Katsina Update

Katsina Update Domin Samar Da Sahihan Labarai

Jami'an SSS sun k**a wanda ake zargi da safarar bindigogi a KanoJami'an Hukumar Tsaron SSS sun k**a wani mutum mai sheka...
12/06/2026

Jami'an SSS sun k**a wanda ake zargi da safarar bindigogi a Kano

Jami'an Hukumar Tsaron SSS sun k**a wani mutum mai shekaru 30 da ake zargi da safarar bindigogi, Muhammad Abubakar a Jihar Kano.

Da suke gabatar da wanda ake zargin a hukumar su da ke Kano, jami'an hukumar DSS sun ce an k**a wanda ake zargin da ke jigilar bindigogi, yayin da yake kan hanyarsa ta jigilar bututun kirar RPG guda hudu, AK-47 guda uku da kuma konkon harsasai biyu (magazine) zuwa wani wuri a Funtua, Jihar Katsina, k**ar yadda jaridar Daily Nigerian ta bayyana.

Ga fassarar jawabin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na ranar Dimokradiyya.SAKON SHUGABA BOLA AHMED TINUBU A RANAR DIMOKU...
12/06/2026

Ga fassarar jawabin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu na ranar Dimokradiyya.

SAKON SHUGABA BOLA AHMED TINUBU A RANAR DIMOKURAƊIYYA TA 12 GA YUNI, 2026

'Yan uwana ’yan Najeriya,

A yau muna bikin dimokuraɗiyya da kuma juriyar ruhin ɗan Najeriya. Tsawon shekaru 27 a jere tun daga ranar 29 ga Mayu, 1999, al’ummarmu ta ci gaba da zaɓar shugabanninta ta hanyar akwatin zaɓe, tana ganin sauyin mulki cikin lumana, tare da warware sabani a kotuna da majalisun dokoki maimakon ta hanyar tashin hankali.

Dimokuraɗiyyarmu ba cikakkiya ba ce, amma tamu ce. Don haka wajibi ne mu ci gaba da kare ta tare da ƙarfafa ta.

A kwanaki masu zuwa, jihohin Ekiti da Osun za su gudanar da zaɓe. Ina kira ga Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), jami’an tsaro da dukkan masu ruwa da tsaki su tabbatar da cewa an gudanar da waɗannan zaɓuka cikin lumana da gaskiya. Dimokuraɗiyya tana raunana idan jama'a s**a rasa amincewa da tsarin zaɓe.

Ga Majalisar Tarayya, Bangaren Shari’a, ’Yan Jarida da Kungiyoyin Farar Hula: ku ne ginshiƙan da ke kare jamhuriyarmu. Ku ci gaba da s**ar gwamnati idan ya dace, ku yi sabani da ni idan kuna da hujja, amma kada ku daina yarda da Najeriya.

Ga matasanmu, Najeriya ita ce gidanku kuma makomarku. Ku gina ta a nan, ku kirkiri sababbin fasahohi a nan, ku yi aiki a nan, ku kuma kada kuri’a a nan. Manyan ƙasashe ba su samu ci gaba ba saboda mutanen da s**a gudu daga matsaloli, sai dai saboda waɗanda s**a tsaya s**a warware su.

Ina miƙa gaisuwa ta musamman ga dakarunmu, jami’an ’yan sanda da jami’an tsaro saboda sadaukarwar da suke yi. Haka kuma ina godiya ga sarakunan gargajiya, malamai da shugabannin al’umma saboda rawar da suke takawa wajen tabbatar da zaman lafiya da sulhu.

A yau muna tunawa da juriyar ’yan Najeriya da s**a ƙi yin kasa a gwiwa wajen kare ’yanci da dimokuraɗiyya. Muna girmama waɗanda s**a fuskanci tsangwama, kurkuku, gudun hijira har ma da rasa rayukansu domin al’ummomin gaba su more dimokuraɗiyya.

