Media Forum Katsina

Media Forum Katsina Media Katsina

GAGGARUMIN FARETIN GIRMAMAWA GA MANZON ALLAH (S A W) A DA'IRAR KATSINAkamar kowacce shekara ƴan'uwa Almajiran Shaikh Zak...
13/09/2025

GAGGARUMIN FARETIN GIRMAMAWA GA MANZON ALLAH (S A W) A DA'IRAR KATSINA

kamar kowacce shekara ƴan'uwa Almajiran Shaikh Zakzaky (H) na Da'irar Katsina, ƙarƙashin Lajnar Islamiyyu na shirya gaggarumin Faretin Girmamawa ga Manzon Allah (s a w), Wanda ƴan Islamiyyu ke gabatarwa.

A wannan shekarar ma a yau Asabar 13/9/2025 - 20/3/1447 an shirya wannan Faretin domin Girmamawa tare da Faranta ran Manzon Allah (s a w). A kan shirya Faretin ne tsakanin Islamiyyun dake Da'irar Katsina baki ɗaya.

Akwan Group (A&B), masu taka Faretin, wanda akan fara kiran (Group B) ne, bayan sun kammala sai (Group A), sannan a lokaci guda kuma ga Alƙalai masu kula da ƙa'idojin Faretin suna lura domin fidda Zakarun da s**a fi nuna bajintarsu.

Daga cikin Islamiyyun da suke halarta a cikin (Group B) akwai: Ɗariƙil Huda Masanawa, Shabbabul Mahdi (a t f), Dinil Islam, Ansarul Mahdi (a t f), da sauransu. Sannan daga cikin (Group A) akwai: Tahriƙil Islam, Irshadussubyan, Fudiyayya Jibia, Fudiyyah Batagarawa, Tarbiyyatul Islam, da sauransu.

Bayan kammala wannan gaggarumin Faretin sai taƙaitaccen jawabi daga wasu ba'adin mutanen da aka gayyato tare da basu shaidar girmamawa (Certificate), daga nan kuma sai Malam Shehu Ɗalhatu Ƙarƙarku ya gabatar da jawabin rufewa.

Malam yayi taƙaitaccen jawabi akan shi manufar shirya irin wannan taron domin kusanto da sauran Al'ummar da muke rayuwa cikinsu, kamar yadda su Malam Zakzaky (H) suke irshadi akai, har yana cewa: “Su Malam Zakzaky (H) s**an ce idan za'a shirya irin wannan to a gayyato sauran ɓangarorin mutane da muke rayuwa tare dasu domin su fahimce mu, kuma ba muna cewa ka ajiye fahimtar ka ba kazo kayi tamu ba, a'a ka fahimce mu, mu fahimce ka, amma mu haɗu a taimaki Addinin Musulunci baki ɗaya”.

Daga ƙarshe bayan ya kammala jawabin kuma anyi addu'a an sallami ƴan'uwa, anfara lafiya, an kammala lafiya.

📷 MediaForumKatsina

/2025
13/09/2025

KAI TSAYE: Gada Wajen Gaggarumin Faretin Girmamawa ga Manzon Allah (s a w), ƙarƙashin Jagorancin Shaikh Zakzaky (H), Wan...
13/09/2025

KAI TSAYE: Gada Wajen Gaggarumin Faretin Girmamawa ga Manzon Allah (s a w), ƙarƙashin Jagorancin Shaikh Zakzaky (H), Wanda ƴan Islamiyyu ke gabatarwa a duk shekara.

A wannan shekarar ma yanzu haka taron ya fara gudana a Filin ATC dake nan cikin garin Katsina.

Ƴan Islamiyyu ne daga sassa daban-daban na yankin Katsina ke gabatar da Faretin.

Cikakken Rahoto na nan tafe.

📷 MediaForumKatsina

/2025
13/9/2025

Update Alhamdulillah! Bayan halartar taron ƙasa da ƙasa na haɗin kan Musulumi karo na 39, a Jamhuriyar Musulunci ta Iran...
12/09/2025

Update

Alhamdulillah! Bayan halartar taron ƙasa da ƙasa na haɗin kan Musulumi karo na 39, a Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Jagora Sheikh Ibraheem Zakzaky (H) ya dawo gida Nigeria lafiya.






12/September/2025

Jagora Sheikh Zakzaky (H) tare da Sheikh Yakub Yahya Katsina a wajen taron Makon Haɗin Kai a Iran.          09/September...
09/09/2025

Jagora Sheikh Zakzaky (H) tare da Sheikh Yakub Yahya Katsina a wajen taron Makon Haɗin Kai a Iran.






