Accuracy News 24/7

  • Home
  • Accuracy News 24/7

Accuracy News 24/7 Katsina

Na Gamsu Da Cire Tallafin Mai Da Shugaban Kasa Tinubu Ya Yi - Cewar Mawaki RararaShahararren mawakin siyasa a Najeriya D...
03/06/2023

Na Gamsu Da Cire Tallafin Mai Da Shugaban Kasa Tinubu Ya Yi - Cewar Mawaki Rarara

Shahararren mawakin siyasa a Najeriya Dauda Adamu Kahutu Rarara, ya bayyana cewa ya ji dadi akan cire tallafin mai da sabon Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi a Najeriya.

Mawaki Rarara ya bayyana wannan matsaya tashi ne a wata tattaunawa da ya yi da Kafar Sadarwa ta DCL, kuma Accuracy News 24/7 ta kalato.

A cewar Rarara, Tinubu ya cire tallafin mai ne ba don ya kuntata ma yan Najeriya ba ne, illa iyaka wani mataki ne na fara daidaita lamurra a Kasar, bayan da aka rantsar da shi a matsayin Shugaban Kasa.

Dama dai tuni da damar yan Najeriya ke ta kiraye-kiraye akan cire tallafin man, inda suke ganin cewa baya da wani amfani ga talakawan Najeriya, domin kuwa wasu tsirarun mutane ne ke amfana da shi.

A cewar Rarara" Tinubu da dukkan iyalan shi masu arziki ne, ba sun zo mulkin Najeriya ba ne don su karu da kudin Kasar, dukkan su da shi Tinubu da matar shi da ya'yan shi duk masu arziki ne, basu bukatar ko sisin kwabon Najeriya.

A sabili da haka ya bukaci yan Najeriya akan su yi uzuri ga Shugaban Kasar, inda ya tabbatar da cewa da izinin Allah cire tallafin man zai zama alkairi ga yan Kasar, domin ba an yi shi ba ne don a kuntata masu, sai dai don a kawo gyara.

Mawaki Rarara ya kuma roki yan Najeriya akan su kara jajurcewa wurin gudanar da addu'oin samun nasarar sabuwar Gwamnatin ta Tinubu, domin inganata rayuwa da kyautata jin dadin su.

Mai tsawatarwa Na Majalissar Dokokin Jihar Adamawa, Haruna jilantikiri, Ya Koma Tuka Keke Domin Nuna Rashin Amincewarsa ...
03/06/2023

Mai tsawatarwa Na Majalissar Dokokin Jihar Adamawa, Haruna jilantikiri, Ya Koma Tuka Keke Domin Nuna Rashin Amincewarsa Da Matakin Da Gwamnatin Tinubu Ta Dauka Na Cire Tallafin Man Fetur A Najeriya.

Hoto: Amina Abdullahi Yola

Yadda Wani Kwamarad Ya Tsara Harkokin Rayuwar Shi Na Yau Da Kullum Bayan Cire Tallafin Man FeturA matsayina na Kwamarad ...
03/06/2023

Yadda Wani Kwamarad Ya Tsara Harkokin Rayuwar Shi Na Yau Da Kullum Bayan Cire Tallafin Man Fetur

A matsayina na Kwamarad Zubairu Magaji Ahmad na yanke hukunci Kamar haka:

1. Duk wata tafiya da zata lashe abinda yakai N1000 NA SOKE TA. Wannan ya shafi tarurruka, daure-dauren aure, wanda ya Zama dole.

2. Duk tafiyar da Zan kashe N2000 wadda bazan samo N5000 ba na SOKE TA.

3. Tafiyar da Zan samu daidai kudin da na kashe kuwa sai nayi dogon nazari.

4. Zan kwana biyu ba'a ganni online ba, saboda cike gibin da janye tallafin man fetur ya jawo.

Wannan matsaya sai abinda Allah yayi jama'a.

Nagode
Cmrd.Zubairu Magaji Ahmad
C.E.O: ZBINMAK3 GLOBAL RESOURCES
Just for fun😂😅😅😅

An Kaddamar Da Sabon Tambarin Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Kwararu Ta Najeriya, Tare Da Canza Sunan Gasar Daga NPFL, ...
02/06/2023

An Kaddamar Da Sabon Tambarin Gasar Cin Kofin Kwallon Kafa Ta Kwararu Ta Najeriya, Tare Da Canza Sunan Gasar Daga NPFL, Zuwa ( Nigeria Premier League) Wato Firimiyar Najeria.

Amarya Da Ango.Allah Ya Bada Zaman Lafiya Da Zuri'a Dayyiba.
02/06/2023

Amarya Da Ango.

Allah Ya Bada Zaman Lafiya Da Zuri'a Dayyiba.

