen jihar Katsina wato Motion Picture Practitioners Association of Nigeria (MOPPAN), taron da ya gudana a Dakin taro na tsohon gidan Gwamnatin jihar Katsina, ya samu halartar manyan baki daga Gwamnatin Katsina da kuma 'ya'yan kungiyar ta MOPPAN.

Wadanda aka rantsar a wajen sun hada da Comrade Lawal Rabe Lemoo a matsayin Chairman, Aminu Musa Bukar a matsayin mataimakin Chairman,Yasir Abubakar a matsayin Babban maga takarda, Rabe Halliru a matsayin mataimakin maga takarda, Ibrahim Shehu a matsayin ma'ajin kungiyar. Sauran sun hada da Rufa'atu S. Idris a matsayin Sakatariyar Kudi, Aliyu Ibrahim a matsayin Sakataren tsare-tsare, Ibrahim Sani a matsayin mai bincike I Hussaina Muhammad mai bincike II, Ummulkhairi Abubakar Sakatariyar walwala da jin dadi, Rabi'u M. Yaro a matsayin PRO I sai Suwaiba Auwal: PRO II.

Babban bako mai jawabi na farko a wajen, shine mai bawa Gwamnan Katsina shawara akan fatauci da miyagun kwayoyi da safarar bil'adam Hon. Hamza Muhammad Burodoo, ya jawo hankiln Matasa akan illar sha da fataucin miyagun kwayoyi da kuma musifar da ka iya fuskanta ga masu harkar fataucin jama'a. Mai bawa Gwamnan Katsina shawara na musamman akan sha'anin tsaro, Alhaji Ibrahim Katsina, ya yabawa Kungiyar ta MOPPAN dakuma sanya hannu a karkashin ofishin sa domin bawa 'ya'yan kungiyar horo, domin kara sanin mak**ar sana'ar tasu, inda anan take ya bada umarni ga Dakta muktar El'kasim malamin jami'ar Ahamdu Bello dake Zariya da su tattauna da shugabannin na MOPPAN akan bada horon.

Malam Sabo Musa Hassan Shine mai taimakawa Gwamnan Katsina akan maido da al'amura Cif da cif, wa'azi yayi da nasiha akan matsalar da ake fama da ita ta tsaro a jihar Katsina, inda ya bayyana abin a matsayin jarabawa wadda Allah ne kadai zai iyakance ta, mu musulmi abinda ke namu addu'a da komawa ga Allah injishi.

Shugaban kungiyar na MOPPAN da aka rantsar dasu yayi jawabin godiya ga mahalarta taron gami da bijiro da wasu bukatu ga Gwamnatin jihar Katsina a gaban Sakataren Gwamnati, inda ya nemi da Gwamnatin ta jiha ta samar da Ofishin tace finafinai, a jihar. Sana yayi roko da a samar masu da Ofishin din-din-din, da zasu dunga gudanar da ayyukan su.

A karshe kungiyar ta karrama shugaban hukumar kula da hanyoyi na jihar Katsina Engr. Surajo Yazid Abukur bisa jajircewarsa da taimakon kungiyar dare da rana, inda wasu matasa masu kishin jihar Katsina s**a wakilce shi.

Bakin da s**a halarci wajen sun hada da Sakataren Gwamnatin jihar Katsina Alh. Muntari Lawal, mai bawa Gwamnan katsina shawara akan sha'anin tsaro Alh. Ibrahim Katsina, mataimaki na musamman ga Gwamna akan maido da al'amura k**ar yanda suke, Barasta Aminu Danbaba daga Maidangana Chamber, Shugaban Kamfanin AA Moda Gellary (Tafidan kaita) Wakilin mai martaba Sarkin Katsina, da mai taimakawa Gwamna na musamman akan matasa da wasanni Alh. Ibrahim Khalil, Danjarida mai Kamfanin matasa Media Links masu buga jaridar Katsina City News, Taskar Labarai da The Links Malam Danjuma Katsina, Daraktoci daga ma'aikatar yada labarai ta jihar katsina da sakatarorin din-din-din na ma'aikatar da sauran al'umma.

Ka Samu Naka Kyautar Dala $2 Din Kuwa?Mara wallet ma'ajiya ce ta Kudi da kuma cinikayya da hada-hadar coins wadda za ta ...
21/08/2022

Ka Samu Naka Kyautar Dala $2 Din Kuwa?

