Blueprint Hausa

Blueprint Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Blueprint Hausa, Media/News Company, Katsina.

Blueprint Hausa jarida ce mai kawo ingantattun labarai cikin harshen Hausa domin ilimantarwa da faɗakarwa da nishaɗantarwa daga gida Nijeriya da ƙasashen waje don sanin halin da duniya take ciki.

Da Ɗumi-Ɗumi:- Dole Ne Nasiru Elrufa'i Ya Fuskanci Hukunci - Inji Kungiyoyin matasan Arewacin Najeriya Ƙungiyoyin farare...
26/02/2026

Da Ɗumi-Ɗumi:- Dole Ne Nasiru Elrufa'i Ya Fuskanci Hukunci - Inji Kungiyoyin matasan Arewacin Najeriya

Ƙungiyoyin fararen hula daga Arewacin Najeriya da kuma kudancin kasar nan sun jaddada kiran cewa dole Elrufa'i ya fuskanci dukkan tuhume-tuhumen da ake masa, babu wani tsohon shugaba da yafi karfin doka ko waye shi.

Abubuwan daya aikata lokacin da yake kan karagar mulki tun daga kwace kadarorin al'umma, take hakkin dan'adam, k**a mutane ba gaira ba dalili, ya zama dole yanzu ya fuskanci hukuncin abinda ya aikata.

Daga Nura Jamilu
Shugaban masu rajin kare demokradiyya na Kaduna

18/02/2026

Dole Elrufa'i Ya Rufewa Mutane Baki Ya Fuskanci Tuhume-tuhumen Da Ake Masa ~ Inji Kungiyar DWI

Kungiyar Democracy Watch Initiative (DWI) ta yi kira dangane da binciken da ake yi wa tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai. A halin yanzu yana fuskantar bincike daga hukumomin yaki da cin hanci da kuma hukumomin tsaro da dama, ciki har da Economic and Financial Crimes Commission (EFCC) da Department of State Services (DSS). Kungiyar ta ce kokarinsa na karkatar da hankalin jama’a daga wadannan manyan zarge-zarge ba gaskiya ba ne, kuma hakan na iya zama barazana ga tsaron kasa.

El-Rufai ya amince cewa sun kutsa cikin hanyoyin sadarwa wayar National Security Adviser (NSA), abin da ya nuna rashin mutunta dokoki da tsarin tsaron kasa. DWI ta ce wannan ba siyasa ba ce kawai, illa keta doka da kuma cin amana da aka dora wa shugabanni.

A wani bayani da ya fitar, El-Rufai ya ce ya nemi karin haske daga NSA kan rahotannin shigo da sinadarin thallium sulphate mai matukar hadari. Duk da cewa gaskiya da rikon amana suna da muhimmanci, hanyar da ya bi ta jawo tambayoyi maimakon bayar da amsoshi. Maimakon ya maida hankali kan tuhumar da ake masa, sai ya nemi sauya labari domin ya nuna kansa a matsayin mai kishin kasa, alhali yana karkashin bincike.

DWI ta jaddada cewa babu wanda ya fi karfin doka, komai mukaminsa ko tsohon matsayinsa. Ta bukaci El-Rufai ya fuskanci doka domin tabbatar da adalci da kare tsaron kasa. Doka ita ce ginshikin dimokuradiyya, kuma dole ne kowa ya dauki alhakin ayyukansa.

Kungiyar ta kuma roki hukumomi su hanzarta bincike ba tare da tsangwama ba, tare da kare mutuncin cibiyoyin kasa. Ta gargadi jama’a da kada su bari siyasa ta dauke musu hankali daga manyan batutuwan tsaro da adalci.

A karshe, DWI ta sake jaddada bukatar a binciki dukkan matakan da El-Rufai ya dauka tare da tabbatar da ya amsa tambayoyi kan sak**akon ayyukansa. Ta ce sai an tabbatar da gaskiya da rikon amana ne kawai za a samu Najeriya mafi tsaro da dimokuradiyya ga kowa.