Tsohan Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari Ya Kai Ziyara A Fadar Mai Martaba Sarkin Daura Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buh...
02/06/2023

Tsohan Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari Ya Kai Ziyara A Fadar Mai Martaba Sarkin Daura

Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, Ya kai ziyarar barka da juma'a a fadar mai martaba Sarkin Daura Alhaji Faruk Umar Faruk.

Ziyarar na da nufin mika godiya ga Mai Martaba Sarkin akan gagarumar Daba da aka shirya mashi, a lokacin da ya dawo gida bayan karewar wa'adin mulkin shi.

Raɗe-raɗin Cewa Na Mallaki Naira Tiriliyan 9 Labarin Kanzon Kurege Ne - Cewar Gwamna Lawal Dauda DareGwamnan jihar Zamfa...
02/06/2023

Raɗe-raɗin Cewa Na Mallaki Naira Tiriliyan 9 Labarin Kanzon Kurege Ne - Cewar Gwamna Lawal Dauda Dare

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya musanta ikirarin da ake yi na cewa ya bayyana kadarorin da ya kai naira triliyan 9.

Gwamnan a wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sulaiman Idris ya fitar a ranar Juma’a a Gusau, ya bayyana labarin a matsayin ƙage da aka shirya domin kawar da hankalin sabuwar gwamnati daga yunƙurinta na ceto Zamfara.

Ya kara da cewa wadanda s**a fadi zabe ne s**a yaɗa ƙarairayin, kamar yadda s**a yi a lokacin yaƙin neman zabe.

Sanarwar ta bayyana cewa sabuwar gwamnati ta fara aiki kuma ta mayar da hankali wajen ganin ta samar da natsuwar da ake bukata a cikin harkokin mulki a jihar domin sauke nauyin alhakin da ke kan ta.

Sanarwar ta kara da cewa: “Ba za a dauke mana hankali da irin wadannan labaran na karya da ke kafafen sada zumunta ba, domin gwamnatinmu ta kuduri aniya kuma ta mayar da hankali kan kudirinta na magance matsalar tsaro da ilimi da samar da ruwan sha da inganta kiwon lafiya da noma da sauran kalubalen tattalin arziki da s**a addabi jihar.

Muna kuma aiki ba dare ba rana domin ganin mun sauke nauyi da ayyukan da gwamna ya yi alkawrin gudanarwa.” kamar yadda sanarwar ta ce.

Gwamnan ta bakin mai magana da yawunsa ya ce gwamnatinsa na matukar aiki a kokarinta na cetowa da kuma sake gina jihar Zamfara, inda ta mayar da hankali wajen ganin ta cika alkawuranta.

Ya kuma buƙaci jama’a da su yi watsi da ƙaryar da ake yaɗawa da gangan domin a ɓata wa sabuwar gwamnatinsa suna.

Dan Majalissar Tarayya Na Mazabar Mashi Da Dutsi Da Hukumar Zabe Ta Baiwa Takardar Sheda, Nazifi MB Mashi, Ya Ziyarci Da...
02/06/2023

Dan Majalissar Tarayya Na Mazabar Mashi Da Dutsi Da Hukumar Zabe Ta Baiwa Takardar Sheda, Nazifi MB Mashi, Ya Ziyarci Dan Takarar Gwamnan Jihar Katsina Na Jam'iyyar PDP Sanata Yakubu Lado Danmarke.

Tsadar Man Fetur A Najeriya.......Wani Dalibin Jami'ar Maiduguri Kenan Da Ya Fara Zuwa Makaranta Akan Jakin Sa Sabili Da...
02/06/2023

Tsadar Man Fetur A Najeriya.......

Wani Dalibin Jami'ar Maiduguri Kenan Da Ya Fara Zuwa Makaranta Akan Jakin Sa Sabili Da Tsadar Man Fetur Da Ake Fuskanta A Najeriya.

NLC Zata Shiga Yajin Aiki Akan Cire Tallafin Man FeturKungiyar Kwadago ta Najeriya NLC, ta shirya shiga yajin aiki na ga...
02/06/2023

NLC Zata Shiga Yajin Aiki Akan Cire Tallafin Man Fetur

Kungiyar Kwadago ta Najeriya NLC, ta shirya shiga yajin aiki na game gari bisa ga cire tallfin man fetur da gwamnatin Kasar ta yi.

Majiyar Accuracy News 24/7 ta bayyana cewa, Kungiyar zata tsunduma yajin aikin game garin ne a ranar Laraba mai zuwa, idan har Gwamnatin Tarayya bata dauki wani mataki ba akan lamarin.

Idan dai za'a iya tunawa, Shugaban Kasa Ahmed Bola Tinubu ya sanar da cire tallafin man a cikin wannan mako, kamar yadda Gwamnatin baya ta tsara.

