Da’irar Rimi

Da’irar Rimi Salam
Wannan shafi mallakar Da’irar Rimi ne ƙarkashin jagorancin Shaikh Zakzaky (H). Bissalam

Za ku riƙa samun labarai, Hotuna, bidiyo da sauransu dangane da Harkar Musulunci da ma al’umma baki ɗaya.

HAR ZUWA YANZU ALMAJIRAN SHAIKH IBRAHIM YAQOUB AL-ZAKZAKY(H) NA CIGABA DA BUKUKUWAN GHADEER-KHUM A NIGERIA.Daga Abdurrah...
04/07/2024

HAR ZUWA YANZU ALMAJIRAN SHAIKH IBRAHIM YAQOUB AL-ZAKZAKY(H) NA CIGABA DA BUKUKUWAN GHADEER-KHUM A NIGERIA.

Daga Abdurrahman Tasi'u Rimi.

Yau Alhamis 27/12/1445H Wanda yai dai-dai da 4/07/2024M Almajiran Shaikh Zakzaky(H) a karamar hukumar Rimin jihar Katsina Nigeria, sun gabatar gabatar da shagulgulan bikin Edil Ghadeer-Khum nuna murna da zagayowar irin ranar da Manzon tsira(S) ya nasabta Imam Aliyu bin Abidalib(As) a matsayin khalifa wanda zai gaje shi a bayansa.

Bukukuwan sun fara tun da yammacin karfe huda da mintuna(mintota) wanda Matasa s**a gabatar da takaitaccen zageyen Muzahara da sakin wakokin da suke isar da sako ga al'umar gari. Bayan kammala Muzahara Ittihadu sun cigaba da majalisi har zuwa lokacin sallar Magriba aka tashi.

Bayan dawowa daga sallah Program ya cigaba da gudana a Muhallin tsohuwar makarantar Fudiyya dake unguwar Kofar-yamma cikin garin Rimin, wanda bayan bude taro da addu'a da sauran abubuwan da aka saba Dalibai Yan Fudiyya sun bayar da tsaraba wanda ta hada da wakoki da karatukan Ayoyi da Hadisan da s**a dangancin Ghadeer-Khum din.

Daga Karshe an saurari jawabi daga bakin wakilin yan'uwa na Da'irar wato Malam Aminu Usman Jakara har zuwa kammalawa aka gabatar da walima aka yi addu'a aka sallami kowa.

Ga hotunan yadda shagulgulan s**a gudana mun dauko maku a kasa.

'irarRimiMediaForum.
04Jul2024M_27-12-1445H.

ALJANNA TA MASU IMANI CE; SAI DAI ZAI IYA YIYUWA MUTUM YA ZAMANA BASHI DA IMANI AMMA YA YI WASU AIYUKA WAƊANDA MUSULUMCI...
15/06/2023

ALJANNA TA MASU IMANI CE; SAI DAI ZAI IYA YIYUWA MUTUM YA ZAMANA BASHI DA IMANI AMMA YA YI WASU AIYUKA WAƊANDA MUSULUMCI YAKE JINJINA MASU YA SAMU SAUƘIN WANI ABU DAGA AZABAR ALLAH.

Kamar wasu su Ukku waɗanda s**a yi shawarar cewa ya k**ata su kashe Manzon Allah(S) saboda Abu jahil saboda haka s**a ɗauro kayansu tun daga Makkah har Madina s**a zo su ga bayan Manzon(S), Sai Allah ta'alah ya sanar da Manzo(S), Manzon Allah ya aika Imamu Ali ya fafata da su ya kashe ɗaya ya zo da biyu aka ce ma ɗaya to ka yi imani sai ya ce gaskiya shi ba zai yi Imani ba a aika shi inda na farkon ya tafi( inda aka aika na farkon lahira kenan) saboda haka aka durƙusar da shi aka gama da shi.

A ka zo wurin na Ukkun aka ce yai Imani ya ce shi ba zai Imani ba k**ar yadda wannan ya faɗa ya ce shi ba zai yi Imani ba, saboda haka a aika shi inda magabatansa s**a tafi aka durƙusar da shi za'a sare mashi wuya Jibrilu ya sauko ya ce a ƙyale shi! to an yi mamakin wannan sai Manzon Allah(S) yake cewa Jibrilu(AS) ya zo ya gaya mashi cewa to wannan mutunen mutunen kirki ne. kafiri ne fa ya zo da mummunan niya ta kashe Manzo(S)! amma yana da kyakkyawar ɗabi'ar da Allah ke so "ko ba'a lura ba" shi ne sai aka tambaye shi ga abunda Jibrilu(AS) ya zo da saƙo cewa kana da wata kyakkyawar ɗabi'a menene kake yi wanda ya baka dama ka samu wannan matsayin? sai yake cewa shi tunda yake bai taɓa ɗaure fuskarsa ga wani ba wato shi koda yaushe fuskarsa a sake take kowa yadda yake kallonsa da fuska kuma haka yake a cikin zuciyarsa baya kallon mutum da fuska zuciyarshi tana kallon da wani abu ko kuma zuciyarsa na kallonsa(wani) da wani abu shi kuma ya ɗaure masa fuska ko wani abu mai k**a da haka.

