Media Forum Katsina Update

Media Forum Katsina Update Mediar 'Yan'uwa almajiran Sayyid Ibraheem Zakzaky (H), Katsina.

TARON WA'AZIN GORON SALLAH A GARIN KATSINA Ƴan'uwa Musulmi Almajiran Shaikh Zakzaky (H), na Da'irar Katsina sun gudanar ...
27/05/2026

TARON WA'AZIN GORON SALLAH A GARIN KATSINA

Ƴan'uwa Musulmi Almajiran Shaikh Zakzaky (H), na Da'irar Katsina sun gudanar da Taron Wa'azin Goron Sallah kamar yadda aka saba duk shekara.

A yau ma, 10/Zulhajji/1447, Wanda yayi dai-dai da 27/5/2026, an gudanar da Taron Wa'azin Goron Sallar a filin ATC dake cikin garin Katsina.

Sheikh Yaƙub Yahya Katsina ne ya gabatar da jawabi a muhallin taron.

A cikin jawabinsa, Sheikh Yaƙub Yahya ya bayyana yanda al'ummar Musulmi ke ta ƙoƙarin haɗe kansu inda yake cewa; “Lallai yanzu al'umma sun fara shiga hayyacinsu irin yanda suke ta ƙoƙarin haɗe kansu waje ɗaya don tunkarar Zalunci, tun lokacin da aka fara yaƙin Iran da Americ@ da Isra'il@, lallai Musulmi sun fara gane mafitarsu ita ce haɗe kai”.

Sannan ya cigaba da magana akan muhimmancin haɗin kai, inda yake cewa; “Lallai haɗin kai shine babban matakin kowacce nasara, sannan koyarwar Manzon Allah (s a w), itace sahihiyar hanya, kuma wasu abubuwan da akeyi duk babu su a koyarwar Annabi (s a w) da Sahabbansa, har Khalifofinsa ma basuyi abinda akeyi yanzu ba”.

Daga ƙarshe ya kawo yanda matsalolin tsaro da taɓarɓarewar ƙasa ke ƙaruwa inda yake cewa; “Lallai akwai hanyoyin kawo ƙarshen wannan matsalar rashin tsaron da taɓarɓarewar ƙasar shine jihadi saboda Allah, al'umma su san wanene maƙiyinsu, sannan su tashi su kauda Zaluncin Azzalumai, kamar yadda su Malam (H) s**a sha faɗa, tabbatar da Adalci wajibi ne, ta hanyar karantarwar gidan Manzon Allah (s a w), wannan shine mafita”.

Bayan kammala jawabin, Sheikh Yaƙub Yahya, yayi addu'a, sannan aka sallami ƴan'uwa.

#عيدالاضحي






1447/2026

*GORON SALLAH! GORON SALLAH!! GORON SALLAH!!!*Yan'uwa musulmi Almajiran Sayyid Ibrahim Yakubu Zakzaky H na Da'irar Katsi...
26/05/2026

*GORON SALLAH! GORON SALLAH!! GORON SALLAH!!!*

Yan'uwa musulmi Almajiran Sayyid Ibrahim Yakubu Zakzaky H na Da'irar Katsina na gayyatar Daukacin al'ummar musulmi zuwa wajen wa'azin Goron Sallah Babba (idil Kabir), Wanda za a gudanar kamar haka:

RANA: Gobe Laraba 10/12/1447 daidai da 27/05/2026

LOKACI: Karfe 4 da rabi na yamma

WURI: Filin Atc Kofar kwaya Katsina

Da fatan za a kiyaye lokaci tare taya mu yada wannan sanarwar ga sauran yan'uwa.

Muna fatan Allah ya karbi Ibadunmu a wannan rana ta Arafat.

