Alfijir Radio

Alfijir Radio Alfijir Radio Hasken Al’umma
(2)

Hukumar da ke kula da wutar lantarki ta Najeriya, Nigerian Electricity Regulatory Commission, (NERC) ta fara wani shiri ...
04/06/2026

Hukumar da ke kula da wutar lantarki ta Najeriya, Nigerian Electricity Regulatory Commission, (NERC) ta fara wani shiri da zai ba jama'a masu amfani da lantarki damar samar da wutar lantarki ta kansu daga hanyoyi daban-daban, tare da sayar da sauran wacce su ka rage ga babban layin lantarki na ƙasa.

A wata sanarwar da hukumar ta wallafa a shafinta na X, ranar Laraba, hukumar ta ce manufar wannan ƙuduri shi ne fadaɗa hanyoyin samar da lantarki, da haɓɓaka samar da lantarki abin dogaro, tare da ƙarfafawa masu zuba jari a fannin samar da lantarki.

A ƙarƙashin wannan tsari, masu amfani da lantarki, da ake kira "prosumers" za su iya sanya na'urorin sola domin amfanin kansu, sannan su ba kamfanonin rarraba lantarki sauran lantarkin da su ka rage domin kamfanoni su saya.

A ƙarƙashin tsarin dai, masu gidaje, 'yan kasuwa da masu masana'antu da s**a zuba jari wajen samar da lantarkin kansu, musamman lantarki mai amfani da hasken rana (solar energy), a yanzu za su rage kuɗin lantarkin da su ke biya, yayin da za su riƙa shan lantarkin da s**a samar da kansu, sannan su samu 'yan kuɗaɗe daga lantarkin da su ka ba babban layin lantarki na ƙasa wanda basa amfani da shi.

Tsarin ya tanadi cewa, idan kwastomoma na son shiga cikinsa, tilas sai ya yi haɗaka da kamfanonin rarraba lantarki, sannan ya sanya na'urorin samar da lantarki da aka aminta da su, tare da samun sahalewar kamfanonin rarraba lantarki.

Haka kuma, ana so sai na'urorin da kwastoma ya sanya sun kai ƙarfin kilowatts 50 zuwa Megawatt 1.5.

Sannan tilas ne sai kwastoma ya rattaba hannu kan yarjejeniyar biyan kuɗi ta Net Billing Agreement tare da yin rijista da hukumar NERC.

NERC ta bayyana cewa kwastomomin da aka amince wa shiga tsarin za a sanya musu mita wadda za ta riƙa auna adadin lantarkin da s**a sha daga babban layin lantarki, da kuma lantarkin da su ka ba babban layin lantarkin.

Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce ya na fatan ganawa da Jagoran Addini na Iran, Mojtaba Khamenei, yayin da Washington ...
04/06/2026

Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce ya na fatan ganawa da Jagoran Addini na Iran, Mojtaba Khamenei, yayin da Washington da Tehran ke zargin juna da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta.

Ya fadi haka ne ranar Laraba, 3 ga Yunin 2026.

Ana kyautata zaton na jikkata Mojtaba Khamenei, ɗan shekara 56, a hari ta sama da Amurka-Isra'ila su ka kai wanda ya hallaka mahaifinsa, Ali Khamenei, kuma har yanzu ba a ganshi ya fito a bainar jama'a ba tun lokacin da aka naɗa shi domin ya gaji mahaifinsa.

"Zan so in haɗu da shi, kuma ina fatan za mu haɗu wata rana, ya dai danganta da yadda aka tsara," in ji shugaban na Amurka ya faɗa wa shirin Podcast na "Pod Force One" na New York Post.

04/06/2026

Shirin Tambarin Alfijir

Nazari akan nadewar tafin sawu da ake haihuwar yara dashi.

Wasila Yusuf G/gida ke gabatar da shirin.

Rundunar ’yan sandan jihar Katsina ta ce ta dakile wani yunkurin satar shanu da wasu da ake zargin ’yan bindiga ne s**a ...
04/06/2026

Rundunar ’yan sandan jihar Katsina ta ce ta dakile wani yunkurin satar shanu da wasu da ake zargin ’yan bindiga ne s**a kai a kauyen Gidan Dan Maye da ke kan hanyar Gangaren Makurdi zuwa Jargaba a karamar hukumar Bakori.

