Katsina Daily News

Katsina Daily News Domin samun labarai masu inganci kan lokaci 07068099976

Hadisinmu Na Yau Jumu'ah 30 Muharram 1447 (25 July 2025)Manzon Allah SAW ya ce; Na rantse da wanda rayuwata ke a hannunS...
25/07/2025

Hadisinmu Na Yau Jumu'ah 30 Muharram 1447 (25 July 2025)

Manzon Allah SAW ya ce; Na rantse da wanda rayuwata ke a hannunSa, ɗayanku ba zai yi imani ba har sai ya so ni fiye da (yanda yake son) mahaifinsa da ƴaƴansa.

Narrated by Abu Huraira RA:

Allah's Messenger PBUH said, "By Him in Whose Hands my life is, none of you will have faith till he loves me more than his father and his children."

Sahih Al-Bukhari.

Ban tausai yar film din Hausa ta fashe da kuka saboda yanzun an daina sa ta cikin film don duk ta komade an gama yayinta...
24/07/2025

Ban tausai yar film din Hausa ta fashe da kuka saboda yanzun an daina sa ta cikin film don duk ta komade an gama yayinta, bayan a baya tana cikin yan mata masu bala'in kyau a masana'antar Kannywood

A Shekarun Baya Na Yi Tashen Da Babu Irin Abinda Ban Mallaka Ba A Masana'antar Fim, Amma Yanzu Har Gudun Saka Ni A Fim Ake Yi Saboda Ana Kallo Na Da Kuskuren Da Na Yi A Baya, Cewar Ummi Nuhu

Ummi Nuhu ta kara da cewa duk da cewa tana kaunar harkar fim har yanzu, amma koda ta je neman a saka ta a fim, sai a ki saka ta, saboda ana waiwayar kuskuren da ta yi a baya.

Cikin kuka Ummi, ta ce a yanzu ba ta da wata sana'a da ta iya illa harkar fim gashi kuma an daina yi da ita, kuma tana fama da rashin lafiya wanda ya kamata a ce ana saka ta a fim domin ta kula da kanta.

Tsohuwar jarumar dai ta bayyana hakan ne a hirar ta da Hadiza Gabon a shorinta na 'Gabon Talk Shaw', kamar yadda Rariya ta nakalto.

Wani karin abin tausayi a lamarin Ummi Nuhu shine, ta ce har yanzu ba ta taba yin aure ba, duk da cewa shekarunta sun ja.

Labari mai sosai zuciyaYan bindiga sun afka garin Dandogo yankin Maigora ta karamar hukumar Faskari sun yi mummunan ta'a...
24/07/2025

Labari mai sosai zuciya

Yan bindiga sun afka garin Dandogo yankin Maigora ta karamar hukumar Faskari sun yi mummunan ta'addanci inda rahotanni s**a tabbatar sun kashe mutum biyu tare da kwasar mutane da dama

Kamar yadda Katsina Daily News ta samu lamarin ya afku da yammacin yau Alhamis, inda s**a mamaye garin da manyan makamai, cikin waɗanda yan bindigar s**a kashe har da matashin dalibi Nasir Isyaku da kuma Awal Jari

Kofarmu a buɗe take ga Kwankwaso da duk wani mai son shiga APC za mu karbe shi hannu bibbiyu - Inji sabon shugaban APC N...
24/07/2025

Kofarmu a buɗe take ga Kwankwaso da duk wani mai son shiga APC za mu karbe shi hannu bibbiyu - Inji sabon shugaban APC Nentawe Yilwatda

Shararren dan wasan rastalin Hogan ya mutu yana sa shekara 71 a dunuyaHogan ya shahara a bangaren damben turawa wato Ras...
24/07/2025

Shararren dan wasan rastalin Hogan ya mutu yana sa shekara 71 a dunuya

Hogan ya shahara a bangaren damben turawa wato Rastalin a wajen shekarar 1980 zuwa 1990

Shi ne dan wasan da duk yadda aka kusa cin sa, da abokin karawarsa ya kuskura ya bugar masa kai, to xai taso yana jijjiga har sai ya kashe wancan

Da duminsa; Gwamnatin Tinubu ta yi watsi da Arewa ta je taba ta gida bangaren kudancin Nijeriya - Inji Kwankwaso
24/07/2025

Da duminsa; Gwamnatin Tinubu ta yi watsi da Arewa ta je taba ta gida bangaren kudancin Nijeriya - Inji Kwankwaso

