Katsina City News

Katsina City News Our target is to cover all the news from Dank**a to Damari

This Page is under Matasa Media Links Nigeria LTD, publisher's of Katsina Times, Online Newspaper, Katsina City News, Magazine of Events, History and Culture and Jaridar Taskar Labarai (Vanacular online newspaper)

18/10/2025

Video 📸

Ba Yanzu Aka Fara Ce mana Makiya Annabi ba ~ Prof. Sani Umar Rijiyar Lemo OON

A Tribute to My Friend, Brother, and Confidant: Dr. Aminu Shuaibu Safana (1961-2007)
18/10/2025

A Tribute to My Friend, Brother, and Confidant: Dr. Aminu Shuaibu Safana (1961-2007)

Engr. Nura KhalilOn October 17, eighteen years ago, that tragic, cold morning on the floor of the National Assembly, the....

Hedkwatar Tsaro Ta Karyata Jita-jitar Yunkurin Juyin Mulki, Ta Bayyana Dalilin Soke Bikin Cika Shekaru 65 Da Ƙasar Najer...
18/10/2025

Hedkwatar Tsaro Ta Karyata Jita-jitar Yunkurin Juyin Mulki, Ta Bayyana Dalilin Soke Bikin Cika Shekaru 65 Da Ƙasar Najeriya Ta Samu ’Yanci

Katsina Times

Hedkwatar Tsaron Ƙasa (DHQ) ta musanta wani rahoton da wani shafin intanet ya wallafa, wanda ke ikirarin cewa soke bikin cika shekaru 65 da Najeriya ta samu ’yanci yana da nasaba da wani yunkurin juyin mulki.

A cikin wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labaran Tsaro, Birgediya Janar Tukur Gusau, ya fitar a ranar Asabar, 18 ga Oktoba, 2025, DHQ ta bayyana rahoton a matsayin ƙarya, mai cike da mugunta da kuma nufin tada hankalin jama’a da zubar da amincewa tsakanin al’umma.

Sanarwar ta ce an soke bikin ne domin bai wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu damar halartar wani muhimmin taron haɗin gwiwa a ƙasashen waje, tare da bai wa dakarun Najeriya damar ci gaba da mayar da hankali kan yaƙi da ta’addanci, rikicin ’yan tawaye da ’yan fashi da makami a faɗin ƙasar.

DHQ ta kuma bayyana cewa k**a wasu jami’an soja 16 da ake bincike a kansu, ba shi da alaƙa da jita-jitar juyin mulki da ake yaɗawa, illa dai wani bincike ne na cikin gida da aka saba gudanarwa don tabbatar da ɗa’a da ƙwarewa a cikin rundunar soja. Ta ce an kafa kwamitin bincike kuma za a bayyana sak**akonsa bayan kammala aiki.

“Hedkwatar Tsaron Ƙasa tana nan daram bisa biyayya ga Kundin Tsarin Mulkin Ƙasa da kuma gwamnatin tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙasa kuma Babban Kwamandan Rundunar Sojin Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, GCFR,” in ji sanarwar.

DHQ ta roƙi ’yan Najeriya da su yi watsi da rahoton ƙarya, tare da ci gaba da ba da goyon baya ga jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya, ci gaba, da haɗin kai a cikin ƙasa.

Hedkwatar Tsaro, Abuja

DHQ Dismisses Coup Allegation, Clarifies Independence Day Parade Cancellation
18/10/2025

DHQ Dismisses Coup Allegation, Clarifies Independence Day Parade Cancellation

The Defence Headquarters (DHQ) has debunked an online report alleging that the cancellation of activities marking Nigeria’s 65th Independence Anniversary....

Mazauna Karamar Hukumar Safana Karkashin Jagorancin Hon. Ahmad Dayyabu Safana Sun Shirya Taron Godiya Ga Gwamna RaddaDag...
18/10/2025

Mazauna Karamar Hukumar Safana Karkashin Jagorancin Hon. Ahmad Dayyabu Safana Sun Shirya Taron Godiya Ga Gwamna Radda

Daga:- Muhammad Ali Hafizy. Katsina Times. 18 Oktoba 2025.

Tsohon ɗan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Batsari, Safana da Ɗan Musa Hon. Ahmad Dayyabu Safana ya shirya taron godiya ga Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda PhD game da ayyukan alkairin da yake yi ma kananan hukumomin da kuma jihar Katsina baki daya.

Taron ya gudana a ranar Asabar 18 ga watan Oktoba 2025, a dakin taro na Munaj dake cikin garin Katsina, ya kuma samu halartar Mataimakin shugaban Jam'iyyar APC na jihar Katsina Hon. Bala Abu Musawa, Mashawarci na musamman ga Gwamna Radda akan kananan hukumomi Hon. Alhaji Lawal Rufa'i Safana, Sakataren jam'iyar APC na jihar Barr. Suleman Namadi. Da kuma 'ya'yan jam'iyar APC na kananan hukumomin.

Taron an shirya shi ne domin sada zumunci, tare da godiya ga Gwamna Radda akan ayyukan cigaba da yake yi ma kananan hukumomin Safana da Batsari da kuma Ɗan Musa da kuma jihar Katsina baki daya.

Hon. Bala Abu Musawa mataimakin shugaban Jam'iyyar APC na jihar Katsina, a nashi jawabin ya yi jinjina ta musamman ga tsohon dan majalisar a Irin ayyukan alkairin da yake yi ma kananan hukumomin, ya kuma yaba mashi a irin kokarin da ya yi na shirya taron, tare da bayyana shi a matsayin wani jigo na jam'iyar a kanana hukumomin musamman karamar hukumar Safana.

