Blueprint Hausa

Blueprint Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Blueprint Hausa, Media/News Company, Katsina.

Blueprint Hausa jarida ce mai kawo ingantattun labarai cikin harshen Hausa domin ilimantarwa da faɗakarwa da nishaɗantarwa daga gida Nijeriya da ƙasashen waje don sanin halin da duniya take ciki.

Ba zamu lamunci Atiku da El-Rufai su siyasantar da mutuwar Buhari tare da cin moriyar mutuwar a wajen zaman makokinsa ba...
18/07/2025

Ba zamu lamunci Atiku da El-Rufai su siyasantar da mutuwar Buhari tare da cin moriyar mutuwar a wajen zaman makokinsa ba --Kungiyar DWI

Kungiyar Democracy Watch Initiative (DWI) ta bayyana matuƙar ɓacin ranta da yadda Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai s**a nuna halayen son zuciya da ƙaŕaiŕàyi a lokacin jana’izar tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari. A yayin da mutane ke cikin alhini, su kuma sun sauya jana’izar zuwa wata dama ta siyasa don yaudarar jama’a da neman tagomashi.

Atiku da El-Rufai sun nuna kansu k**ar su ne masoyan Buhari na hakika, alhali tarihi ya tabbatar da cewar sun sha s**a da yakar manufofinsa da akidunsa. Wannan yunkuri nasu, ba wai kawai rashin gaskiya ba ne, har ma da rashin mutunta irin gudunmawar da Buhari ya bayar ga ƙasa, da kuma wulakanta ra’ayin al’umma da ke makoki.

Ya k**ata a tuna cewa Atiku ya fara zama babban abokin adawar Buhari tun shekarar 2003, inda ya tsaya takara da shi a zaɓuka da dama. A tarihi, Atiku yana canza jam’iyya bisa la’akari da ribar kansa, ba don wata akida ba. Ya bar PDP ya koma APC lokacin da Buhari ke da tasiri, sannan ya sake komawa PDP da zarar Buhari ya ci zaɓe. Wannan yana nuna halin rashin gaskiya da son zuciya da ke tattare da siyasar Atiku.

A gefe guda kuwa, El-Rufai wanda ya dade yana jinƙayar Buhari da jama’arsa, ya bayyana a jana’iza yana kokarin nuna wata tsantsar goyon baya da ba ta taɓa kasancewa da shi ba. Wannan hanya ce ta neman amincewa da mutanen Arewa cikin lokaci mai rauni da radadi.

Kungiyar DWI tana kira ga al’ummar Najeriya musamman ‘yan Arewa da su kasance masu hankali da fahimta. Kada mu bari wasu yan siyasa su ci moriyar makokinmu da tarihin mutanen kirki k**ar Buhari. Ya k**ata a tuna da makircin da waɗannan mutane s**a aikata a baya da kuma yadda s**a kasance masu son kansu da rashin kishin kasa.

DWI tana nan daram a kan matsayinta na cewa siyasar yaudara ba za ta samu karbuwa ba. Muna roƙon kowa da kowa da ya mutunta rayuwa da gado da Buhari ya bari – rayuwar gaskiya, tsantseni

Sabuwar Jarida Mai Suna "Latest Post "Ku yi Following din shafin jaridar domin samun ingantattun labarai na yankin Arewa...
06/07/2025

Sabuwar Jarida Mai Suna "Latest Post "

Ku yi Following din shafin jaridar domin samun ingantattun labarai na yankin Arewa;

👇👇👇👇👇👇👇👇👇👇

https://www.facebook.com/share/1HkTF3jab3/

" Latest Post " Sabuwar jarida ce da zata dinga kawo muku ingantattun labaran yankin Arewacin Najeriya tare da sharhi fashin baki, wayar dakan al-ummar yankin, kan dukkannin wani abu da ya shige musu duhu.

Haka zalika jaridar zata dinga baku dama wurin isarda sakonninku zuwa ga inda kuke bukatan isarwa cikin sauki.

