12/06/2026
Takaitattun Labaran Safe daga A M Hausa na 12 Yuni 2026
🇳🇬 Najeriya
•Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga masu ɗaukar nauyin ta’addanci da su mika wuya ko su fuskanci matakan gwamnati.
•Majalisar Dokoki ta ƙasa ta amince da kudirin kafa ‘yan sandan jihohi domin ƙarfafa tsaro a faɗin ƙasar.
•Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Dimokuraɗiyya (12 ga Yuni) a matsayin ranar hutu ta ƙasa.
•Sojojin saman Najeriya sun kai hare-hare kan maboyar ‘yan ta’adda a jihar Borno, inda aka ce an kashe wasu kwamandoji da mayaƙa.
Jihar Katsina
•Majalisar Dattawa ta nuna damuwa kan yunƙurin yin sulhu da ‘yan bindiga a wasu jihohi ciki har da Katsina.
•Dikko Umaru Radda ya bayyana sabon matsayi game da batun sulhu da ‘yan bindiga yayin da ake ci gaba da kokarin dawo da zaman lafiya a jihar.
•Jami’an tsaro na ci gaba da gudanar da ayyukan daƙile hare-haren ‘yan bindiga a yankunan da abin ya fi shafa.
Wane labari ne yafi jan hankalin ka?