12/07/2025
MU'UTAMAR ƊIN ASHURA DA TATTAKIN ARBA'IN NA ZANGON MALUMFASHI: Ƙarfafa Gwiwar Mabiya Imam Hussain (A.S). Na Shekarar 1447H_2025M.
Daga: Hassan Abubakar Ahmad Ktn
An gudanar da babban taron mu’utamar na Tattakin Arba’in na bana a Markazin ‘yan uwa na Da’irar Katsina, a ranar Asabar 17/01/1447H daidai da 12/07/2025M. Taron ya fara ne da misalin ƙarfe 11:30 na safe, bayan an gudanar da rajistar mahalarta a ƙofa ƙarƙashin kulawar Malam Zuladaini Bello da Malama Mariya Zakariya a ɓangaren Sisters, domin tabbatar da tsari da bin jagoranci.
Taron ya samu halartar manyan malamai, shugabannin kwamitoci, wakilan yankuna, da mahalarta daga sassa daban-daban na jihar.
Taron ya buɗe da addu’a da karatun Alƙur’ani mai girma daga bakin Malam Aminu, sai kuma waƙoƙi daga Ittihadu. Daga nan ne Malam Yusuf Abdullahi (MC) ya gabatar da Malam Basiru Usta domin wakiltar Malam Abdullahi Tukur wajen bayyana manufar wannan mu’utamar na shekarar 1447H/2025M.
Inda yake cewa:
Manufar wannan taron mu’utamar ita ce shirya da horar da ‘yan uwa domin gudanar da Tattakin Arba’in na bana cikin tsari, sadaukarwa da kuma biyayya ga jagoranci. An buƙaci fahimtar ainihin ma’anar sadaukarwar Imam Hussain (AS), koyi da shi a aikace, da kuma samar da shiri na tsaro, lafiya, tsabtace zuciya da jiki, da isar da sako cikin kwanciyar hankali da k**ala.
Jawabi na farko: Malam Abdullahi wakilin 'yan uwa na Hunƙuyi: "Mahimmancin Sadaukarwar Ashura da Tattakin Arba'in"
A jawabin farko na mu’utamar, Malam Aminu Ibrahim Kudan ya gabatar da Malam Abdullahi Hunƙuyi, wakilin ’yan uwa daga Hunƙuyi, wanda ya yi cikakken bayani mai zurfi kan sadaukarwar Ashura da girmanta a matsayin asalinta na Tattakin Arba’in.
Malam Abdullahi ya fara da ziyara ga Imam Hussain (AS), cikin nuna girmamawa da tawali’u, inda ya ce: "Wannan maudu’i na Sadaukarwar Ashura, ya fi karfina a matsayina na ɗalibi. Malami ya k**ata a ba shi, ba ni ba. Amma biyayya ce ta kawo ni."
A cikin bayaninsa, ya zayyana yadda sadaukarwar Imam Hussain (A.S) ba wai tarihi ne kawai ba, amma makaranta ce ta koyon azama, jimiri da tawakkali. Ya kawo misalai daga tarihin Ashura da yadda hakan ya kafa tubalin koyi ga al’ummar musulmi.
Malam Abdullahi ya zurfafa cikin bayanin ma’anar sadaukarwa, yana cewa: “Duk abin da ka sadaukar don Imam Hussain (A.S), babu riya, babu son zuciya, kuma hakan shi ne tushen nasara.”
Bayan haka, ya jaddada cewa kowane mataki da aka ɗauka cikin tattakin Arba’in, ya zama cikakken misali na tsarkakakken tsari da himma, domin gina kai da al’umma.
Daga ƙarshe, mai gabatar da shi ya ƙara jinjina da ta’aliki, inda ya ambaci wata ƙissa mai ban tausayi daga tarihin Sayyida Zainab (SA), a matsayin cikakkiyar fatawa ta sadaukarwa da juriya.
Jawabi na biyu: Malam Ilyasu Jibia: "Koyi da Sadaukarwar Imam Hussain (A.S) Ne Jigon Nasarar Iran Akan Yahudawa"
Sai aka gabatar da Malam Ilyasu Jibia, wakilin ’yan uwa na garin Jibia, wanda Malam Abubakar Magaji Ingawa ya gabatar da shi.