Ba Ribadu Ne Matsalarka Ba: Gwamnatin Jihar Kaduna Ce Ta Kai Ka Gaban Hukuma Ka Tafi Ka Amsa Laifukan Da Ake Tuhumarka Y...
14/02/2026

Ba Ribadu Ne Matsalarka Ba: Gwamnatin Jihar Kaduna Ce Ta Kai Ka Gaban Hukuma Ka Tafi Ka Amsa Laifukan Da Ake Tuhumarka

Ya k**ata ka Fuskanci Zarge-Zargenka, Ka Daina Ɗorawa Wasu Laifi.

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, dole ne ya daina yaudarar jama’a ta hanyar karkatar da akala daga ainihin batun da ake tuhumarsa da shi.

Zarge-zargen cin hanci da rashawa da almundahana da s**a taso daga mulkinsa ba ƙananan batutuwa ba ne da za a shafe su da siyasa ko surutai.

Abin da ya fi ba jama’a mamaki shi ne yadda yake ƙoƙarin janyo sunan Nuhu Ribadu cikin wannan rikici, alhali ba shi ne ya kai ƙarar ba. Gwamnatin Jihar Kaduna ce da kanta ta miƙa batun ga Independent Corrupt Practices Commission (ICPC) da kuma Economic and Financial Crimes Commission (EFCC) domin a bincike shi.

Don haka duk wani yunƙuri na jefa wani cikin wannan batu wata dabara ce ta neman kawar da hankali daga gaskiya.
A lokacin mulkinsa a Kaduna State, an sha fama da zarge-zargen karkatar da kuɗaɗen jama’a, rushe gidaje ba tare da adalci ba, da yanke shawara ba tare da bin ƙa’ida ba.

Yanzu da aka buɗe bincike, abin da ya k**ata shi ne ya fito ya kare kansa a gaban doka, ba ya ɓoye a bayan siyasa ba.
Idan yana da gaskiya, kotu da hukumomin yaƙi da cin hanci za su tabbatar. Amma idan akwai laifi, dole ne ya fuskanci hukunci k**ar kowane ɗan ƙasa.

Bayan zarge-zargen cin hanci da rashawa, Elrufa'i ya kasance mutum mafi take hakkin mutane a lokacin da yake mukin jihar Kaduna, cikin waɗanda ya gallazawa har da su tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya Sanata Shehu Sani.

Irin wannan mutanen ba su cancanci tausayawa agun talakawa ba ko kaɗan, Yak**ata su fuskanci hukunci mai tsauri akan abubuwan da s**a aikata.

Daga matashin Ɗan gwagwarmaya
Muhammad Nur Kaduna.

Kogunan Gusa Shine Amsa A Jihar Zamfara 2027A yau Jihar Zamfara na bukatar shugaba nagari, mai hangen nesa, mai tausayi ...
09/02/2026

Kogunan Gusa Shine Amsa A Jihar Zamfara 2027

A yau Jihar Zamfara na bukatar shugaba nagari, mai hangen nesa, mai tausayi ga talaka, kuma wanda ya san halin da al’umma ke ciki.

Ba kowa ba ne zai iya ɗaukar wannan nauyi, sai mutumin da Allah ya horewa baiwa da basira, kwarewa, da kuma kishin jama’a. Daga cikin irin wadannan mutane, sunan Kogunan Gusau ya fito fili ba tare da shakka ba.

Kogunan Gusau mutum ne da ya shahara wajen taimakon jama’a, gina al'umma, da tsayawa tsayin daka wajen kare muradun al’umma. Tarihinsa ya nuna cewa shi shugaba ne mai sauraron jama’a, wanda ke da fahimtar matsalolin tsaro, tattalin arziki, ilimi da walwalar al’umma. Ba wai kawai a iya magana ya tsaya ba, faɗa da aikatawa sunanshi.

A tsawon lokaci, Kogunan Gusau ya nuna jajircewa, hakuri da kwarewa a harkokin shugabanci da siyasa. Yana da fahimta mai zurfi game da jihar Zamfara daga karkara zuwa birane, kuma yana da zuciyar haɗa kan jama’a ba tare da nuna bambanci ba. Wannan shi ne irin shugabancin da Zamfara ke nema a wannan lokaci mai muhimmanci.

