Arewa Daily Updates

Arewa Daily Updates Domin Samun Sahihan Labarai nagaskiya da Ɗumiɗuminsu da s**a shafi Al'umma Da Al'amuran yau da kullum

HON A.A BASHEER FUNTUA DAN TAKARAR MAJALISAR TARAYYA MAI NEMAN WAKILTAR KANANAN HUKUMOMIN FUNTUA-DANDUME YA GWANGWAJE WA...
21/02/2026

HON A.A BASHEER FUNTUA DAN TAKARAR MAJALISAR TARAYYA MAI NEMAN WAKILTAR KANANAN HUKUMOMIN FUNTUA-DANDUME YA GWANGWAJE WANI MATASHI DA KYAUTAR KUƊI NAIRA (500,000) DOMIN DOGARO DAKAI.

Assabar 21-Febuary-2027, Hon Basheer Abdullahi (A.A Basheer Funtua), Dan takarar Majalisar Tarayya mai neman wakiltar Kananan Hukumomin Funtua da Ɗandume a zaɓen shekarar 2027, ya ci gaba da nuna jajircewarsa wajen tallafa wa matasa da ƙarfafa dogaro da kai a tsakanin al’umma.

A wannan karo, Hon. A.A Basheer Funtua ya gwangwaje wani matashi ɗan asalin Garin Mahuta ‘A’, Karamar Hukumar Ɗandume, mai suna Kabiru Sufee Mahuta (K.B), da kyautar zunzurutun kuɗi har Naira 500,000, domin tallafa masa wajen bunƙasa kasuwancinsa da ƙara masa jarin sana’a.

Wannan tallafi na daga cikin manufofin Hon. Basheer na ƙarfafa matasa su tsaya da kafafunsu ta hanyar sana’o’i da kasuwanci, tare da rage zaman banza da dogaro da wasu. Matakin ya zo ne a matsayin ƙarfafawa da nuna kulawa ga matasan da ke da himma da ƙwazo wajen neman na kansu.

Kabiru Sufee Mahuta ya bayyana matuƙar farin cikinsa bisa wannan karamci, inda shi da iyalansa da abokan arziki s**a miƙa godiya ta musamman ga Hon. A.A Basheer Funtua, tare da yi masa fatan alheri da addu’ar Allah Ya ba shi nasara a burinsa na wakiltar al’ummar Funtua da Ɗandume a Majalisar Tarayya.

Haka zalika, Alhaji Babangida Mahuta ya yi godiya ƙwarai a madadin al’ummar Garin Mahuta, yana mai bayyana wannan tallafi a matsayin abin alfahari da kuma shaida ta karamci da tausayi da Hon. Basheer ke nunawa ga al’umma, musamman marasa ƙarfi da matasa masu tasowa.

Lallai wannan aiki ya ƙara fito da halin karamci, tausayi da kishin al’umma da Hon. A.A Basheer Funtua ke da shi, tare da tabbatar da aniyarsa ta kawo ci gaba mai ma’ana ga Kananan Hukumomin Funtua da Ɗandume.



RAMADAN 03 🌙✨SAƘON BARKA DA SHAN RUWA.Daga Dan takarar Majalisar Tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Funtua/Ɗandume,H...
20/02/2026

RAMADAN 03 🌙✨
SAƘON BARKA DA SHAN RUWA.

Daga Dan takarar Majalisar Tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Funtua/Ɗandume,
Hon. A.A. Basheer Funtua.

Yana miƙa saƙon barka da shan ruwa ga daukacin al’ummar Musulmi, musamman al’ummar ƙananan hukumomin Funtua da Ɗandume, bisa nasarar kammala azumin yau cikin koshin lafiya, natsuwa da zaman lafiya.

Wannan wata mai alfarma wata ne na ibada, hakuri, tausayi da kyautatawa juna. Wata ne da muke ƙara kusantar Ubangijinmu ta hanyar azumi, salloli, addu’o’i da ayyukan alheri. Ina kira gare mu gaba ɗaya da mu ci gaba da dagewa wajen ibada, taimakon marasa galihu, da kuma ƙarfafa zumunci a tsakaninmu.

Allah Maɗaukakin Sarki Ya karɓi azuminmu da sauran ibadunmu, Ya gafarta mana kura-kuranmu, Ya yafe mana zunubanmu, Ya azurta mu da rahamarsa da albarkar wannan wata mai girma.

