Media Forum Katsina

Media Forum Katsina Media Katsina

Wanda Ya Raba Addini Da Hukuma, Ya Gina Mulki Ba Tushen Allah. — Cewar Sheikh Yaqoub Yahaya Katsina.Daga: Hassan Midiya ...
21/07/2025

Wanda Ya Raba Addini Da Hukuma, Ya Gina Mulki Ba Tushen Allah. — Cewar Sheikh Yaqoub Yahaya Katsina.

Daga: Hassan Midiya Katsina

A cikin wani muhimmin jawabi da ya ƙayatar da zukata, ya kuma zurfafa tunani a zukatan ma’abota gaskiya, wakilin 'yan uwa musulmi almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) na da'irar Katsina. Sheikh Yaqoub Yahaya Katsina, ya bayyana cewar ba bu bambanci tsakanin Addini da Hukuma a tsarin Musulunci na gaskiya. Wannan jawabi ya gudana ne a ranar Talata 31 ga watan Oktoba, 2023, a wajen bukin Mauludin Manzon Allah (SAWW) da aka gudanar a garin Jahun, Jihar Jigawa.

“Addini shi ne Tushe, Hukuma kuma Mai Gadinsa”

Cikin salo mai ƙayatarwa da cike da hikima, Sheikh ɗin ya fassara dangantakar da ke tsakanin addini da shugabanci k**ar jiki da rai, wanda babu ɗaya cikin su da zai rayu ba tare da ɗayan ba. Ya ce:

“Abin da baya da tushe zai rushe, abin da ba shi da mai gadinsa zai lalace. Gini da ba a kafa shi bisa tushe ba, to ruguzowa zai yi”

Sheikh Yaqoub ya ci gaba da cewa duk wata hukuma a Duniya ko ta adalci ko ta fasadi tana da tasiri a rayuwar mutane. Idan ta zama hukuma mai gaskiya, jama’a za su rabauta da Duniya da Lahira. Amma idan ta kasance hukuma ta shirka da zalunci, to ya zama dole ga Mumini ya tsaya akan addininsa ya nisanta kansa daga bin irin wannan jagoranci.

"Idan hukuma ta bi tafarkin Allah, an rabauta. Idan ta saɓa, Mumini ya nisanta, domin bauta mata na iya janyo shi cikin shirka da halaka.”

Tsarin Raba Addini da Mulki Daga Turawan Mulkin Mallaka Ne:

Sheikh Yaqoub ya fayyace cewa an dasa tunanin raba mulki da addini ne ta hanyar tsarin da Turawan mulkin mallaka s**a shigo da shi. Wannan tsari ba na Musulunci bane, kuma ba shi ne manhajar da Annabi Muhammad (SAWW) ya zo da ita ba.

"In ka ga an raba Addini da Hukuma, to Turanci ne tsarin Turawa ne. Allah da Manzonsa ba su zo da hakan ba.”

Ya ƙara da cewa duk wani yunƙuri na tabbatar da addini ba zai yiwu ba sai an dunkule Hukuma da Addini cikin tsari guda.

Malamin ya kafa tarihi da hujjoji daga rayuwar Shehu Usman Ɗan Fodiyo (R.A), wanda ya farka daga bacci na tsawon ƙarni, ya tashi da muradin shimfiɗa Daular Musulunci bisa tsarkin Shari’a.

Shehu ya iske sarakuna suna rayuwa da iko bisa addini ba tare da tsoron Allah ba, wasu na karkata zuwa al'ada da jahilci. Sai Shehu ya dawo da komai kan madaidaiciyar hanya.

“Shehu ya ce, ‘Kai Sarki ba komai ba ne da kanka, kai wakilin Allah ne, kuma dokokin Allah ne za ka jagoranci mutane da su.’”

Almajiran Shehu su ne s**a jagoranci sallar Juma’a da Idi, s**a zama alƙalai, kwamandoji, da jagororin gari. Wannan tsarin ya zauna tsayin shekaru 100 kafin Bature ya zo ya rushe shi da tsarin mulkin mallaka.

A ya yin bayani mai hikima, kuma Sheikh ɗin ya fayyace cewa Musulunci bai yaƙi sarauta ko masarautu ba, sai dai idan ita sarautar ce ta yaƙi Musulunci. Idan ta rungumi gaskiya, to sai a barta da mulkinta bisa bin Shari’a.

“Musulunci ba yana faɗa bane da Sarauta. Amma idan Sarauta ce ta yaƙi Musulunci, sai Musulunci ya kare kansa. Idan ta karɓi gaskiya, sai a barta a kai, a koya mata daidai.”