Sanarwa daga Da'irar Katsina

update

MAULUDIN IMAM RIDHA (AS) NA GAMAYYAR ISLAMIYYUN SARIYYAR IMAM ALI ZAINUL ABIDIN A KATSINA.A daren ranar Litinin 1 ga wat...
18/05/2026

MAULUDIN IMAM RIDHA (AS) NA GAMAYYAR ISLAMIYYUN SARIYYAR IMAM ALI ZAINUL ABIDIN A KATSINA.

A daren ranar Litinin 1 ga watan Zul-Hajji, 1447H, wanda ya yi daidai da 18 ga watan Mayu, 2026M, an gudanar da taron Mauludin Imam Ridha (AS) na gamayyar Islamiyyun da suke ƙarƙashin Sariyyatul Imam Ali Zainul Abidin a Katsina.

An fara taron da buɗe shi da addu’a tare da gabatar da karatun Alƙur’ani mai girma, sannan aka ci gaba da waƙoƙin yabo ga Ahlul-Baiti (AS), cikin yanayi na farin ciki da girmamawa ga wannan munasaba mai albarka.

Daga bisani, Malam Bishir MB ya gabatar da makasudin wannan taro, inda ya bayyana cewa haɗuwar tasu ba wai taro na al’ada kawai ba ne, illa wata hanya ce ta raya al’amuran Ahlul-Baiti (AS) da kuma tabbatar da cewa ƙaunar iyalan Manzon Allah (SAWW) tana nan a zukatan al’umma. Ya bayyana cewa tunawa da rayuwar Imamai na daga cikin hanyoyin ilmantar da matasa da ƙarfafa su wajen koyi da halaye da dabi’un bayin Allah na gari. Haka kuma ya jaddada cewa irin waɗannan taruka suna taimakawa wajen haɗa zukata da ƙarfafa zumunci tsakanin ɗalibai da malamai.

Bayan haka, aka gabatar da mai gabatarwa wanda ya kasance Malam Yaqoub Idris Katsina. Kafin gabatar da babban mai jawabi kuwa, ɗalibai daga Islamiyyu daban-daban sun gabatar da muƙalu masu ɗauke da bayanai kan rayuwar Imam Ridha (AS).

Madarasatul Tahrikul Islam, ta bakin Malam Hussaini Tasi’u, ta gabatar da muƙala kan haihuwar Imam Ridha (AS), inda ya yi bayani kan asalin haihuwar Imam ɗin da irin yanayin gidan da ya tashi, yana mai bayyana cewa tun daga ƙuruciyarsa ya kasance cikin ilimi, tarbiyya da ibada.

Sai Madarasatul Irshadun Islam, ta bakin Malama Fatima Bishir, wacce ta gabatar da muƙala kan ilimin Imam Ridha (AS). Ta bayyana yadda Imam Ridha ya kasance mashahuri wajen ilimi da hikima, inda malamai da masu neman ilimi daga wurare daban-daban suke zuwa domin amfana daga iliminsa da fahimtarsa.

Haka kuma Madarasatul Azzahara Gidan Kaji, ta bakin Malama Khadijah Sani, ta yi bayani kan ibadar Imam Ridha (AS), inda ta kawo yadda Imam ɗin ya kasance mai yawaita bautar Allah, haƙuri da tawakkali, duk kuwa da irin ƙalubalen da ya fuskanta a rayuwarsa.

A nata ɓangaren, Madarasatul Rasulul Akram, ta bakin Malama Khadijah Zunaidu, ta gabatar da muƙala kan mu’ujizozin Imam Ridha (AS), inda ta yi bayanin wasu daga cikin abubuwan mamaki da hikimomi da s**a bayyana a rayuwarsa, waɗanda s**a nuna matsayinsa da kusancinsa ga Allah (SWT).

Daga bisani, babban mai jawabi ya fara da miƙa godiya ga Allah (SWT) bisa damar da Ya bayar na halartar wannan taro mai albarka domin raya munasabar Ahlul-Baiti (AS). Bayan haka ya tsunduma cikin jawabi mai zurfi kan rayuwar Imam Ridha (AS), inda ya bayyana cewa Imam Ridha ya kasance fitila ce ta ilimi, haƙuri da jagoranci a cikin al’umma.

