Dawisu Reporters

Dawisu Reporters Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Dawisu Reporters, Media/News Company, Katsina.

YANZU YANZUfassarar hira da Jagoran juyin-juya hali na Kasar Iran Ayatollah khumenei wacca ya gabatar A gidan Talabiji n...
27/06/2025

YANZU YANZU
fassarar hira da Jagoran juyin-juya hali na Kasar Iran Ayatollah khumenei wacca ya gabatar A gidan Talabiji na Aljazeera.

Daga: Tajuddeen Shuaibu koki.

A yau ne gidan talabijin na Aljazeera ya kawo hira kai tsaye da jagoran juyin juya hali na ƙasar iran bayan tsagaita wuta akan yaƙin da s**a fafata da ƙasar yahudu da ƙasar amurka

Acikin hirar tasa Ayatullah Khomeini yace :-

- Ƙasar amurka tace mu miƙa wuya toh baza mu miƙa wuya ba domin mu ba bayin kowa bane zamu cigaba da ayyukanmu kuma koyau aka taɓa mu za aji mu

- Kasar amurka tace mu dakatar da shirinmu na nukiliya wanda har s**a kawo hari domin su lalata mana shiri amma ba suyi nasara ba, inaso trump ya sani insha Allah cikin wata august zamu cigaba da ayyukanmu na nukiliya

- Sannan ina kira da alummar ƙasar iran suyi haƙuri akan aminchewa da mukayi na tsagaita wuta ba munyi bane saboda da wani dalili mun aminche ne saboda sune s**a fara yaƙin kuma sun nemi a dakata

- Duk wata ƙasa a duniya dake tunanin ta shirya yaƙi da ƙasar iran a faɗa mata muna sauraronta

Kaɗan daga cikin abubuwan da jagoran ƙasar iran ya fada kenan a hira da yayi a karon farko bayan fara yaƙi da ƙasar yahudu da amurka.

An kashe wa Isra’ila mutum 29 da jikkata 3,345 a yaƙin ƙasar da IranƘasar Isra’ila ta ayyana cewa mutum 29 ne s**a mutu,...
27/06/2025

An kashe wa Isra’ila mutum 29 da jikkata 3,345 a yaƙin ƙasar da Iran

Ƙasar Isra’ila ta ayyana cewa mutum 29 ne s**a mutu, yayin da mutum 3,345 s**a jikkata a yaƙin da aka gudanar tsakanin ƙasar da Iran.

Ma’aikatar Lafiya ta ƙasar ta ce baya ga wannan adadin, mutane sama da 11,000 ne aka ɗaiɗaita tare da raba su da muhallansu a yanzu.

First Jumuah of 1447..
27/06/2025

First Jumuah of 1447..

Macron ya ce “mummunan abu zai iya faruwa” idan Iran ta fice daga kungiyar  yarjejeniyar hana yaɗuwar makaman nukiliyaSh...
27/06/2025

Macron ya ce “mummunan abu zai iya faruwa” idan Iran ta fice daga kungiyar yarjejeniyar hana yaɗuwar makaman nukiliya

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana haka ne a ranar Alhamis cewa hare-haren da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran sun kasance “a zahiri masu tasiri,” amma “mummunan yanayi mafi hatsari” zai kasance ne idan Iran ta fice daga yarjejeniyar hana yaɗuwar makaman nukiliya ta duniya.

“Abu mafi muni shi ne idan sakamakon wannan hari ya janyo ficewar Iran daga Non-Proliferation Treaty (NPT), wanda hakan zai iya haifar da tangarda da rauni a ƙoƙarin duniya gaba ɗaya,” in ji Macron ga manema labarai bayan taron koli na Tarayyar Turai a Brussels.

Macron ya ce domin kiyaye yarjejeniyar — wacce aka kulla domin rage yaduwar makaman nukiliya zai yi magana cikin 'yan kwanaki masu zuwa da mambobi biyar na Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya. Ya ce ya riga ya fara tattaunawar da kiran waya da Shugaba Donald Trump a ranar Alhamis, inda ya shaida masa irin tuntubar da Faransa ta yi da Tehran “cikin ‘yan kwanaki da sa’o’i da s**a wuce.”

“Fatanmu shi ne a samu daidaituwar ra’ayi,” in ji Macron, yana mai ƙarawa da cewa burin shi ne “kar a sake komawa” ga gina makaman nukiliya daga Iran.

Iran ta sanya hannu kan yarjejeniyar hana yaɗuwar makaman nukiliya (NPT) a shekarar 1970, inda ta dauki alkawarin sanar da Hukumar Makaman Nukiliya ta Duniya (IAEA) duk wani sinadarin nukiliya da take da shi.

Amma kwanan nan Iran ta fara shirye-shiryen da ka iya kai ta ga ficewa daga wannan yarjejeniya, tana zargin IAEA da yin aiki da “Isra’ila a yakin da take yi da Iran.”

A karshen makon da ya gabata, jiragen yakin B-2 na Amurka sun kai wa cibiyoyin nukiliyar Iran guda biyu hari da manyan bama-baman GBU-57 da ke shiga cikin ƙasa. Haka kuma wani jirgin ruwan yaki mai ɗauke da makamai masu linzami ya kai hari kan cibiyar uku da makaman Tomahawk.