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 11 na dare a ranar 2 ga Yuni, 2026, inda maharan s**a yi awon gaba da shanu 12 tare da wasu tumaki da ba a tantance adadinsu ba.

Bayan samun rahoton faruwar lamarin, jami’an ’yan sanda karkashin jagorancin DPO na Bakori tare da hadin gwiwar masu sintiri na sa-kai sun bi sawun maharan har zuwa kusa da kauyen Gidan Baushe.

A nan ne aka yi musayar wuta mai zafi tsakanin bangarorin biyu, lamarin da ya tilasta wa maharan tserewa da raunukan harbin bindiga bayan sun yi watsi da dukkan dabbobin da s**a sace.

Rundunar ta tabbatar da cewa an kwato dabbobin gaba daya kuma an mayar da su ga masu su. Kwamishinan ’yan sandan jihar Katsina, Ali Umar Fage, ya yaba wa jami’an da s**a gudanar da aikin, tare da jaddada kudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Ya kuma bukaci jama’a da su ci gaba da bai wa jami’an tsaro sahihan bayanai domin dakile ayyukan masu aikata laifuka.

04/06/2026

Wannan shine karo na 7 da tsohon mataimakin Shugaban Najeriya, Atiku Abubakar yake neman a bashi dama ya zama shugaban kasar.

Ya kuke kallon takarar Atiku Abubakar a shekarar nan ta 2027?

Kotun Tarayya da ke Abuja ta ɗage sauraron ƙarar da ke ƙalubalantar shugabancin rikon ƙwarya na jam’iyyar ADC zuwa ranar...
03/06/2026

Kotun Tarayya da ke Abuja ta ɗage sauraron ƙarar da ke ƙalubalantar shugabancin rikon ƙwarya na jam’iyyar ADC zuwa ranar 8 ga Yuni.

Alƙali Peter Lifu ne ya ɗage shari’ar bayan lauyan Nafiu Bala ya nemi ƙarin lokaci saboda rashin halartar lauyoyin wasu ɓangarorin da ke son shiga cikin shari’ar, yayin da INEC ma ba ta samu wakilci a zaman kotun ba.

A yayin shari’ar, lauyoyin waɗanda ake ƙara sun amince da buƙatar ɗage zaman, amma sun bayyana cewa wasu jinkirai da aka samu sun samo asali ne daga wasu matakan da mai ƙarar ya ɗauka a baya.

Alƙalin ya jaddada cewa masu ƙara ba su da ikon zaɓar kotun da za ta saurari shari’arsu, tare da tabbatar da cewa za a yi saurin sauraron karar bisa umarnin Kotun Koli.

Nafiu Bala, tsohon mataimakin shugaban ADC na ƙasa, yana neman kotu ta hana David Mark, Rauf Aregbesola da sauran shugabannin rikon ƙwarya gudanar da harkokin jam’iyyar. Ya yi zargin cewa nadin shugabannin ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ADC da kuma dokokin zaɓe.

Alƙalin ya umarci a sanar da dukkan ɓangarorin da ke son shiga cikin shari’ar cikin sa’o’i 24 tare da gabatar da dukkan takardunsu kafin zaman kotu na gaba.

Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da kudirin dokar kafa Hukumar Kawar da Zazzabin Cizon Sauro ta Kasa bayan kammala ...
03/06/2026

Majalisar Dattawan Najeriya ta amince da kudirin dokar kafa Hukumar Kawar da Zazzabin Cizon Sauro ta Kasa bayan kammala karatu na uku.

Sanata Ned Nwoko ne ya dauki nauyin kudirin, wanda ke da nufin samar da wata hukuma ta musamman da za ta jagoranci kokarin dakile da kuma kawar da cutar zazzabin cizon sauro a fadin kasar.

Kwamitin Lafiya na Majalisar Dattawa ya bayyana cewa sabuwar hukumar za ta hada kai da hukumomi da kungiyoyi daban-daban wajen aiwatar da shirye-shiryen rigakafi, bincike, wayar da kan jama’a da kula da muhalli domin rage yaduwar cutar.