Jawabin nasa ya ta’allaka ne da yadda jigon koyi da Imam Hussain (A.S) ke daga cikin asalin nasarar Jamhuriyar Musulunci ta Iran akan Yahudawan duniya. Ya fara da godiya da sallamawa, cikin tawali’u da jin nauyin alhakin jawabin, yana cewa: "Wannan maudu’i ba na irina ba ne, amma biyayya ta tilasta min isar da sakon."
Malam Ilyasu ya yi bayani dalla-dalla kan dangantakar sadaukarwar Imam Hussain (A.S) da yadda Iran ta karɓi wannan hanya ta juriya, tsayawa akan gaskiya da tsantsan biyayya ga jagoranci, wanda hakan ya haifar da nasarori a fannin siyasa da tsaro.
Ya ce:
"Sadaukarwa ita ce mutum ya zuba dukkan ƙoƙarinsa akan gaskiya, k**ar yadda Imam Hussain (AS) ya yi."
"Iran ta koyi wannan, ta aiwatar da shi, har ta kai matakin da ta fi karfin Yahudawan Duniya."
Ya zayyana cewa Iran tana iya harba mak**ai fiye da dubu biyu a cikin kwanaki biyu, kuma mak**an da ake harba Mata ne ke mayar da martani, Maza har yanzu basu fara ba. Ya ce Iran tana da mak**ai masu suna Sijjil da Habhab, wadanda ke da matsayi mai girma a fannin tsaron ƙasa.
"Iran tana harba mayar da martani daga kilomita dubu biyu, kuma cikin minti uku take isa inda aka nufi (Hara)."
"Tirakar mak**an su ba a hangowa a ido. Wannan ba komai bane illa sak**akon koyi da Imam Hussain (A.S)."
Daga ƙarshe, Malam Abubakar Magaji Ingawa ya gabatar da ta’aliki, yana ƙara haske kan cewa Iran tana mayar da martani ne kawai in an tsokane ta, kuma hakan na cikin ƙa’idar jihadin kare kai, irin yadda Imam Hussain (A.S) ya yi y.
Bayani Daga Kwamitoci: An gabatar da bayani daga ɓangarori da s**a samu halarta na kwamiti k**ar haka:
1. Isma: Malam Zubairu M. Dikko ya ja hankalin ‘yan uwa su kiyaye shan magani da inganta lafiyar tafiya.
2. Amiru bin Ma’aruf: Malam Abdullahi ya ja hankalin ‘yan uwa akan bin umarni da tsari.
3. Direbobi: Malam Hamza Lawal ya buƙaci a riƙa kawo jerin sunayen matafiya da wuri don samun isassun motoci.
4. Matasa: Malam Sirajo Abdullahi ya roƙi iyaye da wakilai su baiwa matasa aiki da kwarin gwiwa.
5. Media: Malam Basiru Usta ya buƙaci a mutunta ayyukan masu ɗaukar hoto da bidiyo, a guji tsoma baki ya yin aiki, kuma a tabbatar da yanayi na juyayi ya yin ɗaukar hoto.
6. Sisters: Malama Mariya Zakirya ta roki matan da su kiyaye tsafta da k**ala, su kula da yara, kuma su san yanayin da ya dace da tafiya.
7. Hurras: Malam Abdullahi Ɗanɗagoro ya buƙaci a baiwa masu tsaro haɗin kai, a bi sahu da tsari k**ar yadda kwamiti ya tsara, a kuma bada rahoto idan an ga wani abu da ba daidai ba.
Sallah da Cin Abinci: An gabatar da Sallar da cin abinci ƙarƙashin jagorancin Malam Yusuf Abdullahi. Daga nan aka ci gaba da mu’utamar.
Isar da Sakon Tattakin Arba’in: Malam Usman Sabo ATC ne ya karɓi sakonnin tattakin bana. Duk da cewar lokaci bai ba da damar tattaunawa da yawa ba, an roƙi mahalarta da su kai sako ga mai kula da tattaunawa.
