21/02/2026
HON A.A BASHEER FUNTUA DAN TAKARAR MAJALISAR TARAYYA MAI NEMAN WAKILTAR KANANAN HUKUMOMIN FUNTUA-DANDUME YA GWANGWAJE WANI MATASHI DA KYAUTAR KUƊI NAIRA (500,000) DOMIN DOGARO DAKAI.
Assabar 21-Febuary-2027, Hon Basheer Abdullahi (A.A Basheer Funtua), Dan takarar Majalisar Tarayya mai neman wakiltar Kananan Hukumomin Funtua da Ɗandume a zaɓen shekarar 2027, ya ci gaba da nuna jajircewarsa wajen tallafa wa matasa da ƙarfafa dogaro da kai a tsakanin al’umma.
A wannan karo, Hon. A.A Basheer Funtua ya gwangwaje wani matashi ɗan asalin Garin Mahuta ‘A’, Karamar Hukumar Ɗandume, mai suna Kabiru Sufee Mahuta (K.B), da kyautar zunzurutun kuɗi har Naira 500,000, domin tallafa masa wajen bunƙasa kasuwancinsa da ƙara masa jarin sana’a.
Wannan tallafi na daga cikin manufofin Hon. Basheer na ƙarfafa matasa su tsaya da kafafunsu ta hanyar sana’o’i da kasuwanci, tare da rage zaman banza da dogaro da wasu. Matakin ya zo ne a matsayin ƙarfafawa da nuna kulawa ga matasan da ke da himma da ƙwazo wajen neman na kansu.
Kabiru Sufee Mahuta ya bayyana matuƙar farin cikinsa bisa wannan karamci, inda shi da iyalansa da abokan arziki s**a miƙa godiya ta musamman ga Hon. A.A Basheer Funtua, tare da yi masa fatan alheri da addu’ar Allah Ya ba shi nasara a burinsa na wakiltar al’ummar Funtua da Ɗandume a Majalisar Tarayya.
Haka zalika, Alhaji Babangida Mahuta ya yi godiya ƙwarai a madadin al’ummar Garin Mahuta, yana mai bayyana wannan tallafi a matsayin abin alfahari da kuma shaida ta karamci da tausayi da Hon. Basheer ke nunawa ga al’umma, musamman marasa ƙarfi da matasa masu tasowa.
Lallai wannan aiki ya ƙara fito da halin karamci, tausayi da kishin al’umma da Hon. A.A Basheer Funtua ke da shi, tare da tabbatar da aniyarsa ta kawo ci gaba mai ma’ana ga Kananan Hukumomin Funtua da Ɗandume.