Jaridar Ingantattun Labarai

Jaridar Ingantattun Labarai Domin Samar Da Sahihan Labarai

ƳA'YAN TSAFFIN SHUGABANNIN KASA: Hajia Maryam Umar Musa Yar'adua, Mai Ɗakin Tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Ibrahim...
22/07/2025

ƳA'YAN TSAFFIN SHUGABANNIN KASA: Hajia Maryam Umar Musa Yar'adua, Mai Ɗakin Tsohon Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Ibrahim Shehu Shema Tare Da Hajia Zainab Sani Abacha, Mai Ɗakin Sanata Yakubu Lado Danmarke

YANZU-YANZU: Fastocin Takarar Omoyele Sowore Da Dan Bello Sun Fara Bayyana A NàjeriyaShin Kana Ɗaya Daga Cikin Ƴan Najer...
22/07/2025

YANZU-YANZU: Fastocin Takarar Omoyele Sowore Da Dan Bello Sun Fara Bayyana A Nàjeriya

Shin Kana Ɗaya Daga Cikin Ƴan Najeriya Da Zasu Iya Zaɓar Wannan Haɗin A Zaɓen 2027?

Da Dumi-DumiSanata Natasha ta shiga majalisa a kafa, bayan jami’an tsaro sun hana motocinta shiga harabar majalisar
22/07/2025

Da Dumi-Dumi

Sanata Natasha ta shiga majalisa a kafa, bayan jami’an tsaro sun hana motocinta shiga harabar majalisar

🟢SIYASA: Girmama Marigayi Buhari da Tinubu ya yi ne ya sa za mu goyi bayansa a 2027 - Sarkin DauraSarkin Daura, Alhaji U...
22/07/2025

🟢SIYASA: Girmama Marigayi Buhari da Tinubu ya yi ne ya sa za mu goyi bayansa a 2027 - Sarkin Daura

Sarkin Daura, Alhaji Umar Farouk Umar, ya bayyana cewa dalilin da ya sa masarautarsu za ta goyi bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaben shugaban ƙasa na 2027 shi ne don girmama marigayin Muhammadu Buhari da goyon bayan da Tinubu ya bayar wa masarautar Daura da iyalan Buhari .

Sarkin Daura ya bayyana cewa Shugaba Tinubu ne zaɓinmu a 2027. Muna nan daram a bayansa, kuma za mu ci gaba da goyon bayan gwamnatinsa domin ta samu nasara”

A lokacin da Sanata Oluremi Tinubu, matar Shugaban ƙasa, da mata girmammiya s**a kai ta’aziya ga iyalan marigayin Buhari a Daura, Sarkin ya jagoranci taron wajen yin rera taken **“Tinubu, Tinubu, Tinubu in 2027”** .

Sarkin ya yabawa Buhari a matsayin ɗan ƙasa mai nagarta da ya ɗaukaka sunan Daura da ƙasa baki ɗaya, sannan nuna cewa Tinubu ya nuna haɗin kai da masarautarsu yayin makokin marigayin Buhari .

Sama da Yara Miliyan Ɗaya na Fama da Matsananciyar Yunwa a Gaza, Isra'ila na Amfani da Yunwa a matsayin Makamin kare Dan...
22/07/2025

Sama da Yara Miliyan Ɗaya na Fama da Matsananciyar Yunwa a Gaza, Isra'ila na Amfani da Yunwa a matsayin Makamin kare Dangi kan Falasdinawa marasa laifi a Gaza.

MINISTAN MATASA....Ganin irin yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tsaya tsayin daka wajen jana'izar marigayi tsohon Shuga...
22/07/2025

MINISTAN MATASA....

Ganin irin yadda Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tsaya tsayin daka wajen jana'izar marigayi tsohon Shugaban Nigeria Muhammadu Buhari da kuma kyakkyawar alakar dake tsakanin Buhari da Tinubu sai nake ganin abu ne mai kyau a siyasa Shugaba Tinubu ya bawa Yusuf Buhari mukamin Minista musamman Ministan Matasa...

Yin hakan zai kara dankon zumunci sosai...

A yanzu Yusuf Buhari yana da shekara 33 a duniya shekarun da zasu bashi damar tsayawa kowacce irin takara a Nigeria...

A bangaren siyasar Arewa kasancewar Yusuf Buhari minista a gwamnatin Tinubu hakan zai iya zama dalilin da Tinubu zai samu karin magoya baya daga yankin Arewa Maso Yamma.....

Daga Rabi'u Biyora.