A ya yin rufe mu’utamar shirin Tattakin Arba’in da ya gudana a Markazin 'yan uwa na da’irar Katsina, Malam Usman Sabo ATC ya gabatar da wani ƙayyadadden jawabi mai cike da shawarwari da tunatarwa ga mahalarta, kafin miƙa alƙalamin ƙarshe ga wakilin 'yan uwa na da'irar Katsina, Sheikh Yaqoub Yahya Katsina.
Malam Usman ya fara ne da tunasarwa ga wakilai da su sanar da 'yan uwa muhimmancin kiyaye lizami da ladabi a lokacin tafiya, yana mai jaddada cewa, "’Yan uwa da zasu fito su san mi ya fito da su." A cewarsa, wannan tafiya ba ta barin gida kawai ba ce, sai an fito da tsari da ruhi.
Ya kuma jaddada cewa, “Kyakkyawan ɗabi’a su jagoranci wannan tafiya. Idan muka tafi, zamu haɗu da mutane, dole ne mu kare haƙƙinsu.” Ya ce wajibi ne a kula da zamantakewa, a guji ɗabi’un da ka iya bata hoton tafiya ko mayar da ita abin kyama.
A ƙarshe, Malam Usman ya isar da sakon Kwamitin Tattakin Arba’in zuwa ga 'yan uwa na yankin Malumfashi, inda ya ce: "Muna miƙa sako banama su, linka basira."
Daga nan Sheikh Yaqoub Yahya Katsina ya hau mimbari domin gabatar da jawabin rufewa, wanda ya kasance tamkar kammalawa da jigo ga dukan abubuwan da aka tattauna a taron.
Ya fara ne da godiya ga Allah da ya basu damar gudanar da wannan mu’utamar cikin zaman lafiya, yana mai cewa: "Muna yi wa Allah godiya da ya bamu aron lumfashi da lokaci da muka samu damar sake gudanar da wannan mu’utamar na tattakin arba’in na bana, mai taken sadaukarwa da koyi da Imam Hussain (A.S)."
Sheikh ya bayyana cewa ya saurari jawaban da s**a gabata kafin zuwansa, ya kuma yabawa irin hikima da zurfin tunani da s**a mamaye bayanan. A cewarsa, "Sadaukarwar Imam Hussain (A.S) ita ce nasara, ita ce makarantarmu." Ya kawo misalai irin su yadda Imam ya yi da sahabbansa, waɗanda s**a ce masa: “Miye amfanin rayuwa bayan babu kai?” Wannan, inji Sheikh, ita ce sadaukarwar da muke buƙata.
Sheikh ya bayyana cewa, sadaukarwar Imam Hussain ta kasance haske da darasi ga Duniya, har wasu fitattun shugabannin Duniya s**a yi koyi da shi. "Mandela ya yi koyi da shi, Mahatma Gandhi ya yi koyi da shi har ya yantar da India," inji shi. Saboda haka, ya ce:
"Makarantar Imam Hussain (A.S) makaranta ce ta sadaukarwa, ba sharholiya ba.”
Sheikh ya kuma jaddada sakon Jagora Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), yana mai cewa:
“'Yan uwa da suke wakilarta yankuna k**ar yadda Malam (H) ya ce, a buɗe littafi a karantar da mutane dalilin da ya haifar da Karbala har zuwa wannan lokacin.”
A cewarsa, wannan karatu shi ne zai bayyana haƙiƙanin gaskiya, ya kuma ƙara jan hankalin mahalarta da cewa, su yi biyayya ga jagoranci a kowane lokaci, ba kawai a lokacin Tattaki ba. Ya ce:
“Kowane wanda kuka ga an sanya to ya cancanta. Saboda haka a bashi damarsa, kuma a kimanta damarsa. Wannan shi ake kira lizami.”
A ƙarshe, Sheikh Yaqoub ya tunatar da mahalarta muhimmancin kare haƙƙin wasu, yana cewa: “Kada ku yarda wani ya yi muku Allah ya isa.”
Bayan haka, Malam Yusha’u Aliyu ya gabatar da jawabin godiya ga dukan mahalarta da waɗanda s**a bayar da gudunmawa, sannan aka rufe taron da addu’a daga bakin malam ɗin.
📸 Media Forum Katsina
Kofar Marusa – Birnin Katsina
17/Muharram/1447H_12/Yuli/2025M