Lamarin cire tallfin man ya haifar da tashin gwauron zabi na kayan masarufi a fadin Kasar ta Najeriya, wanda ya sanya yan Kasar cigaba da kuka akan lamarin.

Masha Allah.Amarya Da Ango, Allah Ya Sanya Albarka Ya Basu Zaman Lafiya.
02/06/2023

Masha Allah.

Amarya Da Ango, Allah Ya Sanya Albarka Ya Basu Zaman Lafiya.

MB Mashi Ya Karbi Shedar Lashe Zabe Daga INEC Bayan Kotu Ta Kwace Daga MajigiriZababben Dan Majalissar Tarayya mai wakil...
02/06/2023

MB Mashi Ya Karbi Shedar Lashe Zabe Daga INEC Bayan Kotu Ta Kwace Daga Majigiri

Zababben Dan Majalissar Tarayya mai wakiltar Kananan Hukumomin Mashi da Dutsi Honorabul Nazifi MB. Mashi, ya karbi shedar lashe zaben shi daga Hukumar Zabe Ta Kasa Mai Zaman Kanta.

Mika shedar lashe zaben ga M.B Mashi ya biyo bayan hukuncin da kotu ta yanke inda aka amshi kujerar daga hannun Tsohon Shugaban Jam'iyyar PDP na Jihar Katsina Alhaji Salisu Yusuf Majigiri.

A sabili da hakan ne ya sanya Hukumar Zaben ta bi umarnin kotun kuma ta mika takardar shedar lashe zabe ga M.B Mashi.

Shugaban Majalissar Dokokin Jihar Katsina Ya Zama Jakadan Zaman Lafiya Na DuniyaWasu Kungiyoyin Kasa Da Kasa masu suna "...
02/06/2023

Shugaban Majalissar Dokokin Jihar Katsina Ya Zama Jakadan Zaman Lafiya Na Duniya

Wasu Kungiyoyin Kasa Da Kasa masu suna "Leeway Peace and Human Rights Foundation" da "Access To Human Rights International da "Alliance Of The People Of The World" da Cholan Book Of World Record da sauransu, sun karrama Shugaban Majalissar Dokokin Jihar Katsina Alhaji Tasi'u Musa Maigari, a matsayin Jakadan Zaman Lafiya na Duniya na shekarar 2023.

Majiyar Accuracy News 24/7 ta bayar da rohoton cewa, bikin bayar da lambobin yabon wanda ya gudana a dakin taro na Shugaban, ya samu halartar Dan Majalissa mai wakiltar Karamar Hukumar Kankia Alhaji Salisu Hamza Rimaye, da takwaran shi na Karamar Hukumar Ingawa Alhaji Abubakar Suleiman Tunas.

Mai magana da yawun Kungiyoyin ya bayyana cewa, sun yanke shawarar karrama Shugaban Majalissar ne bayan gudanar da zurfin bincike akan Shugaban Majalissar da ya fi tafiyar da harkokin shugabancin shi cikin salama a fadin Jihohin Najeriya.

A cewar shi, shugaban Majalissar ya bayar da dumbin gudummuwa ta fuskar tabbatar da kyakkyawar alaka tsakanin Majalissar da bangaren zartaswa na Jihar, wanda ya sanya aka cimma dumbin nasarori wajen shimfida dumbin ayyukan cigaba ga jama'ar Jihar Katsina.

Ya yi fatan cewa lambar yabon zata kara kwarin guiwa ga Shugaban Majalissar ta fuskar kara kaimi wurin kawo cigaban al'umma da Jihar Katsina baki daya.

A nashi jawabin, Shugaban Majalissar Alhaji Tasi'u Musa Maigari ya bayyana godiyar shi akan wannan karamci da Kungiyoyin s**a yi mashi.

Alhaji Tasi'u Musa Maigari ya danganta nasarorin da Majalissar ta samu bisa ga hadin kai da goyon bayan da ya samu daga yan uwanshi sauran yan majalissu, sai ya yi masu godiya akan hakan.

Daga nan sai ya bada tabbacin cewa zai kara jajircewa wurin taimakon al'umma da kuma kawo cigaban Jihar Katsina.

Shugaba Ahmed Bola Tinubu, Ya Gana Da Gwamnonin Jam'iyyar APC A Fadar Shugaban Kasa.
02/06/2023

Shugaba Ahmed Bola Tinubu, Ya Gana Da Gwamnonin Jam'iyyar APC A Fadar Shugaban Kasa.

Address


Telephone

+2347033444156

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Accuracy News 24/7 posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Accuracy News 24/7:

Shortcuts

  • Address
  • Telephone
  • Alerts
  • Contact The Business
  • Claim ownership or report listing
  • Want your business to be the top-listed Media Company?

Share