Malamin ya yi bayani kan yadda Imam Ridha (AS) ya rayu a wani lokaci mai cike da ƙalubale da matsin lamba daga mahukunta, amma duk da haka bai gushe ba wajen kare addini da koyar da gaskiya. Ya bayyana cewa Imam Ridha ya yi amfani da hikima, ilimi da kyakkyawar mu’amala wajen jawo zukatan mutane zuwa ga tafarkin Allah.

Ya ƙara da cewa rayuwar Imam Ridha (AS) tana ɗauke da darussa masu yawa ga matasa, musamman ta fuskar neman ilimi, haƙuri a lokacin jarabawa da kuma tsayuwa kan gaskiya ba tare da tsoro ba. Ya jaddada cewa Ahlul-Baiti (AS) ba tarihi kawai ba ne, su makaranta ce ta tarbiyya da gyaran rayuwa.

Haka kuma malamin ya yi kira ga ɗalibai da matasa da su ƙara himma wajen neman ilimi da raya addini, tare da riƙo da halayen Imam Ridha (AS) na tawali’u, karamci da tausayi ga jama’a. Ya bayyana cewa al’umma ba za ta gyaru ba sai ta koma ga koyarwar Alƙur’ani da tafarkin Ahlul-Baiti (AS).

Daga ƙarshe, an rufe taron da addu’a, inda aka roƙi Allah Ya ƙara haɗa zukatan muminai, Ya ba su ikon koyi da Ahlul-Baiti (AS), tare da neman albarka da kariya ga al’umma baki ɗaya.

Media Forum Katsina Update
__ Litinin: 18/Mayu/2026M.

11/05/2026

Addu'ar Sheikh Yaƙub Yahya Katsina akan duk masu amsar kuɗaɗe da sunan Harka ko wata Mu'assasa a cikin Harkar Musulunci Ƙarƙashin Jagorancin Shaikh Zakzaky (H).



Media Forum Katsina Update
11/05/2026

MAULUDIN IMAM ALIYU AR-RIDHA (A.S)Ɗaliban Fudiyya waɗanda s**a kammala karatunsu a Shekarar 2011 (FOSA CLASS OF 2011), s...
09/05/2026

MAULUDIN IMAM ALIYU AR-RIDHA (A.S)

Ɗaliban Fudiyya waɗanda s**a kammala karatunsu a Shekarar 2011 (FOSA CLASS OF 2011), sun shirya gagarumin Mauludin Imam Aliyu Ar-ridha (a.s) a yau Asabar 09/05/2026, a Markazu Ahlul-baity dake cikin garin Katsina.

Bayan buɗe taro da addu'a, Karatun Alqur'ani,waƙe, sai maƙasudin wannan program, bayan nan kuma sai aka gabatar da paper presentation, wadda aka tsakuro tarihin Imam Ridha (a s) a taƙaice, tun daga Haihuwarsa har zuwa Shahadarsa. Daga nan sai jawabi.

Malam Abubakar Maje ne ya gabatar da jawabi a muhallin, in da ya bayyana wasu daga cikin karamomi da darajoji na Imam Ridha (a s), inda yake cewa; “Imam Ridha (a s) bai taɓa yin kaki (zubar da yawu) ya zubar a wajen wani ba, saboda tsabar jin nauyin mutane, sannan Allah ya yarje masa duk wanda yayi tawassul dashi to zai ga Ijaba”.

Sannan ya cigaba da cewa; “Yazo a ruwaya akwai lokacin da aka shiga matsalar ruwa, aka kira Imam Ridha (a s) da niyyar a ƙure shi, ana masa magana cikin isgili ana cewa idan kai jikan Annabi (s a w) ne muna son ka samar mana da ruwa a wajen nan (Bisa dutse) cikin yardar Allah kuma yana ɗan ƙwanƙwasawa da dutse sai ga ruwa ya ɓulɓulo kuma ana amfani dashi har yanzu”.

