Alktv post

Alktv  post Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Alktv post, Media/News Company, Katsina.

'YAN NAJERIYA 10 DA SUKAFI KOWA WAUTA:1. Dalibin da yake zaune a gida saboda yajin aiki, amma ba ya da katin zaben da za...
05/07/2022

'YAN NAJERIYA 10 DA SUKAFI KOWA WAUTA:

1. Dalibin da yake zaune a gida saboda yajin aiki, amma ba ya da katin zaben da zai canja shugabannin da s**a jefa shi cikin wannan hali.

2. Dalibin da ya gama karatu, yana zaune gida shekara da shekaru babu aikin yi, kuma ya kasa mallakar katin zabe.

3. Talakan da ke kuka da tsadar rayuwa, kuma ya kasa zuwa ya mallaki katin zabe.

4. Ma'aikacin da ya yi shekara da shekaru babu karin albashi, kuma ya kasa mallakar katin zabe.

5. Dan kasuwar da kasuwancinsa ya tabarbare sak**akon hauhawar farashi da rashin ciniki, ya kuma kasa mallakar katin zaben.

6. Manomin da 'yan bindiga s**a hana noma, kuma ya kasa mallakar katin zaben da zai canja shugabannin da s**a kasa ba shi tsaro.

7. Mutumin karkara da 'yan bindiga s**a hana zama gida, kuma ba ya da katin zabe.

8. Mutumin birni da yake fama da matsalar ruwa da wuta, amma ba ya da katin zabe.

9. Macen da ta rasa mijinta ko danginta saboda rashin tsaro, amma ta kasa mallakar katin zabe.

10. Wawan wawaye shi ne wanda ya mallaki katin zabe amma ya ki fita ya yi zabe, wai ko ya jefa kuri'a ba ta da amfani.

Jama'a mu yi kokari mu mallaki katin zabe. Katin zaben nan shi ne makamin talaka da zai yaki shugabanni 'yan jari-hujja. Yanzu haka hukumar zabe ta tsawaita lokacin karbar kati har zuwa wani lokaci.

Allah ya zaba mana shugabanni na gari.

In kunne yaji jiki yayi Arziki.

“Dan Nanaye Ya Mutu Amma Duk An Bi An Damu Sai Ka Ce Wani Mutumin Kirki Ne Ya Mutu” Ra'ayin Jamilu Al-Hassan HarunaWanna...
05/07/2022

“Dan Nanaye Ya Mutu Amma Duk An Bi An Damu Sai Ka Ce Wani Mutumin Kirki Ne Ya Mutu”

Ra'ayin Jamilu Al-Hassan Haruna

Wannan shi zai nuna maka irin yadda jahilci ya yi mana katutu. Ku da za ku yi murna ɓarnar da yake yaɗawa ta tsaya amma abun haushi har da masu addini suke yayata al'amarin mutuwarshi. Kawai kubroƙa masa gafara a can gefe tsakaninku daga ku sai Allah. Ɓarnar da yake yaɗawa ta tsaya sai mu taya juna murna”, cewarsa.

MAJIYA: Muryoyi

DA DUMI-DUMI: An Gano Naira Miliyan 414, Da S**a Salwanta A Kar Kashin Gwamnatin ZulumRahotanni daga jihar Borno na cewa...
02/07/2022

DA DUMI-DUMI: An Gano Naira Miliyan 414, Da S**a Salwanta A Kar Kashin Gwamnatin Zulum

Rahotanni daga jihar Borno na cewa miliyan 414 ta bace a gwamnatin gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum an rasa me aka yi da ita.

Kudin sun bacene a ma’aikatu 5 dake jihar ta Borno.

Jami’in gwamnatin jihar, Shettima Bukar ya bayyana cewa, an gabatar da tambayoyi kan yanda aka yi amfani da kudaden a wadannan ma’aikatu amma har yanzu ba’a amsa wadanan tambayoyi ba.

An dai kashe kudinne a shekarar 2019.

INNALILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UNFitacciyar Fuska A Manhajar Tiktok Shatu Bawa Ta Rasu, Bayan Fama Da Gajeriyar Rashin...
02/07/2022

INNALILLAHI WA INNA ILAIHIR RAJI'UN

Fitacciyar Fuska A Manhajar Tiktok Shatu Bawa Ta Rasu, Bayan Fama Da Gajeriyar Rashin Lafiya.