Mara wallet ma'ajiya ce ta Kudi da kuma cinikayya da hada-hadar coins wadda za ta fara aiki nan da wata mai k**awa.

Ga duk wanda ya yi rajista da ita a yanzu, za su ba shi dala $2 kyauta wato kwatankwacin naira #1,200 Kudinmu na Nijeriya.

Mutum zai iya cire kudin nasa da zarar sun kaddamar da ita a wata mai k**awa. Wannan ko tantama babu.

Idan ka bi likau din nan da ke a kasa, zai kai ka inda za ka yi rajistar ta hanyar saka kibdau dinka wato Email, sai ka je ka ciki ka yi confirmation din sa, sannan ka dawo ka sauke shi a Playstore. Daga nan za ka ga dala $2 din cif-cif.

Mun kawo maku ita ne kyauta don ku amfana, ba tare da kun yi wani aiki ba.

Katsina a cikin fargaba: Masu garkuwa da mutane sun sake shiga Unguwar Shola...Zaharaddeen Ishaq Abubakar  City News 🗞️R...
07/08/2022

Katsina a cikin fargaba: Masu garkuwa da mutane sun sake shiga Unguwar Shola...

Zaharaddeen Ishaq Abubakar City News 🗞️

Rahotanni da muka samu na cewa mahara sun shiga Unguwar Shola Quarters a daren jiya Asabar, inda s**a yi harbe-harbe, da jikkata da dama daga cikin su. Kuma ana saran sun tafi da wasu mazauna Unguwar.

Ƙasa ga kwana hamsin ɓarayin sun taɓa shiga Unguwar inda s**a kwashi mutane s**ayi garkuwa da su. A ɗan tsakaninnan masu garkuwa da mutanen sun matsawa wasu yankunan kusa da Birnin Katsina, inda a cikin kwanaki biyu s**a kai hari a ƙauyen dake bayan barikin Sojoji na katsina s**a sace Mutane s**a tafi babu wata turjiya, haka kuma Ɓarayin s**a riƙa karakaina a ƙauyen Ɗan Tsauni dake a hanyar Babbar Ruga bisa Titin Batsari s**a kashe Mutane s**a kore Dabbobi tare da tafiya da wasu Mutanen.

Unguwar Shola Quarters tana Yammacin garin Katsina bayan Babbar Asibitin koyarwa ta Gwamnatin Tarayya.

MATSALAR TSARO: Mawakin Siyasa Rarara ya shirya taron Addu'a wa ƙasaZaharaddeen Ishaq Abubakar  City NewsShahararren maw...
01/08/2022

MATSALAR TSARO: Mawakin Siyasa Rarara ya shirya taron Addu'a wa ƙasa

Zaharaddeen Ishaq Abubakar City News

Shahararren mawaƙin Siyasa kuma shugaban ƙungiyar 13x13 Movement ya shirya taron yiwa ƙasa Addu'a, a garin Kano.

Taron da aka kira na haɗin kai ba na Siyasa ba, saboda Matsalar rashin tsaro ne a ƙasa kuma ya shafi kowa, ko daga wane yanki ka fito ko jam'iyyar ka idan har kai mai kishin ƙasa ne, dole kaso ta samu dauwamammen zaman lafiya. Inji Rarara

Taron da ya haɗa Alarammomi, mahaddata, Dattawan ƴan Kanywood Maza da Mata, da sauran al'uma. Angudanar da shi a garin Kano ranar Litinin, inda akayi saukar Alqur'ani mai girma da yanka raƙuma, aka rabawa duk wanda baya samu halartar taron domin neman sauƙi akan halin da ƙasar ta shiga na rashin tsaro.

Shugaban na 13x13 Dauda Kahutu Rarara da yake zantawa da manema labarai a wajen taron yace "Mun zaɓi wannan hanyar ne saboda shi Alqur'ani waraka ne ga kowa da komi, kuma halin da muke ciki mafitar mu kawai itace Addu'a, a matsayin mu na sauran al'umma. Itama Gwamnati tayi nata jami'an tsaro suyi nasu, mu kuma muyi Addu'a. Najeriya ta shiga wani irin hali wanda idan har ba amfita daga wannan matsalar ta rashin tsaro ba to zaɓen ma da muke hanƙoro ba zai yiyu ba." Inji shi.

