Hausa.Com

Hausa.Com "Hausa.Com" gidan labarun hausa, da sauran abubuwan da s**a shafi yau da kullum Hausa.Com☑️

08/03/2025

Yau ne ranar mata ta duniya wace shawara zakuba
Mata ayau

TIRƘASHI: Wani Lokacin Idan Yazomin Ji Nake Kamar Na Yi Kuka, Bobrisky Ya Bayyana Yadda Yake Shan Azaba Yayin Da Jin|n A...
07/12/2024

TIRƘASHI: Wani Lokacin Idan Yazomin Ji Nake Kamar Na Yi Kuka, Bobrisky Ya Bayyana Yadda Yake Shan Azaba Yayin Da Jin|n Al'ad@ Yazo Masa.
Bobriski

YAU RANAR HAUSA 26/8/2024Ranar Hausa (Ko kuma  ) da turanci Hausa Day, Rana ce da aka keɓance domin nuna muhimmancin har...
26/08/2024

YAU RANAR HAUSA 26/8/2024

Ranar Hausa (Ko kuma ) da turanci Hausa Day, Rana ce da aka keɓance domin nuna muhimmancin harshen Hausa, da tattauna hanyoyin bunƙasa shi da kuma jawo hankali akan irin ƙalubalen da harshen yake fuskanta.an fara bikin farko a shafukan sada zumunta musamman ta shafin twitter da niyyar hada L1 da L2 na masu magana da harshen Hausa. An zaɓi ranar 26 ga watan Augusta domin tuna ranar da aka ƙirƙiro haruffan "ƙ" da "ɗ" da "ɓ" wanda babu su a haruffan Turanci.

A Yayin bikin na cika shekara 5, mutane fiye da 400,000 s**a gudanar da bikin ta yanar gizo da wasu kasashen da Hausawa suke zaune a sassa daban daban na duniya irinsu Faransa, Amurka, Kamaru, Ghana, Nijar, da Najeriya, kuma a irin wanan rana hausawa na duniya na cika shafukan zumunta da da zantuttuka masu nuna Alfahari da yarensu, wasu wajajen s**an shirya bukukuwa a wanan rana.

Asali

Ranar Hausa dai ta samo asali ne a shekarar 2015 bayan ɗan jarida Abdulbaqi Aliyu Jari da wasu abokansa na shafukan sada zumunta s**a ayyana ranar a matsayin ranar da masu magana da harshen Hausa za su haɗu su tattauna ci gaba da kalubalen da harshen ke fuskanta a karni na 21. Kuma ana bikin Ranar Hausar ne a 26 ga watan Agustan kowace shekara a Duniya.

Muhimmanci

An ƙirƙiri wannan rana ce domin duba da mahinmancin ta ko kuma mahinmancin da zata bada. Makasudin wannan rana dai itace. Domin ciyar da yaren hausa gaba, al'ummar su, al'adunsu da kuma samun hadin kan hausawa a duniya baki daya.

A kowace shekara idan ranar ta zagayo ma'abota shafukan sada zumunta ke yin amfani da tambarin domin tattaunawa da yin muhawara.

Nasarorin da aka samu

Wadanda s**a ƙirƙiro wannan ranar sun ce sun yi haka ne domin tuna wa da al'ummar Hausa game da muhimmancin harshen da yadda za a ciyar da shi gaba.

Sannan kuma ranar ta kasance a matsayin wata rana da ake ƙalubalantar al'ummar Hausawa domin fiddo da sabbin bincike da nazarce-nazarce domin habbaka harshen na Hausa.

Babbar nasarar da za a ce

Assalamu Alaikum Masoya Manzon Allah Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi wa Alihi Wasallama).Barkan Ku Da Safiya 🕌Yau lit...
12/08/2024

Assalamu Alaikum Masoya Manzon Allah Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi wa Alihi Wasallama).

Barkan Ku Da Safiya 🕌

Yau litini 12 Ga Watan Agusta 2024.

Ranar 12 ga Watan August ce rana ta 224 a cikin Shekara A Kalandar MIladiyya; Yau Ya Rage Saura 141 Zuwa Karshen Shekara. Wanda Yayi daidai da 7 Ga Watan Safar na Shekara 1446 Bayan Hijirar Manzo Allah Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi wa Alihi Wasallama), Daga Makkah 🕋 Zuwa Madina 🕌 Yau Ya Rage Saura Kwanaki 200 cif A Soma Azumin Watan Ramadan Mai Albarka. Wanda Za A Fara a Ranar Juma'a 28 Ga Watan Fabrairu Na Shekarar 2025 In Sha Allah 🙏🙏🙏.