Muna kira gare ka, Kogunan Gusau, da ka amsa kiran al’umma. Ka tsaya ka fafata domin karɓar kujerar Gwamnan Jihar Zamfara a 2027 insha Allahu, domin mutane da dama sun yarda kai ne mutumin da ya dace da wannan aiki.

Zamfara na bukatar shugaba mai tsoron Allah, gaskiya, hangen nesa da kuma karfin gwiwar kawo sauyi, kuma wadannan siffofi suna tare da kai.

Allah Ya taimaka, Ya ba da nasara, kuma Ya sanya abin da ya fi alheri ga Jihar Zamfara da al’ummarta.

Muhammad Nura
Chairman Koguna Alheri Ne

Ɗaruruwan matasa magoya bayan Professor Isa Ali Pantami (Majidadin Daular Usmaniyya kuma Wazirin Pantami) sun gudanar da...
01/02/2026

Ɗaruruwan matasa magoya bayan Professor Isa Ali Pantami (Majidadin Daular Usmaniyya kuma Wazirin Pantami) sun gudanar da taro a karamar hukumar Funakaye, jihar Gombe.

A yayin gudanar da taron an kara wayar da kan matasan kan abunda ya shafi harkar rubuce-rubuce a kafafen sada zumunta da wayar da kansu.

Haka zalika matasan Funakaye sunyi kira tare da roko ga Professor Isa Ali Pantami da ya daure ya fito takarar Gwamnan jihar Gombe a zaben 2027.

Mutanen Funakaye sunyi dan-dazo Mazansu da matansu sun fito daga kowane yanki na fadin karamar hukumar, domin nuna soyayya da kaunarsu ga Majidadin Daular Usmaniyya.

Wannan yake kara nunawa da tabbatar da cewa mutanen jihar Gombe na kowane yanki a shirye suke domin bada gudummuwarsu na ganin Professor Isa Ali Pantami, ya zama Gwamnan jihar Gombe a zaben 2027.

An Jaddada Yaƙi Da Shan Miyagun Ƙwayoyi Da Jagoranci Nagari A Babban Taron Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya "CNG" A...
16/01/2026

An Jaddada Yaƙi Da Shan Miyagun Ƙwayoyi Da Jagoranci Nagari A Babban Taron Gamayyar Kungiyoyin Arewacin Najeriya "CNG" A Birnin Sakoto

Ƙungiyar Coalition of Northern Groups (CNG) ɓangaren ɗalibai ta samu gagarumar nasara wajen shirya laccar bai ɗaya da aka gudanar a Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari da ke Sakkwato.

An gudanar da laccar ne ƙarƙashin jagorancin Mai Martaba HRH Farfesa Sambo Wali Junaid (Wazirin Sakkwato), inda manyan masu jawabi s**a yi jawabai masu armashi kan batutuwa masu muhimmanci da s**a shafi kyakkyawan jagoranci nagari, illolin shan miyagun kwayoyi, da kuma mummunan tasirin "Hate speech" a makarantun gaba da sakandare da ma al’umma baki ɗaya.

Taron ya samu halartar ɗalibai masu yawa daga fannoni daban-daban, abin da ke nuna yadda matasa ke da ƙwazo da sha’awar rungumar kyawawan ɗabi’u, haɗin kai da jagoranci nagari.

Hakika, laccar ta ilmantarwa ta kuma yi tasiri sosai, inda ta haɗa zukatan matasa masu burin gina kyakkyawar makoma mai ɗorewa da ci gaban al’umma.

Masu Yada Karya Akan Gwamna Bauchi Bala Muhammad Ba za su yi nasara ba - Arewa Democratic Agenda Muna jan hankalin jama’...
07/01/2026

Masu Yada Karya Akan Gwamna Bauchi Bala Muhammad Ba za su yi nasara ba - Arewa Democratic Agenda

Muna jan hankalin jama’a game da wani labari na ƙarya da ake yaɗawa a kafafen sada zumunta, wanda ake zargin cewa an bai wa wata ƙungiya da ake alaƙantawa da ta’addanci kuɗi daga Gwamnatin Jihar Bauchi. Wannan labari ba shi da tushe, b***e Malama, babu hujja, kuma ƙarya ce tsagwaronta.

