Katsina City News

Katsina City News Our target is to cover all the news from Dankama to Damari

This Page is under Matasa Media Links Nigeria LTD, publisher's of Katsina Times, Online Newspaper, Katsina City News, Magazine of Events, History and Culture and Jaridar Taskar Labarai (Vanacular online newspaper)

NPC CHAIRMAN CALLS FOR DEDICATED BUDGET LINES FOR CRVS
31/07/2025

NPC CHAIRMAN CALLS FOR DEDICATED BUDGET LINES FOR CRVS

The Chairman of the National Population Commission (NPC), Hon. Nasir Isa Kwarra, has called for dedicated budget lines for Civil....

Madugun Adawa a Katsina, tsohon Sakataren Gwamnati, tsohon Dantakarar Gwamna Mustapha Inuwa ya fice daga PDP a Hukumance
31/07/2025

Madugun Adawa a Katsina, tsohon Sakataren Gwamnati, tsohon Dantakarar Gwamna Mustapha Inuwa ya fice daga PDP a Hukumance

Katsina Gov. Condemns Fresh Bandit Attack in Dutsinma, Vows to Strengthen Security Measures
31/07/2025

Katsina Gov. Condemns Fresh Bandit Attack in Dutsinma, Vows to Strengthen Security Measures

By Tayyibat Ummi Yakub | Katsina Times Thursday, July 31, 2025The Katsina State Government has strongly condemned a fresh attack....

‎Kungiyar "Good Governance Club" Ta Ziyarci Hukumar KASSROMA, Ta Kuma Jaddada Ƙudurinta Na Saya Wa Gwamna Radda Tikitin ...
31/07/2025

‎Kungiyar "Good Governance Club" Ta Ziyarci Hukumar KASSROMA, Ta Kuma Jaddada Ƙudurinta Na Saya Wa Gwamna Radda Tikitin Tsayawa Takara a Zaben 2027.

‎Daga Muhammad Ali Hafizy, Katsina Times.

‎Kungiyar Good Governance Club wadda take rajin tabbatar da shugabanci na gaskiya, a karkashin jagorancin shugaban kungiyar, Comrd Shehu Usman Yusuf Kofar Soro, ta ziyarci shugaban hukumar kula da kuma gyara hanyoyi ta jihar Katsina. Engr. Surajo Yazid Abukur, tare da karrama shi da lambar yabo a matsayin wanda ya samar da cigaba a cikin al'umma.

‎Ziyarar wadda ta gudana a ranar Alhamis 31 ga watan Yuli na shekarar 2025, a shelkwatar hukumar dake Katsina, ta samu jagorancin kungiyar Good Governance Club, tare da rakiyar wasu wakilai daga cikin kungiyoyin al'umma.

‎Comrd Shehu Kofar Soro a jawabin da ya gabatar yayin ziyarar, ya jaddada kudurin kungiyar da yake jagoranta na zama ƙungiya ta farko da tayi yunkuri tare da shelanta cewa zata saya ma gwamna Radda tikitin tsayawa takarar gwamnan jihar Katsina a zabe mai zuwa na 2027.

‎"Gwamna Radda, gwamna ne na al'umma, kuma cigaban da ya kawo wa jihar Katsina ba karami bane, shiyasa wannan kungiyar ta Good Governance Club taga dacewa ta saya mashi tikitin tsayawa takara a zabe mai zuwa na 2027, domin ya ci gaba da ayyukan alkairin da yake yi wajen samar wa jihar Katsina ci-gaba mai ɗorewa" inji shi.

‎Ya kara da cewa "Hukumar KASROMA a jihar Katsina, ta samu kyakkyawan sauyi ta dalilin samun jagoranci na gari a karkashin shugaban hukumar Engr Surajo Yazid Abukur" ya ce, Hukumar ta samar wa al'ummar jihar Katsina hanyoyi masu kyau tare da tabbatar da kiyaye abubuwan da suke sanya aukuwar hadari a kan tituna. Inji shi.

‎Shugaban hukumar KASSROMA ta jihar Katsina, Engr Surajo Yazid Abukur. Ya yi jinjina ta musamman ga kungiyar, tare da tabbatar masu da cewa zai kasance a tare da su, da kuma tabbatar da cigaba jihar Katsina a karkashin jagorancin gwamna Malam Dikko Umar Radda.

