Katsina Daily News

Katsina Daily News Domin samun labarai masu inganci kan lokaci 07068099976
(1)

Yau Asabar ana can ana fafata zaben gwamna a jihar Anambra da jam'iyyar APGA mai zakara ke mulkiJihar mai ƙananan hukumo...
08/11/2025

Yau Asabar ana can ana fafata zaben gwamna a jihar Anambra da jam'iyyar APGA mai zakara ke mulki

Jihar mai ƙananan hukumomi 21 da rumfunan zaɓe 5,718, a yau ne ake sa ran al'ummar jihar su zabo sabon gwamna

Daga cikin manyan yan takarar kujerar gwamnan a jihar har da gwamnan jihar mai ci wato Chukwuma Soludo na jam'iyyar APGA

Ga jerin sunayen manyan wadanda ke hamayyar kujerar a yau

Chukwuma Soludo na jam'iyyar APGA

Prince Nicholas Ukachukwu na jam'iyyar APC

George Moghalu na jam'iyyar LP

Jude Ezenwafor na jam'iyyar PDP

John Nwosu na jam'iyyar ADC

A ra'ayinku wace jam'iyya kuke ganin za ta lashe wannan zaben?

Da ɗuminsa; Kungiyar Tarayyar Afirka ta gargadi Amurka kan tsoma baki cikin lamurran Najeriya tare da kira ga tattaunawa...
08/11/2025

Da ɗuminsa; Kungiyar Tarayyar Afirka ta gargadi Amurka kan tsoma baki cikin lamurran Najeriya tare da kira ga tattaunawar Diflomasiyya

Kungiyar Tarayyar Afirka (AU) ta bayyana goyon bayanta ga cikakken ikon Najeriya kan harkokinta na cikin gida tare da tabbatar da ’yancin addini da bin doka da oda a kasar.

A wata sanarwa da Hukumar Tarayyar Afirka (AUC) ta fitar, ta jaddada cewa tana da cikakken kishin kiyaye dokokin da ke cikin kundin kafa kungiyar, musamman kan batun ikon kasa, rashin katsalandan, da ’yancin addini.

Hukumar ta ce ta damu da wasu kalamai daga gwamnatin Amurka da ke zargin gwamnatin Najeriya da hannu wajen kashe mabiya addinin Kirista a kasar, da kuma barazanar kai farmakin soja kan kasar.

A cewar sanarwar, Najeriya na daga cikin mambobin AU masu muhimmanci wadanda ke taka rawar gani wajen tabbatar da zaman lafiya, yaki da ta’addanci, da hadin kai a nahiyar.

“AU tana mutunta cikakken ikon Najeriya wajen tafiyar da lamurran tsaronta, tsaron kasa, da ’yancin addini bisa tsarin kundin mulki da ka’idojin kasa da kasa,” in ji sanarwar.

Hukumar ta ce ta amince da matsayar da gwamnatin Najeriya ta sha nanatawa cewa kundin tsarin mulkin kasar yana baiwa kowane dan kasa ’yancin yin addinin da yake so, kuma gwamnati ba ta amince da wani nau’in wariya ko zaluncin addini ba.

Ta kuma jaddada cewa matsalolin tsaro da Najeriya ke fuskanta na da sarkakiya, suna shafar mabiya addinai daban-daban, ciki har da matsalar ta’addanci, satar mutane, rikicin kabilanci da rikicin makiyaya da manoma.

Hukumar ta yi kira da a kara hadin kai tsakanin kasashen yankin da abokan hulɗa na kasa da kasa domin taimakawa Najeriya da sauran kasashen Afirka wajen karfafa matakan tsaro, kare rayuka, da gurfanar da masu aikata laifuka.

“Ya zama wajibi a guji amfani da addini a matsayin makami na siyasa ko bayanin da zai iya haifar da rikici,” in ji AUC.

Hukumar ta kuma bukaci kasashen waje, musamman Amurka, da su ci gaba da tattaunawa da Najeriya ta hanyar diflomasiyya, musayar bayanan tsaro, da taimakon ci gaban ƙwarewa maimakon barazanar kai farmaki, wanda ka iya barazana ga zaman lafiyar nahiyar.

A karshe, Hukumar Tarayyar Afirka ta tabbatar da aniyarta ta ci gaba da tallafawa kasashen mambobinta wajen tabbatar da zaman lafiya, kare hakkin dan Adam, da cigaban tattalin arziki, tare da mutunta ikon kowace kasa da ka’idar rashin tsoma baki.

Ina yan Karaduwa? Shin za ku iya kara ara wa Sanata Muntari Dandutse dama, ya zarce karo na biyu a zaben 2027 da ruwan ƙ...
08/11/2025

Ina yan Karaduwa? Shin za ku iya kara ara wa Sanata Muntari Dandutse dama, ya zarce karo na biyu a zaben 2027 da ruwan ƙuru'unku?

