15/01/2026
Babbar kotun jihar katsina ta rushe shugabancin kungiyar yan katako bayan kwashe sama da Shekaru 24 ba tare da zaɓe ba
Babbar Kotun Jihar Katsina mai lamba 10 ta yanke hukunci na rushe shugabancin ƙungiyar ta yan katako da Alhaji Halle Mu’azu Tudun Yanshanu ke jagoranta.
Kotun ta bayar da wannan umarni ne bayan tabbatar da cewa ƙungiyar ta shafe shekaru ashirin da huɗu (24) ba tare da gudanar da sahihin zaɓe ba.
Wannan lamari, a cewar kotun, ya saɓa wa kundin tsarin mulkin ƙungiyar, wanda ya tanadi cewa dole ne a rika yin zaɓe a duk bayan shekara huɗu (4) domin sabunta shugabanci.
A sakamakon hakan, kotun ta ba wa waɗanda s**a shigar da ƙarar dama su ci gaba da shirya taron Congress domin kafa sabon tsari da kuma gudanar da sabon zaɓe.
Kotun ta amince da kwamitin rikon ƙwarya (Caretaker/Committing) da Alhaji Abu Suleiman Albaba ke jagoranta, tare da Aminu Buhari Kaita a matsayin sakataren kwamitin.
Wannan hukunci yana zama darasi mai ƙarfi ga ƙungiyoyi da ƙungiyoyin sana’o’i a fadin ƙasa, yana nuna cewa bin doka da kundin tsarin mulki ba zaɓi ba ne, wajibi ne.
Haka kuma, ya tabbatar da cewa babu wani shugabanci da zai daɗe idan ba ya tafiya bisa tsarin da aka amince da shi.