Kwamitin ya ce an zabi kalmar “kawarwa” (elimination) maimakon “shafe gaba daya” (eradication) saboda ta fi dacewa da ka’idojin kasa da kasa kan yaki da cutar.

Da yake yabawa da amincewa da kudirin, Sanata Ned Nwoko ya ce Najeriya na da damar kawar da zazzabin cizon sauro kamar yadda wasu kasashe s**a yi.

Ya jaddada cewa hakan na bukatar hadin kai, kyakkyawan tsari da kudurin gwamnati, yana mai cewa lokaci ya yi da za a daina mayar da hankali kan magani kawai, a koma kan rigakafi da kawar da cutar baki daya.

Hukumar Kare Hakkin Masu Amfani da Kaya da Hidima ta Tarayya (FCCPC) ta bayyana cewa ta dakatar da aiwatar da dokokin DE...
03/06/2026

Hukumar Kare Hakkin Masu Amfani da Kaya da Hidima ta Tarayya (FCCPC) ta bayyana cewa ta dakatar da aiwatar da dokokin DEON na shekarar 2025 ne bisa umarnin wata kotun tarayya da ke Legas.

Hukumar ta ce ta dauki wannan mataki ne domin bin doka da oda bayan kotun ta hana ci gaba da aiwatar da dokokin har sai an kammala shari’ar da ake yi kan su.

Dakatarwar ta samu karbuwa daga kungiyoyin masu ruwa da tsaki a bangaren sadarwa, musamman Kungiyar Masu Lasisin Kamfanonin Sadarwa ta Najeriya (ALTON), wadda ta ce matakin zai taimaka wajen dawo da sabis na rancen katin waya da bayanan intanet ga miliyoyin masu amfani.

A cewar kungiyar, kusan mutane miliyan 40 ne s**a rasa damar amfani da wadannan ayyuka bayan da manyan kamfanonin sadarwa s**a dakatar da su saboda sabanin da ya taso tsakanin FCCPC da Hukumar NCC.

Yayin da kamfanonin Airtel da Globacom s**a riga s**a dawo da sabis na rancen kati, har yanzu MTN ba ta maido da shi ba, tana mai cewa tana jiran karin haske daga bangaren shari’a kafin ta dauki mataki.

ALTON ta bukaci FCCPC da NCC su kara hada kai a nan gaba domin kauce wa irin wannan rikicin dokoki da ka iya shafar masu amfani da harkokin sadarwa a kasar.

Jam’iyyar APC ta bayyana cewa za ta yi aiki domin ƙara yawan mata a muƙaman zaɓe da na naɗi gabanin zaɓen shekarar 2027....
03/06/2026

Jam’iyyar APC ta bayyana cewa za ta yi aiki domin ƙara yawan mata a muƙaman zaɓe da na naɗi gabanin zaɓen shekarar 2027.

Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Nentawe Yilwatda, ya bayyana haka yayin da yake karɓar shugabar matan APC ta ƙasa, Mary Alile, tare da shugabannin mata daga shiyyoyi da jihohi a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.

Yilwatda ya ce mata sun taka muhimmiyar rawa wajen gina jam’iyyar, yaƙin neman zaɓe da samun nasarori a zaɓuka, don haka ya kamata su samu ƙarin wakilci a majalisun dokoki, muƙaman gwamnati da shugabancin jam’iyya.

Ya jaddada cewa cancanta ce ya kamata ta zama ma’aunin ba wa mutum muƙami, ba jinsi ba, yana mai cewa mata a APC suna da ƙwarewar da za ta ba su damar gudanar da manyan muƙamai.

Ya kuma yi alƙawarin mara wa mata baya wajen samun muƙamai da shiga kwamitocin yaƙin neman zaɓe a 2027, yana mai cewa manufar “federal character” ba ta taƙaitu ga yankuna kaɗai ba har da daidaiton jinsi.

A nata ɓangaren, Mary Alile ta yaba wa shugabancin Yilwatda tare da kira da a ƙara bai wa mata damar shiga harkokin mulki, tana mai cewa sun taka muhimmiyar rawa wajen nasarorin APC da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu.

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Alfijir Radio posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Alfijir Radio:

Share

Category