Eagle Eye Hausa News

Eagle Eye Hausa News Labarai da dumi dumin su musanman na siyasa

Al'ummar yankin Binoni suna cikin wani hali na rashin kyakykyawar Hanya!!!...Inji wani Dan kishin kasa Comrd Adam Hashim...
27/08/2022

Al'ummar yankin Binoni suna cikin wani hali na rashin kyakykyawar Hanya!!!...

Inji wani Dan kishin kasa Comrd Adam Hashim Binoni

Duba da irin zunzurutun kudi da al'ummar garin Binoni muka sakawa Kungiyar IFAD CASP a karkashin jagorancin CDA/FSA na garin domin samun kashi tara(9) nayin wannan hanyar, cikin ikon Allah hakar mu ta cimma ruwa inda muka gina Kwalbatai biyu na shiga garin Binoni a kan kudi Naira Miliyan Ukku daidai.

Bisa Jarabawa ta ubangiji, a daminar farko tayin wannan aikin ruwa ya zaizayi kwalbati daya, daya kuwa ya janyeta baki daya.

Hakika mutanen Binoni, mutane ne masu kokari wajen yin aikin gayya da hadin kai domin ganin garin yaci gaba da alummar yakin baki daya, dukda duba da cewa a wannan aikin abin ya rigaya yapi karfin mu, sak**akon Hausawa kance "Hannu baya daukar Jikka shi kadai"!.

Munyi karaye-kiraye a gwabnati a wannan lokacin domin ta saka hannu ganin cewa an tallafa mana tun kafin haka ta afku, amma ba amo ba kida ko wani labari mai dadi akan aikin wannan hanyar.

Zaman da ake yanzu haka ko babur baya shiga garin saida 'yan dubaru, uwa uba Motar ita bama a maganarta.

Da wannan ne muke kara kira ga gwabnati ta taimaka ta duba koken domin ceto rayuwar mu dama sauran al'ummar yankin baki daya. 🙏

Rubutawa ; Adam Hashim Binoni.

GOMBE TA TABBATAR DA BULLUWAR CUTAR ƘYANDAR BIRI DAKUMA WASU SASSA DAKE MAKOTAKA DA GOMBEn
03/08/2022

GOMBE TA TABBATAR DA BULLUWAR CUTAR ƘYANDAR BIRI DAKUMA WASU SASSA DAKE MAKOTAKA DA GOMBEn

"... MATSALAR TSARO TASA AN SAKE KAKABA DOKAR HAWAN BABUR A KATSINA..."An Sake Dawo Da Dokar Hana Hawa Babura a Jihar Ka...
01/08/2022

"... MATSALAR TSARO TASA AN SAKE KAKABA DOKAR HAWAN BABUR A KATSINA..."
An Sake Dawo Da Dokar Hana Hawa Babura a Jihar Katsina.....

Biyo bayan Ɗage dokar hana hawa babura da Rundunar Ƴansandan Jihar Katsina tayi domin sauƙaƙa wa jama'a zirga zirga loluttan Azumin da aka gabatar na wannan Shekarar, dokar ta sake dawowa.

Rundunar Ƴansandan Jihar Katsina na Jawo hankali Jama'a cewa yanzu dai an sake dawo da dokar hana hawa babura daga ƙarfe Goma na Dare zuwa ƙarfe Shidda na Safiya 10:00 - 6:00 a ƙwaryar cikin garin Katsina yayinda kuma dokar take fara aiki daga ƙarfe Takwas na Dare zuwa ƙarfe Shidda na Safiya 8:00 - 6:00 a yankunan ƙananan Hukumomin da Matsalolin rashin tsaro s**afi ƙamari.

Dawo da wannan dokar yazama wajibi ne saboda ƙaruwar matsalar rashin tsaro da take faruwa dalilin Ƴan Ta'ada dama wasu masu aikata munana laifuka da suke amfani da babura wajen aiwatar da ta'adancin su.

Wannan Sanarwa tafito ne daga Jami'an hudɗa da jama'a na Rundunar Ƴansandan Jihar Katsina SP Isah Gambo muna fatan Allah ya kawo mana ƙarshen wannan Ibtila'in ya zaunar damu lafiya Amin.

Da Duminsa: Gwamnan Masari ya bayar da hutun sabuwar shekarar musulmiGwamna Masari na jihar Katsina ya aminta da gobe Li...
31/07/2022

Da Duminsa: Gwamnan Masari ya bayar da hutun sabuwar shekarar musulmi

Gwamna Masari na jihar Katsina ya aminta da gobe Litinin 1 ga watan August 2022 ta zama ranar hutu ga dukkanin ma'aikatan jihar, don girmama sabuwar shekarar Musulunci ta 1444

Jawabin hakan na kunshe a sanarwar da Kwamishinan yada labarai na jihar Katsina Sirika ya fitar, k**ar yadda Katsina Media Post News ta samu

Da marecen yau Lahadin nan 31/07/2022 aka tsinci gawar wani bawan Allah a rataye a  garin Jibiya.
31/07/2022

Da marecen yau Lahadin nan 31/07/2022 aka tsinci gawar wani bawan Allah a rataye a garin Jibiya.