Muna kuma tunawa da shugabannin ƙwadago, ’yan jarida, masu fa

Wacce haduwa ce tafi baka mamaki ?
11/06/2026

Wacce haduwa ce tafi baka mamaki ?

HOTO: Yadda aka maida makwancin Sheikh Dahiru Usman Bauchi.
11/06/2026

HOTO: Yadda aka maida makwancin Sheikh Dahiru Usman Bauchi.

Majalisar Dattawa Ta Ba Da Umarnin Kamo Tsohon Shugaban NNPCL, Mele Kyari.Kwamitin Kula da Asusun Jama’a na Majalisar Da...
10/06/2026

Majalisar Dattawa Ta Ba Da Umarnin Kamo Tsohon Shugaban NNPCL, Mele Kyari.

Kwamitin Kula da Asusun Jama’a na Majalisar Dattawan Najeriya ya ba da umarnin kamo tsohon shugaban Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL), Mele Kyari, bayan ya kasa bayyana a gabansa domin amsa tambayoyi kan wasu harkokin kuɗaɗen kamfanin.

An yanke wannan hukunci ne a wani zaman bincike da kwamitin ya gudanar a Abuja ranar Talata, ƙarƙashin jagorancin shugaban kwamitin, Sanata Ibrahim Dankwambo.

Kwamitin na gudanar da bincike ne kan bayanan kuɗaɗen NNPCL daga shekarar 2017 zuwa 2023, inda yake son samun ƙarin bayani daga Kyari kan wasu muhimman batutuwa da s**a shafi kuɗaɗen kamfanin.

Rashin halartar tsohon shugaban kamfanin ya haifar da muhawara tsakanin mambobin kwamitin. Yayin da wasu sanatoci s**a matsa a ɗauki matakin gaggawa a kansa, wasu kuma sun nemi a sake ba shi wata dama domin ya bayyana a gaban kwamitin.

Sanatoci Saliu Mustapha da Tony Nwoye sun bayyana cewa Kyari na karɓar magani a ƙasar Jamus, saboda haka s**a buƙaci a yi la’akari da halin da yake ciki.

Sai dai wasu mambobin kwamitin sun ce babu wata hujja da aka gabatar da ke tabbatar da iƙirarin rashin lafiyar tasa.

Sanata Abdul Ningi ya ce duk wanda ke neman uzuri saboda rashin lafiya ya k**ata ya gabatar da takardun asibiti ko wasu hujjoji na hukuma, maimakon dogaro da bayanan baki kawai.

Daga bisani, Sanata Victor Umeh ya gabatar da ƙudirin fitar da sammacin k**a Mele Kyari, wanda mataimakin shugaban kwamitin, Sanata Peter Nwaebonyi, ya mara wa baya.

Kwamitin ya ce binciken da yake gudanarwa ya shafi tambayoyi kan wasu bayanan kuɗaɗe da aka kiyasta sun haura naira tiriliyan 210 a cikin rahotannin kuɗaɗen NNPCL na shekarun da ake dubawa.

Yadda matasan jihar Katsina s**a amsa kira, wajen halartar tantancewar daukar sabbin kuratan sojoji a barikin sojoji dak...
10/06/2026

Yadda matasan jihar Katsina s**a amsa kira, wajen halartar tantancewar daukar sabbin kuratan sojoji a barikin sojoji dake Katsina

Ce-ce-ku-ce Ya Barke Kan Shirin Kara Wa’adin Shekara Shida Ga Shugabanni a Nijeriya.Wani sabon shiri da ake son gabatarw...
10/06/2026

Ce-ce-ku-ce Ya Barke Kan Shirin Kara Wa’adin Shekara Shida Ga Shugabanni a Nijeriya.

Wani sabon shiri da ake son gabatarwa a Majalisar Tarayya ya janyo muhawara mai zafi a faɗin Nijeriya, bayan da Shugaban Majalisar Dattawa, Opeyemi Bamidele, ya bayyana goyon bayansa ga tsarin bai wa shugaban ƙasa da gwamnoni wa’adin shekara shida kacal ba tare da damar sake tsayawa takara ba.