09/September/2025

DAGA JAMHURIYAR MUSULUNCI TA IRAN: Taron Haɗin Kai Tsakanin Musulmi ya soma Gudana.A yau Litinin 15 ga watan R/Auwal she...
08/09/2025

DAGA JAMHURIYAR MUSULUNCI TA IRAN: Taron Haɗin Kai Tsakanin Musulmi ya soma Gudana.

A yau Litinin 15 ga watan R/Auwal shekara ta 1447 H, dai-dai da 08 ga watan Satumba na shekarar 2025 M, ne aka soma taron Mu’utamar na haɗin kai da kusanto da juna tsakanin ɓangarorin musulunci a faɗin duniya, da ke gudana a Jamhuriyar Musulunci ta Iran ƙarƙashin jagorancin Majma’u Al-taqarrub bainal Mazha’hib.

Taron wanda yake karo na 39 a shekarar bana ya samu halartar Malamai daga Mazhabobi da ƙasashe daban-daban inda Sheikh Yakub Yahya Katsina ma a ɓangaren makarantar Ahlulbiti (A.S) ya samu halarta daga Najeriya.

Wannan Mu’utamar dai ana shirya shi ne duk shekara a cikin satittikan haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (S) a matsayin ramzin haɗin dai da samun kusanci da ƙarfafa soyayya a tsakanin musulmi.

Ga wasu hotunan da aka ɗauka daga ɗakin taron:





07/09/2025
GAGGARUMIN MAULUDIN MANZON ALLAH (S A W) NA DA'IRAR KATSINA YA ƘAYATAR.Lallai a wannan shekara ta 1447/2025, Ƴan'uwa Alm...
06/09/2025

GAGGARUMIN MAULUDIN MANZON ALLAH (S A W) NA DA'IRAR KATSINA YA ƘAYATAR.

Lallai a wannan shekara ta 1447/2025, Ƴan'uwa Almajiran Shaikh Zakzaky (H) sun nuna matukar soyayyarsu ga Manzon Rahama (s a w), ta yanda s**a fito ƙwansu da ƙwarƙwatarsu, don nuna soyayyarsu, kai iya Al'ummar gari ma yanda s**a fito abin gwanin burgewa da ban sha'awa.

Muzaharar wadda ta taso daga Fudiyyah U/madawaki, ta biyo Titin ƙofar ƴanɗaka, ta zagayo titin Rafin Daɗi ta nufi Mobile, daga nan tabi ta Titin Sabon Layi, daga nan ta zagayo Rawun ɗin Ladan Wapa, daga nan kuma ta nufi Filin Samji, inda nan ne aka tuƙe ta.

Lallai anyi Muzaharar da aka jima ba'ayi kalar ta ba, duba da cincirindon ƴan'uwa yanda s**a fito nuna soyayyarsu, sannan ga Sha'irai daban-daban suma ba'a barsu a baya ba.

Ƴan Islamiyyu da Fudiyyoyi kam ansha kwalliya duk dan burge Manzon Rahama (s a w), kuma lallai Annabi (s a w) ya gani, kuma ya yaba.

Bayan ƙarasowa filin rufewa kuma; Malam Shehu Ɗalhatu Ƙarƙarku ya wakilci Shaikh Yakub Yahya wajen gabatar da jawabi, sai dai kafin rufe jawabin, Harisawan Malam Zakzaky (H) sun shigo sun burge Manzon Allah (s a w) da ƙwaƙƙwaran Fareti mai ɗaukar hankali, daga nan kuma sai ya ɗora da jawabin rufewa.

A cikin jawabinsa; Malam Shehu Ɗalhatu Ƙarƙarku yayi godiya ga Allah da irin wannan gaggarumin Maulud da ya gudana, sannan kuma ya jinjina ma ƴan'uwa bisa namijin ƙoƙarin su akan fitowa cikin lokaci da irin sadaukarwar da s**ayi.

Sannan ya cigaba da jawabinsa inda yake cewa; “Al'amarin Maulud daga Allah ne, kuma Maganar da su Malam (H) s**ayi na cewa da Mauludin Manzon Allah (s a w) za'a canza ƙasar nan yana ta tabbata, illa iyaka mu jira lokaci kuma muyi fatan ayi damu”.

Sannan yayi kira ga al'ummar gari da su gane cewa Maulud ba Bidi'a bace kamar yadda Malamansu suke ruɗar su da hakan, babbar Sunnah ce mai ƙarfi, kuma Ibada ce.

Daga ƙarshe ya ƙarfafi ƴan'uwa akan jajircewa wajen sadaukarwa akan duk abinda ya shafi Annabi (s a w) da iyalansa, domin samun tsira gobe ƙiyama.

An fara Muzaharar lafiya, kuma an idar lafiya. Muna addu'ar Allah ya inganta lafiyar su Malam (H) ya bashi kariya a duk inda yake.

