06/11/2022
Assalaamu alaikum wa rahmatullahi wa barakaatuh.
Manzon Allah ya tabbatar mana da cewa duk macen da take bayyanar da jikinta ga jama'a tsinanniya ce a gurin Allah da mala'ikunsa, kuma ya umarcemu da mu tsine mata.
Don haka ba bu sauran wani "ka rubuta sunan Manzon Allah guda d'aya", KO "ka rubuta (S.A.W)" domin kuwa ba zai amfane ne ki da komi ba.
Kin za6i ki zama tsinanniya a gurin Allah kuma za ki zo kina ba bayin Allah masoya annabi umarni? Wannan wace irin rayuwa ce?
To Bari ki ji.
Za ki iya Tara
1 000 000 000 000 comments, amma kuma su zame maki silar Shiga jahannama.
'Yar'uwa, ki gaggauta tuba ki gyara d'abi'unki tun kafin lokaci ya kure maki.
Babu wani mutumin kirki da za ki burge da wannan d'abi'ar ta nuna ma duniya kanki tsirara (ba hijabi), idan baki tuba ba kuma a 'karshen am'amari sai dai wani tsinannen zai aureki, kinga sai tsinancewar taku tayi ta kara shahara.
1. Allah bai halicci mace don ta rinka nuna ma duniya jikinta ba.
2. Allah bai halicci mace don ta nemi shahara ko 'Daukaka ba.
3. Allah bai halicci mace don ta sa6a ma umarninsa da na manzonsa ba.
4. Manzon Allah ya tabbatar mana da cewa dukkan jikin mace al'aura ne ciki kuma har da muryarta. Kuma bai halarta mace ta nuna jikanta ga kowa ba sai muharramanta KO mijinta.
Ke duk mutanen Facebook muharraman ki ne?
Da yawan Matan wannan zamanin ba su ko k**a hanyar shiga Aljanna ba.
@ ya haliccemu ne don mu bauta mashi@@
Allah ya shiryar da mu.