‎Ya kara da cewa, Shugabancin Malam Dikko Umar Radda shugabanci ne na gari, kuma shugabanci ne wanda za'a yi fatan dorewar shi, ya yi godiya ga kungiyar akan yunkurin da s**a yi na saya wa gwamna tikitin tsayawa takara a 2027.

‎"Ayyukan da hukumar KASSROMA ke gabatarwa, ayyuka ne wanda gwamna Radda ya bada umarnin aiwatar dasu, kuma gwamna ya h**e mu da mu cigaba da sauran koken al'umma da kuma tabbatar da cewa munyi masu abinda ya dace" inji shi.

31/07/2025

Video: Cikakken Jawabin Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Katsina Dakta Nasiru Mu'azu Danmusa, ga al'ummar jihar Katsina game da halin tsaro da ake ciki a jihar.

Al-Qalam University Commissions New Medical College with Support from ARS Initiative Africa
31/07/2025

Al-Qalam University Commissions New Medical College with Support from ARS Initiative Africa

Al-Qalam University, Katsina, has officially commissioned its new College of Medical and Allied Health Sciences, a milestone project generously funded....

31/07/2025

Aminu Balele Dan Arewa Danmajalisar Tarayya, ya Kai koken mutanan Kurfi da Dutsan-ma a Majalisa

Of Fraudsters, Illeterates And Jingoists
31/07/2025

Of Fraudsters, Illeterates And Jingoists

.By Abdu Labaran Malumfashi.                  31-7-2025.Nigeria is a country unfortunately ‘blessed’ with lots....

Tsohon Ma’aikacin Gwamnati Ya Koka Kan Jinkirin Biyan Gratuity Tun Shekarar 2020Daga Katsina TimeKabir Ahmed A/Kuka, tso...
31/07/2025

Tsohon Ma’aikacin Gwamnati Ya Koka Kan Jinkirin Biyan Gratuity Tun Shekarar 2020

Daga Katsina Time

Kabir Ahmed A/Kuka, tsohon ma’aikacin gwamnati da ya yi ritaya a jihar Katsina tun daga shekarar 2020, ya bayyana damuwarsa kan yadda har yanzu ba a biya shi haƙƙinsa na Gratuity ba, duk da cika shekaru fiye da huɗu zuwa biyar da ya ajiye aiki.

A cikin wani dogon rubutu da yayi a shafukan yanar gizo ta zamani, Kabir ya bayyana cewa an fara tantance shi a lokacin tsohon gwamna Masari, amma daga baya da ya sake zuwa don tantanceshi a ƙarƙashin wannan sabuwar gwamnati ta Dikko Umar Radda, sai ya samu an yi kuskuren cire sunansa daga jerin waɗanda za a sake dubawa. Wannan kuwa ya jefa shi cikin yanayin damuwa da rashin tabbas tare da sauran abokan aikinsa na gwamnati da s**a tsinci kansu a irin wannan hali na tsallake sunayen su.

“Gaskiya ban so in yi magana ba, amma halin da muke ciki ya tilasta. Na ajiye aiki tun 2020, kuma bayan dogon jira da nayi don a biya ni Gratuity na, sai ga shi an cire sunana daga jerin waɗanda za a sake tantancewa a lokacin da wannan gwamnati ta nemi yin hakan a garon farko. Tun wancan lokaci muka shiga cikin zullumi da rashin tabbas, kullum cikin rashin barci da damuwa muke tare da iyalanmu,” in ji shi.

Kabir yayi hasashen cewa, akwai yuwuwar su daga cikin waɗanda wannan matsala ta shafa da s**a kamu da rashin lafiya, wasu kuwa ƙila sun rasu tun bayan sake tantancewar da aka yi masu watanni uku zuwa huɗu da s**a gabata. Ya kuma bayyana cewa akwai rahotannin da ke cewa Gwamna Dikko Umar Radda ya amince da biyan kuɗin, kuma an ce an fitar da su, amma har zuwa 30 ga Yuli da 2025 da yayi wannan rubutu babu wata alama ko sahihiyar sanarwa da ke nuna hakan.

“In har maigirma Gwamna ya bayar da izinin biyan kuɗin, me ke janyo jinkirin fiye da watanni uku ko huɗu? Ina ne kuɗin s**a makale? Me ke hana a biya?” in ji Kabir cikin damuwa.

Ya kuma nuna damuwa akan yadda kwamitin da ke kula da biyan kuɗaɗen akan rashin yi masu bayanin halin da ake ciki musamman ganin cewa akwai wakilan tsoffin ma’aikata a cikinsu, wanda ya nuna cewa tamkar ana ƙoƙarin sake jefa su cikin wani sabon yanayin ko neman wasu sabbin takardu daga iyalan su bayan su sun bar duniyar wanda hakan zai zamo ƙara bata wani lokacin.