📷 MediaForumKatsina

/2025
06/09/2025

DAGA KATSINA: Yanzu haka Muzaharar Mauludin Manzon Allah (s a w) ta ɗaga.Ƴan'uwa Almajiran Shaikh Zakzaky (H) sun fara g...
06/09/2025

DAGA KATSINA: Yanzu haka Muzaharar Mauludin Manzon Allah (s a w) ta ɗaga.

Ƴan'uwa Almajiran Shaikh Zakzaky (H) sun fara gudanar da Gaggarumar Muzaharar Mauludin Manzon Allah (s a w) kamar yadda aka saba duk shekara.

Ku kasance tare damu domin ganin yanda Muzaharar ke cigaba da gudana.

📷 MediaForumKatsina


6/9/2025

YADDA AKA GUDANAR DA TARON GANGAMI NA FAƊAKAWAR FITA ZAGAYEN MAULUDIN FIYAYYEN HALITTA ANNABI MUHAMMAD (SAWW) A DA’IRAR ...
04/09/2025

YADDA AKA GUDANAR DA TARON GANGAMI NA FAƊAKAWAR FITA ZAGAYEN MAULUDIN FIYAYYEN HALITTA ANNABI MUHAMMAD (SAWW) A DA’IRAR KATSINA. NA SHEKARAR 1447H | 2025M.

Da yammacin ranar Alhamis 11 ga watan Rabi'ul Auwal, 1447H, 04 ga watan Satumba, 2025M, ’yan uwa Musulmi almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) a Da’irar Katsina sun gudanar da gangarumin gangami domin faɗakarwa kan fita zagayen Mauludin Annabi (SAWW). Taron ya gudana a muhallin ’yan uwa da ke Ƙofar Marusa, Katsina.

An buɗe taron da addu’a da karatun Alƙur’ani mai girma, daga nan ’yan Ittihadun Shu’ara s**a gabatar da waƙoƙin yabo. Malam Abdul Rahman ya gabatar da maƙasudin taron inda ya bayyana cewa:

"Manufar wannan haduwar tamu ta gangamin shi ne ƙwaffafa tunanin ’yan uwa dangane da fita zagayen Mauludin fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAWW). Ta yadda za a fita cikin tsari, cikin natsuwa, tare da nuna soyayya ga Manzon Rahma (SAWW) da nuna ai-nafin ƙauna gare shi.”

Daga cikin ɓangarorin da s**a gabatar da jawabi a wurin akwai:

Isma Medical Care: Sun mayar da hankali kan batun lafiya. Sun yi kira ga ’yan uwa su kula da jikinsu yayin zagaye, musamman ta hanyar shan ruwa da kiyaye abinci mai gina jiki. Sun jaddada cewa kiyaye lafiyar jiki wani ɓangare ne na bautar Allah da cika haƙƙin rayuwa.

Hurras (Harisawa): Sun yi nuni da rawar da za su taka wajen tabbatar da tsari da doka. Sun roƙi ’yan uwa da su nuna haɗin kai da biyayya ga jagoranci a yayin tafiya, domin kauce wa duk wani abin da zai iya kawo cikas ga gudanar da zagaye cikin kwanciyar hankali.

Amuru bi-l-Ma’aruf: Sun tunatar da muhimmancin aikata alheri da nisantar mummuna. Sun jaddada cewa fita zagaye ba wai nuna yawan jama’a kaɗai ba ne, illa kuwa isar da saƙon gaskiya da da’a kamar yadda Manzon Allah (SAWW) ya koyar.

Media Forum Katsina: Sun yi kira da a kiyaye daidaiton layi da tsari yayin tafiya, musamman ga ’yan Islamiyya. Sun bayyana cewa duk wani hoto ko bidiyo da ake ɗauka a farkon muzahara yana iya zama tarihin da Duniya za ta kalla, saboda haka wajibi ne a kiyaye natsuwa da tsafta. Sun kuma yi gargadi kan mata (Sisters) da su kiyaye matsayinsu da tsarinsu, saboda kyawawan hotuna na iya shiga kafafen watsa labarai a ko da yaushe.

Sisters (’Yan uwa Mata): Sun yi kira ga Mata da su kiyaye mutunci da tsari a ya yin fita zagaye, tare da tabbatar da sutura mai kyau da daidaituwa a tafiya. Sun jaddada cewa zagayen Mauludi dama ce ta nuna soyayya ga Manzon Allah (SAWW) ta hanyar ladabi da tarbiyya.

Lajnar Islamiyyu: Sun jaddada cewa matasa su kasance a cikin tsari tare da kiyaye lizamin tafiya, daidaita sahu da kiyaye lokaci. Sun bayyana cewa, bin tsari da oda a cikin tafiya wani darasi ne da yake koya wa matasa tarbiyya da ɗa’a a rayuwa baki ɗaya.

