09/05/2026
Gwamna Radda Ya Gana Da Masu Ruwa Da Tsaki na Jihar Katsina
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya yi kira da a inganta haɗin kai, kusanci da al’umma, da kuma inganta hanyoyin sadarwa tsakanin masu ruwa da tsaki na siyasa a jihar Katsina da yankin Arewa maso Yamma.
Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Abuja, wanda ya haɗa manyan jami’ai daga Katsina masu mukamai a gwamnatin tarayya, ‘yan majalisar dokoki, shugabannin hukumomi, ‘yan takarkari da sauran jiga-jigan siyasa.
Gwamna Radda ya jaddada buƙatar farfaɗo da kungiyar masu ruwa da tsaki na Jihar Katsina (Katsina Stakeholders’ Forum) domin ƙarfafa haɗin kai da haɗa hannu wajen ci gaban siyasa da shugabanci a jihar da yankin.
Haka kuma, ya buƙaci masu ruwa da tsaki su ci gaba da bayyana nasarori da manufofin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu tare da ƙarfafa hulɗa da al’umma ta hanyar amfani da kafafen sadarwa da kuma ƙarfafa ayyukan siyasa a daga tushe.
Taron ya kuma tattauna batutuwan shugabanci, siyasa, ƙara tallafawa hukumomin tarayya, da kuma damuwar da ake da ita kan ƙarancin wakilcin yankin Arewa maso Yamma a ɗaukar ma’aikatan gwamnatin tarayya.
MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government
May 9, 2026.