Sheikh Yaqoub ya kammala da jaddada muradinsu na ganin an tabbatar da addini a cikin tsarin rayuwa gaba ɗaya wanda hakan ba zai yiwu ba sai an haɗa Addini da Hukuma bisa tafarkin Manzon Allah (SAWW) da Shehu Ɗan Fodiyo (R.A).

"Tabbatar da Addini ba yana nufin rubuce-rubuce ba ne kawai. Muna magana ne akan tsarin rayuwa: inda Addini da Hukuma s**a dunkule. Wannan shi ne hanƙoronmu.”

Lura: Wannan rahoto ya samo asali ne daga jawabin Sheikh Yaqoub Yahaya Katsina a wajen Mauludin Manzon Allah (SAWW). An fassara shi da salo da tsari domin amfanin masu karatu da mabiyan tsarin daular Musulunci a yau.

18/07/2025

"Masu ganin Buhari bai da matsala wankakke ne fess, bai da laifin komi bawan Allah ne da dai sauransu. Allah madaukakin sarki muna rokon ka ka tashe su tare da su, (Buhari ), ka kai su inda ka kai Buhari, duk inda ka kai Buhari aljanna ko wuta Allah ka kai su tare.

__Sheikh Yakub Yahya Katsina.

̇slam

Sanarwa! Sanarwa!! Sanarwa!!!Dandalin Matasan Harkar Muslunci Ƙarƙashin Jagorancin Shaikh Zakzaky (H) na yankin Katsina ...
17/07/2025

Sanarwa!
Sanarwa!!
Sanarwa!!!

Dandalin Matasan Harkar Muslunci Ƙarƙashin Jagorancin Shaikh Zakzaky (H) na yankin Katsina na sanar da Ɗaukacin Matasa akan Mu'utamar ɗin Wuni ɗaya da za'a shiga, wanda aka saba shiryawa duk ƙarshen wata.

Rana: Asabar 19/07/2025
Lokaci: Ƙarfe 9:00 na safe
Wuri: Sabuwar Markaz Katsina

NB: Akwai haƙƙin shiga Mu'utamar ɗin Naira ₦200 kacal ga dukkan Braza da Sista.

Don neman karin bayani sai a tuntuɓi waɗannan lambobin.

08125979395
08130532320

Wai Har Kun Manta Da Wainar Da Kuka Toya?__ Hassan Abubakar Ahmad Ktn Shekarar 2015 ba ta yi nisa da tarihin zukatanmu b...
15/07/2025

Wai Har Kun Manta Da Wainar Da Kuka Toya?

__ Hassan Abubakar Ahmad Ktn

Shekarar 2015 ba ta yi nisa da tarihin zukatanmu ba, amma akwai wasu da sun manta ko kuwa sun yi da gangan da s**a manta. Wannan hoto, wanda ya bazu a lokacin da jininn al’ummar Harkar Musulunci ke malalewa a Gyallesu da Husainiyya, shi ne hoton walimar kisanmu. Wannan ne lokacin da wasu daga cikin 'yan siyasa da baragurbin malamai ke murna da jin daɗin zubar da jinin ɗan Adam.

Kuna zaune a cikin haske kuna ci da sha, muna cikin duhu muna tara gawar masu neman gaskiya. Kun ɗora fulogi da kwanon abinci, mu kuma muna tara ganganin jiki da gawarwaki. Yanzu kuna son mu manta? Kuna son ku riƙa yi mana wa’azi a 2025, alhalin ku kuka yi mana dariya a 2015?

Wallahi, ba zamu manta ba. Kuma ba zamu yafe ba.

Wannan hoton zai ci gaba da zama shaidu akan wanda ya kasance tare da masu gaskiya da wanda ya ɗora kwanukan farin ciki bisa gawar bayin Allah. A lokacin da aka kasha sama da mutum 1000, a lokacin da aka bi da Shaikh Zakzaky da iyalinsa tamkar dabbobi, kai kuma kana zaune kana ci kana dariya?

Babu wanda ya isa ya ce ya fi mu son wannan ƙasa muna da zafin kishinta fiye da wanda ya jiƙa jininmu domin gyaran mulkinsa.

Don haka, idan mun ce "mun yi murna", wannan murnar na da tushe. Idan mun yi dariya, dariyar mu tana da asali. Domin a lokacin da kuka zubar da jininmu, sai kuka ce "bamu damu ba." Yanzu, da mun sami sarari, kuna so mu yi shiru?