Taron wanda ya haɗa kowa da kowa, da ɗan ƙungiyar 13x13 da wanda baya ciki, da ma ƴan jam'iyyu mabambanta ƴan Fim na da da na yanzu, inda taron ya haɗa zumunci bayan addu'o,i kowa ya tafi cikin raha da begen juna.

22/06/2022

************************************

SANARWA SANARWA SANARWA

Assalam,

Cibiyar bayar da horon sana'oi mai suna KATSINA VOCATIONAL TRAINING CENTER ta shirya taron maraba ga sabbin dalibanta na wannan karon.

Don haka ne cibiyar ta gayyaci daukacin yayan wannan kungiya ta MOPPAN domin halartar wannan taro.

A wajen taron shugaban kungiyar MOPPAN na Jihar Katsina wato Comrade Lawal Rabe Lemoo zai gabatar da kasida mai taken FINA FINAI A KASAR HAUSA.

Don haka ne kungiyar MOPPAN reshen Jihar Katsina ke gayyatar yayanta domin sheda wannan gagarumin taro da zai gudana k**ar haka:

Rana: Alhamis 23-6-2022
Lokaci: Karfe 9:00na safe
Wuri: Dakin taro na KVC dake unguwar Kerau kusa da Gidan Alh. Ladan Wapa.

Allah Ya bada ikon halarta, Ameen

Sanarwa
Yasir Abubakar
SECRETARY MOPPAN KATSINA STATE

# # # # # # # # # # # # # # # # # # # # # # # # # #

Kungiyar MOPPAN Reshen Jihar Kano Ta Kira Taron Masu Ruwa Da Tsaki Kan Harkar Fim. Daga MUKHTAR YAKUBU Kungiyar Kwararru...
02/06/2022

Kungiyar MOPPAN Reshen Jihar Kano Ta Kira Taron Masu Ruwa Da Tsaki Kan Harkar Fim.

Daga MUKHTAR YAKUBU

Kungiyar Kwararru ta masu shirya fim ta ƙasa wato Motion Picture Practitioners Associations of Nigeria (MOPPAN) reshen jihar Kano ta gudanar da wani zama na musamman da dukkanin ɓangarori na masu gudanar da sana'o'in su a cikin masana'antar Kannywwod da suke ƙarƙashin ta da kuma waɗanda suke da alaƙar tafiyar da harkar su tare.

Taron wanda sabon shugaban kungiyar na jihar Kano Ado Ahmad Gidan Dabino MON ya kira a ranar asabar ɗin da ta gabata kuma aka gudanar da shi a wajen taro na Ali Jita Event Center an tattauna a kan matsalolin da suke damun harkar fim da kuma hanyoyin da za a bullo domin warware su.

Sannan a zaman an yi magana a kan gudanar da zaɓuka a kungiyoyin da su ke ƙarƙashin MOPPAN ɗin k**ar daraktoci Masu ɗaukar Hoto (Camara Man) Furodusa jarumai da sauran su.

Tun dai rantsar da sabon shugaban kungiyar Ado Ahmad Gidan Dabino MON ya sha alwashin farfaɗo da darajar harkar fim da masu gudanar da ita, da kuma samar da hanyoyin da za su kawo ci gaba a kungiyar.

Taron dai shi ne na farko da aka yi shi wanda ya samu Halartar mutane masu yawa, wanda Hakan ya nuna masu harkar fim din sun amince da sabon jagorancin na Ado Ahmad Gidan Dabino MON, musamman dai ganin sa a matsayin tsohuwar zuma a cikin masana'antar Kannywwod tun lokacin samar da ita.

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban jam'iyyar PDP na jihar Kano, Shehu Wada Sagagi ya roki gwamnan jihar Rivers, Nyason Wike da ya ta...
18/04/2022

DA ƊUMI-ƊUMI: Shugaban jam'iyyar PDP na jihar Kano, Shehu Wada Sagagi ya roki gwamnan jihar Rivers, Nyason Wike da ya taimaka wajen ganin an Sako Inusa Yellow ko kuma ya taimaka wajen ganin anyi masa adalci.

Wike yace a tura masa bayanan shari'ar gaba daya domin ganin abinda zaiyi.

Gwamna Wike dai ya kawo ziyara jihar Kano ofishin jam'iyyar PDP domin jaddada aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa.

Address

Layout
Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Moppan dakin kara posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Moppan dakin kara:

Share