Yana kuma addu’ar Allah Ya tabbatar da zaman lafiya, haɗin kai da cigaba a ƙasarmu baki ɗaya, musamman a Funtua da Ɗandume.

Allah Ya maimaita mana Yasa Muna cikin waɗan da Za'a ƴanta.

Ramadan Kareem.

FUNTUA/DANDUME, THE TIME FOR MEANINGFUL AND TRANSFORMATIVE CHANGE IS NOW.The people of the Funtua/Dandume Federal Consti...
15/02/2026

FUNTUA/DANDUME, THE TIME FOR MEANINGFUL AND TRANSFORMATIVE CHANGE IS NOW.

The people of the Funtua/Dandume Federal Constituency have clearly demonstrated their collective will, their preference, and the direction in which they desire their representation to move. Through their voices and unwavering support, they have made it evident who they believe embodies their aspirations and future progress.

Leadership is most effective when it reflects the genuine mandate of the people, and once that mandate is expressed, unity becomes our greatest strength. Regardless of personal differences, it is important that we rally behind the individual chosen and supported by the majority, fostering solidarity and a shared commitment to development.

In this spirit of unity and purpose, we stand in support of Hon. A.A. Basheer Funtua, aligning ourselves with the vision and confidence that the constituency has entrusted in him. Together, with collective resolve and cooperation, we can advance the growth and prosperity of Funtua/Dandume.



KADAN DAGA GUDUNMAWAR DA HON. BASHEER ABDULLAHI (A.A BASHEER FUNTUA) YA KE BA DAWA A BANGAREN TAIMAKON AL’UMMA, MUSAMMAN...
05/02/2026

KADAN DAGA GUDUNMAWAR DA HON. BASHEER ABDULLAHI (A.A BASHEER FUNTUA) YA KE BA DAWA A BANGAREN TAIMAKON AL’UMMA, MUSAMMAN GA WAƊANDA IFTILA’IN ’YAN BINDIGA YA SHAFA.

A tsawon lokaci daban-daban, Hon. Basheer Abdullahi, wanda aka fi sani da A.A Basheer Funtua, ya kasance a sahun gaba wajen ba da gagarumar gudunmawa ta jin ƙai da tallafi ga al’umma, musamman ga mutanen da iftila’in ’yan bindiga ya rutsa da su. Wadannan mutane s**an tsinci kansu cikin mawuyacin hali, ba tare da wata mafita ko ƙarfin yin wani abu ba.

A irin waɗannan lokuta masu matuƙar wahala, Hon. A.A Basheer Funtua ya nuna kyakkyawar zuciya da tausayi ta hanyar shiga tsakani domin rage raɗaɗin da al’ummar ke fuskanta. A wasu lokuta, ya ɗauki nauyin biyan kuɗin fansa domin kubutar da waɗanda aka sace, tare da tallafa wa iyalansu ta fuskar ciyarwa da kula da buƙatunsu na yau da kullum a lokacin da suke cikin damuwa, Haka kuma, bayan fitowar waɗanda aka sace, an kula da lafiyarsu ta hanyar ɗaukar nauyin jinya da sauran buƙatun lafiya domin tabbatar da walwalarsu.

A baya-bayan nan, Hon. Basheer Abdullahi ya ɗauki nauyin fansar kimanin mutane goma (10) da ke hannun ’yan bindiga. Daga cikin waɗannan mutane akwai mata masu juna biyu, mata masu jarirai ƙanana (har da jaririn da bai wuce watanni huɗu ba), da kuma tsofaffi maza da mata. Mutanen sun fito ne daga yankuna daban-daban da s**a haɗa da Unguwar Shanu, Bakori, Bagari, da sauran Unguwanni na cikin garin Funtua, da kuma wasu bayin Allah daga Unguwar Kurami ta Bakori Local Government.

Domin samun ’yancin wadannan mutane, Hon. A.A Basheer Funtua ya kashe kuɗaɗe masu yawa da s**a kai Naira Miliyan Goma Sha Biyu (₦12,000,000), tare da bayar da sabbin babura guda biyar (5) ƙirar Boxer, domin cika sharuddan da aka gindaya wajen kubutar da su.

Wannan aiki na alheri ya ƙara nuna irin tausayawa, jajircewa da sadaukarwa da Hon. Basheer Abdullahi ke nunawa ga al’umma mabukata, maza da mata, a kowane lokaci, ba tare da neman yabo ko bayyanawa ba. Ayyukansa na jin ƙai suna kasancewa cikin natsuwa da gaskiya, domin faranta ran Allah da tallafa wa bayinSa.