29/06/2022

Falalar Goman Farko Ta Zul-Hajji
An karbo Hadisi Daga ibn Abbas (R.A) ya ce
Annabi (SAW) ya ce:
Ranar daya ga watan zilhijja ita ce ranar da Allah
(swt) ya gafartawa Annabi Adam (A.S). Duk
wanda ya azimci wannan rana Allah(SWT) zai
gafarta masa kowane irin zunubi tsakaninsa da
shi.
(2) Ranar biyu ga Zulhijja ita ce ranar da Allah
(SWT) ya karbi Addu’ar Annabi Yunus (A.S) ya
fitar da shi daga cikin kifin da ya hadiye shi.
Wanda ya azimci wannan rana yana da lada
kwatankwacin wanda ya raya shekara da ibada .
(3) Ranar uku ga Zulhijja ita ce ranar da Allah
(SWT) ya karbi addu’ar Annabi Zakariyya (A.S)
ya ba shi haihuwa. Duk wanda ya azimci wannan
rana Allah (SWT) zai karbi adduo’insa.
(4) Ranar hudu ga Zulhijja ita ce ranar da aka
haifi
Annabi Isah (A.S). Duk wanda ya azimci wannan
rana Allah zai kare shi daga talauci da musibu.
(5) Ranar biyar ga Zulhijja ita ce ranar da aka
haifi
Annabi Musa (A.S). Duk Wanda ya azimci
wannan rana Allah (SWT) zai kare shi daga
munafunci ko azabar kabari.
(6) Ranar shida ga Zilhijja ita ce ranar da Allah
(SWT) ya yi budin alkhairi ga Annabi (SAW). Duk
wanda ya azimci wannan rana Allah zai dube shi
da rahama, kuma ba zai azabtar da shi ba.
(7) Ranar bakwai ga Zulhijja ita ce ranar da Allah
(SWT) zai sa a rufe kofofin wuta, ba za a bude su
ba har sai wadannan kwanaki goma sun wuce.
Duk wanda ya azimci wannan rana Allah zai rufe
masa kofofi talatin na tsanani a rayuwarsa a
buda masa kofofi talatin na sauki.
(8) Ranar takwas ga Zilhijja ita ce ranar da ake
cewa, ranar tarayya. Duk wanda ya azimci
wannan ranar, babu wanda ya san adadinsa sai
Allah.
(9) Ranar tara ga watan Zulhijja ita ce ranar
hawan Arfa. Allah yana gafartawa duk Alhazan da
ke wurin Arfa. Wanda kuma ba ya wurin aikin
Hajji, idan ya azimci wannan ranar, Allah yana
gafarta masa zunibinsa na shekarar da ta
gabata,
da kuma shekarar da ke tafe.
(10). Ranar goma ga Zulhijja ita ce ranar layya.
Duk wanda Allah ya horewa abin da zai yi layya,
idan ya yanka dabbarsa, digon jini na f

24/06/2022

*AMINCHI COMMUNICATION*
MUNA SAYARDA DATA AKAN FARASHI ME SAUKI
*MTN*
500MB #160 (30 DAYS)
1.GB # 300
2.GB #600
3.GB #900
5.GB #1500
*AIRTEL*
500 MB #250 (30DAYS)
1.GB #400
2.GB #800
3.GB #1500
5.GB #1800
*GLO*
1.3GB (14 DAYS) #530
2.9GB (30 DAYS ) #1000
4.1GB (30 DAYS) #1500
7. GB (7 DAYS) #1550
5.8GB (30 DAYS) #2000
*9MOBILE*
500MB #550 (30 DAYS)
1.5GB #1050 (30 DAYS)
2.GB (30 DAYS)
3.GB #1500 (30 DAYS)
4.5GB 2050 (30 DAYS)
*DOMIN KARIN BAYANI*
08032723282
08027022096
09061111507
FOR TRANSFER
ACCT NO 3085485531
ACCT NAME UMAR MANSUR
BANK FIRST BANK
ACCT NO 1374395457
ACCT NAME MANSIR UMAR
BANK ACCESS BANK
*MUN GODE*

YADDA DUBUN DAN DANFARA MUSA L MAJE TA CIKA HAR AKA K**A SHI.Game da yadda aka yi nasarar cafke musa L maje Saurayi da y...
17/06/2022

YADDA DUBUN DAN DANFARA MUSA L MAJE TA CIKA HAR AKA K**A SHI.

Game da yadda aka yi nasarar cafke musa L maje Saurayi da ya shahara yana danfarar mata har ma da maza, da wani Facebook account din bogi mai suna Zahra Mansur

Wani mutum yaga guntun bidiyon wata mata a wayar Musa. Musa ya dauki bidiyon ne cikin rashin sanin matar. Bidiyon gashin kantane bata kulle ba yagani a wayan musa, amma ba wani bidiyo bane da yake bayyana tsiraici sosai, amma dai dole ta dau mataki in ta gani.

