04/05/2026
Kudin Shiga Na Jihar Katsina Ya Koma Naira Biliyan Huɗu Daga Naira Miliyan 400 – Gwamna Radda
A ranar Litinin 4 ga Mayun 2026, Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, ya bayyana hakan lokacin da ya karɓi baƙuncin mambobin Revenue Mobilization Allocation and Fiscal Commission (RMAFC) a wata ziyarar aiki da s**a kawo mashi a gidan gwamnatin jihar Katsina.
Tawagar wadda Kwamishinan Tarayya mai wakiltar Jihar Plateau, Sa’ad Bello Ibrahim, ya jagoranta, ta bayyana cewa ziyarar na da nufin tattara muhimman bayanai daga jihohi domin tallafawa aikin hukumar na sake duba da tantance tsarin rabon kuɗaɗen shiga na ƙasa.
Ya bayyana cewa wannan aikin na cikin shirin Gwamnatin Tarayya na yin cikakken bitar tsarin rabon kuɗi tsakanin Gwamnatin Tarayya, jihohi da ƙananan hukumomi, Wannan bita, wadda doka ta tanada a riƙa yi duk bayan shekaru biyar amma ta dade ba a gudanar da ita ba, na da nufin tabbatar da cewa rabon arzikin ƙasa ya kasance cikin adalci da daidaito bisa buƙatun zamani.
A cewar sa, sake fasalin tsarin zai taimaka wajen ƙara ƙarfin kuɗi da ikon gudanarwa ga jihohi da ƙananan hukumomi, tare da rage dogaro da Gwamnatin Tarayya. Hakan kuma zai ba da damar rarraba kuɗaɗen shiga bisa gaskiya, la’akari da yawan jama’a, matakin ci gaba, da bukatun kowace jiha.
Ya ƙara da cewa bayanan da ake tattarawa daga irin wannan ziyara za su taka muhimmiyar rawa wajen samar da sabon tsarin rabon kuɗi da zai dace da halin tattalin arzikin ƙasar nan a yanzu.
A yayin ziyarar, mambobin tawagar sun haɗa da Kwamishinan Tarayya mai wakiltar Jihar Bayelsa, da kuma Kwamishinan Tarayya mai wakiltar Jihar Katsina, Kabir Mashi.
A nasa jawabin Gwamna Radda ya yaba da wannan yunƙuri, yana mai jaddada muhimmancin sake fasalin tsarin rabon kuɗi domin inganta ci gaban jihohi da ƙara ingancin hidimar gwamnati ga al’umma.
Gwamnan ya bayyana cewa kuɗin shiga na cikin gida na Jihar Katsina ya samu gagarumin ƙaruwa, inda ya tashi daga Naira miliyan 400 zuwa Naira biliyan huɗu. Ya ce wannan ci gaba ya samo asali ne daga ingantattun tsare-tsaren gwamnati na faɗaɗa hanyoyin samun kuɗaɗen shiga, ƙarfafa tsarin haraji, da kuma tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin kuɗi.
Ya kuma tabbatar wa tawagar RMAFC cikakken goyon bayan gwamnatin jihar da haɗin kai a tsawon lokacin da za su yi a Katsina domin gudanar da aikin su cikin nasara.
MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government
May 4, 2026.