Ku bayya mana amsarku, ta hanyar rubuta E idan kun gamsu, in kuma ba ku gamsu da ya zarce ba sai ku rubuta A'A a cikin comment 👇

Hadisinmu Na Yau Asabar 17 Jumada Awwal 1447 (08 November 2025)Manzon Allah SAW ya ce; Babu wata kasawa, ko cuta, ko tak...
08/11/2025

Hadisinmu Na Yau Asabar 17 Jumada Awwal 1447 (08 November 2025)

Manzon Allah SAW ya ce; Babu wata kasawa, ko cuta, ko takaici, ko baƙin ciki, ko wata damuwa, ko wani rashin jin daɗi, da zai samu wani Musulmi, dai-dai da tsirar ƙaya, face Allah Ya share masa wasu daga cikin zunubansa.

Narrated Abu Sa'id Al-Khudri and Abu Huraira RA:

The Prophet PBUH said, "No fatigue, nor disease, nor sorrow, nor sadness, nor hurt, nor distress befalls a Muslim, even if it were the prick he receives from a thorn, but that Allah expiates some of his sins for that."

Sahih Al-Bukhari.

Ƙungiyar Miyetti Allah ta koka tare da yin Allah wadai kan hare-haren da ake kai wa Fulani a jihar Benue
07/11/2025

Ƙungiyar Miyetti Allah ta koka tare da yin Allah wadai kan hare-haren da ake kai wa Fulani a jihar Benue

Ɗaliban karamar hukumar Faskari dake karatu a Jami'ar FUDMA sun karrama shugaban lamuran ɗalibai na Jami'ar Farfesa Garz...
07/11/2025

Ɗaliban karamar hukumar Faskari dake karatu a Jami'ar FUDMA sun karrama shugaban lamuran ɗalibai na Jami'ar Farfesa Garzali Muhammad Garaba da gagarumar lambar yabo, tare da taya murnar zama Farfesa

Alhamdulillah! A yau, 7/11/2025, cikin ikon Allah, Kungiyar Daliban Karamar Hukumar Faskari* na *Federal University Dutsin-Ma (FALSA FUDMA CHAPTER), karkashin jagorancin *Cmrd. Rabiu Sani Faskari , ta kai ziyarar girmamawa ga Dean Student Affairs Prof. Garzali Muhammad Garba*, a ofishinsa domin taya shi murna bisa samun karin matsayi zuwa
professorship

A yayin ziyarar, kungiyar ta mika masa lambar yabo a matsayin karramawa da godiya bisa gudunmawar da yake bayarwa, da goyon baya ga daliban Karamar Hukumar Faskari gaba ɗaya.

Prof. Garzali Muhammad Garba ya bayyana farin cikinsa da wannan ziyara, tare da nuna matuƙar jin daɗinsa bisa wannan karamci. Haka kuma, ya gode sosai da irin wannan karramawa daga kungiyar, ya kuma yi musu fatan alheri tare da basu shawarwari masu amfani domin ci gaban kungiyar da kuma dalibai gaba ɗaya.

Allah ya ƙara ɗaukaka kungiyar FALSA FUDMA Chapter.

Rikicin PDP na ci gaba da daukar sabon salo, yayin da bangaren Wike s**a kafa sabon kwamitin amintattu na jam'iyyar
07/11/2025

Rikicin PDP na ci gaba da daukar sabon salo, yayin da bangaren Wike s**a kafa sabon kwamitin amintattu na jam'iyyar

Yadda gwamnan Katsina ya halarci sallar Jumu'ah a yau a birnin tarayya AbujaMasallacin wane gari sallar Jumu'ah ta riske...
07/11/2025

Yadda gwamnan Katsina ya halarci sallar Jumu'ah a yau a birnin tarayya Abuja

Masallacin wane gari sallar Jumu'ah ta riske ku a yau?

Dan majalisar wakilai na Kankara/Faskari/Sabuwa ya tura tawaga zuwa Kankara don yin ta'aziyyar rashe-rasheYau 7/11/2025 ...
07/11/2025

Dan majalisar wakilai na Kankara/Faskari/Sabuwa ya tura tawaga zuwa Kankara don yin ta'aziyyar rashe-rashe

Yau 7/11/2025 Shugaban Matasan jihar katsina Alh Hamza Mamman Sheme Yawakilci Dan majalissar Tarayya Na Mazabun Kankara Faskari Sabua Rt Hon. Engr.Shehu Dalhatu Tafoki wajen Gaisuwar Mahaifin su Hamisu Domawan Pauwa Yayi Masu Gaisuwa Tare Da Adduoin Allah Yajikanshi da Rahama Tare Sauran Musulmin Duniya Yasamu Rakiyar
✅Nasiru Salisu LA To the Tafoki
✅Hon Shamsu Mola SA Youth to the Tafoki
✅Hon Aminu Sulaiman (bindinga )

SA Media
Sulaiman bature kankara

In da ran ka; Kotu Ta Ci Mage Tarar Naira Miliyan Biyu Ko Zama Gidan YariWata kotu a ƙasar Faransa ta ci wata mage mai s...
07/11/2025

In da ran ka; Kotu Ta Ci Mage Tarar Naira Miliyan Biyu Ko Zama Gidan Yari

Wata kotu a ƙasar Faransa ta ci wata mage mai suna Remi tarar fiye da naira miliyan biyu, saboda yawan kutsawa cikin gidan makwabta ba tare da izini ba.

