13/08/2026
Rahoton Labarai
KATSINA
A yayin bikin Ranar Matasa ta Duniya (International Youth Day) da aka gudanar a Jihar Katsina, wanda kungiyar matasa ta kasa reshen jahar katsina karkashin jagoranahin Yusuf abubakar.
matashiya ‘yar jarida, wadda kuma ita ce Shugabar kamfanin gidan jarida na Fadak Media Hub, Fatima Dauda Kurfi, ta yi kira ga matasa da su kasance masu ƙaunar juna, su rungumi kyawawan ɗabi’u tare da ba da gudummawa wajen gina makoma mai kyau ga ƙasa.
Fatima Dauda Kurfi, wadda ta fito daga Ƙaramar Hukumar Kurfi ta Jihar Katsina, ta bayyana a jawabinta cewa kyawawan ɗabi’u su ne ginshiƙin ci gaban kowace al’umma. Ta ce idan aka yi watsi da tarbiyya da kyawawan halaye, hakan na nufin an raunana tushen ci gaban ƙasa.
Ta ƙara da cewa matasa su ne ginshiƙan gina makomar Najeriya, don haka ya zama wajibi su kasance masu kishin ƙasa, jajircewa da kuma amfani da basirarsu wajen kawo ci gaba.
A matsayin wani ɓangare na ƙudurin da take da shi na bunƙasa rayuwar matasa ta hannun kamfaninta na Fadak Media Hub, Fatima ta yi alƙawarin horas da matasa maza yadda za su yi amfani da kafafen sada zumunta da sauran dandamalin zamani cikin hikima, domin su samar wa kansu sana’o’i masu ɗorewa da kuma dogaro da kai.
Hakazalika, ta bayyana cewa ta hannun cibiyarta ta Her Majesty Beauty Lounge, za ta ci gaba da ƙarfafa matasa mata ta hanyar ba su horo kan sana’o’i daban-daban, ciki har da sana’ar kwalliya (Make-up Artistry) da sauran sana’o’in da za su taimaka musu su dogara da kansu tare da inganta rayuwarsu.
Fatima Dauda Kurfi ta ce babban burinta shi ne ganin matasa sun zama masu dogaro da kai, masu anfani ga al’umma, kuma abin alfahari ga iyayensu, al’ummominsu da kuma ƙasa baki ɗaya.
Taron ya samu halartar manyan baƙi da dama, ciki har da Mai Girma Uwargidan Gwamnan Jihar Katsina, Hajiya Fatima Dikko Radda, da ɗan takarar kujerar Majalisar Dokokin Tarayya, Hon. Abba Dahiru Mangal, tare da manyan jami’an gwamnati, shugabannin hukumomi da kuma fitattun ’yan kasuwa daga sassa daban-daban.
Masu halartar taron sun yaba da jawabin da kuma ƙudurin Fatima Dauda Kurfi na ci gaba da tallafa wa matasa, tare da bayyana cewa irin waɗannan shirye-shirye za su taimaka wajen bunƙasa rayuwar matasa da kuma ci gaban al’umma.
An kammala taron da addu’o’in fatan alheri ga matasa tare da fatan Allah Ya ƙara masu hikima da nasara domin cigaban kasar mu.