Muna Addu'ar Allah ya bamu sa'a da Nasara, mu gabatar da ayyukanmu cikin gaskiya da tsoron Allah. Amin

Kungiyar “Arewa Media Writers” Ta Rushe Shuwagabanin Kungiyar Na Kananan Hukumomi 34 Na Jihar Katsina Kungiyar marubutan...
25/06/2025

Kungiyar “Arewa Media Writers” Ta Rushe Shuwagabanin Kungiyar Na Kananan Hukumomi 34 Na Jihar Katsina

Kungiyar marubutan Arewa a kafafen sadarwar zamani “Arewa Media Writers” karkashin jagorancin shugaban kungiyar na jihar Katsina Comrd Nura Siniya, ta rushe shuwagabannin kungiyar na kananan hukumomi 34 na jihar Katsina.

Kungiyar “Arewa Media Writers” reshen jihar Katsina ta rushe dukkanin shuwagabannin Kananan Hukumomin biyo bayan karewar wa'adin mulkinsu tun a ranar 17, ga watan June 2025. bisa tsari na doka.

Haka kuma, kungiyar za ta sake kafa sabon shugabanci bisa jajircewa da kwazo a kananan hukumomi 34 na jihar, da za su ci gaba da bai wa kungiyar gudunmawa da goyan baya domin kai wa ga nasara.

Daga karshe Kungiyar “Arewa Media Writers” ta gode ma dukkanin tsofaffin shuwagabannin kungiyar na kananan hukumomi 34 bisa ga gudunmawar da s**a bada domin ci gaban kungiyar a fadin jihar Katsina.

Sa Hannu ✍️
Sakataren kungiyar Arewa
Media Writers na jihar Katsina
Zaharaddeen Gandu.

Kungiyar AJAM Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Nasarorin Da Ta Cimmawa Wajen Dawo da Zaman Lafiya A ArewaGamayyar Kungiy...
01/06/2025

Kungiyar AJAM Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Nasarorin Da Ta Cimmawa Wajen Dawo da Zaman Lafiya A Arewa

Gamayyar Kungiyar Ayyukan Arewa (AJAM) ta jinjina wa Gwamnatin Tarayya bisa manyan nasarori da ta samu wajen dawo da zaman lafiya da tsaro a yankin Arewa, wanda da can ya kasance cike da matsalolin ta’addanci da miyagun laifuka.

Kungiyar ta bayyana musamman rawar da Ma'aikatar Tsaro ke takawa wajen aiwatar da manyan ayyukan tsaro masu amfani da fasahar zamani a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa maso Tsakiya.

A cikin wata sanarwa da mai jagorantar kungiyar, Lauretta Bako ta fitar a ranar Alhamis, AJAM ta bayyana cewa an samu gagarumin ci gaba a fannin tsaro a yankin, wanda hakan ya biyo bayan dabarun rundunonin tsaro da gwamnatin ke aiwatarwa.

"A yau muna rayuwa a wani sabon yanayi na tsaro fiye da da, inda aka kore Boko Haram zuwa matsugunan duhu, yayin da shugabannin masu garkuwa da mutane da ‘yan bindiga s**a hallaka ko s**a tsere."

"Nasarorin da aka samu wajen kawar da ‘yan bindiga, ‘yan ta’adda da kuma sarkakiyar hanyoyin aikata laifi, tare da farfado da tattalin arzikin yankuna, ya nuna ingancin wannan tsari."

A cewar AJAM, daya daga cikin ginshikan wannan nasara shine Operation FANSAR YAMMA, wanda ya samu nasarori da dama, ciki har da hallaka sanannen shugaban ‘yan bindiga, Kachalla Dogo Isah, tare da wasu ‘yan ta’adda 44 a jihar Zamfara.

Sanarwar ta kara da cewa, “Kashe fitattun masu aikata laifi ciki har da masu sayar da mak**ai da shugabannin ‘yan bindiga ya tarwatsa manyan hanyoyin aikata laifi, tare da isar da sako ga sauran masu laifi cewa gwamnati ba za ta yarda da rashin tsaro ba.”

Tasirin wadannan matakan tsaro ya wuce kidayar alkaluma kawai; yana da tasiri kai tsaye ga rayuwar yau da kullum ta ‘yan kasa. Hanyoyi k**ar hanyar Kaduna-Abuja, wanda da can aka fi jin tsoro, yanzu sun fi aminci ga matafiya, hakan kuma yana taimakawa wajen kasuwanci da zirga-zirga.