To ku sani:

Damuwa ba damuwar waɗanda s**a yi dariya a lokacin da jininmu ke zuba bane. Kuma ƙiyayya ba ta daga wajen wanda bai manta da gawar mahaifinsa ba.

__ Hassan Ɗan Sister Katsina
__ Talata 15/07/2025M.

‎“Wanda duk ya ƙanƙantar da darajar Annabi koda da girman gashin gira ne to ya bar Musulunci”‎‎__Shaikh Yakub Yahya Kats...
12/07/2025

‎“Wanda duk ya ƙanƙantar da darajar Annabi koda da girman gashin gira ne to ya bar Musulunci”

‎__Shaikh Yakub Yahya Katsina a wajen Tafseer zama na Goma 30/03/2023 | 08/09/1444.

📸Media Forum Katsina.
Kofar Marusa Katsina
12/07/2025.

Yahudawa Sun Fi Jin Daɗin Malamin Da Bai Jin Daɗin Iran. _ Cewar Sheikh Yaqoub Yahya Katsina.Daga: Hassan Abubakar Ahmad...
12/07/2025

Yahudawa Sun Fi Jin Daɗin Malamin Da Bai Jin Daɗin Iran. _ Cewar Sheikh Yaqoub Yahya Katsina.

Daga: Hassan Abubakar Ahmad Ktn

A lokacin rufe Mu'utamar na Najnar Tattakin Arba'in na zangon Malumfashi da ya gudana a Markazin 'yan uwa ta Kofar Marusa, Sheikh Yaqoub Yahya Katsina ya zazzaga magana mai nauyi da ta ƙunshi gargaɗi, fallasa da nasiha, musamman kan yadda makiya Musulunci ke amfani da wasu mutane masu laƙabi da malamai don tada fitina a tsakanin al’umma.

“Yahudawa suna ƙoƙarin sanya shakku cikin al’ummar Musulmi ta hanyar amfani da wasu malamai da s**a ɗade suna musu aiki a ɓoye,” in ji Sheikh Yaqoub cikin cike da haƙiƙanin zance.

Sheikh ɗin ya bayyana cewa a ƙasar Iran an k**a wasu daga cikin waɗannan malamai da s**a ɓullo da k**anni na addini, amma a asali “yaran Yahudawa” ne, waɗanda s**a jima suna wa abokan gaba hidima.

A cewar Sheikh Yaqoub, wannan makirci bai tsaya a Iran ba. A Najeriya ma akwai masu riƙe da matsayi na addini amma zuciyarsu tana wa Yahudawa aiki. Ya ce alamominsu sun bayyana daga ƙiyayya da gidan Annabi (SAWW) har zuwa mummunan furuci kan Iran da goyon bayan maƙiya Ahlul-baity (A.S).

Sheikh Yaqoub ya ja hankalin al’umma da kada su bari irin waɗannan mutane su yi musu ruɗu, yana mai cewa:

"Yana daga cikin saƙon Imam Hussain (A.S) a kunyatar da waɗannan malamai, a ya ye musu riga, a gansu tsirara ba sai an ce Sheikh wane ba, ko Dr wane ba, ko Professor wane ba. Idan suna cikin yaran Yahudu, to sai a bayyana su k**ar yadda Imam Hussain ya kunyatar da Yazid har ya mayar da shi tsirara."

Sheikh ɗin ya sake jaddada cewa Ashura ba kuka kawai bace ita hanyar hujja ce, hanyar tsayin daka akan gaskiya, da wulaƙanta munafunci, musamman na waɗanda s**a fake da rigar malamai. Ya ce Imam Hussaini (A.S) ya kunyatar da Yazidu ne ba da takobi ba, sai da hujja da gaskiya kuma yau, wannan hujja tana rayuwa.

“Daga cikin sakon Imam Hussaini (A.S) akwai kunyatar da malamai munafukai. Ko da sun tsaya kan mimbari, ko da suna da masallatai, idan su ne masu tallafa wa makiya gidan Manzon Allah (SAWW), to wannan Ashura tana jira su, kuma zata fallasa su,” in ji Sheikh ɗin cikin taka-tsantsan.

A ƙarshen jawabinsa, Sheikh ya jan hankali 'yan uwa da cewa babban taimakon da za a iya yi wa tafarki mai tsarki shi ne: kada a cutar da shi daga cikin gida. Ya ce idan mutum bai iya kare tafarki ba, to ya guji zama matsala gare shi.

"Mu taimaki tafarkin Hussaini da ƙanƙan da kai da ɗaukaka da tsarewa. Kada mu bashi haushi. Kada mu janyo masa kunya. Kada tafarki ya samu rauni saboda muna ciki,” in ji shi.