Harwala yau, ya cigaba da cewa; “Allah ya bashi Mu'ujizoji daban-daban, duk da ya gamu da jarabawoyi kala-kala daga Sarakunan zamaninsa”.

Bayan kammala jawabin anyi tambayoyi da Amso shi akan jawabin da Malamin yayi, tare da bada kyautuka, tare da raba kyautar katin waya.

Daga ƙarshe an yanka Cake, sai akayi addu'a aka sallami ƴan'uwa.




09/05/2026

ADDU'AR CIKA KWANAKI ARBA'IN (40) DA RASUWAR MARHUM MALAM SANI LAWAL FUDIYYA.Ƴan'uwa Musulmi Almajiran Shaikh Zakzaky (H...
08/05/2026

ADDU'AR CIKA KWANAKI ARBA'IN (40) DA RASUWAR MARHUM MALAM SANI LAWAL FUDIYYA.

Ƴan'uwa Musulmi Almajiran Shaikh Zakzaky (H), na Da'irar Katsina sun haɗu domin yin addu'o'i na musamman na cikar kwanaki Arba'in (40), da Rasuwar Marhum Malam Sani Lawal Fudiyyah.

A yau Juma'a 8/5/2026, ne ya cika kwanaki Arba'in (40), da Rasuwa, yanzu haka ana cigaba da addu'o'i na musamman zuwa gareshi.

Daga cikin addu'o'in akwai irin su Yasin, Safkar Alqur'ani wanda Huffaz s**ayi, tare da sauran wasu ba'adin Addu'o'i.

Bayan kammala addu'o'in, Sheikh Yaƙub Yahya, Sheikh Abdulhamid Bello tare da Prof. Abdullahi Ɗanladi sun ƙara da wasu addu'o'in.

Sheikh Yaƙub Yahya Katsina ya nuna alhini da jimamin rashin Malam Sani a matsayin babban rashi a cikin ƴan'uwa, inda yake cewa; “Lallai munyi babban rashi mai wuyar cikewa, domin Malam Sani mutum ne na daban, mai ɗaukar abubuwa da daman gaske a kansa”.

Muna addu'ar Allah ya sabunta Rahama gareshi Alfarmar Sayyeda Zahra (s a).



08/05/2026

SANARWA......Sisters And Academic Fora Niger/Katsina suna sanar da yan uwa maza da mata cewa za su gabatar da mu'utamar ...
07/05/2026

SANARWA......

Sisters And Academic Fora Niger/Katsina suna sanar da yan uwa maza da mata cewa za su gabatar da mu'utamar na wuni a ukku a Niger, a garin Tchaduwa da ke Niger.

Take taro: Kwakwkwafa tunanin yan uwa kan halin da harka take ciki.

Za a shiga taron ranar Alhamis

Akwai manyan Malamai da Masana daga ɓangarori daban-daban da za su gabatar da jawabi wajen taron.

Za a rufe taron da jawabin Jagora Sayyid Zakzaky (H).

Du 14 au 16 Mai 2026
Lieu: Tchaduwa (Republique du Niger)

Za a yi Rijistar Naira 1,500 Ƙuɗin Nigeria, Dala 100 Ƙudin Niger.

Sanarwa:
Sisters and Academic Fora Niger/Katsina

AN SAMU CANJIN LOKACIN ADDU'AR CIKA KWANAKI ARBA'IN (40) TA MARHUM MALAM SANI LAWAL FUDIYYA.Ana sanar da Ƴan'uwa na Da'i...
07/05/2026

AN SAMU CANJIN LOKACIN ADDU'AR CIKA KWANAKI ARBA'IN (40) TA MARHUM MALAM SANI LAWAL FUDIYYA.

