Katsina Daily News

Katsina Daily News Domin samun labarai masu inganci kan lokaci 07068099976
(1)

Labari da duminsa; Yan bindiga karkashin jagorancin Jelani dake yankin Farin Dutse kan hanyar Maigora zuwa Faskari, suma...
17/09/2025

Labari da duminsa; Yan bindiga karkashin jagorancin Jelani dake yankin Farin Dutse kan hanyar Maigora zuwa Faskari, suma sun sako karin wasu mata uku yan garin Kadisau da s**a yi garkuwa da su a kwanakin baya

Cikakken labari mai hade da bidiyo na nan tafe

Labari da duminsa; Sakamakon sasancin da ƙaramar hukumar Faskari ta yi da yan bindiga, yanzun haka sun fara sako mutum 2...
17/09/2025

Labari da duminsa; Sakamakon sasancin da ƙaramar hukumar Faskari ta yi da yan bindiga, yanzun haka sun fara sako mutum 28 da s**a yi garkuwa da su ba tare da an biya ko sisin kwabo ba

Jagoran yan bindiga Isya Akwashi Garwa shi ne ya mika wa karamar hukumar su yanzun haka

Waɗanda yan bindigar s**a saka mafi akasarinsu sun fito daga Mairua da Kanen-haki da yar Dabaru

Sauran labari cikin bidiyo na nan tafe

Gwamnatin Tarayya ta fara aikin  samar da wutar lantarki daga hasken rana a  Asibitin Koyarwa na Aminu Kano.Shugaban Huk...
17/09/2025

Gwamnatin Tarayya ta fara aikin samar da wutar lantarki daga hasken rana a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano.

Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Makamashi ta Ƙasa (ECN) Dr Mustapha Abdullahi ya ce wutar lantarkin mai ƙarfin Megawatt huɗu (4MW) za ta bai asibitin damar rabuwa da layin wutar lantarki na ƙasa baki ɗaya.

Dr Mustapha Abdullahi, ya ce aikin na daga cikin manufofin Renewed Hope Agenda na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.

Ya bayyana cewa wannan tsari zai kawo ƙarshen matsalar yawan yanke wuta a asibitin, lamarin da a baya ya haddasa asarar rayukan marasa lafiya guda uku a lokacin da ayyukan asibitin s**a tsaya cak.

“Da wannan tsari, ba za a sake samun irin waɗannan matsaloli ba. Burinmu shi ne mu samar da makamashi mai tsafta da nagarta wanda zai ƙarfafa cibiyoyin kiwon lafiya tare da inganta rayuwar ’yan Najeriya,” in ji shi.

Da duminsa; NECO ta saki sakamakon jarabawar sakandare na 2025Yayin da ɗalibai 818, 492 daidai da kaso 60.26 cikin ɗari ...
17/09/2025

Da duminsa; NECO ta saki sakamakon jarabawar sakandare na 2025

Yayin da ɗalibai 818, 492 daidai da kaso 60.26 cikin ɗari ne s**a sami aƙalla kiredit 5 gami da Turanci da Lissafi

Jama'a Sun Cika Tare Da Jera Layi A Gidan Kadiriyya Dake Kano Domin Karbar Ruwan Da Aka Tsòma Gashìn Mañzòn Allah SAW Da...
17/09/2025

Jama'a Sun Cika Tare Da Jera Layi A Gidan Kadiriyya Dake Kano Domin Karbar Ruwan Da Aka Tsòma Gashìn Mañzòn Allah SAW Da Babban Shehin Kadiriyya Ya Ayyana Mallakarsa

Dan gwagwarmaya Alh  Ismai'la Bangori Bako ya shawarci shuwagabannin ƙananan hukumomin jihar Katsina da su yi adalci, su...
17/09/2025

Dan gwagwarmaya Alh Ismai'la Bangori Bako ya shawarci shuwagabannin ƙananan hukumomin jihar Katsina da su yi adalci, su zabo jajirtattun mutanen da s**a wahala a baya, domin daukar su a matsayin sabbin S-A 50 da Dikko Radda ya bada umarnin kowace ƙaramar hukuma ta ɗauka

Matashi ɗan gwagwarmaya Alh Samaila Bangori Bako, ya shawarci shuwagabannin kananan hukumomin jihar Katsina su 34, da su yi duba kana da nazari wajen zabo jajirtattun matasa, wadanda s**a wahala wa jam'iyya, kuma suke bada goyon baya wajen tallata tare da yada manufofin gwamna Dikko Radda, domin nada su mukaman masu taima masu da gwamna ya bada umarni.