Sannna ya ce bai taɓa samun wani abu nasa ba ba tare da ya yi tarayya da wani a cikin wannan abun nasa ba, wato abun duniyarsa bai taɓa rufe masa ido ba in ya samu abu sai ya yi tarayya da wani a cikin wannan abun da ya samu. Manzon Allah(S) ya ce to wannan ɗabi'ar ce Allah(S W T) ke so tattare da shi shi saboda haka ya ce a ƙyale shi.

To da ya ji wannan saboda shi ne aka aiko Jibrilu ya zo da babban saƙo ya ce haka addinin Musulunci ke son mutanen kirki? Sai ya ce Ashhadu an la'ilaha illallah Muhammadurrasulullah nan yai Imani

Daga wani bangare na Khuɗuba da Shaikh Yaqoub Yahya Katsina ya gabatar a can baya mai taken AMALU SALIH.

__Abdurrahman Tasi'u Rimi
6/June/3023(17/04/144)

10/06/2023

Daga Katsina; Yanzu haka a wurin Mauludin Annabi Isah.

CIKIN HOTUNA: MAULUDIN IMAM RIDHA(A.S) A DA'IRAR RIMI.___Abdurrahman Tasi'u Rimi.Ƴan'uwa Musulmi Almajiran Shaikh Ibrahi...
31/05/2023

CIKIN HOTUNA: MAULUDIN IMAM RIDHA(A.S) A DA'IRAR RIMI.

___Abdurrahman Tasi'u Rimi.

Ƴan'uwa Musulmi Almajiran Shaikh Ibrahim Yaqoub Al-zakzaky(H) na Da'irar Rimin Jihar Katsina sun gabatar da taron mauludin ɗaya daga cikin Imaman shiriya na gidan Annabta wato Imam Aliyu Bin Musa Arridha(A.S) wanda ya kasance shi ne Imami na takwas(8) daga cikinsu.

Taron wanda gabata a cikin daren yau Laraba 11/4/1444H wanda yai dai-dai da 31/05/2023, wanda taron ya samu halartar mutane da dama na cikin garin Rimin.

Malam Aminu Usman Jakara wanda shi ne wakilin ƴan'uwa na garin shi ne ya gabatar da jawabi a muhallin taron k**ar yadda zaku gani a cikin hoto na farko daga jerin hotunan da muka ɗauko maku a wurin taron Mauludin.

'irarRimiMediaForum.
31MAY2023.

Tawagar Jami'an El-Rufai sun bi dare sun rushe gidan marayu wato gidan Marigayi Alhaji Hamid Ɗanlami dake babban Dodo Za...
28/05/2023

Tawagar Jami'an El-Rufai sun bi dare sun rushe gidan marayu wato gidan Marigayi Alhaji Hamid Ɗanlami dake babban Dodo Zariya.

Sannan har wala yau sun rushe makarantar Fudiyyah dake garin Bomo a ƙaramar hukumar Sabon Garin Zariya.

GAGGARUMAN MUZAHARAR ƘIN AMINCEWA DA TA'ADDANCIN GWAMNATIN JAHAR KADUNA DA REALESE PASSPORTS A GARIN KATSINA.Ƴan uwa Alm...
26/05/2023

GAGGARUMAN MUZAHARAR ƘIN AMINCEWA DA TA'ADDANCIN GWAMNATIN JAHAR KADUNA DA REALESE PASSPORTS A GARIN KATSINA.

Ƴan uwa Almajiran Sheikh Ibrahim Yaƙub Al'zakzaky Hafizahullah na Da'irar ta Katsina sunfito Muzaharar kin amincewa da Zalinci da akeyi wa ƴan uwa na jahar Kaduna da Zaria, da Gwamnatin jahar takeyi masu.

Gwamnatin k**akarya ta jahar Kaduna ta Nasuru El'rufa'i ta na rushe wa ƴan uwa na Kaduna da Zaria muhalai, da Makarantun Addini da na Boko. A bisa zalinci da danniya. Masu Muzaharar a yayin ita Muzaharar sunata raira Slogan mai taken ƴanci da kin amincewa da da ta'addancin da ake wa ƴan uwa tare kakkausan matarni zuwa gaa Gwamnatin jahar ta Kaduna.

Ƴan uwa sun ƙara jadda wa Gwamnatin cewa, ita shi'ar "Tana a zukata take ba a gini ba". Sannan ta ɓangare guda s**a ƙara jaddamashi cewa;"Rushe Makarantu bazai hana Ilimartar da 'ya'yanmu ba."

Malam Dalhatu Ƙarƙu shi ne mai jawabi a muhalin rufe ita ai nafin Muzaharar ta kin amincewa da Zalincin da akeyi mana. Malam ya ja hankalin Gwamnatin jahar Kaduna da ita ai nafi Gwamnatin Nigeria gabakiɗaya akan passport ɗin Malam Zakzaky Hafizahullah.

Anyi Lafiya an tashi Lafiya ga wasu hotuna da muka ɗauko maku a yayin Muzaharar.


( #0018)

Address

Rimi Local Government
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Da’irar Rimi posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share