Kasuwanni a wurare irin su Giwa, Birnin Gwari da Jibia suna samun sabuwar rayuwa, inda shugabannin al’umma da jama’a ke tabbatar da ingancin tsaro. Farfadowar harkokin kasuwanci na da nasaba kai tsaye da nasarorin da sojoji s**a samu tare da samar da yanayi mai kyau ga kasuwanci.

Gina Brigade na National Mission Force a Samaru Kataf shima ya taka rawa wajen warware matsalolin tsaro a Kudu ta Kudancin Kaduna, wanda ya haifar da ingantattun yanayin zamantakewa da tattalin arziki. A cikin watanni ukun farko na shekarar 2025 kadai, an hallaka ‘yan ta’adda 122 kuma an k**a fiye da 1,000 daga cikin masu laifi.

A matsayinmu na Arewa Joint Action Movement, muna tare da kokarin da Ma’aikatar Tsaro ke yi wajen kare al’ummominmu da dawo da fata a zukatan jama’a. Muna fahimtar cewa har yanzu akwai kalubale, amma nasarorin da aka samu sun haskaka mana hanya. Zamu ci gaba da goyon bayan manufofi da matakan da za su kawo zaman lafiya, tsaro da cigaba mai dorewa a Arewarmu.

Peter Obi Ya Karyata Jita-Jitar Zama Mataimakin Atiku A Zaben 2027 – Inji Obidient MovementDaga Comr Haidar H Hasheem Ob...
19/05/2025

Peter Obi Ya Karyata Jita-Jitar Zama Mataimakin Atiku A Zaben 2027 – Inji Obidient Movement

Daga Comr Haidar H Hasheem

Obidient Movement ta bayyana cewa rahoton da ke yawo a kafafen yada labarai na cewa tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP a zaben 2023 Mr. Peter Obi ya amince ya zama mataimakin Alhaji Atiku Abubakar a wani sabon hadin gwiwar siyasa da ake kokarin kafa wa gabanin zaben 2027, karya ne kuma babu gaskiya a cikin rahotan.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Nana Kazaure, Daraktar Sadarwa da Tsare-Tsare ta kungiyar, ta fitar a ranar 19 ga Mayu, 2025, inda ta bayyana cewa rahoton ya kasance kirkirar wasu marubuta ne kawai, kuma hakan yana iya janyo rudani da kuskuren fahimta a tsakanin jama'a.

Ta ce ko da yake ana ci gaba da gudanar da tattaunawa cikin lumana da wasu manyan ‘yan siyasa da masu ruwa da tsaki don samar da hadakar da za ta ceto Najeriya, babu wata tantama cewa Mr. Obi bai amince da mukamin mataimaki ba, kuma babu wata yarjejeniya da ta shafi hakan.

Sanarwar ta bayyana cewa manufar Mr. Obi da Obidient Movement ita ce samar da cikakken hadin kai don yaki da mulkin rashin nagarta, cin hanci da rashawa, yunwa, talauci, matsalar kiwon lafiya, da karancin ilimi ga yara ba siyasar karbar mukami kawai ba.

Kungiyar ta sake jaddada cewa Mr. Obi har yanzu na cikin jam’iyyar Labour Party, kuma idan zai sauya sheka ko jam’iyya a nan gaba, zai bayyana hakan da kansa.

Daga karshe, Obidient Movement ta bukaci 'yan Najeriya da kafafen yada labarai da su kauce wa yada jita-jita da rahotannin da ka iya tada tarzoma saboda rashin tushe, su maida hankali wajen taimakawa tare da gina Najeriya mai inganci da adalci.

Ranar: 19/05/2025
Sa hannu: Nana Kazaure, Daraktar Sadarwa da Tsare-Tsare, Obidient Movement

05/05/2025

Katafaren ginin gidan alfarma kenan da Kauran Bauchi ya ginawa kansa don jindadinsa yayin da al'ummar Bauchi ke cikin kunci da tsananin talauci a jihar

Me za ku ce?