Wasu rahotanni dai tuni s**a karaɗe kafafen sadarwar zamani, inda ake yada cewa gwamna Dikko Radda ya ba dukkanin shuwagabannin kananan hukumomin jihar Katsina umurnin su dauki sabbin masu taimaka masu kwara hamsin-hamsin tare da rika biyan su albashin naira dubu hamsin-hamsin kowannensu duk watan duniya

Sauki ya kusa samuwa Motocin tanka na dakon mai mallakin kamfanin Dangote, sun fara dakon mai kyauta zuwa ko'ina a fadin...
17/09/2025

Sauki ya kusa samuwa

Motocin tanka na dakon mai mallakin kamfanin Dangote, sun fara dakon mai kyauta zuwa ko'ina a fadin kasar nan

Idan har Tinubu bai gyara ba, a 2027 ba zan zabe shi ba, sai dai a kore ni a APC - Kalou Dan Batsari ya ɗau zafiDaga Kal...
17/09/2025

Idan har Tinubu bai gyara ba, a 2027 ba zan zabe shi ba, sai dai a kore ni a APC - Kalou Dan Batsari ya ɗau zafi

Daga Kalou ɗan Batsari.

Jama’a ku zama shaida na rantsi da girman Allah idan shugaban ƙasa bai gyara wasu kura-kurai ba, to bazan zaɓe shi a zaɓen 2027 ba sai dai a koreni daga APC ko kuma inyi shinkafa da taliya!

Jama’a inason ku gane cewa lokaci ya yi daya kamata mu riƙa tsayawa muna lissafa irin yadda yan siyasar da muka zaɓa suke jagorantarmu bayan mun zaɓesu, domin hakan ya zama wani ma’auni da zamu yanke masu hukunci a zaɓen gaba.

Domin Allah na tsaya na lissafa na kuma gano cewa duk wani shugaba ko wakilin da na zaɓa, amman ya gaza akan abubuwa kaso 70 a cikin 100 na abinda nike tsammani daga gareshi ya yi, to wallahi bazan sake zaɓen shi ba!

Ko’a cikimmu akwai kujerun da bazan sake zaɓen su ba koda ace sunci zaɓen cikin gida wato na fidda gwani kenan, saboda irin yadda s**a kasa tare da gazawa wajan kyautata ma Al, ummar da s**a sha wahala s**a zaɓe su, shi yasa mukeson a bari ayi zaɓen fitar da gwani tunda siyasar dimukuraɗiyya ce muke yi ba ɗoki ɗora ba.

A yanzu tsawan shekara biyu kenan cif, akwai abubuwa da yawa da zan iya lissafowa wanda gwamnatin tarayya ta ƙirƙiro wanda kai tsaye a wurina domin Allah ya cutar dani a matsayina na ɗan ƙasa! wanda kuma in aka kwatanta da wanda kuma tayi ya taimaki rayuwata to baikai wanda na sha wahala ba. Misali:

1. Cire tallafin mai
2. Cire tallafin wuta
3. Tsadar data
4. Saka haraji a bankuna da sauransu barkatai.

Haka zalika akwai abubuwan da ake ɗaukewa daga arewa a mayar dasu kudu wanda babu wani dalili mai ƙarfi nayin hakan da ya gamsar dani . Ina son musani cewa lokacin yin wata siyasa ta gaba ɗaya saboda aƙidar party koda mutum baiyi abinda ya kamata ba, to domin Allah ya wuce.

Abinda nike tsammani shine duk garin da aka samu attack na yan bindiga da yayi sanadiyyar kashe aƙalla mutum 5! to ya kamata ace shugaban ƙasa ya zo wannan garin domin jajanta ma Al,ummar wannan yankin ko kuma ya naɗo kwamiti daga fadar shi domin jajantama al,ummar wannan yankin tunda suma sun zaɓe shi, kai koda ma basu zaɓe shi ba tunda suma yan ƙasa ne, inkau har bai iya zuwa to suma sai inga bai kamata su zaɓe shi ba.