Ya kamata APC Kano ta janye kalamanta da neman afuwa akan zargina da AUDU BULAMA BUKARTI da Jaafar Jaafar akan tayar da ...
12/08/2024

Ya kamata APC Kano ta janye kalamanta da neman afuwa akan zargina da AUDU BULAMA BUKARTI da Jaafar Jaafar akan tayar da tarzoma nan da awa 48. In ba haka ba, za’a shiga NEXT LEVEL.
Inji matashinnan Dan bello

06/08/2024
Da safiyar yau Litinin:Zanga zanga yayi sanadin kawo karshen Gwamnatin Malama Hasina Sheikh ta kasar Bangladesh wacce ta...
05/08/2024

Da safiyar yau Litinin:

Zanga zanga yayi sanadin kawo karshen Gwamnatin Malama Hasina Sheikh ta kasar Bangladesh wacce ta shafe shekaru 15 tana mulkin kasar (daga 2009 zuwa yau 2024).
~ Asalin zanga zangar ta faro ne ranar Asabar data gabata daga wasu 'daliban Jami'o'i da s**a fito domin yin zanga zangar Lumana da yin korafi akan Gwamnatin Sheikh Hasina cewa lallai tayi gyara akan tsarin daukan aiki da gudanarwar gwamnatin kasar, inda s**a ce Prime Ministan din taki sauraren korafin su.

Masu korafin sun fusata ne tun bayan da kotun kolin kasar tayi hukunci cewa ba za'a gyara tsarin daukan aiki da salon gudanar da gwamnatin ba.
~ Matasan sunce tsarin yana favoring Prime Minister din ce da kuma jam'iyyar ta da wadanda suke a hannun daman PM. Sun ce arzikin kasar wasu tsiraru ne ke wadaka dashi.

Zanga zangar ta b***e daga Student Protest ta koma ta gama gari washegari (jiya) Lahadi, inda tayi zafi sosai, hakan yasa Hasina Sheikh ta fice daga kasar cikin gaggawa a cikin jirgi Mai saukar Ungulu na sojojin kasar.
~ A yanzu haka sojoji ke rike da kasar. Rundunar Sojin kasar tace ta kame iko da fadar shugaban kasar kuma za'a kafa Gwamnatin rikon kwarya (Interim Government) nan da watanni kadan masu zuwa.

Hasina Sheikh 'yar shugaban kasar Bangladesh na farko ne wato Sheikh Mujibur Rahman wanda shine shugaban kasa na farko a kasar.

Hasina Sheikh ta taba yin mulkin kasar daga 1996 zuwa 2001, sai kuma daga 2009 zuwa 2024 yau Litinin data ajiye mulkin kasar ko kuma Sojoji s**a kifar da gwamnatin nata bayan korafin matasan kasar yayi yawa kan salon mulkin ta.

Ku Karanta Cikakken Jawabin Shugaba Tinubu Na Safiyar Yau Cikin Harshen Hausa
04/08/2024

Ku Karanta Cikakken Jawabin Shugaba Tinubu Na Safiyar Yau Cikin Harshen Hausa

Gwarzon Shekarar✊ 2024. 🇳🇬
01/08/2024

Gwarzon Shekarar✊ 2024. 🇳🇬

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sa hannu kan dokar albashi mafi ƙanƙanta (naira 70,000) ranar Litinin a Fadar gwamnatin...
29/07/2024

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sa hannu kan dokar albashi mafi ƙanƙanta (naira 70,000) ranar Litinin a Fadar gwamnatin ƙasar.

Wasu ƴan majalisar kamar Shugaban Majalisar Dattijan Najeriya Sanata Godswill Akpabio da mataimakinsa Sanata Barau Jibrin bikin sanya hannun.

📸 - Dada Olusegun/X

AREWA MUFARKA...Matasan Nigeria sunkara harzuka da jaddada yin zangazanga Saboda ganin yadda wani dansiyasa ya siyama di...
21/07/2024

AREWA MUFARKA...
Matasan Nigeria sunkara harzuka da jaddada yin zangazanga
Saboda ganin yadda wani dansiyasa ya siyama diyarsa MOTA ta kimanin naira miliyan 36
Bayan ta kammala karatunta na makarantar secondary dake Abuja
Mezakuce gameda wannan




DA DUMI-DUMI: 💥💥Ƴan Bindiga Sun Sako Mahaifiyar Mawaki Dauda Adamu Abdullahi Kahutu RararaAllah Uban Giji Ya Kyauta Gaba...
17/07/2024

DA DUMI-DUMI: 💥💥
Ƴan Bindiga Sun Sako Mahaifiyar Mawaki Dauda Adamu Abdullahi Kahutu Rarara

Allah Uban Giji Ya Kyauta Gaba Ya Kara Tsare Mu Daga Wa'innan Mutane

Address

Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa.Com posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share