Ministan Tsaron Najeriya Mohammed Badaru Abubakar, Ya Karɓi Baƙuncin Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya Kan Harkokin Jinƙai...
30/04/2025

Ministan Tsaron Najeriya Mohammed Badaru Abubakar, Ya Karɓi Baƙuncin Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya Kan Harkokin Jinƙai

A ranar Talata, 29 ga Afrilu 2025, mai girma Ministan Tsaro na Ƙasa, H.E. Mohammed Badaru Abubakar, CON, mni, ya karɓi baƙuncin Mr. Mohamed Malick Fall, wanda shi ne Wakilin Majalisar Ɗinkin Duniya a Najeriya kuma mai kula da harkokin jinƙai.

Tattaunawar wanda aka gudanar a ofishin Ministan dake Ship House, Abuja, ta mayar da hankali ne kan yadda Najeriya za ta ƙara tallafawa ayyukan jinƙai da Majalisar Ɗinkin Duniya ke gudanarwa a ƙasar.

Me za ku ce kan ajiye mukamin da Dr Hakeem Baba Ahmed yayi?Dr Hakeem Baba Ahmed, shine tsohon mai magana da yawun kungiy...
04/04/2025

Me za ku ce kan ajiye mukamin da Dr Hakeem Baba Ahmed yayi?

Dr Hakeem Baba Ahmed, shine tsohon mai magana da yawun kungiyar Dattawan Arewa, shine za kuji kullum yana kalubalantar Gwamnati a duk inda tayi kuskure a gidajen Rediyo da Television da kafofin sada zumunta.

Tun ranar da Tinubu ya bashi mukamin mai bashi shawara ya turashi Ofis din Kashim aka daina jin duriyarshi, ya daina cewa komai akan sha'anin kasar.

Yasha caccaka da shagube iri-iri a wurin al-umma, yau da safe kwatsam sai ga sanarwar ya ajiye mukaminshi a jaridar Daily Trust.

ƊAN BELLO ƘATON MAƘARYACI NE KUMA AZZALUMI.Sanarwa daga Jibwis Nigeria ✍️Na kalli Video da Dan Bello yayi yana zargin Sh...
01/04/2025

ƊAN BELLO ƘATON MAƘARYACI NE KUMA AZZALUMI.

Sanarwa daga Jibwis Nigeria ✍️

Na kalli Video da Dan Bello yayi yana zargin Sheikh Abdullahi Bala Lau da kungiyar Izala da karban kudi a hanun Gwamnatin tarayya da sunan gina ajujuwa, kuma yake cewa wai an cinye kudin ba'ayi aikin ba.

Abunda ya bani mamaki shine yanda tsananin son ɓata sunan Malamai ya rufewa Dan Bello ido ya gagara gane description na aikin gine-ginen ajujuwan da yake magana akai, wanda duk wanda yake da ilimi kuma ya sanya nutsuwa zai gane meye abun yake nufi cikin sauki.

Aiyyukan ginin ajujuwa da Dan Bello ya nuna, CONSTITUENCY PROJECTS na HON. MUKHTAR ALIYU BETARA, Dan Majalisar tarayya mai wakiltar Bayo/Biu/Kwaya-Kusar... Federal Constituency a Majalisar Wakilai.

Yanda description na aikin yake shine, Hon. Mukhtar Betara ya saka zai gina ajujuwa wa kungiyar Izala da Sheikh Bala Lau yake jagoranci, wacce itace ake cewa "IZALA KADUNA", haka nan zai gina ajujuwa a makarantun kungiyar Izala da Sheikh Muhammad Sani Yahaya Jingir yake jagoranci, wacce ita ake nufi a takaddar da cewa IZALA JOS, kuma zai ginawa yan Darika ma har bangarori biyu, dukka za'ayi wannan gini ne a Kwaya-Kusar LGA Borno State, k**ar yanda yake jikin screenshot da nayi attaching a kasa.

Sunan JOS da KADUNA da akayi amfani dashi ba anyi ne don bambancewa tsakanin Izala 1&2, ba wai aiyyukan a JOS da KADUNA suke ba, k**ar yanda shi Dan Bello ya fada.

Haka nan abunda Dan Bello ya saka na cewa an ware kudade domin ginin ajujuwa a JIBWIS Collage of Education Jega, Kebbi State, shima Constituency projects ne na Senator da yake wakiltar yankin a Majalisar dattijai, Senator Muhammad Adamu Aliero, kuma Senator Aliero shi ya gudanar da aikinsa da kansa, ba kungiyar Izala aka turawa kudi ba k**ar yanda Dan Bello ya fada.