To a ranar Talata ne labarin ganin video yazo ma matar, Wani ne ya kira ta ya shaida mata cewa ya ga bidiyonta a wayar Musa, inda hankalinta ya tashi ta rasa ya zatai kuma bata so ta masa magana kai tsaye.

Sai ta nimi taimakon wani mutum ta sanar da shi ba tare da shi musa ya san cewa an gaya mata ba, sai wanda aka gaya mawa ya yanke shawarar tunkarar shi ta hanyar kai shi ga hukuma ba tare da saninsa ba, kuma bazasu bari ya saniba to amma suna bukatar dubarar yadda zasuyi masa, shi ne Muka ce wa matar ta kira shi ta gaya masa tana Kano tana son ganinsa. Daman musa nasan ganin yasake haduwa da ita, jin wannan labarin na cewa zai hadu da matan nan, har yana ce mata shifa ya kosa su hadu!

A daren Talata ne ta buga masa waya. Kuma shi wanda aka gayamawa ya taimaka mata s**a tafi Kano ranar Laraba da sassafe. Saboda muhimmancin lamarin, kuma basaso su rasa musa, basa so a samu matsala, K**a musa nada Muhimmanci sosai a wajan su, so sun isa Kano da wuri a ranar laraba.

A takaice an k**a musa tare da jami'an yan sanda da mutanan da s**aje Kano da matar da taimakon wasu mutane, musa ya gigice da ya ganshi a hannun hukuma kuma suma wa yanda s**ai rakiyar sun gigice bisa ganin yadda musa yazo hannu,

‘Yan sandan cikin ladabi da kwanciyar hankali sun tambaye shi bidiyon amma ya musanta. Ya musanta duk zargin da ake masa, yace babu wani bidiyo mai k**a da na matar a wayar shi, da yanda s**a bincika wayansa ne fa anan ne a kaga bidiyon, Nan Musa ya fara kuka yana nadama Yana neman gafarar matar.

SARAUTA-Jerin Ƴaƴan Marigayi Sarkin kano HRH Alhaji Ado Bayero Alhaji Dr.Ado Bayero1. Alhaji Sanusi Ado Bayero 2. Alhaji...
16/06/2022

SARAUTA-Jerin Ƴaƴan Marigayi Sarkin kano HRH Alhaji Ado Bayero

Alhaji Dr.Ado Bayero
1. Alhaji Sanusi Ado Bayero
2. Alhaji Aminu Ado Bayero
3. Alhaji Nasiru Ado Bayero
4. Alhaji Usman Ado Bayero
5. Alhaji Bashir Ado Bayero
6. Alhaji Mahmoud Ado Bayero
7. Alhaji Ibrahim Ado Bayero
8. Alhaji Shehu Ado Bayero
9. Alhaji Abdullahi Ado Bayero
10. Alhaji Bello Ado Bayero
11. Alhaji Ali Ado Bayero
12. Alhaji Abbas Ado Bayero
13. Alhaji Inuwa Ado Bayero
14. Alhaji Ahmad Ado Bayero
15. Alhaji Kabiru Ado Bayero
16. Alhaji Umar Ado Bayero
17. Alhaji Tijjani Ado Bayero
18. Alhaji Auwalu Ado Bayero
19. Alhaji Ado Ado Bayero
20. Alhaji Sani Ado Bayero
21. Alhaji Salisu Ado Bayero
22. Alhaji Abdullahi Ado Bayero
23. Alhaji Sadiq Ado Bayero
24. Alhaji Zubairu Ado Bayero
25. Alhaji Ismail Ado Bayero
26. Alhaji Zakari Ado Bayero
27. Alhaji Abubakar Ado Bayero
28. Rabiu Ado Bayero
29. Alhaji Yusuf Ado Bayero
30. Alhaji Mustapha Ado Bayero
31.Ahmed Ado Bayero
32.Alhaji Abdulhamid Ado Bayero
Mata:
33. Aishatu Ado Bayero
34. Hasiya Ado Bayero
35. Maryam Ado Bayero
36. Rukayyah Ado Bayero
37. Zainab Ado Bayero
38. Saratu Ado Bayero
39. Sadiya Ado Bayero
40. Khadija Ado Bayero
41. Hajara Ado Bayero
42. Nafisatu Ado Bayero
43. Aishatu Ado Bayero
44. Saudatu Ado Bayero
45. Mariya Ado Bayero
46. Ummal Kaltime Ado Bayero
47. Saude Ado Bayero
48. Amina Ado Bayero
49. Saadatu Ado Bayero
50. Aisha Ado Bayero
51. Asma’u Ado Bayero
52. Salamatu Ado Bayero
53 Hauwa Ado Bayero
54 Rabi Ado Bayero
55. Yahanasu Ado Bayero
56. Saudat Ado Bayero
57. Hafsat Ado Bayero
58. Fati Ado Bayero 57. Maimuna Ado Bayero
59. Bilkisu Ado Bayero
60. Zahra’u Ado Bayero
61. Aminatu Ado Bayero
62. Sakina Ado Bayero
63. Ummal Khair Ado Bayero.