Babu wani lokaci da Gwamnatin Jihar Bauchi, ko Mai Girma Gwamna Sanata Bala Mohammed, ya amince ko ya ba da umarnin bai wa kowace ƙungiya da ke da alaƙa da ta’addanci kuɗi, ko ta kowace hanya. Wannan zargi an ƙirƙire shi ne kawai domin ɓata suna, yaudarar jama’a, da tayar da fitina.

Haka kuma muna kira ga jama’a da su yi watsi da irin waɗannan labaran ƙarya, su kuma guji yaɗa bayanan da ba su tantance ba.

Gwamnatin Jihar Bauchi ta himmatu wajen tabbatar da tsaro, zaman lafiya, da bin doka da oda, tare da haɗin gwiwa da hukumomin tsaro na ƙasa.

Duk wanda ke yaɗa wannan labari na ƙarya, yana da niyyar ɓata sunan shugabanci da ya samu amanar jama’a, kuma hakan ba zai hana gwamnati ci gaba da ayyukan alheri da ci gaban jihar Bauchi ba.

Gaskiya ce za ta yi nasara a kowane lokaci.

Kungiyar Arewa Media Writers Ta Yi Kira Ga Shugaba Tinubu Da Ya Gaggauta Sauke Ministan Abuja, Nyesom Wike…Kungiyar ta c...
05/01/2026

Kungiyar Arewa Media Writers Ta Yi Kira Ga Shugaba Tinubu Da Ya Gaggauta Sauke Ministan Abuja, Nyesom Wike

…Kungiyar ta ce dole ne a dakatar da duk wani yunkuri da ke barazana ga dimokaradiyya, zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

Daga Kungiyar “Arewa Media Writers”

Kungiyar Marubutan Arewa "Arewa Media Writers" ƙarƙashin jagorancin Shugaban Ƙungiyar na Ƙasa, Comr. Haidar H. Hasheem (Kano), ta nuna matuƙar damuwa tare da yin Allah-wadai da abin da ta bayyana a matsayin k**a-karya, nuna wariya da cin zarafin ‘yan ƙasa, da ake zargin Ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Nyesom Wike, na aikatawa.

Kungiyar ta ce abin takaici ne yadda ake zargin Ministan da amfani da ƙarfin iko wajen cuzgunawa ‘yan Arewa da ‘yan adawa, musamman saboda banbancin ra’ayin siyasa, abin da hakan ke tauye ‘yancin ‘yan ƙasa tare da zama barazana ga tsarin dimokaradiyyar Najeriya.

A cewar ƙungiyar, ana zargin Wike da amfani da hukumar EFCC da jami’an tsaro wajen tsoratarwa da musgunawa abokan hamayya, lamarin da ke haifar da fargaba, rashin adalci da rashin amincewa ga hukumomin gwamnati.

Kungiyar Arewa Media Writers ta kuma nuna damuwa kan yadda Ministan ke yin furuci da ayyuka masu ɗauke da wariya ga al'ummar Hausawa/Fulani, inda ta jaddada zargin da Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad, ya yi a baya-bayan nan, wanda yace ya samu wata masaniya daga mai jiya mai tushe dake nuna cewa hatta hukumomin EFCC, Wike ke amfani da su wajen matsin lamba ga yan adawa, haka kuma ya tabbatar dasa hannun Ministan wajen ƙoƙarin bata masa suna ta hanyar jingina shi da zargin ɗaukar nauyin ta’addanci a kotu.

Kungiyar ta bayyana cewa irin waɗannan zarge-zarge ba komai ba ne illa kiyayya ta kabilanci da siyasar adawa, wanda hakan ya saba wa ruhin haɗin kan ƙasa. Idan baku manta ba tun a lokacin da Wike ke Gwamnan Jihar Rivers, an samu rahotannin rusa masallatai, rufe shaguna da gidajen ‘yan Arewa, tare da korar su daga jihar, abin da har yanzu ke ci wa zukatan al’umma tuwo a ƙwarya.

Haka kuma ƙungiyar ta yi tsokaci kan sauke Sakataren Ilimi na Abuja, Dr. Danlami, wanda ɗan Arewa ne, inda ta ce yadda aka yi hakan ya ƙara nuna amfani da iko ba bisa ƙa’ida ba, tare da mayar da shi aiki bisa wasu sharudda.