Shima wannan aikin daƙiƙi Dan Bello yace wai ba'ayi ba, kuma karya ne Senator yayi aikin k**ar yanda yayi alkawari a wani taron kaddamar da Collage din (Akwai hoton allon kaddamar da ginin da Sunan Senator Aliero, da kuma hotunan makarantar a kasa).

Wallahi tallahi na jima da gane cewa abubuwa da yawa da Dan Bello yake fada shaci-faɗi ne kawai, yana samun karbuwa ne a wajen mutane kawai saboda yana attacking shugabanni ne, sak**akon rashin jituwa da take tsakanin talakawa da shugabanni.

Duk wanda yake son fahimtar gaskiya kan abunda na fada, ya nutsu ya sake kallon video Dan Bello with an open and objective mind.

Lalle Ɗan Bello ya tabka kuskure a wannan bincike da yace yayi, wanda ke ciki da sharri da cin mutunci ga shugaban mu, wannan kuma ya kara tabbatar mana da cewa akwai waɗanda suke ɗaukar nauyin sa da bashi bayanan ƙarya, domin biyan buƙatar kan su.

Da farko dai yace Sheikh Abdullahi Bala Lau Yana da akawun sunfi guda talatin, wannan ƙarya ne tsagworanta, zamu so ya kawo mana cikekken bayani akan waɗannan akawun guda talatin da ya faɗa ɗaya bayan ɗaya.

Duk waɗannan zarge-zarge da Ɗan Bello yayi basu da alaƙa da Sheikh Bala Lau ko ofishin sa a matakin ƙasa, kuma bai san da su ba.

A ƙusa da ƙarshe Ɗan Bello ya bada adireshin wani office a garin Lau dake jahar Taraba, wannan ƙarya ne, Sheikh Bala Lau bayi da wani office dake zama a Lau mallakar sa, in banda gidansa wanda in yaje garin yake sauƙa da iyalansa.

A ƙarshe Ɗan Bello ya ƙarƙare da cin mutuncin shugaban mu da ƙiransa da suna na ƙasƙanci.

Matsayar mu: Da farko dai mun kai ƙararsa wajen Allah, tare da addu'ar Allah ya nuna misali da shi, shi da dukkan masu aiki irin nasa, su girbi abun da s**a shuka tun anan duniya.

Abu na biyu, zamu je kotu da shi domin yazo ya bada dukkan bayanan abun da ya faɗa, musamman yadda ya samo BVN tunda munsan ko hukuma ce zatayi bincike irin haka, sai ta nemi izini daga mahukunta, Insha Allah da Ɗan Bello da waɗanda suke temaka masa da labaran ƙarya ƙarshenku yazo, domin sai gaskiya ta bayyana Insha Allah.

Sannan akwai buƙatar Ɗan Bello yasan waye shugaba Sheikh Abdullahi Bala Lau a ɓangaren kasuwanci tun kafin ya zama shugaban JIBWIS, yafi ƙarfin waɗannan kuɗin da yake ambatawa. ~Jibwis Nigeria

Kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD sun kawo muku sabuwar Datar MTN mai Expired kwanaki 30 da kwanaki 7 mai suna (DATASHARE) ...
31/03/2025

Kamfanin ABBA PANTAMI DATA LTD sun kawo muku sabuwar Datar MTN mai Expired kwanaki 30 da kwanaki 7 mai suna (DATASHARE)

Masu jiran kamfanin MTN su dawo da datar MTN SME, su hakura su koma amfani da DataShare mai expired kwanaki 30 ko kuma su koma amfani da datar GLO domin suna da Network mai kyau kuma Datarsu tana da sauki, domin har yau MTN basu fara batun dawo da SME ba.

1GB 7DAYS
1.5GB 7DAYS
2GB 30DAYS
3.5GB 30DAYS
10GB 30DAYS
12.5GB 30DAYS
16.5GB 30DAYS
20GB 30DAYS
36GB 30DAYS

Bayan wannan akwai MTN GIFTING mai sauki da Expired kwanaki 1 da 2 da kwanaki 7.