Jawabin Sheikh Yaqoub Yahya Katsina a wannan rana, ya sake tunatar da Duniya cewa musiba mafi girma ita ce idan munafunci ya shigo ta ƙofar limanci da malunta. Kuma babu wata hanya ta ceto irin ta gaskiya, da tsayuwa kan tafarkin Ahlul-baity (A.S) da ƙaryata shaiɗanu cikin riga da hula.

“Kowane malami da ke ƙin Ahlul-baity (A.S) a zuciyarsa, to yana cikin makircin Yazidu a yau. Kuma Ashura ba zata yi shiru akansa ba.”

__ Hassan Midiya Katsina
__ Asabar 12/07/2025M.

MU'UTAMAR ƊIN ASHURA DA TATTAKIN ARBA'IN NA ZANGON MALUMFASHI: Ƙarfafa Gwiwar Mabiya Imam Hussain (A.S). Na Shekarar 144...
12/07/2025

MU'UTAMAR ƊIN ASHURA DA TATTAKIN ARBA'IN NA ZANGON MALUMFASHI: Ƙarfafa Gwiwar Mabiya Imam Hussain (A.S). Na Shekarar 1447H_2025M.

Daga: Hassan Abubakar Ahmad Ktn

An gudanar da babban taron mu’utamar na Tattakin Arba’in na bana a Markazin ‘yan uwa na Da’irar Katsina, a ranar Asabar 17/01/1447H daidai da 12/07/2025M. Taron ya fara ne da misalin ƙarfe 11:30 na safe, bayan an gudanar da rajistar mahalarta a ƙofa ƙarƙashin kulawar Malam Zuladaini Bello da Malama Mariya Zakariya a ɓangaren Sisters, domin tabbatar da tsari da bin jagoranci.

Taron ya samu halartar manyan malamai, shugabannin kwamitoci, wakilan yankuna, da mahalarta daga sassa daban-daban na jihar.

Taron ya buɗe da addu’a da karatun Alƙur’ani mai girma daga bakin Malam Aminu, sai kuma waƙoƙi daga Ittihadu. Daga nan ne Malam Yusuf Abdullahi (MC) ya gabatar da Malam Basiru Usta domin wakiltar Malam Abdullahi Tukur wajen bayyana manufar wannan mu’utamar na shekarar 1447H/2025M.

Inda yake cewa:

Manufar wannan taron mu’utamar ita ce shirya da horar da ‘yan uwa domin gudanar da Tattakin Arba’in na bana cikin tsari, sadaukarwa da kuma biyayya ga jagoranci. An buƙaci fahimtar ainihin ma’anar sadaukarwar Imam Hussain (AS), koyi da shi a aikace, da kuma samar da shiri na tsaro, lafiya, tsabtace zuciya da jiki, da isar da sako cikin kwanciyar hankali da k**ala.

Jawabi na farko: Malam Abdullahi wakilin 'yan uwa na Hunƙuyi: "Mahimmancin Sadaukarwar Ashura da Tattakin Arba'in"

A jawabin farko na mu’utamar, Malam Aminu Ibrahim Kudan ya gabatar da Malam Abdullahi Hunƙuyi, wakilin ’yan uwa daga Hunƙuyi, wanda ya yi cikakken bayani mai zurfi kan sadaukarwar Ashura da girmanta a matsayin asalinta na Tattakin Arba’in.

Malam Abdullahi ya fara da ziyara ga Imam Hussain (AS), cikin nuna girmamawa da tawali’u, inda ya ce: "Wannan maudu’i na Sadaukarwar Ashura, ya fi karfina a matsayina na ɗalibi. Malami ya k**ata a ba shi, ba ni ba. Amma biyayya ce ta kawo ni."

A cikin bayaninsa, ya zayyana yadda sadaukarwar Imam Hussain (A.S) ba wai tarihi ne kawai ba, amma makaranta ce ta koyon azama, jimiri da tawakkali. Ya kawo misalai daga tarihin Ashura da yadda hakan ya kafa tubalin koyi ga al’ummar musulmi.

Malam Abdullahi ya zurfafa cikin bayanin ma’anar sadaukarwa, yana cewa: “Duk abin da ka sadaukar don Imam Hussain (A.S), babu riya, babu son zuciya, kuma hakan shi ne tushen nasara.”

Bayan haka, ya jaddada cewa kowane mataki da aka ɗauka cikin tattakin Arba’in, ya zama cikakken misali na tsarkakakken tsari da himma, domin gina kai da al’umma.