Muna yi mishi addu'ar Allah ya jikanshi ya gafarta masa, mu kuma idan ta mu ta zo ya saka mu cika da imani.

Labari Da Dumi DuminsaAranar 11 Ga Watannan ne Wato July Za'a Zauna Zaman Mukabala Da Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara M...
16/06/2022

Labari Da Dumi Duminsa

Aranar 11 Ga Watannan ne Wato July Za'a Zauna Zaman Mukabala Da Sheikh Abduljabbar Nasiru Kabara Mai Shekaru 50 Aduniya
Wanda Ake Zargin Yayi Batanci Ga Fiyayyen Halitta Annabi Muhammad Sallallahu Alaihi Wasallama
Kuma Yace alittafan Addinin. Muslunci Yagani K**arsu
صحيح البخاري Sahihul Bkr
التاريخ مدينة دمشق
سير اعلام النبلاء
معجم الكبير
Dadai Sauransu
Iya Malalan Kano Za'a Zauna Dasu K**arsu
Dr Abdallah Gadon Kaya
Dr Musa Asadussunnah
Dadai Sauransu.
Za'ahaska Live Abbc Hausa Dadai Sauransu

16/06/2022

KISA!!!

A zamanin khalifa Umar dan Khattaab, wasu mutane uku s**a zo masa suna rike da wani saurayi s**a ce, Ya Amiral muminina! Wannan mutum ya kashe mana mahaifinmu.

Umar: kai donme ka kashe musu uba?

Saurayi: Ni makiyayi ne, rakumata ce ta ci itaciyar gonar mahaifinsu, sai mahaifinsu ya bugi rakumin da dutsi, rakuma ta mutu, ni kuma na dauki dutsin na buge shi
ya mutu.

Umar: saboda haka zan tsaida haddi akanka.

SAURAYI: ka saurara mini kwana uku, mahaifina ya mutu ya barni da kanwata da kuma dukiya, idan ka kasheni dukiyar da yar uwata zasu tozarta Kamini Uzuri naje na raba Dukiyar.

Umar: wa zai lamunceka?

Saurayi ya duba cikin mutane sai ya nuna Sahabi "Abu Dhar".

Umar: ka lamunce masa Ya Aba Dharr?

Abu Dharri: na'am

Umar: ba ka san mutum ba ka lamunce, to idan ya gudu haddi zai koma kanka.

Abu Dharr: na yarda.

Saurayi ya tafi, aka kwana biyu, an shiga na so uku, saurayi bai zo ba,

Hankalin kowa ya tashi akan Abu Dharri kar haddi ya koma kansa.

Kafin sallar magariba sai ga saurayi ya zo a gajiye, ya tsaya a gaban khalifa Umar.

Saurayi: na mika dukiyar ga kawuna yanzu ina hanunka, ka tsaida haddi
akaina.

Cikin mamaki Umar ya ce: me ya dawo da kai bayan ka sami dama da za ka
iya gudu abinka?

Saurayi: na ji tsoro, Kar a ce cika alkawari ya Kare
cikin mutane.

Umar ya juya ga Abu Dharr: me ya sa ka lamunce
masa?

Abu Dharr: na ji tsoro, kar a ce alheri ya Kare cikin
mutane.

Wannan jawabi ya yi tasiri ga masu Neman jinin ubansu, s**a ce sun yafewa
saurayi.

Umar: don me?

S**a ce: muna tsoro, kar a ce afuwa ta Kare a cikin mutane.

Ni ma na isar muku da wannan labari ne don ina tsoron kar a ce kira/tunatarwa zuwaga aikata alkhairi (wato da'awa) ya Kare cikin mutane. Don Allah kai ma ka tura kar ace yada alheri ya qare cikin mutane.

Allah Kaji Kan Malamanmu da sauran yan uwanmu das**a Rigamu Gidan Gsky

16/06/2022
16/06/2022

Muna yi ma kowa da kowa brk da zuwa wannan sabon dandali inda za mu rinka kawo muku sahihan labarai, tattaunawa akan matsalolin al ummarmu, fadakarwa, wa'azantarwa har ma da nishadantarwa Insha Allah

Address

Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Alktv post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share