Tabbas kamar yadda nasha faɗa a baya mai girma gwamnan jihar katsina malam Dikko umar Raɗɗa ya zuwa yanzu ya cimma abubuwa da yawa a nan jihar waɗanda sun taimaki Al,ummar jihar katsina ƙwarai da gaske, to amman gaskiyar magana muna muƙatar buƙatar kulawa ta musamman daga gwamnatin tarayya akan abubuwa da yawa a katsina da ma arewa baki ɗaya bawai iya katsina kaɗai ba, duba da irin wahalar da mutanammu suke sha! Ko yanzu a cikin damanar nan kazo ƙaramar Hukumata ta Batsari kaga irin yadda magidanta ke kwana waje dasu da iyalansu sakamakon rushewar gidajen su da ruwa yayi kuma basu da kuɗin gyara shi, amman sai zaɓe ya zo kuma ace kowa ya ɗauko katin zaɓen shi! 😭

Amman ayi mugani in tusa na hura wuta.

Abin a jinjinaMatashin Dan Siyasa Kuma Mai Gidauniyar Taimakon Al'umma Ta Guga Global Foundation Ya Biya Kudin Gyaran Wu...
17/09/2025

Abin a jinjina

Matashin Dan Siyasa Kuma Mai Gidauniyar Taimakon Al'umma Ta Guga Global Foundation Ya Biya Kudin Gyaran Wutar Nepa Ta Tsiga District Wacce Ta Hade Da Ward Din Tsiga, Barde Da Wutar Dawan Musa Wacce Tayi Watanni A Lalace.

Amb Abduljabbar Surajo Guga Sarkin Hanyar Katsina kuma Garkuwan Matasan Hausa ya biya kudin gyara wutar Nepa da ta lalace tsawon watanni a garuruwan Tsiga , Barde, Dawan musa da kewaye , inda jim kadan bayan yaji matsalar ya tura state coordinator dinsa Mal. Isiya Mai Tabarmi garin Tsiga aka biya kudin gyaran.

A madadin Al'ummar Tsiga Barde Dawan musa da kewaye dani Jagoran matasa Dubu Yen Bakori da Danja muna Maka godiya tare da Addu'ar Allah ya saka maka da Alkairi kuma Allah ya ida Nufi Amin.

Signed by: Tsiga Faisal
DG 1000 YOUTHS FOR ABDULJABBAR GUGA MOVEMENT.

Hadisinmu Na Yau Laraba 24 Rabi'ul Awwal 1447 (17 September 2025)Annabi SAW ya ce: Ku nemi tsarin Allah daga wahalhalun ...
17/09/2025

Hadisinmu Na Yau Laraba 24 Rabi'ul Awwal 1447 (17 September 2025)

Annabi SAW ya ce: Ku nemi tsarin Allah daga wahalhalun matsananciyar annoba, daga mummunan ƙarshe da mummunar ƙaddara

Narrated by Abu Huraira RA:

The Prophet PBUH said; "Take refuge with Allah from the difficulties of severe calamities, from having an evil end and a bad fate."

Sahih Al-Bukhari.

Da duminsa; Shugaban kasa Tinubu ya dawo Nijeriya cikin daran nan, bayan ya katse hutunsa a kasashen Turai don ci gaba d...
16/09/2025

Da duminsa; Shugaban kasa Tinubu ya dawo Nijeriya cikin daran nan, bayan ya katse hutunsa a kasashen Turai don ci gaba da yi wa Nijeriya hidima

"Ya zama tilas duk limamin da zai yi huɗuba ranar Juma'a ya kawo mana takardar mu tantance" - Inji Gwamnan Naija BagoMi ...
16/09/2025

"Ya zama tilas duk limamin da zai yi huɗuba ranar Juma'a ya kawo mana takardar mu tantance" - Inji Gwamnan Naija Bago

Mi za ku ce a kan haka?

Address

Nagogo Road Kofar Durbi Katsina
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Daily News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katsina Daily News:

Share