Muna miƙa godiya da addu’a ga Allah Maɗaukakin Sarki, muna roƙonSa da Ya ƙara ba shi lafiya, nisan kwana da ikon ci gaba da ayyukan alheri da yake yi wa al’umma a kowane lokaci. Allah Ya saka masa da alheri, Ya kuma sa waɗannan ayyuka su zama sanadin zaman lafiya, haɗin kai da kwanciyar hankali a cikin al’umma baki ɗaya.

TAYA MURNA!Hon. Basheer Abdullahi, wanda aka fi sani da A.A. Basheer Funtua, a ranar Assabar, 31 ga Janairu, 2026, ya ha...
01/02/2026

TAYA MURNA!

Hon. Basheer Abdullahi, wanda aka fi sani da A.A. Basheer Funtua, a ranar Assabar, 31 ga Janairu, 2026, ya halarci Bikin Kammala Karatu Karo na 45 Wanda Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya ta Gudanar, inda ya kasance a matsayin ɗaya daga cikin ɗaliban da s**a kammala digirin digirgir (MSc) a fannin Kimiyyar Siyasa da Nazarin Harkokin Kasa da Kasa.

An gudanar da bikin kammala karatun ne a babban harabar jami’ar da ke Zariya, wanda ya kasance wani muhimmin mataki a tafarkin ilimi, tare da nuna sakamakon shekaru na jajircewa, ladabi, da kwazo a harkar ilimi.

Nasarar kammala wannan karatun na digirin digirgir ta Hon. Basheer Abdullahi na kara tabbatar da jajircewars a ga neman ilimi, bunkasa basira da ilimi, da kuma gina kwarewa domin inganta shugabanci nagari da hidimar Al’umma.

Halartarsa a wannan biki na nuni da cikakken imani da yake da shi cewa ilimi ginshiki ne na ci gaban kai da kuma habakar al’umma baki daya.

Muna ƙara tayashi Murna tare da Addu'o'i Sosai akan Ubangiji Allah yasa Albarka a cikin wannan Karatu da yayi cikin Nasara tare da sakamako mai ƙyau.

HAPPY BIRTHDAY HON. AMINU HALILU YANKARA – S.A. ON YOUTH AND SPORTS, FUNTUA LOCAL GOVERNMENTFriday, 2nd January 2026On t...
02/01/2026

HAPPY BIRTHDAY HON. AMINU HALILU YANKARA – S.A. ON YOUTH AND SPORTS, FUNTUA LOCAL GOVERNMENT

Friday, 2nd January 2026
On this blessed Friday, we joyfully celebrate Hon. Aminu Halilu Yankara, the Special Adviser on Youth and Sports for Funtua Local Government and the Chairman of the State Forum of Youth S.As, as he marks his 35th birthday — born on 2nd January 1991.

This special occasion offers an opportunity to reflect on his impactful journey, unwavering dedication, and selfless contributions to youth development, sports advancement, and grassroots growth across the region.

Hon. Aminu Halilu Yankara is widely recognized for his:
- Excellent interpersonal relationships
- Patience and humility
- Integrity and sense of responsibility
- Competence in youth and sports engagement
- Generosity and commitment to community service

As a rising star in Katsina State, especially in Funtua, he continues to inspire hope through leadership and service. His visionary role in politics and community development makes him a role model to aspiring youths and future leaders.

On behalf of the entire community, we extend our warmest congratulations and best wishes. May Allah bless him with long life, sound health, continued success, and fulfillment of his noble aspirations.

KUNGIYAR CI-GABAN GARIN DIKKE TA KARRAMA SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR FUNTUA HON AUDU GOYA DA HON BARA'U YUSUF MAIKWAI DIKKE...
31/12/2025

KUNGIYAR CI-GABAN GARIN DIKKE TA KARRAMA SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR FUNTUA HON AUDU GOYA DA HON BARA'U YUSUF MAIKWAI DIKKE....

Kungiyar Ci gaban Garin Dikke, Mai Suna Dikke Consultative Forum DCF
Dake Karamar Hukumar Funtua Ta Karrama Shugaban Karamar Hukumar Funtua Hon Abdulmutallab Jibrin Sulaiman Goya da Hon Bara'u Yusuf Maikwai Dukke Supervisory Councilor Health Department Funtua Local Government Council Da Lambobin Girmamawa bisa kyakkyawan Jagoranci da Cigaban karamar Hukumar Funtua.

