Freedom Hausa

Freedom Hausa Freedom Hausa
Domin samun labaran cikin gida da na ketare.

Wata kungiya a jihar Kano, ta turawa majalisar dokokin jihar Kano takaddar neman a rushe sabbin masarautun jihar, tare d...
07/02/2024

Wata kungiya a jihar Kano, ta turawa majalisar dokokin jihar Kano takaddar neman a rushe sabbin masarautun jihar, tare da dawo da Sunusi Lamido Sunusi, a matsayin Sarki. Me za ku ce akan wannan kudiri nasu?

07/02/2024

Da Ɗumi-ɗumi: Jami'ar Wudil ta dakatar da Malamin daya Mari Ɗalibai da sanya su tsallan ƙwaɗo, kuma za ta daƙile faruwar hakan.

07/02/2024

Zabi Daya
Nigeria taci ko 100k ??

Majalisar dattawan Najeriya, ta gayyaci hafsoshin tsaron Najeriya kan sace dalibai a jami'o'i.
06/10/2023

Majalisar dattawan Najeriya, ta gayyaci hafsoshin tsaron Najeriya kan sace dalibai a jami'o'i.

Duk Wanda Yasan Yayi Rejister To Ba Sai Yakaraba .Mai girma mistar harkaki jinkai da rage radadin talauci,  Dr bette edu...
06/10/2023

Duk Wanda Yasan Yayi Rejister To Ba Sai Yakaraba .

Mai girma mistar harkaki jinkai da rage radadin talauci, Dr bette edu, tace za'ayi amfani da tsohon register da akayi ne abay wajen biyan kudi sannan za'akara mutum 3m daga wurarenda ya dace a fadin kasar, register zai fara daga wannan watan da muke ciki na October Sannan za'abiya nan bada jimawa ba

RRR Ga Lambobin Wasu Jahohin Najeriya

Kowa yayi kokari yacika idan kuma kataba cikawa bakasamu kajira

Abia – *969*44 #
Bayelsa – *969*53 #
Kogi – *969*26 #
Imo – *969*235 #
Rivers State – *969*50 #
Ebonyi – *969*44 # *969*40 # for Ohaukwu-ebonyi
Ekiti – *969*52 #
NASARAWA STATE: – *969*90 #
Lagos – *969*98 #
Katsina – *969*77 #
Gombe code- *969*76 #
Adamawa – *969*22 #
Maiduguri – *969*10 #
Osun State – *969*54 #
Oyo – *969*20 #
Bauchi – *969*113 #
Abuja – *969*67 #
Sokoto State. *969*84 #
Yobe -*969*12 #
Anambra – *969*22 #
Akwa Ibom – *969*52 #
Cross River – *969*54 #
Kebbi – *969*86 #
Taraba – *969* 66 #.

Gwamnan jihar Katsina Malam Dr. Dikko Umaru Radda, zai dauki nauyin dalibai 'yan asalin jihar Katsina zuwa karatu kasash...
04/10/2023

Gwamnan jihar Katsina Malam Dr. Dikko Umaru Radda, zai dauki nauyin dalibai 'yan asalin jihar Katsina zuwa karatu kasashen waje.

Mai girma gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, PhD, ya amince da a fara tattara takardun neman guraben Karatu (wato scholarship) daga dalibai ‘yan asalin jihar Katsina zuwa Jami’o’in Kasashen waje wanda Gwamnatin Jiha za ta dauki nauyinsu.

Kwasakwasan da za a karanta sune; Karatun ilimin likita (wato MBBS) Karatun ilimin kirkire-kirkiren Na’ura mai kwakwalwa dake da kaifin basira (wato Artificial Intelligence) Karatun ilimin tattalin arziki dake da alaka da hallittu da tsirrai. (wato Bio-Economy).

