Fadak Media Hub

Fadak Media Hub Media for a better world!

Amadadin daukacin Ma'aikatan FADAK Media hub Muna taya Al'umma Murnar zagayowar babbar Sallah Eid kabir. Ayi shagalin bi...
27/05/2026

Amadadin daukacin Ma'aikatan FADAK Media hub Muna taya Al'umma Murnar zagayowar babbar Sallah Eid kabir. Ayi shagalin bikin sallah lafiya.
Mun gode da bibiyar shafukan mu da kuke a ko da yaushe. 👌🙏

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Laraba 27 ga Mayu da Alhamis 28 a matsayin ranakun hutu domin bikin Babbar Sallah na w...
25/05/2026

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Laraba 27 ga Mayu da Alhamis 28 a matsayin ranakun hutu domin bikin Babbar Sallah na wannan shekara.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Babbar Sakatariyar ma’aikatar ma’aikatar harkokin Cikin Gida, Magdalene Ajani ta fitar.

Sanarwar ta ce ministan Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo ya taya al’ummar Musulmin Najeriya da mazauna kasashen waje murnar bikin, yana mai bayyana Eid-el-Kabir a matsayin biki mai cike da darussan sadaukarwa, biyayya ga Allah Madaukakin Sarki da tausayi ga alumma.

Ministan ya bukaci ‘yan Najeriya da su yi amfani da lokacin Sallah wajen yin addu’o’i domin samun zaman lafiya, tsaro da ci gaban kasa

JAMB ta saki sakamakon jarrabawar UTME na ɗalibai 279 da ta riƙeHukumar shirya jarabawar shiga manyan makarantu ta ƙasa,...
21/05/2026

JAMB ta saki sakamakon jarrabawar UTME na ɗalibai 279 da ta riƙe

Hukumar shirya jarabawar shiga manyan makarantu ta ƙasa, wato JAMB, ta sanar da sakin sakamakon jarabawar UTME guda 279 da ta riƙe bisa zargin aikata maguɗin jarabawa.

JAMB ta bayyana cewa ta ɗauki matakin ne bayan gudanar da cikakken bincike kan wasu sakamakon da aka sanya wa ido tun lokacin gudanar da jarabawar da kuma bayan kammalawarta.

A cikin wata sanarwa da mai ba hukumar shawara kan hulɗa da jama’a, Dokta Fabian Benjamin, ya sanya wa hannu, an ce an saki wasu daga cikin sakamakon ne bayan bincike ya nuna babu hujjar da ke nuna ɗaliban sun yi maguɗi.

Sai dai hukumar ta ce ta soke sakamakon wasu ɗaliban da aka tabbatar sun aikata maguɗin jarabawa, yayin da ake ci gaba da bincike kan wasu cibiyoyin jarabawa da aka samu rahotannin ayyukan da ake zargi.

JAMB ta yi gargaɗin cewa duk ɗalibin da aka samu da laifi bayan kammala binciken, za a soke sakamakonsa.

Hukumar ta kuma buƙaci ɗaliban da har yanzu ba su ga sakamakonsu ba su duba matsayinsu ta hanyar aika saƙon “UTMERESULT” zuwa 55019 ko 66019 da lambar wayar da s**a yi rajista da ita.

Gwamnan jihar Kano, Engineer Abba Kabir Yusuf ya gargadi tsohon maigidan sa, Sanata Rabi'u Kwankwaso da kar ya dauki shi...
20/05/2026

Gwamnan jihar Kano, Engineer Abba Kabir Yusuf ya gargadi tsohon maigidan sa, Sanata Rabi'u Kwankwaso da kar ya dauki shiru-shiru da ya ke yi a matsayin tsoro.

Gwamnan na Kano na magana ne a lokacin babban taron kaddamar da Sulaiman Kawu Sumaila a matsayin Dan Takarar Majalisar Dattawa na Kano ta Kudu a karkashin jam'iyyar APC.

Engr. Abba Kabir ya yi barazanar cewa idan a ka kai shi bango, to zai fara maganganu.

Kusan wannan ne karon farko da a ka ji Abba Kabir Yusuf na kalubalantar Kwankwaso kai tsaye, tun lokacin da su ka raba gari a siyasance.

Ya bayyana cewa yin shiru a matsayin ibada ne ba wai tsoro ba ko kuwa yarinta, domin babu yadda za a yi dan shekara 69 ya kira dan Shekara 63 yaro.

Gwamnan na Kano ya roki bangaren na Kwankwaso da ya ja girman shi ya yi shiru, in ba haka ba to za su fara jin bayanai dalla dalla, baki da fassara.

Ya tabbatar da cewa zaman lafiyar Kano shi ne abinda ya ke ba fifiko, amma idan tura ta kai bango zai fara mayar da raddi.

Tsohon ministan tsaro, Theophilus Danjuma, ya bayar da gudunmawar Naira biliyan 3 yayin ƙaddamar da littafin tarihin tso...
20/05/2026

Tsohon ministan tsaro, Theophilus Danjuma, ya bayar da gudunmawar Naira biliyan 3 yayin ƙaddamar da littafin tarihin tsohon shugaban ƙasa, Yakubu Gowon mai suna “My Life of Duty and Allegiance” da aka gudanar a Abuja ranar Talata.

Haka kuma shugaban rukunin kamfanonin Dangote, Aliko Dangote, ya sayi kwafi 25 na littafin kan Naira miliyan 500 ta hannun wakilinsa, Mansur Ahmed.

Shugaban BUA Group, Abdul Samad Rabiu, shi ma ya sayi kwafi na littafin da kudinsu ya kai naira miliyan 25.