Ana sanar da Ƴan'uwa na Da'irar Katsina cewa akwai addu'ar cika kwanaki Arba'in (40), da Rasuwar Marhum Malam Sani Lawal Fudiyya, wanda Allah ya karɓi Rayuwarsa a ranar Lahadi 29/03/2026.

Rana; Gobe Juma'a 08/05/2026.

Lokaci: 5:00pm

Wuri: Gidanshi da ke Filin Polo Turaruka Katsina.

Ana barar addu'ar Ƴan'uwa hadiya zuwa ga ruhin shi.

📸 MediaForumKatsinaUpdate.

INNALILLAHI WA INNA ILAIHIRRAJIUN..!Allah ya yi ma Sirajo mai Asharalle rasuwa yanzu cikin daren nan, Ubangiji Allah yaj...
30/04/2026

INNALILLAHI WA INNA ILAIHIRRAJIUN..!

Allah ya yi ma Sirajo mai Asharalle rasuwa yanzu cikin daren nan, Ubangiji Allah yajiƙansa da rahma yasa aljanna ce makomar sa.

DAGA MARKAZ KATSINA: Ƴan'uwa Almajiran Shaikh Zakzaky (H) na Da'irar Katsina sun shirya taron Mauludin Imam Aliyu Arridh...
30/04/2026

DAGA MARKAZ KATSINA: Ƴan'uwa Almajiran Shaikh Zakzaky (H) na Da'irar Katsina sun shirya taron Mauludin Imam Aliyu Arridha (A.S) a yau Alhamis 30/4/2026 - 12/11/1447.

Program ɗin wanda ya samu Halartar Manyan Baƙi daga Ƙasar Iraqi, sun kawo ziyarar sannan sun albarkaci program ɗin da kalamai na ƙarfafawa akan Hadissai daga A'imma (A.S) akan falalar raya Al'amarin Ahlul baity (A.S).

Bayan shinfiɗa da Sheikh Yaƙub Yahya Katsina yayi tare da nuna godiyarsa ga Allah da kuma ƴan'uwa akan addu'o'in su akan neman Lafiya da ya je, sannan ya gabatar da manyan baƙin sai s**a fara jawabi.

Da yake jawabi, ɗaya daga cikin Manyan baƙin ya bayyana jin daɗinsa da wannan ziyarar inda yake cewa; “Munyi murna matuƙa da ganin waɗannan kyawawan fuskokin naku, babban abin godiya ne gareku da Allah ya sanya ku cikin mabiya Ahlul baity (A.S), kamar yadda yazo a cikin Hadith cewa; “Allah yayi Rahama ga duk wanda ya Raya Al'amarinmu”.

Sannan ya cigaba da cewa; “Wanda duk ya Mutu da Soyayyarmu (Iyalan Annabi (S.A.W) ya Mutu Shahidi, kuma wanda ya Mutu da Wulayar Ahlul baity (A.S), Allah zai ɗaukaka matsayinsa”.

Bayan ya kammala nasa jawabin, Ɗayan baƙon ma yayi nasa takaitaccen jawabin, inda yake cewa; “Muna bada haƙuri bisa taƙaita kalmominmu da zamuyi, kasantuwar muna da ziyarori dayawa, lallai munji daɗin ganinku, kuma muna tayaku murna kasancewarku cikin Masoya Ahlul baity (A.S)”.

Bayan kammala jawaban su, sun bada kyautar Tuta daga Haramin Imam Husaini (A.S), tare da Hirzozi, Sheikh Yakub Yahya Katsina yayi godiya da nuna jin daɗinsa da wannan ziyara, daga nan kuma ya cigaba da jawabinsa akan munasabar Haihuwar Imam Aliyu Arridha (A.S).

Bayan ya kammala, anyi addu'a aka sallami ƴan'uwa.




12/DhulQa'ada/1447
30/04/2026

Address

Kofar Marusa
Katsina

Telephone

+2348038139613

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Media Forum Katsina Update posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Media Forum Katsina Update:

Share