Ku sauke manhajar application din ABBA PANTAMI DATA LTD a PlayStore suna da network mai inganci da jajirtattun customer care.

Kungiyar Arewa Media Writers Tana Kira Da A Gaggauta Hukunta Wadanda S**a Kashe Matafiya ‘Yan Arewa a Jihar EdoDaga Kung...
28/03/2025

Kungiyar Arewa Media Writers Tana Kira Da A Gaggauta Hukunta Wadanda S**a Kashe Matafiya ‘Yan Arewa a Jihar Edo

Daga Kungiyar Arewa Media Writers

Kungiyar marubutan Arewa a kafafen sadarwar zamani, Arewa Media Writers, karkashin jagorancin shugaban ƙungiyar na ƙasa, Comr Haidar H. Hasheem, tana kira da kakkausar murya ga gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da su gaggauta daukar mataki kan kisar gillar da aka yi wa wasu Mafarauta ‘yan Arewa a jihar Edo yayin da suke tsaka da tafiya zuwa Arewacin Najeriya.

Rahotanni sun tabbatar da cewa wasu Mafarauta da s**a taso daga jihar Fatakwal domin komawa Arewa sun gamu da ajali a hannun wasu miyagu, wadanda s**a tare motarsu, s**a fito da su, sannan s**a zarge su da cewa 'yan ta’adda ne. Ba tare da bincike ba, s**a kashe su tare da banka musu wuta har lahira.

Shaidun gani da ido sun tabbatar da cewa mutanen da aka kashe Mafarauta ne na gaskiya, wadanda ke tafiya da mak**ai k**ar yadda doka ta amince, ba ‘yan bindiga ba. Bayan sun kashe su, wadannan makasan sun ci zarafin littafin Alkur’ani mai girma da aka samu a hannunsu, inda s**a wulakanta shi, s**a takashi da ƙeta, wanda wannan babban cin mutunci ne ga addinin Musulunci da Musulmi baki daya.

Arewa Media Writers tana mai jan hankalin hukumomin tsaro da su gaggauta gudanar da cikakken bincike don gano wadanda s**a aikata wannan danyen aiki, tare da hukunta su k**ar yadda doka ta tanada. Ba za mu amince da irin wannan kisan gilla da cin zarafin addininmu ba tare da daukar matakin da ya dace ba.

Haka zalika, muna kira ga gwamnatoci na jihohi da na tarayya da su dauki matakan kare rayuka da dukiyoyin 'yan Arewa da ke zaune a kudancin Najeriya, domin tabbatar da zaman lafiya da hadin kai a kasa baki daya.

A ƙarshe, muna yin kira ga shugabannin Arewa, ‘yan majalisar tarayya, da sanatoci da su tashi tsaye domin tabbatar da an hukunta wadanda s**a aikata wannan ta’asa. Babu wata al’umma da za ta ci gaba idan ana ci gaba da zaluntarta ba tare da daukar matakin da ya dace ba

Ministan Tsaron Najeriya Badaru Abubakar Ya Kai Ziyara “Depot Na Sojojin Najeriya Dake Garin ZariyaMai Girma Ministan Ts...
25/03/2025

Ministan Tsaron Najeriya Badaru Abubakar Ya Kai Ziyara “Depot Na Sojojin Najeriya Dake Garin Zariya

Mai Girma Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar CON, mni, ya kai ziyarar tantancewa ta yini guda a Depot na Rundunar Sojojin Najeriya da ke Zariya a yau, Talata, 25 ga Maris, 2025.

A yayin ziyarar, Minista da tawagarsa sun samu cikakken bayani daga Kwamandan Depot, Manjo Janar AB Mohammed, kan tsarin aiki, gudanar da ayyuka, da horon da ake bai wa sojoji a cibiyar.

Cikin tawagar Ministan akwai Sakataren Dindindin na Ma’aikatar Tsaro, Ambasada Gabriel Tanimu Adudu; Mai Ba da Shawara Kan Fasaha, Janar AT Jibril (Rtd); da Babban Jami’in Ma’aikata, Birgediya Janar AA Garba.

📸 -Mati Ali
PA Media & Publicity to the Hon Minister of Defense.

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Blueprint Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Blueprint Hausa:

Share