Daliban da suke da sha’awar shiga shirin su kasance suna da takardu kamar haka:-
Takardar Sakamakon gama makarantar sakandare WAEC/NECO a zama guda, da yabo (wato credit) akalla takwas (8) a darussa kamar haka:-

Darasin ilimin kwakwaf (Physics)
Darasin ilimin hada magunguna (Chemistry)
Darasin ilimin sanin hallittu da tsirrai (Biology), kona Ilimin Aikin Gona (Agric Science)
Darasin Turanci
Darasin Lissafi
Darasin ilimin Na’ura Mai Kwakwalwa [a inda keda bukatar haka]

Bugu da kari, daliban da ke neman karatun likitanci (wato MBBS), wajibi ne su kasance suna da sakamako mai daraja ta “A” ko “B” akalla a darussa ukku masu alaka.
Sauran Kwasakwasan biyu kuma (wato, Artificial intelligence da Bio Economy) dole dalibi ya kasance yana da sakamako mai matakin daraja “A” ko “B” akalla guda biyu (2).
Sannan dole dalibi ya kasance bai gaza shekaru goma sha shidda (16) ba, kuma bai wuce shekaru ashirin da biyu (22) ba na haihuwa a lokacin neman wannan gurbin Karatu.
Daliban da s**a gama makarantun gwamnati kawai ne za su shiga wannan shiri.
Sannan Kowace Karamar Hukuma za ta samu wakilci a cikin daliban da za a tantance a kuma dauka.

Za a aiko da takardun neman gurbin karatun tare da Takardun shaidar gama makarantar primary da na sakandare WAEC/NECO, Takardar haihuwa, Takardar shaidar zama dan Karamar hukuma, Takardar shaidar nuna hali n

'Yan bindiga sun sace dalibai mata guda biyar cikin daren jiya Talata na jami'ar FUDMA, da ke karamar hukumar Dutsinma j...
04/10/2023

'Yan bindiga sun sace dalibai mata guda biyar cikin daren jiya Talata na jami'ar FUDMA, da ke karamar hukumar Dutsinma jihar Katsina. Muna Addu'ar Allah ya kubutar dasu cikin aminci, Allah ya kawo mana karshen wannan musifan.

03/10/2023

Ministar kula da walwala da rage radadin talauci, Betta Edu ta fara tantance iyalai masu fama da talauci da za a riƙa turawa tallafin dubu 25 duk wata har tsawon watanni Uku

Yanzu ta fara da jihar Lagos

YANZU YANZU: Mahukunta Nijeriya sun saki fasfo ɗin Sheikh Ibrahim Zakzaky.Daga Fatima Nuraddeen Dutsin-ma.“A wani rahoto...
02/10/2023

YANZU YANZU: Mahukunta Nijeriya sun saki fasfo ɗin Sheikh Ibrahim Zakzaky.

Daga Fatima Nuraddeen Dutsin-ma.

“A wani rahoto dake Bayyana mana yanzu haka cewa mahukunta Nijeriya sun saki fasfo Jagoran Harkan Musulunci a Nijeriya Sheikh Ibrahim Zakzaky.

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta saki fasfo ɗin jagoran Harkar Musulunci da aka fi sani da 'yan Shi'a wato Shaikh Ibraheem Zakzaky wanda sanadiyar riƙe fasfo ɗin nasa yasa bai bar Nijeriya ba domin fita ƙasar waje neman lafiyasa tun bayan sakinsa da wanke shi da kotu ta yi da shi da mai ɗakinsa shekaru 2 da s**a gabata.”

Abokiyar kungiyar kwadago wato TUC ta sanar da batun fasa shiga yajin aikin sai baba-ta-gani. Sauran kungiyar kwadago NL...
02/10/2023

Abokiyar kungiyar kwadago wato TUC ta sanar da batun fasa shiga yajin aikin sai baba-ta-gani. Sauran kungiyar kwadago NLC.

Da Dumi-Dumi!Ta tabbata Bola Tinubu namu na Najeriya amfani yayi sa certificate din wata mace mai suna Bola A. Tinubu da...
02/10/2023

Da Dumi-Dumi!

Ta tabbata Bola Tinubu namu na Najeriya amfani yayi sa certificate din wata mace mai suna Bola A. Tinubu da tayi karatu a Chicago State University.

Daga Abba Hajiya

02/10/2023

Har zuwa yanzu cikin daren nan, kungiyar kwadago suna chan fadar shugaban kasa, suna ta tattaunawa, muna sa ran jin matsayar da s**a yanke, da zaran sun fito daga tattaunawar.

Address

Katsina

Telephone

+2347061811216

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Freedom Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Freedom Hausa:

Share