Kungiyar Dukke Consultative Forum (DCF) ta karrama Mai Girma Hon. Abdulmutallab Jibrin Sulaiman Goya, Shugaban Karamar Hukumar Funtua, da kuma Hon. Bara’u Yusuf Maikwai, Supervisory Councilor mai kula da Sashen Lafiya na Karamar Hukumar Funtua, da Lambobin Yabo na Girmamawa.

Wannan karramawa ta zo ne bisa gagarumin ƙoƙari, jajircewa da sadaukarwar da suke yi wajen inganta ci gaban Karamar Hukumar Funtua, musamman a fannoni daban-daban na raya kasa, kula da jin daɗin al’umma, bunkasa harkokin lafiya da tallafa wa marasa ƙarfi a kowane lokaci.

Shugabancinsu ya kasance abin koyi, domin suna ci gaba da nuna nagartaccen jagoranci, gaskiya da kishin al’umma, tare da ɗaukar manufofi masu alfanu da ke ƙarfafa ci gaba mai ɗorewa ga al’ummar Funtua baki ɗaya.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya ƙara musu hikima, lafiya da ƙarfin guiwa, Ya tsawaita musu rai cikin hidima, Ya albarkaci dukkan ayyukansu, tare da ba su ikon cigaba da jagorantar al’umma bisa adalci da gaskiya domin ci gaban Karamar Hukumar Funtua da ƙasa baki ɗaya.

Ubangiji Allah yasa Alkairee 🙏

SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR MULKI TA FUNTUA,HON. ABDULMUTALLAB JIBRIN GOYA YA SAKE SANYA WASU BAYIN ALLAH CIKIN FARIN CIKI....
22/12/2025

SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR MULKI TA FUNTUA,
HON. ABDULMUTALLAB JIBRIN GOYA YA SAKE SANYA WASU BAYIN ALLAH CIKIN FARIN CIKI.

Alhamdulillahi, a yau Litinin 22 ga Disamba, 2025, Mai Girma Shugaban Karamar Hukumar Funtua, Hon. Abdulmutallab Jibrin Goya, ya sake nuna jajircewarsa wajen tallafa wa al’umma, inda ya kai gagarumin tallafi ga al’ummar Unguwar Dahiru Dake karkashin Makera Ward.

Tallafin da aka bayar ya kunshi daukar nauyin magunguna, raba kayan abinci, bayar da kudaden cefane, tallafin kudin jari domin kananan sana’o’i, raba buhunan masara, tare da daukar dawainiyar karatun ‘ya’yan wasu daga cikin al’ummar yankin, tun daga matakin firamare har zuwa jami’a, a matsayin kyauta domin karfafa gwiwa da inganta rayuwar al’umma.

An tabbatar da wadannan ayyuka ne karkashin jagoranci da kulawar Ma’aikatan ASW (Auxiliary Social Workers) na Sashen Jin Kai (Social Welfare Funtua), tare da hadin gwiwar Hon. Alh. Bara'u Yusuf Maikwai Dukke, Supervisory Councilor Health Department na Karamar Hukumar Funtua, Alh. Lawal (P.A), Alh. Isiyaku Milloniya, ‘yan kwamitin Jam’iyyar APC na Unguwar Dahiru, da kuma ‘yan kwamitin Hon. Audu Goya na Makera Ward.

Al’ummar da s**a ci gajiyar wannan tallafi sun bayyana godiya da farin cikinsu, tare da yin addu’o’i ga Ubangiji Allah da Ya saka wa Mai Girma Shugaban Karamar Hukumar Funtua da mafificin alkhairi, Ya kara masa lafiya, tsari da kariya daga duk wani sharri ko zagon kasa, sannan Ya ba shi ikon ci gaba da fita kunyar al’ummar Karamar Hukumar Funtua baki daya.

Al'ummar da s**a ci gajiyar tallafin Sun hada da; Mallam Sani Danta-Aya ya samu jarin kuɗi ₦150,000. Mallam Shuaibu, Mustapha Amfani, Mallam Sani Makaho, Mallam Salisu Mai Gwanjo, Mallam Sa’idu, Mallam Hussaini Gurgu, Oga Rabe da Audu Gayu sun amfana da buhun masara, kuɗin cefane da kuma ɗaukar nauyin jinyarsu, yayin da aka ɗauki nauyin magunguna ko aikin jinya ga waɗanda ke fama da lalura.