Da’irar Katsina: A matsayinta na jagorar shirya taron, Da’irar ta yi kira ga dukkan Zones, Hilƙoƙi da Forums da su ƙara haɓɓaka Mauludojin su a gida-gidansu. Haka kuma ta yi jan hankali ga matasa kan muhimmancin mu’amala ta gari a duk inda suke, tare da ƙarfafa haɗin kai domin cigaban Harka a Katsina.

Daga ƙarshe, Malam Usman Ɗalhatu Ƙarƙarku ya gabatar da jawabin rufewa inda ya nuna muhimmancin bin shawarwarin da aka bayar. Ya ce:

“Wannan gangami ba wai kawai taron jan hankali ba ne, illa kuwa taro ne na tabbatar da shirye-shiryenmu wajen fita zagayen Mauludi cikin tsari. Idan muka kiyaye doka, muka kiyaye oda, muka tabbatar da haɗin kai, to lallai zagayenmu zai zama abin koyi. Wannan ita ce hanyar nuna soyayyar mu ga Manzon Allah (SAWW), ba da baki kaɗai ba, har ma da hali da tsari.”

Ya kuma ƙarfafa ’yan uwa da su kasance masu daidaita kai, masu ƙaunar juna, tare da rungumar shawarwari da aka bayar domin zagayen ya gudana cikin nasara da cikar buri.

__ Hassan Midiya Katsina
📸 Media Forum Katsina
Alhamis 04/Satumba/2025M.

DAGA KATSINA: Gangamin Shirin Mauludin Manzon Allah (s a w) a Da'irar Katsina.Ƴan'uwa Almajiran Shaikh Zakzaky (H) suna ...
04/09/2025

DAGA KATSINA: Gangamin Shirin Mauludin Manzon Allah (s a w) a Da'irar Katsina.

Ƴan'uwa Almajiran Shaikh Zakzaky (H) suna gudanar da Gangami akan shirin fita Zagayen Mauludin Manzon Allah (s a w) na Da'irar Katsina baki ɗaya a Markaz dake garin Katsina.

Yanzu haka program ɗin na cigaba da gudana.

Cikakken rahoto na nan tafe...

📷 MediaForumKatsina

/2025

04/9/2025

ADMISSION! ADMISSION!! ADMISSION!!!Assalamu Alaikum Warahmatullah_ . *Amadadin Hukumar Makarantar FUDIYYAH COMMUNITY ACA...
02/09/2025

ADMISSION! ADMISSION!! ADMISSION!!!

Assalamu Alaikum Warahmatullah_ .

*Amadadin Hukumar Makarantar FUDIYYAH COMMUNITY ACADEMY
*Shagari Low-cost Katsina**
Na farin cikin sanar da Iyaye cewa an fara Sayar da Form Domin Ɗaukan Sabbin Ɗalibai a ɓangarorin Makarantar kamar haka:👇

1️⃣ Ɓangaren Islamiyya Nursery Section

2️⃣. Ɓangaren Primary Section

3️⃣. Ɓangaren Junior Secondary Section

4️⃣. Transfer a Dukkan Bangarori tun daga Nursery, Primary har zuwa Jss section

Kuɗin Form #1000 kacal.

Duk mai buƙatar Form ɗin zai iya zuwa Harabar Makarantar da ke Shagari Low-cost Katsina, kokuma a tuntuɓi waɗannan waɗanda keda alhakin siyar da Form ɗin, Domin neman ƙarin bayani:

1. Muhsin Jamilu
2. Zaharaddeen Abdulhadi
3. Mudassir Adam
4. Abu Abdullahi Gambo
Ko a tuntuɓesu ta Lambobi kamar haka:

08130532320
08130630271
09033334917
08138574820

Sanarwa: Daga Hukumar Gudanarwa ta Fudiyyah Community Academy Shagari Low-cost Katsina.

DAGA ZONE ƊIN IMAM HASSAN (A S), ZONCE (C): Mauludin Fiyayyen Halitta Annabi (s a w) ke gudana yanzu haka.Kamar ko wacce...
01/09/2025

DAGA ZONE ƊIN IMAM HASSAN (A S), ZONCE (C): Mauludin Fiyayyen Halitta Annabi (s a w) ke gudana yanzu haka.

Kamar ko wacce shekara ƴan'uwa Almajiran Shaikh Zakzaky (H) na Zone (C) s**an shirya Mauludin Annabi (s a w), a bana ma an shirya Mauludin a Primary ɗin Gafai dake cikin garin Katsina.

Babban baƙo mai Jawabi shine Malam Iliyasu Jibia, yanzu haka yana cigaba da jawabi a muhallin taron.

Cikakken rahoto na nan tafe.

📷 MediaForumKatsina
/2025

1/9/2025

Address

Kofar Marusa
Katsina

Telephone

+2348038139613

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Media Forum Katsina posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Media Forum Katsina:

Share