Cikin hotuna; Yadda Tinubu ya jagoranci rantsar da Farfesa Nentawe Yilwatda a matsayin sabon shugaban jam'iyyar APC na k...
24/07/2025

Cikin hotuna; Yadda Tinubu ya jagoranci rantsar da Farfesa Nentawe Yilwatda a matsayin sabon shugaban jam'iyyar APC na kasa baki ɗaya

Yanzun abin da ya rage ma jam'iyyar zaben sabbin shuwagabannin jam'iyyar na matakin mazabu, ƙananan hukumomi da kuma jihohin Nijeriya

Sanarwa! Sanarwa! ! Sanarwa!!! Makarantar BALM GIRLS SCIENCE AMD ISLAMIC STUDIES SECONDARY SCHOOL dake cikin garin Zango...
24/07/2025

Sanarwa! Sanarwa! ! Sanarwa!!!

Makarantar BALM GIRLS SCIENCE AMD ISLAMIC STUDIES SECONDARY SCHOOL dake cikin garin Zangon Daura

Na sanar da ɗalibai da iyayen yara cewa ta fara bayar da adimishin a waɗannan guraben

Sashen haddace Al-Qur'ani cikin shikara ɗaya (Boarding)

SS1 science tare da haddar Al-Qur'ani (Boarding)

JS1 tare da haddar Al-Qur'ani (Boarding)

Ga masu sha'awar sa ƴaƴansu wannan makarantar za su iya tuntuɓar hukumar makarantar ta wannan lambar 08036260636

BALM GIRLS SCIENCE AMD ISLAMIC STUDIES SECONDARY SCHOOL ga lada ga al'ada

Tashin hankali! Ƴan bindiga sun shiga Kyaware ta ƙaramar hukumar Sabuwa sun kashe mutum 4 tare da yin awon gaba da wasu ...
24/07/2025

Tashin hankali! Ƴan bindiga sun shiga Kyaware ta ƙaramar hukumar Sabuwa sun kashe mutum 4 tare da yin awon gaba da wasu mutum 10

A labarin da Katsina Daily News ke samu a daran jiya da misalin karfe 11:40pm na dare har zuwa 1:20am yan bindiga dauke da manyan makamai s**a afka ƙauyen Kyaware na karamar hukumar Sabuwa, inda s**a yi mummunan ta'addanci a garin

Kamar yadda wani mazaunin garin da lamarin ya rutsa da yan uwansa Nazifi Ashiru ya sheda wa Katsina Daily News ya ce daga cikin wadanda aka kashe din akwai Nazifi Mamman, da Abubakar Lamba da Ussaini Bako sai kuma Zaituna Lado

Waɗanda kuma akai garkuwa da su a yankin sun hada da
1)Abubakar Ismail
2)Aminu Abdullahi
3)Abba Salisu
4)Saminu Dan gude
5)Abdurrashid Buhari
6)Umar Ismail
7) Ibrahim Dan gude
8)Asabe Abdullahi Da goyan danta
9)Larai LADO da goyan danta
10)Bilkisu Bako

Nazifi ya roki gwamnati da ta taimaka ta kai masu jami'an tsaro a yankin sakamakon munanan hare-haren yan ta'adda da suke kai masu a yankin, ga zaman zullmi da ɗarɗar kullum

24/07/2025

Jawabin sabon shugaban jam'iyyar APC na kasa Nentawe Yilwatda bayan an rantsar da shi

Ana ci gaba da tattaki zuwa Abuja don duba lafiyar jikin gwamna Dikko Radda, yayin da a yau ma gwamna Namadi na Jigawa y...
24/07/2025

Ana ci gaba da tattaki zuwa Abuja don duba lafiyar jikin gwamna Dikko Radda, yayin da a yau ma gwamna Namadi na Jigawa ya je har gidan gwamnatin jihar Katsina dake Abuja dun yin dubiya ga Dikko Radda bisa haɗarin motar da ya yi a Katsina

A karon farko APC ta zabi Farfesan Boko a matsayin shugaban jam'iyyarta na kasa baki ɗayaMinistan jin kai farfesa Nentaw...
24/07/2025

A karon farko APC ta zabi Farfesan Boko a matsayin shugaban jam'iyyarta na kasa baki ɗaya

Ministan jin kai farfesa Nentawe Yilwatda shi Uwar jam'iyyar APC ta kasa ta zaba a matsayin sabon shugaba jam'iyyar da ya maye kujerar Ganduje

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Daily News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katsina Daily News:

Share