Daga ƙarshe, mai gabatar da shi ya ƙara jinjina da ta’aliki, inda ya ambaci wata ƙissa mai ban tausayi daga tarihin Sayyida Zainab (SA), a matsayin cikakkiyar fatawa ta sadaukarwa da juriya.

Jawabi na biyu: Malam Ilyasu Jibia: "Koyi da Sadaukarwar Imam Hussain (A.S) Ne Jigon Nasarar Iran Akan Yahudawa"

Sai aka gabatar da Malam Ilyasu Jibia, wakilin ’yan uwa na garin Jibia, wanda Malam Abubakar Magaji Ingawa ya gabatar da shi.

Jawabin nasa ya ta’allaka ne da yadda jigon koyi da Imam Hussain (A.S) ke daga cikin asalin nasarar Jamhuriyar Musulunci ta Iran akan Yahudawan duniya. Ya fara da godiya da sallamawa, cikin tawali’u da jin nauyin alhakin jawabin, yana cewa: "Wannan maudu’i ba na irina ba ne, amma biyayya ta tilasta min isar da sakon."

Malam Ilyasu ya yi bayani dalla-dalla kan dangantakar sadaukarwar Imam Hussain (A.S) da yadda Iran ta karɓi wannan hanya ta juriya, tsayawa akan gaskiya da tsantsan biyayya ga jagoranci, wanda hakan ya haifar da nasarori a fannin siyasa da tsaro.

Ya ce:

"Sadaukarwa ita ce mutum ya zuba dukkan ƙoƙarinsa akan gaskiya, k**ar yadda Imam Hussain (AS) ya yi."

"Iran ta koyi wannan, ta aiwatar da shi, har ta kai matakin da ta fi karfin Yahudawan Duniya."

Ya zayyana cewa Iran tana iya harba mak**ai fiye da dubu biyu a cikin kwanaki biyu, kuma mak**an da ake harba Mata ne ke mayar da martani, Maza har yanzu basu fara ba. Ya ce Iran tana da mak**ai masu suna Sijjil da Habhab, wadanda ke da matsayi mai girma a fannin tsaron ƙasa.

"Iran tana harba mayar da martani daga kilomita dubu biyu, kuma cikin minti uku take isa inda aka nufi (Hara)."

"Tirakar mak**an su ba a hangowa a ido. Wannan ba komai bane illa sak**akon koyi da Imam Hussain (A.S)."

Daga ƙarshe, Malam Abubakar Magaji Ingawa ya gabatar da ta’aliki, yana ƙara haske kan cewa Iran tana mayar da martani ne kawai in an tsokane ta, kuma hakan na cikin ƙa’idar jihadin kare kai, irin yadda Imam Hussain (A.S) ya yi y.

Bayani Daga Kwamitoci: An gabatar da bayani daga ɓangarori da s**a samu halarta na kwamiti k**ar haka:

1. Isma: Malam Zubairu M. Dikko ya ja hankalin ‘yan uwa su kiyaye shan magani da inganta lafiyar tafiya.

2. Amiru bin Ma’aruf: Malam Abdullahi ya ja hankalin ‘yan uwa akan bin umarni da tsari.

3. Direbobi: Malam Hamza Lawal ya buƙaci a riƙa kawo jerin sunayen matafiya da wuri don samun isassun motoci.

4. Matasa: Malam Sirajo Abdullahi ya roƙi iyaye da wakilai su baiwa matasa aiki da kwarin gwiwa.

5. Media: Malam Basiru Usta ya buƙaci a mutunta ayyukan masu ɗaukar hoto da bidiyo, a guji tsoma baki ya yin aiki, kuma a tabbatar da yanayi na juyayi ya yin ɗaukar hoto.

6. Sisters: Malama Mariya Zakirya ta roki matan da su kiyaye tsafta da k**ala, su kula da yara, kuma su san yanayin da ya dace da tafiya.

7. Hurras: Malam Abdullahi Ɗanɗagoro ya buƙaci a baiwa masu tsaro haɗin kai, a bi sahu da tsari k**ar yadda kwamiti ya tsara, a kuma bada rahoto idan an ga wani abu da ba daidai ba.

Sallah da Cin Abinci: An gabatar da Sallar da cin abinci ƙarƙashin jagorancin Malam Yusuf Abdullahi. Daga nan aka ci gaba da mu’utamar.

Isar da Sakon Tattakin Arba’in: Malam Usman Sabo ATC ne ya karɓi sakonnin tattakin bana. Duk da cewar lokaci bai ba da damar tattaunawa da yawa ba, an roƙi mahalarta da su kai sako ga mai kula da tattaunawa.