Haka kuma, an tallafa wa mahaifiyar wata yarinya mai lalurar ƙwaƙwalwa da kuɗin sayen sabulu da buhun masara. Bugu da ƙari, an tabbatar da kulawa da makarantar ‘ya’yan Mallam Sani Makaho, Mallam Salisu Mai Gwanjo, mahaifiyar yarinya mai lalura da Mallam Sa’idu. Duk tallafin an bayar da su ne ƙarƙashin jagorancin Shugaban Karamar Hukumar Funtua, Hon. Abdulmutallab Jibrin Goya.

UWARGIDAN GWAMNAN JAHAR KATSINA HAJIYA ZULAIHAT DIKKO UMAR RADDA TA YABAMA SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR FUNTUA BISA AYYUKAN ...
20/12/2025

UWARGIDAN GWAMNAN JAHAR KATSINA
HAJIYA ZULAIHAT DIKKO UMAR RADDA TA YABAMA SHUGABAN KARAMAR HUKUMAR FUNTUA BISA AYYUKAN RAYA ƘASA DA CIGABAN AL'UMMA.

Yau Assabar, 20 ga Disamba, 2025, Mai Girma (First Lady) Uwargidan Gwamnan Jihar Katsina,Hajiya Zulaihat Dikko Umar Radda, PhD, ta kai ziyara ta aiki zuwa Garin Funtua, inda ta kaddamar da manyan ayyukan raya kasa guda biyu (2) da Gwamnatin Karamar Hukumar Funtua ta aiwatar domin amfanin al’umma a karkashin Jagorancin Hon Alh Abdulmutallab Jibrin Goya.

A yayin ziyarar, Uwargidan Gwamnan ta kaddamar da Babbar Cibiyar Lafiya ta Zamani (Primary Health Care – PHC) da ke Sabuwar Abuja, tsallaken Bye-pass Funtua, wadda aka sanya mata suna (Audu Goya Community Health Clinic). An bayyana cewa wannan katafariyar cibiyar lafiya za ta taimaka matuka wajen inganta kiwon lafiya, musamman ga mata, yara da mazauna yankin da kewaye.

Haka zalika, Hajiya Zulaihat Dikko Umar Radda ta kuma kaddamar da Katafaren Cibiyar Koyar da Sana’o’in Hannu ta Zamani, dake cikin farfajiyar Karamar Hukumar Mulki ta Funtua, wadda aka sanya mata suna Her Excellency Hajiya Zulaihat Dikko Umar Radda Skill Acquisition Centre. Cibiyar na da nufin bai wa matasa da mata horo a fannoni daban-daban na sana’o’in zamani domin dogaro da kai da rage zaman banza.

Uwargidan Gwamnan Jihar Katsina ta bayyana matukar farin ciki da gamsuwa bisa ganin wadannan ayyuka na raya kasa, inda ta yabawa Shugaban Karamar Hukumar Funtua, Hon. Abdulmutallab Jibrin Goya, kan yadda yake gudanar da ayyukansa da jajircewa ba dare ba rana. Ta ce ayyukan da yake aiwatarwa ayyuka ne na zahiri a kasa, ba furuci kawai ba, tare da jaddada cewa ya zama abin koyi a tsakanin dukkan Shugabannin Kananan Hukumomi a Jihar Katsina.

A nasa jawabin, Shugaban Karamar Hukumar Funtua ya nuna matukar godiya bisa wannan ziyara ta aiki da kuma amsar gayyata da Uwargidan Gwamnan ta yi. Ya bayyana cewa kaddamar da wadannan ayyuka alama ce ta hadin kai da goyon bayan Gwamnatin Jihar Katsina ga ci gaban Karamar Hukumar Funtua.

A yayin taron, an kuma karrama Hon. Abdulmutallab Jibrin Goya (Audu Goya) da lambar yabo ta Gwarzon Ciyamomin Jahar Katsina, ciki har da lambar yabo zuwa ga His Excellency Gwamnan Jihar Katsina, Sai lambar yabo da Girmamawa Ga her Excellency Hajiya Zulaihat Dikko Umar Radda bisa gudunmawar da take bayar wajen ci gaban al’umma musamman Marayu da Marasa ƙarfi, da aiwatar da ayyukan raya kasa a cikin jahar Katsina.