Masu goyon bayan wannan tsari na cewa zai bai wa shugabanni damar mayar da hankali kan gudanar da mulki da aiwatar da manufofinsu, maimakon kashe lokaci da albarkatu wajen shirye-shiryen neman wa’adi na biyu.

Sai dai kuma shirin ya haifar da fargaba a tsakanin wasu ‘yan Najeriya, inda suke ganin akwai yiwuwar a yi amfani da shi wajen ƙoƙarin tsawaita zaman masu mulki a kan karagar mulki ta wata hanya.

Masana harkokin shari’a da siyasa sun bayyana cewa kudirin ba zai iya zama doka ba sai an yi gyaran kundin tsarin mulkin Nijeriya na shekarar 1999. Hakan kuma na buƙatar samun amincewar kashi biyu bisa uku na mambobin Majalisar Tarayya da kuma akalla majalisun dokoki 24 na jihohin ƙasar.

Yayin da wasu ke ganin tsarin zai rage kuɗaɗen da ake kashewa wajen zaɓe tare da ba shugabanni damar ɗaukar tsare-tsare masu muhimmanci ba tare da la’akari da tasirin siyasar sake zaɓe ba, wasu kuwa na zargin cewa akwai wata manufa ta siyasa da ke tattare da kudirin.

Masu s**a sun jaddada cewa matsalolin da s**a shafi rashin tsaro, tsadar rayuwa da bunƙasa tattalin arziki su ne ya k**ata su fi ɗaukar hankalin masu mulki a wannan lokaci, maimakon buɗe sabon muhawara kan wa’adin shugabanci.

Haka kuma sun tunatar da cewa irin wannan yunƙuri ya taɓa tasowa a lokuta daban-daban a tarihin siyasar Najeriya, amma bai samu amincewar Majalisar Tarayya ba.

A yanzu dai, masu sharhi na ganin makomar wannan kudiri za ta dogara ne da yadda ‘yan Najeriya, ƙungiyoyin farar hula da kuma ‘yan majalisa za su karɓe shi a watanni masu zuwa.

Ministan ƙudin Isra'ila Bazalel Smotrich ya zama jami’in gwamnatin ƙasar na biyu da Faransa ta hanawa shiga ƙasar cikin ...
09/06/2026

Ministan ƙudin Isra'ila Bazalel Smotrich ya zama jami’in gwamnatin ƙasar na biyu da Faransa ta hanawa shiga ƙasar cikin 'yan watannin nan, bayan Ministan Tsaron Ƙasar Itamar Ben Gvir da ya fuskanci irin wannan mataki a ranar 23 ga watan Mayun wannan shekara saboda cin zarafin Falasɗiwa.

Zan Gina Matatar Man Fetur Na Alkaleri Idan Na Zama Gwamnan Jihar Bauchi, Cewar Naziru Sheik Dahiru BauchiDan gidan mari...
09/06/2026

Zan Gina Matatar Man Fetur Na Alkaleri Idan Na Zama Gwamnan Jihar Bauchi, Cewar Naziru Sheik Dahiru Bauchi

Dan gidan marigayi Shehin Malamin, yana neman takarar gwamnan Bauchi ne a karkashin jam'iyyar APGA.

Wace fata za ku yi masa?

YA RASU A HANNUN MASU GARKUWA DA MUTANE.Kaijama'a INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'U...
09/06/2026

YA RASU A HANNUN MASU GARKUWA DA MUTANE.

Kaijama'a INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN

INNA LILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN

Kowa da irin hanyar da Allah zai karbi rayuwar sa.

Allahu Akbar, Allahu Akbar, Allah ya yi wa Malam Yahaya Billi (Shugaban Izala na Besse) rasuwa a hannun kidnappers a jiya. Don haka za a gabatar da salatul Ga'ib a yau k**ar haka, Wuri: Garkan Sarki, Lokaci: 4:30, Sanarwa.

JIBWIS BESSE Media Team

Address

Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Update posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katsina Update:

Share