A ya yin rufe mu’utamar shirin Tattakin Arba’in da ya gudana a Markazin 'yan uwa na da’irar Katsina, Malam Usman Sabo ATC ya gabatar da wani ƙayyadadden jawabi mai cike da shawarwari da tunatarwa ga mahalarta, kafin miƙa alƙalamin ƙarshe ga wakilin 'yan uwa na da'irar Katsina, Sheikh Yaqoub Yahya Katsina.

Malam Usman ya fara ne da tunasarwa ga wakilai da su sanar da 'yan uwa muhimmancin kiyaye lizami da ladabi a lokacin tafiya, yana mai jaddada cewa, "’Yan uwa da zasu fito su san mi ya fito da su." A cewarsa, wannan tafiya ba ta barin gida kawai ba ce, sai an fito da tsari da ruhi.

Ya kuma jaddada cewa, “Kyakkyawan ɗabi’a su jagoranci wannan tafiya. Idan muka tafi, zamu haɗu da mutane, dole ne mu kare haƙƙinsu.” Ya ce wajibi ne a kula da zamantakewa, a guji ɗabi’un da ka iya bata hoton tafiya ko mayar da ita abin kyama.

A ƙarshe, Malam Usman ya isar da sakon Kwamitin Tattakin Arba’in zuwa ga 'yan uwa na yankin Malumfashi, inda ya ce: "Muna miƙa sako banama su, linka basira."

Daga nan Sheikh Yaqoub Yahya Katsina ya hau mimbari domin gabatar da jawabin rufewa, wanda ya kasance tamkar kammalawa da jigo ga dukan abubuwan da aka tattauna a taron.

Ya fara ne da godiya ga Allah da ya basu damar gudanar da wannan mu’utamar cikin zaman lafiya, yana mai cewa: "Muna yi wa Allah godiya da ya bamu aron lumfashi da lokaci da muka samu damar sake gudanar da wannan mu’utamar na tattakin arba’in na bana, mai taken sadaukarwa da koyi da Imam Hussain (A.S)."

Sheikh ya bayyana cewa ya saurari jawaban da s**a gabata kafin zuwansa, ya kuma yabawa irin hikima da zurfin tunani da s**a mamaye bayanan. A cewarsa, "Sadaukarwar Imam Hussain (A.S) ita ce nasara, ita ce makarantarmu." Ya kawo misalai irin su yadda Imam ya yi da sahabbansa, waɗanda s**a ce masa: “Miye amfanin rayuwa bayan babu kai?” Wannan, inji Sheikh, ita ce sadaukarwar da muke buƙata.

Sheikh ya bayyana cewa, sadaukarwar Imam Hussain ta kasance haske da darasi ga Duniya, har wasu fitattun shugabannin Duniya s**a yi koyi da shi. "Mandela ya yi koyi da shi, Mahatma Gandhi ya yi koyi da shi har ya yantar da India," inji shi. Saboda haka, ya ce:

"Makarantar Imam Hussain (A.S) makaranta ce ta sadaukarwa, ba sharholiya ba.”

Sheikh ya kuma jaddada sakon Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), yana mai cewa:

“'Yan uwa da suke wakilarta yankuna k**ar yadda Malam (H) ya ce, a buɗe littafi a karantar da mutane dalilin da ya haifar da Karbala har zuwa wannan lokacin.”

A cewarsa, wannan karatu shi ne zai bayyana haƙiƙanin gaskiya, ya kuma ƙara jan hankalin mahalarta da cewa, su yi biyayya ga jagoranci a kowane lokaci, ba kawai a lokacin Tattaki ba. Ya ce:

“Kowane wanda kuka ga an sanya to ya cancanta. Saboda haka a bashi damarsa, kuma a kimanta damarsa. Wannan shi ake kira lizami.”

A ƙarshe, Sheikh Yaqoub ya tunatar da mahalarta muhimmancin kare haƙƙin wasu, yana cewa: “Kada ku yarda wani ya yi muku Allah ya isa.”

Bayan haka, Malam Yusha’u Aliyu ya gabatar da jawabin godiya ga dukan mahalarta da waɗanda s**a bayar da gudunmawa, sannan aka rufe taron da addu’a daga bakin malam ɗin.