"... Nifa dama ban takurawa kowa saiya zabeni ba.." inji Muhammad BuhariShugaban kasar Nigeriya Muhammadu Buhari yace sh...
31/07/2022

"... Nifa dama ban takurawa kowa saiya zabeni ba.." inji Muhammad Buhari

Shugaban kasar Nigeriya Muhammadu Buhari yace shifa bai takurawa kowa ba akan ya zabeshi, yayi maganar ne a yayin da babban zaben 2023 ke karasowa.

Yace jama'ar su zabi ra'ayin su shi baya takurawa kowa a zabi wane saboda shima bai takurawa kowa sai ya zabe shiba

A yayin da jama'ar gabacin Katsina ke ta dauki ba dadi har na tsawon kwana goma babu ruwan sama, a shukokin su, ruwan da...
31/07/2022

A yayin da jama'ar gabacin Katsina ke ta dauki ba dadi har na tsawon kwana goma babu ruwan sama, a shukokin su, ruwan da aka kwana yi jiya ya nemi ya fara yin banna.

Ruwan dai yana bine a wata magunawar ruwa da aka fara ba'a ida ba da ke a chan baranda a cikin garin Muduru, majiyar mu ta tabbatar mana da cewa aikin ne ake cikin yi amma an daina saboda damina wanda kuma hakan babbar barazana ce ga jama'ar wannan yankin.

Tuni dai jama'ar garin s**a fara fadi tashin ganin yadda za'a shawo kan matsalar dun dawuri, ta wani ɓangare kuma sunyi kira ga mahukunta musamman masu alhakin idasa aikin dasu dubesu da idanun tausayi suzo su idasa aiki.

Gwamnan Borno, Farfesa Babagana Umaru Zulum, ya jagoranci raba tsabar kuɗi N172 miliyan ga talakawa masu ƙaramin karfi 3...
26/07/2022

Gwamnan Borno, Farfesa Babagana Umaru Zulum, ya jagoranci raba tsabar kuɗi N172 miliyan ga talakawa masu ƙaramin karfi 30,436 da kuma wasu magidanta da ibtila'in ambaliyar ruwa ya shafe su a yankin karamar hukumar Danboa, kudancin Borno.

Mazauna 30,000, mafi yawa mata da zawarawa, sun samu tallafin N5,000 da tufafi, sauran Magidanta 436 da ibtila'in Ambaliya ta shafa sun samu kuɗi N50,000, kayan abinci da sauran su.

Hotuna: Prof. Babagana Zulum

MAKOMAR JAMAA TA SHINE KE TUNZURA NI AKAN GAYAWA MUTANE MUHIMMANCIN ZAƁAR   INJI Abubakar AbzubrJAMAAR MU MUKE SANYAWA F...
26/07/2022

MAKOMAR JAMAA TA SHINE KE TUNZURA NI AKAN GAYAWA MUTANE MUHIMMANCIN ZAƁAR INJI Abubakar Abzubr

JAMAAR MU MUKE SANYAWA FARKO A CIKIN HIDIMAR SIYASA DOMIN A DUNIYA AKE BIYANTA...

Yakai dan uwa k fahimci wani abu Na zabi nabi dallatun mani ne ba saboda zato ba domin k**ar yadda n fada a baya matukar ka taba samun wata dama to mukan sanya ta a mizani ne mu auna ka.... Bama da lokacin da zamuyi maka uzuri domin munyi wa wasu jiya da shekaran jiya bamuji da daɗi ba.

Jama'a ta da kuma mutuncin su a idon wakilin su, na daya daga cikin dalilan dake ta tunzura Ni dakuma nusar dasu irin garabasar dake a cikin zabar dallatu dakuma masu k**a masa, a matsayin jagororin mu....

Idan bukatar kai da kai ne babu abinda na rasa a abokan takarar sa, amma meye makomar jama'a ta bayan samun nasara. Kamar yadda nace idan ana maganar personal per**bo**n to kowacce gwamnati bata bukatar sauyi domin dolenta tayiwa na kusa da ita. wanda su kadai kuma basu isa su zamo Alkalai ba.... Jama'ar da ake wakilai ina magana akan game garin jama'a wani mizani s**a ajiye kamun ludanyin gudanarwar Wakilinsu?

Saboda haka da wannan nake kira da babbar murya cewa muyi amfani da hankalin mu dakuma basirar da Allah yayi mana gami da ADUA muzo mu zabi ALIYU HARUNA JANI domin shiga daga cikin jerin wadanda ake kafa Misali da constituent dinsu..
...Dallatu and only in MANI/BINDAWA

✍️✍️ Abubakar Abzubr
07030504515

Gwamnan Kaduna Nasir El-Rufa'i, takwararsa na Jihar Zamfara, Bello Matawalle da Simon Lalong na Jihar Plateau da tsohon ...
26/07/2022

Gwamnan Kaduna Nasir El-Rufa'i, takwararsa na Jihar Zamfara, Bello Matawalle da Simon Lalong na Jihar Plateau da tsohon shugaban APC na kasa, Adams Oshiomhole da Omisore sun ziyarci Kashim Shettima, abokin takarar Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.

Abubakar Abzubr

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Eagle Eye Hausa News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share