“Shin sai an rika tura mu cikin rami ɗaya bayan ɗaya sannan a biya iyalanmu haƙƙinmu?

A ƙarshe, Kabir ya roƙi Gwamna da kuma masu kusanci da shi da su fahimci halin da wasu daga cikin al’ummar jihar ke ciki, musamman su tsaffin ma'aikata tare da ɗaukar matakin gaggawa domin ganin an biya waɗanda s**a ajiye aikin haƙƙinsu.

“Duk wanda ke cikin wannan aikin, ya sani cewa wata rana shima zai tsinci kansa a irin wannan hali. Su ma wadanda s**a ajiye din su tuna kafin a biya su sai da s**a fuskanci 'yar matsala koda kuwa cikin kwana 3 da ajiye aikin su aka biya su. Ina roƙon Gwamna da duk wani mai ruwa da tsaki acikin batun da a duba wannan lamari da idon rahama,” in ji Kabir Ahmed A/Kuka.

Al’ummar Mani da Dutsi Sun Nemi Gwamnatin Katsina Ta Taimaka Ta Gyaran Hanyar Da Ta Hade SuDaga Katsina TimesAl’ummar ka...
31/07/2025

Al’ummar Mani da Dutsi Sun Nemi Gwamnatin Katsina Ta Taimaka Ta Gyaran Hanyar Da Ta Hade Su

Daga Katsina Times

Al’ummar karamar hukumar Mani da Dutsi a Jihar Katsina sun yi kira ga Gwamnatin Jihar Katsina karkashin jagorancin Gwamna Malam Dikko Umaru Radda da ta gaggauta gyaran hanyar da ta hade karamar hukumar Mani da ta Dutsi, wadda s**a ce ta lalace matuka kuma tana zama barazana ga lafiyar jama’a da dukiyoyinsu.

Wannan kiran na zuwa ne ta bakin wani dan yankin, Ibrahim Abdurrahman, wanda ya bayyana cewa hanyar na da matukar muhimmanci ga zirga-zirgar al’umma, kasuwanci da samun kula ta lafiya, musamman ga mata masu juna biyu da marasa lafiya da ke bukatar gaggawar zuwa asibiti.

A cewarsa, "Wannan hanya ta kasance hanyar rayuwa ga dubban jama'a da ke amfani da ita domin zuwa kasuwanni, asibitoci da makarantu. Amma yanzu ta koma hanyar hadari wadda ke barazana ga lafiyar al’umma."

Ya ce lalacewar hanyar na janyo manyan matsaloli da s**a hada da faduwar motoci, karancin sufuri, da kuma karancin samun agaji cikin gaggawa ga marasa lafiya. Ya bukaci Gwamnati da ta duba wannan matsala da idon rahama, tare da daukar matakin gyara cikin gaggawa.

Al’ummar yankin sun bayyana cewa akwai garuruwa da dama da ke cin gajiyar wannan hanya, ko da yake ba kan hanyar kai tsaye suke ba, amma suna amfani da ita wajen gudanar da harkokinsu na yau da kullum.

Sun bayyana cewa gyaran wannan hanya zai taimaka matuka wajen bunkasa tattalin arziki da walwalar al’umma a wannan yanki.

A karshe, sun roki gwamnatin jihar da ta dauki wannan bukata da muhimmanci, domin hakan zai kara faranta ran jama’a da kuma karfafa musu gwiwa wajen ci gaba da goyon bayan gwamnatin da ke ci gaba da aiwatar da manufofinta a fadin jihar.

Katsina govt moves to heal wounds of Insecurity with direct relief to victims
31/07/2025

Katsina govt moves to heal wounds of Insecurity with direct relief to victims

By Fauziyya Lawal, Katsina The Katsina State Government has once again extended a hand of support to victims of banditry in....

31/07/2025

Ministan Kasafin Kuɗi da Tsare-tsare, Atiku Bagudu, ya yi bayani kan yadda muhimman tsare-tsare da gwamnati ta kawo za suci gaba da inganta cigaban ƙasa.

Address

No. 5 Maikudi Abdullahi Building Opposite Dan Marina Filling Station , Yahaya Madaki Way Kofar Kaura Underpass Katsina .
Katsina
820231

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina City News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katsina City News:

Share