📸 Media Forum Katsina
Kofar Marusa – Birnin Katsina
17/Muharram/1447H_12/Yuli/2025M

Ba Ka Isa Ka Kwaikwayi Jagora Ɗari Bisa Ɗari Ba, Amma Ka Guji Bata Masa Zuciya. _ Inji Sheikh Yaqoub Yahya Katsina Daga:...
10/07/2025

Ba Ka Isa Ka Kwaikwayi Jagora Ɗari Bisa Ɗari Ba, Amma Ka Guji Bata Masa Zuciya. _ Inji Sheikh Yaqoub Yahya Katsina

Daga: Hassan Abubakar Ahmad Ktn

A wani taron mu’tamar da ya gudana a yankin Sokoto a shekarar 1436 Hijira, 2015 Miladiyya, Sheikh Yaqoub Yahya Katsina ya gabatar da jawabi mai zurfi da hikima, inda ya bayyana cewa addini gwaji ne jarabawa ce da mutum ke cikin ta har ya koma ga Ubangijinsa. Kuma cin wannan jarabawar, a cewarsa, shi ne biyayya ga jagoranci da sadaukar da kai cikin tsantsar ikhlasi, koda kuwa da gazawar ɗan Adam.

"Addini jarabawa ce. Sai dai mutum ya roƙi Allah ya bashi ikon cin ta. Amma cin jarabawar cikin addini shi ne biyaya ga jagora,” in ji Sheikh ɗin.

Ya jaddada cewa ba za a iya cimma cikakkiyar biyayya ɗari bisa ɗari ba, saboda ƙuntatawar ɗan Adam k**ar rashin fahimta, gazawa, ko ƙarancin hangen nesa. Amma kodayake ba zai kai matakin jagora ba, mutum na iya kwaikwayon sa da ƙoƙari da neman daidaito.

Ya ce:

“Shi jagora na musamman ne. Allah ne ke gina shi. Shiyasa Allah yace babu wanda zai iya yin k**ar Manzon Allah (SAWW), sai dai a ɗan kwaikwaya.”

Sheikh Yaqoub ya kawo misalin yadda hatta Shehu Abdullahi (R.A) a lokacin da ya fuskanci matsala ko ruɗani, sai ya koma wajen Shehu Usman Ɗan Fodiyo domin neman mafita da shawara. Wannan, a cewarsa, alamar cewa koda babban almajiri ne, yana buƙatar sauƙaƙa kai da mayar da komai ga jagora.

Ya ci gaba da cewa:

“Al-mahimmu mutum ya yi ƙoƙari koda 99 cikin 100 ya samu, sai wancan guda ɗayan ya zama gazawa, kuskure, ko rashi fahimta. Amma fa kada ya cutar da zuciyar jagora.”

“Kada Mu Yi Wa Jagora Abin Da Zai Sosa Masa Zuciya”

Sheikh Yaqoub ya jaddada cewa babban taimakon da almajiri zai iya yiwa jagora (H) shi ne kada ya ɓata masa rai. Idan kuwa muka haifar masa da damuwa daga ciki, miye bambancinmu da waɗanda ke yaki da shi daga waje?

"Idan har zamu iya haifar wa jagora matsala daga cikinmu, to me ya banbanta mu da makiya daga waje?”

Jawabin na Sheikh Yaqoub Yahya Katsina ya ƙara jaddada muhimmancin sadaukarwa, biyayya da kulawa da jagora ba ta hanyar ƙwazo kaɗai ba, har da tsarkake zuciya daga cutar da shi da kowane hali ko zato.

___ Hassan Midiya Katsina
___ Alhamis 10/07/2025M.

10/07/2025

BAYAR DA JINI DOMIN IMAM HUSAINI A KATSINA:- Tattaunawar Media Forum Katsina da wasu daga cikin masu dibar jinin (NBTS) da kuma wakili daga shashen lafiya na harkar musulunci (ISMA), da kuma waɗanda aka dibar ma jinin.

Wannan tattaunawar ta gudana ne a ranar Laraba 09/07/2025, rana ta biyu da fara karbar jinin a muhallin marakz dake Kofar Marusa Katsina.

📸 Media Forum Katsina
Kofar Marusa – Birnin Katsina
14/Muharram/1447H_10/Yuli/2025M

JININMU SADAUKARWA NE: Sama da Leda 50 Aka Tara A Da’irar Katsina Bayan Kammala Zaman Ashura.Da’irar Katsina ta Harkar M...
09/07/2025

JININMU SADAUKARWA NE: Sama da Leda 50 Aka Tara A Da’irar Katsina Bayan Kammala Zaman Ashura.

Da’irar Katsina ta Harkar Musulunci ƙarƙashin jagorancin Sheikh Ibraheem Zakzaky (H), ta ci gaba da gudanar da aikin bayar da jini a matsayin sadaukarwa ga Imam Hussain (A.S) bayan kammala zaman Ashura.