Ba wannan kaɗai ba, kungiyar ta kuma nuna damuwa kan zargin amfani da jami’an tsaro wajen tarwatsa rikici a helkwatar jam’iyyar PDP, inda aka ce har aka yi amfani da hayaki mai sa hawaye ga wasu gwamnoni ciki har da Seyi Makinde da Bala Muhammad, lamarin da bai dace ba ga shugabanni da kundin tsarin mulki ya tanadar musu da rigar kariya.

Kungiyar Arewa Media Writers ta jaddada cewa tsarin shugabancin Najeriya bai ginu kan kabilanci, wariya ko ramuwar siyasa ba, illa adalci, daidaito da mutunta ‘yancin kowa.

A ƙarshe, Kungiyar Arewa Media Writers tana kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya gaggauta dakatar da duk wani yunkuri da ke barazana ga dimokaradiyya Najeriya, taka wa Ministan Abuja burki, ko kuma a sauke shi daga mukaminsa, domin kare martabar dimokaradiyya, zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

Arewa Media Writers za ta ci gaba da tsayawa kan gaskiya, adalci da kare haƙƙin al’umma.

✍️✍️
Comr Nura Siniya
Chairman Arewa Media Writer's Katsina Chapter

GWAMNAN JIHAR BAUCHI BALA MUHAMMAD YA FALLASA ASIRIN MINISTAN ABUJA NYESOM WIKEMaigirma Gwamnan jihar mu na Bauchi Senat...
02/01/2026

GWAMNAN JIHAR BAUCHI BALA MUHAMMAD YA FALLASA ASIRIN MINISTAN ABUJA NYESOM WIKE

Maigirma Gwamnan jihar mu na Bauchi Senator Bala Abdulkadir Mohammed (Kauran Daular Usmaniyyah) ya fallasa asiri na makircin da Ministan Abuja Nyesom Wike yake kulla masa da jihar Bauchi gaba daya

Maigirma Gwamna yayi wannan fallasa ne a cikin shirin Sunrise Daily na Channels TV dazu da safe, yace akwai wanda yake shirya min makirci, kuma na san shi, shine Ministan Abuja na yanzu Nyesom Wike, ya fada wa duniya cewa zai kunna wuta a jihata na Bauchi

Kauran Daular Usmaniyyah yaci gaba da cewa; na fahimci Wike ne yake bada umarni wa hukuma irin na EFCC wajen batani, yana bawa mutane cin hanci, yana sayar da filayen Abuja yana amfani dasu wajen cimma burinsa, ba sabon abu bane a gareni saboda na taba rike mukamin Ministan Abuja na shekaru 6 na san komai

Gwamnan Bauchi yaci gaba da cewa; yana da hujjoji daga majiyarsa na sirri dake EFCC wanda s**a tabbatar masa da cewa Wike ne yake tsara duk abinda yake faruwa da ‘yan adawar siyasa a Nigeria

Kaura yace tsohon Accountant General dinsa na jihar Bauchi yaci amanata, ni na kaishi Kotu da kaina domin a masa hukunci, daga bisani Kotu ta bada belinsa, to a yanzu Wike ne yake aiki dashi a Kotu wajen bada shaida na karya akan mukarrabaina da aka k**a

A matsayina na Gwamna wanda na rike manyan muk**ai tun daga Sanata har Minista, ina shugaban al'ummah ta ya zai kasance ina daukar nauyin ta'addanci, ana min wannan sharri ne saboda ina cikin manyan 'yan adawa

Zan bi duk matakan da s**a dace domin na kare kaina, na rubuta wa Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya takardan korafi, tare da sanar da hukumomin tsaro, kuma zan kai korafina zuwa ga hukumonin Majalisar dinkin duniya, inji Maigirma Gwamna

Sannan Gwamna Bala yace Shugaban Kasa Tinubu yana kewaye da 'yan daba, 'yan damfara wadanda suke son ha||akashi a siyasance irinsu Wike

Muna rokon Allah Ya kare jihar Bauchi daga wadanda suke neman jingina mana ta'addanci, Allah Ya sa mugun nufinsu ya kare a kansu da iyalansu kadai.