Bayanan da aka gabatar a gaban kotu sun nuna cewa an umarci mai rikon magen da ya rika biyan kimanin ₦50,000 duk lokacin da Remi ta sake shiga gidan makwabta.

Sai dai duk da wannan hukunci, mage Remi ta ci gaba da shiga gidajen, har ta kai ga yin fitsari a cikin harabar gidan makwabta, abin da ya sake jawo mata sabuwar shari’a a gaban kotu.

Mai rikon Remi ta bayyana cewa ta shiga cikin halin ruɗani sakamakon wannan matsala, tana mai cewa ba ta san matakin da za ta ɗauka ba yayin da suke shirin sake gurfana a gaban kotu a ranar 9 ga watan Disamba, bisa zargin mage mai karya doka.

Rahotanni sun ce tuni aka sake gurfanar da Remi, bayan ta sake karya umarnin kotu duk da hukuncin da aka yanke a baya.

Mai rikon magen ta kara da cewa: “Na rasa inda zan sa kaina a yanzu. Ba na son a ci gaba da hukunta ni saboda halayyar dabbar da ba zan iya sarrafawa gaba ɗaya ba.”

Lamarin ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta a Faransa, inda wasu ke ganin hukuncin abin dariya ne, yayin da wasu ke cewa yana nuna yadda tsarin doka ke kare haƙƙin mallaka da zaman lafiya tsakanin maƙwabta, ko da kuwa abin ya shafi dabba ce.

Yan Arewa ku yi murna; A yau Jumu'ah shugaban kasa Tinubu ya gana da mai alfarma sarkin Musulmi Sa'ad Abubakar a Fadar s...
07/11/2025

Yan Arewa ku yi murna; A yau Jumu'ah shugaban kasa Tinubu ya gana da mai alfarma sarkin Musulmi Sa'ad Abubakar a Fadar shugaban kasa dake A*o Rock Abuja

HON. SURAJO ABDU KWASKWARO YA YI BABBAN KAMU!Daga, Sulaiman Aliyu JifatuA yau siyasar Ba’awa ward ta ɗauki sabon salo,  ...
07/11/2025

HON. SURAJO ABDU KWASKWARO YA YI BABBAN KAMU!

Daga, Sulaiman Aliyu Jifatu

A yau siyasar Ba’awa ward ta ɗauki sabon salo, Dan gwagwarmayar da yake ƙokarin kafa jam'iyyar ADC a Ba’awa Ward, Aliyu Ibn Salmanu Jifatu, ya bayyana ficewarsa daga ADC zuwa APC — a karkashin jagorancin mai girma Hon. Surajo Abdu Kwaskwaro.

Aliyu Jifatu, wanda aka dade ana yi wa kallon daya daga cikin jajirtaccen Ɗan gwagwarmaya a yankin, ya bayyana cewa halayen shugabanci, gaskiya, da jajircewar irin na Hon. Surajo Abdu Kwaskwaro ne s**a ja hankalinsa, s**a kuma sa ya ajiye muƙaminsa domin ya bi tafiyar APC “da zuciya ɗaya”.

Jifatu ya kara da cewa sauya shekar da ya yi ba kuskure ba ne, domin ya kuduri aniyar tsayawa tsayin daka wajen ganin Hon. Surajo ya samu nasarar zarcewa zuwa 2027 tare da goyon bayan manyan jiga-jigan yankin kamar Khairu Salisu Jifatu da kuma musbahu Mustapha jifatu, sun samu jagorancin Nuruddeen adawa na buhari

🔥 Ba shi kaɗai ba!
Bayan sanarwarsa, mutane fiye da goma sun bi sahunsa zuwa APC — ciki har da Youth Leader Ashiru Buhari jifatu da sauran mutane, wadanda s**a yi alkawarin mara baya ga burin da APC ke ginawa a Ba’awa Ward.

A halin yanzu dai, Hon. Surajo Abdu Kwaskwaro ya karɓi su hannu bibbiyu, tare da bayyana cewa kofa a bude take ga duk wanda ke son sauyi na gaskiya a yankin Ba’awa.

Address

Nagogo Road Kofar Durbi Katsina
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Daily News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katsina Daily News:

Share