World News Post

World News Post Muna tabbatar da Sahihancin Labarai

13/05/2026

Majalissar Zartarwa ta Jihar Katsina ta amince da ƙarin kashi 100 na tallafin Karatu ga dukkan Ɗaliban Jihar...

Al'ummar Gusau Da Tsafe Sun Karɓa Kiran Eng. Fagacin Gusau Da Ya Zo Ya Wakilce su Abuja A Zaɓen Shekarar 2027 Daga Yusha...
13/05/2026

Al'ummar Gusau Da Tsafe Sun Karɓa Kiran Eng. Fagacin Gusau Da Ya Zo Ya Wakilce su Abuja A Zaɓen Shekarar 2027

Daga Yushau Gwashi

Al'umma sun gamsu azo ayi kato bayan kato a zaɓen fidda gwani da zai gudana 15 ga wata, kuma za su goyi bayansa domin yin nasara

Jirgin Farko na Alhazzai daga jihar Katsina, ɗauke da Maniyyata 411 ya tashi daga Jihar Katsina zuwa ƙasa mai tsarki, da...
11/05/2026

Jirgin Farko na Alhazzai daga jihar Katsina, ɗauke da Maniyyata 411 ya tashi daga Jihar Katsina zuwa ƙasa mai tsarki, da misalin ƙarfe 2:52 na yammacin yau Litinin.

Ɗan Gwamnan jihar Katsina, kuma Hakimin Radda, Muhammadu Dikko ya ziyarci Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II.📷- Majeeda Stu...
11/05/2026

Ɗan Gwamnan jihar Katsina, kuma Hakimin Radda, Muhammadu Dikko ya ziyarci Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II.

📷- Majeeda Studio

TIRKASHI: Agaichatta Guiccen Atta Kenan, Ministar Yawon Bude Ido Ta Kasar Nijar, Mai Shekaru 30 A DuniyaSannan ita ce ma...
10/05/2026

TIRKASHI: Agaichatta Guiccen Atta Kenan, Ministar Yawon Bude Ido Ta Kasar Nijar, Mai Shekaru 30 A Duniya

Sannan ita ce mace mafi karancin shekaru da aka baiwa mukami a tarihin gwamnatin Nijar.

Me za ku ce?

Gwamna Radda Ya Gana Da Masu Ruwa Da Tsaki na Jihar KatsinaGwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya yi kira da...
09/05/2026

Gwamna Radda Ya Gana Da Masu Ruwa Da Tsaki na Jihar Katsina

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya yi kira da a inganta haɗin kai, kusanci da al’umma, da kuma inganta hanyoyin sadarwa tsakanin masu ruwa da tsaki na siyasa a jihar Katsina da yankin Arewa maso Yamma.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Abuja, wanda ya haɗa manyan jami’ai daga Katsina masu mukamai a gwamnatin tarayya, ‘yan majalisar dokoki, shugabannin hukumomi, ‘yan takarkari da sauran jiga-jigan siyasa.

Gwamna Radda ya jaddada buƙatar farfaɗo da kungiyar masu ruwa da tsaki na Jihar Katsina (Katsina Stakeholders’ Forum) domin ƙarfafa haɗin kai da haɗa hannu wajen ci gaban siyasa da shugabanci a jihar da yankin.

Haka kuma, ya buƙaci masu ruwa da tsaki su ci gaba da bayyana nasarori da manufofin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu tare da ƙarfafa hulɗa da al’umma ta hanyar amfani da kafafen sadarwa da kuma ƙarfafa ayyukan siyasa a daga tushe.

Taron ya kuma tattauna batutuwan shugabanci, siyasa, ƙara tallafawa hukumomin tarayya, da kuma damuwar da ake da ita kan ƙarancin wakilcin yankin Arewa maso Yamma a ɗaukar ma’aikatan gwamnatin tarayya.

MS Ingawa
SSA, Media & Strategy
Katsina State Government

May 9, 2026.