Ku yafe wa Buhari, ba laifinsa ba ne, laifin na jikinsa ne - Darakta a NAFDAC Dr. Abubakar Jimoh ya roƙi ƴan Nijeriya Ts...
22/07/2025

Ku yafe wa Buhari, ba laifinsa ba ne, laifin na jikinsa ne - Darakta a NAFDAC Dr. Abubakar Jimoh ya roƙi ƴan Nijeriya

Tsohon Daraktan Harkokin Jama'a na Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), Dr. Abubakar Jimoh, ya kare marigayi Shugaba Buhari, yana roƙon ƴan Najeriya da su karkata fushinsu zuwa kan na jikin sa.

Abubakar ya roƙi ƴan Najeriya da su yafe wa marigayi Buhari, inda ya roke su da maimakon haka su yi tir da waɗanda su ke jikin sa, wato cabal da kuma waɗanda ya baiwa mukamai da, a cewarsa, s**a lalata kyawawan niyyar gwamnatin Buhari.

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Abubakar wanda yanzu yana matsayin Babban mai binciken a Jami’ar Abuja, ya bayyana marigayi Shugaba Buhari a matsayin “mutum mai tsoron Allah, gaskiya, ɗan ƙasa na gari kuma mai kishin ƙasa” wanda tsare-tsarensa masu kyau s**a samu tangarda daga wasu gungun masu iko a cikin gwamnati.

“Shugaba Buhari yana da tsare-tsare mafi nagarta don ceto Najeriya daga kangin matsin tattalin arziki, rashin tsaro da talauci. Amma waɗanda ya baiwa amana – da wasu mambobin majalisar ministoci – sun yaudare shi. Sun kwace ikon mulki s**a mayar da muradunsu na kai su ka danne manufofinsa na canji.”

Tsohon mai magana da yawun na NAFDAC ya ƙaryata ra’ayoyin da ke cewa babu cabal a lokacin mulkin Buhari, yana jaddada cewa kowace gwamnati tana da nata bangaren da ya kira da “kitchen cabinet da masu tasiri irin na oligarchy.”

An bukaci masu Editing su fito da fuskar wannan mutumin
12/06/2025

An bukaci masu Editing su fito da fuskar wannan mutumin

Jirgin Air India Mai Dauke da Fasinjoji 242 Ya Yi Hatsari a AhmedabadWani jirgin sama mallakin kamfanin Air India wanda ...
12/06/2025

Jirgin Air India Mai Dauke da Fasinjoji 242 Ya Yi Hatsari a Ahmedabad

Wani jirgin sama mallakin kamfanin Air India wanda ya nufi birnin London ya yi hatsari a birnin Ahmedabad na kasar India, jim kadan bayan tashinsa daga filin jirgin saman birnin.

A cewar wani rahoto da aka samu, jirgin yana dauke da fasinjoji 242 a lokacin da lamarin ya faru. Har yanzu hukumomi ba su fitar da cikakken bayani kan musabbabin hatsarin ba, kuma ba a tabbatar da adadin wadanda s**a jikkata ko rasa rayukansu ba.

Ana ci gaba da aikin ceto da bincike a wajen da hatsarin ya faru, yayin da hukumomin tsaro da na kula da sufurin jiragen sama ke gudanar da bincike don gano musabbabin wannan mummunan al'amari.

YANZU-YANZU: Zanga-zanga ta barke a Legas a ranar Dimokiradiyya, bayan Tinubu ya gaza yin jawabi ga Ƴan Najeriya.
12/06/2025

YANZU-YANZU: Zanga-zanga ta barke a Legas a ranar Dimokiradiyya, bayan Tinubu ya gaza yin jawabi ga Ƴan Najeriya.

Amurka ta koro Khaby Lame, matashin da ya fi kowa yawan followers a TikTok, bisa zarginsa da shiga kasar ba bisa ka'ida ...
10/06/2025

Amurka ta koro Khaby Lame, matashin da ya fi kowa yawan followers a TikTok, bisa zarginsa da shiga kasar ba bisa ka'ida ba.

Rahotanni sun ce matashin dan asalin kasar Senegal da Italiya, shi ne ya yarda ya fice daga ƙasar Amurka a karan kansa bayan an tsare shi tsawon kwanaki shida

Jarumi Adam Zango yana cigaba da samun sauki na hatsarin da ya faru dashi.
10/06/2025

Jarumi Adam Zango yana cigaba da samun sauki na hatsarin da ya faru dashi.

Address

Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jaridar Ingantattun Labarai posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Jaridar Ingantattun Labarai:

Share