Ya kara da yabawa ga Gwamna Radda game da kokarin da yake yi musamman ta fannin tsaro, a jihar "Muna godiya ga Gwamna Radda akan ayyukan alkairin da yake yi ma jihar Katsina musamman ta fannin tsaro" inji shi.

Alhaji Bala Abu Musawa ya kuma shawarci tsohon dan majalisar da ya kara kokari wajen hada kan yayan jam'iyyar domin ciyar da jam'iyar gaba, da kuma samun nasarar jam'iyar a zabe mai zuwa. "Ina kira da Alhaji Ahmed Dayyabu Safana da ayi hakuri da juna, ayi hakuri da sauran masu muk**ai wadanda suke cikin jam'iyyar APC, a hadu ayi aiki tare domin samun nasarar jam'iyar a karamar hukumar" inji shi.

Mashawarci na musamman ga Gwamna Radda ga al'amarin kananan hukumomin. Hon. Alhaji Lawal Rufa'i Safana ya yi jinjina ta musamman ga tsohon dan majalisar, ya kuma yaba da irin ayyukan da yake ma al'ummar duk da bai da mukami a tare dashi, sannan kuma ya shawarci tsohon dan majalisar da ya yi hakuri a matsayin shi na jigo a karamar hukumar, a hadu ayi aiki tare domin cigaban jam'iyar APC a matakin karamar hukumar da kuma jiha.

Court Orders Man to Pay DSS N5m For Frivolous Human Rights Suit
18/10/2025

Court Orders Man to Pay DSS N5m For Frivolous Human Rights Suit

A High Court of the Federal Capital Territory (FCT) has ordered one Sunday Dominic to pay the Department of State....

Daily Times Front Page (June 22, 1966): “Boro Sentenced to Death” — The Story of a Revolutionary’s Trial and Legacy
18/10/2025

Daily Times Front Page (June 22, 1966): “Boro Sentenced to Death” — The Story of a Revolutionary’s Trial and Legacy

How Isaac Adaka Boro’s conviction marked a pivotal moment in Nigeria’s early post-independence struggle for justice and minority rightsThe Headline....

Governor Radda Hails Cross River’s Bassey Otu at 66
18/10/2025

Governor Radda Hails Cross River’s Bassey Otu at 66

Katsina State Governor, Malam Dikko Umaru Radda, has congratulated his Cross River State counterpart, Prince Bassey Edet Otu, on his....

Renewed Hope Initiative Empowering Youth, Women Across Nigeria — Northern Coordinator
18/10/2025

Renewed Hope Initiative Empowering Youth, Women Across Nigeria — Northern Coordinator

The Renewed Hope programme of President Bola Ahmed Tinubu’s administration has recorded significant success in improving the welfare of Nigerians,....

Shirin Renewed Hope na Tinubu na Taimaka wa Matasa da Mata a Fadin Kasa — Shugaban Yankin Arewa maso YammaShirin Renewed...
18/10/2025

Shirin Renewed Hope na Tinubu na Taimaka wa Matasa da Mata a Fadin Kasa — Shugaban Yankin Arewa maso Yamma

Shirin Renewed Hope na gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya samu gagarumar nasara wajen inganta walwalar ‘yan kasa, musamman talakawa da marasa galihu a fadin Najeriya.

Shugaban Renewed Hope Grassroot Movement na yankin Arewa maso Yamma, Alhaji Abubakar Lawal Siha Bakori, ne ya bayyana haka yayin tattaunawa da manema labarai a garin Katsina kan ayyukan kungiyar.

A cewarsa, shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bullo da shirye-shirye da dama karkashin tsarin Renewed Hope domin karfafa matasa da mata musamman na karkara, domin su zama ‘yan kasa masu amfani da dogaro da kai.

Alhaji Siha Bakori ya ce tun bayan fara aiwatar da shirin, ya kasance ginshiki wajen inganta ci gaban al’umma ta hanyar samar da guraben ayyukan yi ga matasa da mata a sassa daban-daban na kasa.

Ya bayyana cewa shirin ya kunshi tsare-tsaren tallafi da s**a hada da koyon dabarun noma, sana’o’in hannu, kasuwanci, koyon fasahar zamani, da kuma bunkasa kananan da matsakaitan masana’antu — domin bai wa matasa damar koyon kwarewar da za ta taimaka musu wajen samun ci gaba da dogaro da kai.

Shugaban ya kuma jaddada cikakken goyon bayan da Renewed Hope Grassroot Movement ke bai wa gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, a kokarinsu na bunkasa kasa da jihar Katsina baki daya.

Alhaji Siha Bakori ya yabawa Gwamna Dikko Radda bisa jajircewarsa wajen yaki da rashin tsaro a jihar ta hanyar kafa Community Security Watch, wato jami’an tsaron al’umma, domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali tsakanin jama’a.

Permanent Secretary Enitan Urges Education Ministry Directors to Lead with Discipline, Accountability, and Compassion
18/10/2025

Permanent Secretary Enitan Urges Education Ministry Directors to Lead with Discipline, Accountability, and Compassion

By Katsina Times  The Permanent Secretary of the Federal Ministry of Education, Mr. Abel Olumuyiwa Enitan, has called on Directors....

Address

No. 5 Maikudi Abdullahi Building Opposite Dan Marina Filling Station , Yahaya Madaki Way Kofar Kaura Underpass Katsina .
Katsina
820231

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina City News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katsina City News:

Share