Masu sharhi sun bayyana cewa wadannan ayyuka za su kara haɓɓaka ci gaban tattalin arziki, walwalar al’umma da samar da ingantaccen rayuwa ga al’ummar Funtua, tare da kara tabbatar da kudurin Gwamnatin Karamar Hukumar Funtua na aiwatar da manufofin raya kasa masu dorewa.

Taron ya samu halartar Manyan mutane daga ciki da wajen karamar Hukumar Funtua,Akwai matan Shuwagabannin kananan hukumomin Sabuwa, Faskari, Dandume da Danja, Akwai Sarkin Maskan Katsina Hakimin Funtua Alh Sambo Idris Sambo, Akwai Sardaunan Funtua Alh. Akilu Babai, Director (NAK) Alh Alaliya Funtua, Shugaban jamiyyar APC ta Funtua, Barr. Muhammadu Sani, Kansiloli na karamar Hukumar Funtua, Shuwagabannin Ma'aikatan lafiya na karamar Hukumar Funtua, Ma'aikatan karamar Hukuma, Alh Babangida BB Oil, Da sauran Dukkanin Shuwagabannin jam'iyya Maza da Mata, Shuwagabannin Addini, Shuwagabannin Al'umma da sauran Ilahirin Al'ummar yankin Sabuwar Abuja, dunbin Masoya da Masu Fatan Alkairee.

FUNTUA LOCAL GOVERNMENT CHAIRMAN FLAGS OFF DISTRIBUTION OF RELIEF MATERIALS BY THE OFFICE OF S.A. YOUTH & SPORTSOn Tuesd...
16/12/2025

FUNTUA LOCAL GOVERNMENT CHAIRMAN FLAGS OFF DISTRIBUTION OF RELIEF MATERIALS BY THE OFFICE OF S.A. YOUTH & SPORTS

On Tuesday, 16th December 2025, the Chairman of Funtua Local Government Area, Hon. Abdulmutallab Jibrin Goya, officially flagged off the distribution of relief materials provided by the Office of the Special Adviser on Youth & Sports, aimed at supporting vulnerable residents across Funtua Local Government Area.

The relief package comprised 500 large blankets, 22 cartons of Omo detergent, 10 cartons of bathing soap, as well as 250 cold-weather clothing items for both children and adults. The items were distributed to male and female beneficiaries, including the visually impaired, persons living with disabilities, orphans, the less privileged, and individuals with mental health challenges, drawn from the 11 wards of Funtua Local Government Area.

The intervention was implemented under the leadership of the Office of the Special Adviser on Youth & Sports to the Chairman of Funtua Local Government, who also serves as the Chairman of all S.As on Youth in Katsina State, Hon Aminu Khalil . The initiative forms part of ongoing efforts to alleviate hardship, improve welfare, and enhance the overall well-being of the people.

The event attracted a large turnout, particularly youths of both genders, and was graced by several dignitaries, including Hon. Bara’u Yusuf Maikwai Dukke, Supervisory Councilor for Health, Funtua Local Government Area. Also in attendance were leaders of Izala and Darika groups, the Director of E.S.D., Alhaji Hassan; Alhaji Nura Sani, Supervisory Councilor for E.S.D.; the Information Officer of Funtua Local Government Council; leaders of political parties; Supervisory Councilors; Special Advisers; and youth leaders.

In his address, Hon. Abdulmutallab Jibrin Goya expressed immense satisfaction at the joy and relief evident on the faces of the beneficiaries. He reaffirmed his administration’s commitment to sustained community support, with particular emphasis on assisting the most vulnerable members of society.

DISCLAIMER: CLARIFICATION ON PEACE MEDIATION EFFORTSThe recent engagement undertaken by the Executive Chairman of Funtua...
07/11/2025

DISCLAIMER: CLARIFICATION ON PEACE MEDIATION EFFORTS

The recent engagement undertaken by the Executive Chairman of Funtua Local Government, Hon. Abdulmutallab Jibrin Goya, with certain Fulani groups previously associated with armed activities, was conducted in good faith and with sincere intentions. The purpose of this initiative is to reinforce and sustain the existing peace agreement between the affected Fulani groups and the wider community.

This effort aligns with ongoing reconciliation initiatives carried out across several local government areas in Katsina State, including Faskari, Sabuwa, Dandume, Kankara, Jibiya, Safana, and Dutsin-Ma. Hon. Goya’s visit specifically sought to consolidate peace, strengthen cooperation, rebuild trust, and prevent any resurgence of violence in Funtua and its neighboring communities.