Rahotanni sun bayyana cewa Danjuma ya kuma umarci a saya tare da rabawa dakunan karatu na jami’o’i 20 da s**a bai wa Gowon digirin girmamawa.

Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ne ya wakilci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu a wajen taron da ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, jakadu da manyan hafsoshin soja.

A jawabinsa, Danjuma ya yabawa Gowon kan rawar da ya taka wajen haɗa kan Najeriya bayan yaƙin basasa, musamman ta hanyar manufarsa wadda ya ce ta taimaka wajen sulhunta ƙasa da dawo da zaman lafiya bayan yaƙin.

Trump ya yi fatali da tsarin yarjejeniyar zaman lafiya da Iran ta gabatarShugaban Amurka Donald Trump ya yi watsi da tsa...
13/05/2026

Trump ya yi fatali da tsarin yarjejeniyar zaman lafiya da Iran ta gabatar

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi watsi da tsarin yarjejeniyar zaman lafiya da Iran ta gabatar, biyo bayan da Washington ta gabatar da buƙatar a tsagaita wuta a rikicin da ke tsakanin su.

Kafin wannan lokaci dai Iran ta jaddada cewa ba za ta kawar da kai daga duk wani yunkurin Amurka na farmakar ta ba, ko kuma bai wa jiragen yaki damar wucewa ta mashigin 'Strait of Hormuz'.

Sai dai a dandalinsa na Truth Social, Trump ya bayyana watsi da tsarin da Iran ta gabatar, ba tare da ya yi karin bayani ba, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya isa birnin Nairobi na ƙasar Kenya domin halartar taron Africa-France Summit da za a g...
13/05/2026

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya isa birnin Nairobi na ƙasar Kenya domin halartar taron Africa-France Summit da za a gudanar daga ranar 11 zuwa 12 ga watan Mayu.

Ministan Harkokin Waje na Kenya, Musalia Mudavadi, tare da Ministar Harkokin Wajen Najeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu da Babban Jakadan Kenya a Najeriya, Ambasada Isaac Parashina, ne s**a tarbi shugaban ƙasar.

Ana sa ran taron zai ƙara ƙarfafa kudirin Najeriya na zurfafa alaƙar haɗin gwiwa da ƙasashen Afirka da kuma France a fannoni daban-daban.

An rantsar da Museveni mai shekaru 81 a matsayin shugaban Uganda wa’adi na 7 Shugaban Uganda, Yoweri Museveni, ya sake s...
13/05/2026

An rantsar da Museveni mai shekaru 81 a matsayin shugaban Uganda wa’adi na 7

Shugaban Uganda, Yoweri Museveni, ya sake shan rantsuwa domin fara wa’adi na bakwai a jere, lamarin da ya kara tsawaita mulkinsa na kusan shekaru 40, bayan nasararsa a zaben da ake takaddama a kai da aka gudanar a watan Janairu.

Museveni mai shekaru 81, wanda ya hau mulki tun 1986 bayan ya jagoranci tawaye, ya yi rantsuwar ne a birnin Kampala karkashin tsauraran matakan tsaro da jibge motocin yaki a manyan hanyoyi.

Hukumar zaben Uganda ta ce Museveni ya samu sama da kashi 70 cikin 100 na kuri’un da aka kada, kuma wa’adinsa zai kai har zuwa shekarar 2031.

13/05/2026

An gudanar da Taron "mercy corps " ta cibiyar kula da Yan gudun hijira ta majalisar dinky duniya hadin gwiwa da Gwamnatin jihar katsina
Taron ya tattauna muhimman abubuwa ta s**a shafi hanyoyin da za abi domin daukar matakan kara inganta zaman lafiya a jihar katsina.

Da alama jam'iyyar ADC ta rushe – AkpabioShugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana cewa jam’iyyar hadaka ...
06/05/2026

Da alama jam'iyyar ADC ta rushe – Akpabio

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bayyana cewa jam’iyyar hadaka ta ADC na dab da mutuwa sakamakon yawan ‘yan majalisa da ke ficewa daga cikinta.

Akpabio ya yi wannan bayani ne yayin da yake karanta wasiƙun ficewar wasu ‘yan majalisa daga jam’iyyar, ciki har da ta Sanata Eyinnaya Abaribe, wanda ya koma jam’iyyar Labour Party.

A cikin raha, shugaban majalisar ya shawarci masu ficewa da su riƙa haɗa wasiƙarsu wuri guda, domin kauce wa yawan karanta wasiƙu a kai a kai a zauren majalisa.

Maganar tasa ta jawo dariya daga ‘yan majalisar da ke wurin.

Cikin Hotuna Yadda Ƙungiyar tseren Dawaki ta garin Daura “Premier Horse Racing Daura” ta shirya gasar tseren dawaki domi...
06/05/2026

Cikin Hotuna

Yadda Ƙungiyar tseren Dawaki ta garin Daura “Premier Horse Racing Daura” ta shirya gasar tseren dawaki domin taya Muhammadu Dikko murnar naɗa shi sarautar Gwagwaren Katsina Hakimin Radda.

Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda, ya halarci gasar inda dubban jama’a s**a fito domin shaida wasan al’ada da nuna farin ciki ga sabon Gwagwaren Katsina.

An gudanar da gasar cikin yanayi na armashi da nishaɗi, inda mahaya dawaki daga sassa daban-daban s**a nuna bajinta da ƙwarewa a wasan tseren dawaki na gargajiya.

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Fadak Media Hub posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share