Ƙungiyar “Kano Youth For Good Governance” Ta Caccaki Sanata Rufa’i Hanga Kan Gazawa, A Mazabar Kano Ta Tsakiya Ƙungiyar ...
31/12/2025

Ƙungiyar “Kano Youth For Good Governance” Ta Caccaki Sanata Rufa’i Hanga Kan Gazawa, A Mazabar Kano Ta Tsakiya

Ƙungiyar Kano Youth For Good Governance ƙarƙashin jagorancin Comr. Nura Sale na zargin Sanata Rufa’i Hanga da zama Sanata mafi gazawa a tarihin Kano ta Tsakiya.

Sanata wanda ya kasa kawo ko aiki ɗaya da al’umma za su nuna su ce “ga abin da ya mana”, sai dai zama a Abuja yana cin moriyar mukami tare da iyalinsa, alhali jama’ar Kano ta tsakiya na fama da talauci da rashin kulawa.

Mutumin da ya sanyawa karen gidansa sunan “Kwankwaso” akwai butul-cin da ya wuce wannan, ba soyayya bane, cin mutun-ci ne kai tsaye ga tafiya da kuma abinda al’ummar Kano ke girmamawa, kuma hakan ya nuna a sarari cewa Sanatan ba shi da ki-shin jāma’a ko dābi’ar girmamawa ga Kwankwaso.

Gāzawar Sanata Rufa’i Hanga ya kai matakin da ya kasa taimakawa iyalan marigayi Alh. Yawale, mutumin da ya yi masa riga da wando, ya tsaya masa a lokacin bukata. Wannan hali na nuna cewa Sanatan ba ya tuna alheri, kuma bai cāncanci amānar jāma'ā ba.

Abin mamaki shi ne yadda Sanatan ke fitowa yana zārgin wasu da bụtūlci har sanata ne yake da bakin sukār manyan Jihar Kano, alhali shi ne cikakken misalin abin da yake zargi da gāzawa

Kano Youth For Good Governance na jaddada cewa tarihin Sanata Rufa’i Hanga ba tarihin aiki ba ne, tarihin gāzawa ne, rai-ni da ci-n amānā irin ta siyasa.

Kano Youth For Good Governance
Comrd. Nura Sale Shugaban
Kungiyar Ta Kano.

Kungiyar Matasan Kiristōcin Arewacin Najeriya NCYC Sun Bukaci Tinubu Ya Sallami Ministan Tsaro Bello MatawalleƘungiyar N...
19/12/2025

Kungiyar Matasan Kiristōcin Arewacin Najeriya NCYC Sun Bukaci Tinubu Ya Sallami Ministan Tsaro Bello Matawalle

Ƙungiyar Northern Christian Youth Coalition (NCYC) ta bukaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ya sallami Ministan Ƙasa na Tsaro, Dr. Bello Matawalle, sak**akon zarge-zargen alaƙa da ta'āddān-ci wanda tsohon hadiminsa Musa Kāmarawa yayi ikirari.

A cikin wata sanarwa da Babban Kwamishinan ƙungiyar, Jeremaid Hudso Bako, ya fitar, ƙungiyar ta ce kira da take yi na nufin ƙarfafa gaskiya, riƙon amana, da dawo da amincewar jama’a ga gwamnati, musamman a bangaren tsaro.

Ƙungiyar ta yaba wa Shugaba Tinubu kan tsige tsohon Shugaban Hukumar NMDPRA, Farouk Ahmed, tana mai cewa hakan alama ce ta ƙoƙarin gwamnati wajen yaƙi da cin hanci da rashawa.

Sai dai ta ce ya dace a yi adalci iri ɗaya ga kowa, ciki har da Matawalle mininstan tsaron Najeriya.

NCYC ta jaddada cewa zarge-zargen da ake yi wa Matawalle suna da nauyi sosai, musamman ganin cewa suna da alaƙa da tsaron ƙasa da rayukan al’umma, don haka bai dace a yi shiru a kansu ba.

Ƙungiyar ta ce idan har gwamnatin Tinubu na son a san ta da gaskiya, adalci da shugabanci nagari, to ya zama dole ta ɗauki mataki cikin gaggawa

Kan duk wani jami’i da ake zargi da aikata abubuwan da za su iya lalata amincin ƙasa tare da sauke ƙaramin ministan da kuma gudanar da binciken gaggawa a kansa.