A yau, 09/05/2026, ana cigaba da gudanar da AUREN GATA, wanda yanzu haka ake gudanarwa a kananan hukumomin jihar nan bak...
09/05/2026

A yau, 09/05/2026, ana cigaba da gudanar da AUREN GATA, wanda yanzu haka ake gudanarwa a kananan hukumomin jihar nan baki daya.

SIYASAR KATSINA2027: Shugaban Matasan Jam'iyyar APC, Honarabul Ismail Ƴandaki Ya Fice Daga Jam'iyyar A Katsina Ɗaya Daga...
08/05/2026

SIYASAR KATSINA2027: Shugaban Matasan Jam'iyyar APC, Honarabul Ismail Ƴandaki Ya Fice Daga Jam'iyyar A Katsina

Ɗaya Daga Cikin Shugabannin Jam'iyyar APC Na Jihar Katsina Kuma Shugaban Matasan Jam'iyyar APC Na Shiyyar Katsina, Honarabul Ismail Ƴandaki Ya Fice Daga Jam'iyyar APC.

Honarabul Ismail Ƴandaki Ya Bayyana Ficewarsa A Shafinsa Na Facebook Inda Ya Bayyana Cewa Na Fita Daga Jam'iyyar APC Tare Da Ajiye Muƙamina A Matsayin Shugaban Matasa Na Shiyyar Katsina, Za Mu Fara wata Sabuwar Tafiya.

Da duminsa; Dan majalisar wakilai na mazabar Kankara/Faskari/Sabua Hon Engr Shehu Dalhatu Tafofi ya fice fit daga APC ya...
08/05/2026

Da duminsa; Dan majalisar wakilai na mazabar Kankara/Faskari/Sabua Hon Engr Shehu Dalhatu Tafofi ya fice fit daga APC ya koma PDP, tare da yankar tikitin sake tsayawa takarar kujerar a jam'iyyar adawa ta PDP

Dan majalisar ya kuma kai ma madugun adawar PDP na jihar Katsina Sen Yakubu Lado Danmarke fom din don ya sa masa albarka

Wane fata kuke wa wannan dan majalisar?

Iran ta ce ta ƙwace wani jirgin dakon man fetur da ta bayyana a matsayin “mai laifi” a yankin Tekun Oman (Gulf of Oman)....
08/05/2026

Iran ta ce ta ƙwace wani jirgin dakon man fetur da ta bayyana a matsayin “mai laifi” a yankin Tekun Oman (Gulf of Oman).

Minene kuke tinanin babban abinda ya jawo yi masu hakan ku bayyana mamu ra'ayin ku.

Ya kamata IGP ya bada umarnin gaggawa wajen binciken wanda ake zargi da kashe Dadiyata - Lauya Barista Abba Hikima.Shaha...
08/05/2026

Ya kamata IGP ya bada umarnin gaggawa wajen binciken wanda ake zargi da kashe Dadiyata - Lauya Barista Abba Hikima.

Shahararren Lauya a Nijeriya ya jawo hankalin Babban Sufeton 'yan sandan Nijeriya game da wani mutum da ake wa zargi mai ƙarfi da hannu wajen kashe Dadiyata.

Lauyan ya ce “Babban Sufeton ‘Yan Sanda ya kamata ya bayar da umarnin gaggauta gudanar da bincike mai gaskiya, mai zaman kansa kuma sahihi kan wannan babban zargi.

“Wani Muhammad Musa, tsohon SSA ga Mawatawallen Maradun, ya yi iƙirarin cewa shi da idanunsa ya shaida yadda wani ɗan sanda mai suna Hussaini Gimba ya kashe DADIYATA.

“Idan wannan gaskiya ne, to wannan kaɗai ya isa ya zama hujjar da za ta tabbatar an yi adalci a wannan lamari na musamman da ya daɗe yana ɗaure wa ‘yan Najeriya kai.” Inji Barista Abba Hikima.

Address

Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when World News Post posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share