It is also important to note that, just last week, the Chairman of Sabuwa Local Government attended a wedding ceremony within one of the Fulani settlements. This gesture, like Hon. Goya’s visit, was aimed at deepening mutual understanding and fostering enduring peaceful coexistence between Fulani pastoral communities and the wider Hausa population.

We wish to emphasize that Hon. Abdulmutallab Jibrin Goya, alongside other local government leaders in Katsina State, engages with these groups solely for the purpose of maintaining peace and ensuring community security. There is no evidence of any improper relationship, support, or endorsement beyond conflict resolution efforts aimed at preserving harmony and safeguarding lives and property.

Hon. Goya’s continued leadership demonstrates his firm commitment to promoting stability and sustainable development. It is well recognized that meaningful progress can only be achieved in an atmosphere of peace.

Any narratives suggesting otherwise are misleading. The engagement with the Fulani pastoral communities clearly reflects a renewed dedication to strengthening unity, encouraging mutual respect, and advancing lasting peaceful coexistence among all residents of Funtua Local Government and its environs.

Signed:
Media & Publicity Directorate
Funtua Local Government Council
7th November, 2025

WANENE YA KAWO CIBIYAR ‘YAN SANDA TA (MOPOL) A ƘARAMAR HUKUMAR FUNTUA? SAKON JAGORA HON BARA'U YUSUF MAIKWAI DIKKE Da fa...
25/10/2025

WANENE YA KAWO CIBIYAR ‘YAN SANDA TA (MOPOL) A ƘARAMAR HUKUMAR FUNTUA?

SAKON JAGORA HON BARA'U YUSUF MAIKWAI DIKKE

Da farko, muna ƙara mika Saƙon godiya da jinjina ta musamman ga Sanata Muntari Muhammad Dandutse bisa irin namijin kokarinsa wajen kawo Jami’a da kuma Cibiyar ‘Yan Sanda ta MOPOL a garin Funtua. Wannan gagarumar nasara ta samu tabbaci ne a ranar Alhamis, 23 ga Oktoba, 2025, bisa ga takardar da Sanata Dandutse ya gabatar tun a ranar 7 ga Agusta, 2025, wadda aka sanya mata hatimi da sa hannunsa. Lallai, wannan takarda ce da ta sami amincewar hukumomi, sabanin jita-jitar da ake yadawa cewa wai Lawal Abbas Funtua ne ya kawo wannan aiki wanda gaba ɗaya ba shi da tushe ko hujja.

Haka kuma, muna sake mika godiya da yabo ga Sanata mai wakiltar Yankin Karaduwa, Sanata Muntari Muhammad Dandutse. Tabbas, tarihin Ƙaramar Hukumar Funtua da yankin Karaduwa ba zai kammalu ba ba tare da ambaton sunanka ba. Ka share kukan da al’ummar wannan yanki s**a dade suna yi, ta hanyar jajircewarka tun daga lokacin da ka fara neman a kafa Jami’ar Kimiyyar Lafiya (University of Health Sciences).

Ta hanyar kudirinka na inganta tsaro a cikin Ƙaramar Hukumar Funtua da dukan yankin Karaduwa, ka nuna kwarewa da jajircewa a jagoranci. Sakamakon haka, Gwamnatin Tarayya ta amince da kafa Cibiyar ‘Yan Sanda ta (MOPOL) a garin Funtua nasarar da aka cimma kai tsaye sakamakon kudirin da ka gabatar a gaban Majalisar Dattawa, kamar yadda aka ambata a baya.

Lallai, wannan ci gaba, tare da sauran ayyuka masu yawa da ka aiwatar tun bayan hawanka ofis a matsayin Sanata, sun tabbatar da cewa kana da cikakken cancanta ga kowane yabo da girmamawa daga al’ummar yankin nan. Haka kuma, kana da cikakken cancantar sake samun goyon bayan jama’ar Karaduwa domin ci gaba da kawo musu ci gaba da walwala.

Mun gode sosai, Sanata Muntari Muhammad Dandutse.

An rubuta a ranar Jumma’a, 24 ga Oktoba, 2025.

Sa hannu:
Comr. Bilyaminu Lawal Funtua (E-sign)

Address

Katsina

Telephone

+2348065223687

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Arewa Daily Updates posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Arewa Daily Updates:

Share