Shugaba Trump kansa ya bayyana hare-haren a matsayin “nasara mai ban mamaki a fagen soja,” kuma ya ce suna da Burin

Yadda aka gudanar da Sallar Juma'a ta farko a sabuwar shekarar Musulunci ta 1447A.H a Masallacin Annabi SAW na Madina.📸:...
27/06/2025

Yadda aka gudanar da Sallar Juma'a ta farko a sabuwar shekarar Musulunci ta 1447A.H a Masallacin Annabi SAW na Madina.

📸: Inside the Haramain

Dalilan da su ka sanya Ganduje ya ajiye mukaminsa na shugabancin jam'iyyar APC na ƙasa A cikin wani mataki da ya ba da m...
27/06/2025

Dalilan da su ka sanya Ganduje ya ajiye mukaminsa na shugabancin jam'iyyar APC na ƙasa

A cikin wani mataki da ya ba da mamaki, Abdullahi Umar Ganduje, Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, ya yi murabus daga mukaminsa nan take.

Ganduje, tsohon Gwamnan Jihar Kano, ya bayyana dalilin neman lafiya a matsayin abin da ya sa ya yanke shawarar sauka daga kujerar, yana mai cewa yana bukatar mayar da hankali kan lafiyarsa.

Jaridar PREMIUM TIMES ta rawaito cewa duk da cewa takardae murabus din na sa ta danganta saukarsa da batun lafiya, majiyoyi da ke da masaniya da al’amarin sun nuna cewa akwai yiwuwar rikici na siyasa a cikin jam’iyyar ya taka rawa wajen yanke shawarar da ya dauka.

Jaridar Premium Times ta rawaito cewa, ana danganta saukarsa da zarge-zargen almundahana da s**a shafi harkar kuɗi, inda wasu mambobin jam’iyyar s**a bayyana rashin jin daɗinsu kan “yawan bukatun kuɗi fiye da kima” da ofishinsa ke kakaba.

Saudiyya ta bayar da tallafin Dala miliyan 30 ga mutanen GazaƘasar Saudiyya ta sanar da bayar da tallafin Dala miliyan 3...
27/06/2025

Saudiyya ta bayar da tallafin Dala miliyan 30 ga mutanen Gaza

Ƙasar Saudiyya ta sanar da bayar da tallafin Dala miliyan 30 ga Hukumar Kula da Falasɗinawa domin taimaka wa Falasɗinawa kan halin matsi na tattalin arziki sanadiyyar yaƙin ƙasar da Isra’ila.

Saudiyya ta ba da wannan taimakon ne a birnin Amman, kuma za a yi amfani da shi a ɓangarorin kiwon lafiya, ilimi, da biyan albashin ma’aikatan gwamnati.

Amurka ta cimma yarjejeniya da China don hanzarta fara jigilar kayayyaki zuwa Amurka, a daidai lokacin da ake ƙoƙarin ka...
27/06/2025

Amurka ta cimma yarjejeniya da China don hanzarta fara jigilar kayayyaki zuwa Amurka, a daidai lokacin da ake ƙoƙarin kawo ƙarshen yakin kasuwanci tsakanin manyan ƙasashen biyu na duniya.
Ƙarin bayani a sashin muhawara
📸AP

YANZU-YANZU: Wutar Daji ta kutsa wasu yankunan Isra'ila. Wata gagarumar wutar daji ta auka wa yankin Ness Ziona da ke ku...
27/06/2025

YANZU-YANZU: Wutar Daji ta kutsa wasu yankunan Isra'ila.

Wata gagarumar wutar daji ta auka wa yankin Ness Ziona da ke kusa da birnin Tel Aviv, inda ta babbake wasu gidaje lamarin da ya tilasta wa hukumomi kwashe mutane daga gidajensu, kamar yadda gidan rediyon Rundunar Sojin Isra'ila ya ruwaito ranar 26 ga watan Yuni

Rahoton — TRT

“Mai tsoron barazana a ke yi wa barazana” martanin da jagoran ƙasar Íran Sheikh Ayatullah Khameni kenan ga shugaban ƙasa...
19/06/2025

“Mai tsoron barazana a ke yi wa barazana” martanin da jagoran ƙasar Íran Sheikh Ayatullah Khameni kenan ga shugaban ƙasar Amurka Donald Trump bayan ya yi barazanar cewa Amurka za ta iya kaiwa Íran hari.

Yadda birnin Tel Aviv na Isra'ila ya kasance a safiyar yau AlhamisHoto: Iran military
19/06/2025

Yadda birnin Tel Aviv na Isra'ila ya kasance a safiyar yau Alhamis

Hoto: Iran military

HOTUNAN:Farmakin da Iran takai cibiyar saka hannun jari na Isra'ila mai suna Diamond Exchange District
19/06/2025

HOTUNAN:
Farmakin da Iran takai cibiyar saka hannun jari na Isra'ila mai suna Diamond Exchange District

Address

Katsina

Telephone

+2348039922227

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dawisu Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share