Ya k**ata Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Bincike Na Gaggawa Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga Da Musa Kamarawa Yayi Ga...
15/12/2025

Ya k**ata Gwamnatin Tarayya Ta Kafa Kwamitin Bincike Na Gaggawa Kan Zargin Alaƙa Da Yan Bindiga Da Musa Kamarawa Yayi Ga Bello Matawalle - Inji Comr Haidar hasheem kano

Dole a gaggauta binciken Musa Kamarawa da kuma Ƙaramin Ministan Tsaron kan alaƙa da yan bindiga domin tabbatar da tsaron al'ummar Arewacin Najeriya.

Ni, Comr. Haidar H. Hasheem, ɗan Arewa kuma mai kishin zaman lafiya da tsaron ƙasa, ina bayyana damuwa mai tsanani kan manyan zarge-zargen da ke yawo a fili, musamman ikirarin da tsohon mataimaki na musamman ga tsohon Gwamnan Zamfara, Musa Kamarawa, ya yi a faifan bidiyo dangane da Ministan Tsaron Ƙasa na yanzu, Bello Matawalle.

Waɗannan zarge-zarge sun haɗa da alaƙa da ’yan bindiga, zargin tura kuɗaɗe ga fitaccen shugaban ’yan bindiga Bello Turji, sayen motocin Hilux ga yan ta'adda, da kuma tallafawa da dukiya k**ar gidaje, saya musu dusa da sauran kayan more rayuwa, tare da zargin cewa wasu ’yan siyasa daga Zamfara da maƙwabtanta sun taka rawa a hakan.

Waɗannan ba ƙananan maganganu ba ne. Zarge-zarge ne masu nauyi da ke nuna yiwuwar alaƙa mai zurfi tsakanin wasu masu rike da madafun iko da ’yan bindiga, abin da ke iya rushe ƙoƙarin jami’an tsaro tare da ƙara jefa rayukan al’umma cikin haɗari.

Ina da cikakken ra’ayi cewa musantawa kawai ba za ta wadatar ba. Idan ba a yi cikakken bincike ba, shakku zai ci gaba da ƙaruwa, kuma amincewar jama’a ga gwamnati da hukumomin tsaro za ta ƙara raguwa.

Haka kuma, matakin kai ƙara kan Sheikh Murtala Asada yana iya fassaruwa a idon jama’a a matsayin yunƙurin tsoratarwa da hana faɗin gaskiya, maimakon kare mutunci. Ina kira ga Sheikh Asada da ya fito da duk wata hujja da ke hannunsa, domin gaskiya ita ce ginshiƙin adalci, haka kuma bayyana dukkan gaskiyarsa gaban kotu zai taimaka don tabbatar da kare tsaron ƙasa.

A bayyane yake cewa babu wanda ya fi ƙarfin doka, kuma duk wani yunƙurin kare masu hannu a ta’addanci yana raunana tsaro tare da cin zarafin mutanen Arewa da Najeriya baki ɗaya.

Saboda haka, ina kira da a gaggauta kafa bincike mai zaman kansa, marar son zuciya, wanda Majalisar Ƙasa, hukumomin tsaro, da Ofishin Babban Lauyan Ƙasa za su jagoranta, domin binciken kuɗaɗe, kayan aiki, sadarwa da duk wata hulɗa da ka iya taimaka wa ’yan bindiga.

Dole ne a kare masu fallasa gaskiya, kuma duk jami’in gwamnati da aka samu da laifi ya fuskanci hukunci ba tare da la’akari da matsayinsa ko ƙarfin ikonsa ba.

Arewa ta sha wahala ƙwarai sak**akon ’yan bindiga. Wannan lokaci ne na fuskantar gaskiya, ba na ɓoyewa ba. Lokacin shiru ya wuce. Lokacin gaskiya, adalci da ɗaukar mataki ya yi.

Ɗan'uwanku
Comr. Haidar H. Hasheem
Ɗan Arewa Mai Kishin Tsaro Da Tabbatar Da Adalci

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Blueprint Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Blueprint Hausa:

Share