A yau Laraba 13 Muharram 1447H (09/07/2025), aka shiga rana ta biyu na wannan aiki mai alaƙa da ruhin Karbala, wanda ake gudanarwa a Markaz na Kofar Marusa cikin birnin Katsina.

Sama da leda hamsin da wani abu (50+) na jini aka tattara tun daga ranar Talata zuwa yau Laraba, k**ar yadda kwamitin bayar da jini ya tabbatar.

Sheikh Yaqoub Yahya Katsina, wakilin ’yan uwa a Da’irar Katsina, ya bayyana cewa:

"Bayar da jini wata hanya ce da ke haɗa sadaukarwa da ceton rayuka. Wannan shi ne Labbaika Ya Hussain da ayyuka, ba da magana kawai ba."

Muhalli: Markaz, Kofar Marusa.
Lokaci: Bayan kammala zaman juyayi.
Gudanarwa: Jami’an lafiya da ’yan uwan da s**a sahale tsari mai inganci.

📸 Media Forum Katsina
Kofar Marusa – Birnin Katsina
13/Muharram/1447H_09/Yuli/2025M

Sayyid Zakzaky Ya Zame Mana Hanya Zuwa Wajen Allah (Swt). — Inji Sheikh Yaqoub Yahaya Katsina.Daga: Hassan Abubakar Ahma...
09/07/2025

Sayyid Zakzaky Ya Zame Mana Hanya Zuwa Wajen Allah (Swt). — Inji Sheikh Yaqoub Yahaya Katsina.

Daga: Hassan Abubakar Ahmad Ktn

Sheikh Yaqoub Yahaya Katsina ya bayyana cewar Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), babban jagoran Harkar Musulunci a Najeriya, ya zama tsani kuma hanya ga waɗanda ke neman yanci da kusanci da Allah (Swt).

A cewar Sheikh ɗin:

“Sayyid Zakzaky Hafizahullah ya nuna mana yadda ake samar da 'yanci. Kuma ya nuna mana yadda ake zuwa wajen Allah (Swt).”

Wannan furuci yana nuni ne da girman rawar da Sayyid Zakzaky ke takawa wajen shiryar da al’umma zuwa tafarkin Allah ta hanyar haƙuri, gwagwarmaya da tsayin daka.

Sheikh ɗin ya bayyana hakan ne a wani jawabi da ya gabatar cikin natsuwa cike da girmamawa, yana ƙarfafa wa almajiran Sayyid guiwa da su ci gaba da riƙo da darussa da halayen da Jagoran ya gina su da su.

A bisa wannan furuci, ya ƙara jaddada cewa ba kawai Jagora ne Sayyid Zakzaky ba, illa kuwa jagora ne na ruhaniya da addini wanda ya sada mutane da tafarkin tsarkaka.

__ Hassan Midiya Katsina
__ Laraba 09/07/2025M.

Cikin Hotuna: Yadda Yan Uwa Na Da'irar Katsina S**a Fara Bayar Da Jini A Kofar Marusa Don Girmama Imam Hussain (A.S).Ko ...
08/07/2025

Cikin Hotuna: Yadda Yan Uwa Na Da'irar Katsina S**a Fara Bayar Da Jini A Kofar Marusa Don Girmama Imam Hussain (A.S).

Ko bayan an kammala kwanaki goma na zaman juyayin shahadar Imam Hussain (A.S), 'yan uwa almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H) a Da’irar Katsina, sun ci gaba da nuna cewa sadaukarwa ba ta tsaya a kuka da waƙa ba har jini ake bayarwa.

A yau, a unguwar Kofar Marusa, cikin birnin Katsina, an fara bayar da jini a muhallin Markaz domin hidima ga al’umma da kuma ci gaba da rayar da ruhin Karbala da Imam Hussain (A.S) ya tsayu akai.

A cikin waɗannan hotuna, muna ganin zuciya da aiki, ruhi da halayya suna miƙa kansu daidai da manufa: "Labbaikai Ya Hussain" ba da baki kaɗai ba, amma da jiki, da ƙoƙari, da jini.

Wannan aiki ba kawai taimako bane, ibada ce da sadaukarwa, domin jinin Hussain ne ya ceci addini, kuma jinin bayinsa na ci gaba da ceto rayuka.

📸 Media Forum Katsina
Kofar Marusa – Birnin Katsina
12/Muharram/1447H_08/Yuli/2025M

Address

Katsina

Telephone

+2348038139613

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Media Forum Katsina posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Media Forum Katsina:

Share