Dawisu Reporters

Dawisu Reporters Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Dawisu Reporters, Media/News Company, Katsina.

Munafùķài Ne Kawài Za Sù Yì Kìrà Da A Sakè Zabaŕ Mùślim-Mùsĺim Tiket, Inji Sheik Ahmad Gumi
26/05/2025

Munafùķài Ne Kawài Za Sù Yì Kìrà Da A Sakè Zabaŕ Mùślim-Mùsĺim Tiket, Inji Sheik Ahmad Gumi

YANZU-YANZU: Arewa Ita Ce Babbar Garkuwar Nijeriya, Kuma Tana Da Ƙarfin Sauya Halin Da Ƙasar Ke Ciki    -Inji Peter ObiO...
25/05/2025

YANZU-YANZU: Arewa Ita Ce Babbar Garkuwar Nijeriya, Kuma Tana Da Ƙarfin Sauya Halin Da Ƙasar Ke Ciki

-Inji Peter Obi

Obi ya bayyana hakan ne yayin taron National Political Consultative Group (North) da aka gudanar a ranar Lahadi a birnin tarayya Abuja.

“Na sha faɗi cewa Arewa na da damar canja Nijeriya. Babban arzikin wannan ƙasa yana Arewa.”

"Arzikin ƙasa da albarkatun da Allah ya azurtawa Arewa da su, kamar noma, albarkatun ƙasa, da yawan jama’a masu aiki tuƙuru, na nuni da cewa yankin na da ƙarfin jawo ci gaba mai ɗorewa ga Nijeriya baki ɗaya." Inji Obi

Sheik Maqari Ya Kaiwa Sheik Asadus-Sunnah Ta'aziyyar Rasuwar Mahaifyarsa
01/05/2025

Sheik Maqari Ya Kaiwa Sheik Asadus-Sunnah Ta'aziyyar Rasuwar Mahaifyarsa

MATSANAN CIYAR WUTAR DAJI TA KUNNO KAI A KASAR ISRA'ILA. A halin yanzu, Ƙasar Isra’ila na fuskantar babbar wutar daji da...
30/04/2025

MATSANAN CIYAR WUTAR DAJI TA KUNNO KAI A KASAR ISRA'ILA.

A halin yanzu, Ƙasar Isra’ila na fuskantar babbar wutar daji da ta mamaye wasu sassan ƙasar, wadda mahukuntan kasar s**a bayyana da cewa sun kasa shawo kanta, duk da ɗaukar matakan kashe ta da sukeyi ba dare ba rana.

DA DUMI DUMI: 2027 Munyi kyakkyawan Tsari Hatta Wanda Ba'a Haifaba Zamuyi Masa Albashi idan kuka Sake Bamu dama a karo n...
30/04/2025

DA DUMI DUMI: 2027 Munyi kyakkyawan Tsari Hatta Wanda Ba'a Haifaba Zamuyi Masa Albashi idan kuka Sake Bamu dama a karo na biyu, Bola Tinubu ga yan Nigeria

Me Zaku Ce

Mucire San Zuciya da Adawa Wato Gaskiya abunda Hon Sani Aliyu Danlami yayi a Katsina Central abun ayabamasane bamu Taba ...
30/04/2025

Mucire San Zuciya da Adawa Wato Gaskiya abunda Hon Sani Aliyu Danlami yayi a Katsina Central abun ayabamasane bamu Taba samun dan Majalisar da ya kyautatama na taredashiba a Constituency dinmu ba dan Haka Ina mika Sakon taya Murna gabMutanan da ya Temaka dafatan Allah yasakamashi da Alkhairi yasa duk Shekara yaci gaba da Irin Wannan abun Alkhairin Kuma Ina kira da Sauran Yan Majalisu suyi koyi da Irin Wannan abun Alkhairin

Sakon Hon.Aliyu Umar Sarkin Yaki Tshohon Dan Takarar Majalisar Tarayya na Katsina Central

30/03/2025

MUNA YIMA AL'UMMAR MUSULMIN DUNIYA BARKA DA SALLAH DAFATAN ALLAH YA KARBI IBADUNMU

AL'UMMAR CIKIN BIRNI SUNYI TARON ADDU'A GA MAHAIFIYAR MAI GIRMA GWAMNAN JIHAR KATSINA MALAM DIKKO UMAR RADDA PhD. A kark...
29/03/2025

AL'UMMAR CIKIN BIRNI SUNYI TARON ADDU'A GA MAHAIFIYAR MAI GIRMA GWAMNAN JIHAR KATSINA MALAM DIKKO UMAR RADDA PhD. A karkashin jagoroncin; Honorable Mubarak Lamis Gafai.

A yau Alhamis 27 ga watan Maris, 2025. Hon. Mubarak Lamis Gafai ya jagoranci al'ummar cikin birni da kewaye, domin yin addu'a ga mahaifiyar gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda PhD.

Allah ya yima Hajiya Safara'u Radda, rasuwa a ranar Lahadi 23 ga watan Maris 2025. Wanda aka gudanar da ta'aziyyarta kamar yadda addini ya tanada.

Taron addu'ar, ya sami halartar manyan malamai da limamai da shuwagabannin al'umma na wannan yanki. An gabatar da saukar al-qur'ani mai girma, tare da addu'oi ga ruhin mamaciyar.

Daga karshe, al'ummar s**a mika sakon ta'aziyyarsu ga al'ummar jihar Katsina baki daya, musamman mai girma gwamna.

Da fatan Allah ta'ala yayi mata rahama da jin kai, yasa haske a makwancin ta. Allah ya kula da zuriyar data bari.

Da farko dai, Muna Mika Ta’aziyya ga yan uwan da Abokanan Arziki da ilahirin Mutanen Arewa a bisa Waenda wannan Ibtila’i...
29/03/2025

Da farko dai, Muna Mika Ta’aziyya ga yan uwan da Abokanan Arziki da ilahirin Mutanen Arewa a bisa Waenda wannan Ibtila’in Kisan Gilla a Faru dasu a Wani Gari a Edo State.

Nayi matukar Girgiza, Zuciyata ta kasa Ganin wannan Kisan Gillan da wasu bara gurbi mutanen kuma fa Yan Nigeria ne, waenda zuciyansu ya kekashe, wa’enda talauci yayi musu katutu a zuciyansu , saboda kwai kishi na jahilci akan su yan Arewa ne!

Na tsani Nuna Kabilanci ko na bangaren yare, Ko na Addini ko kuma Jinsi, ko kuma na Gari, wannan Abun ba karamin koma baya yake jawo wa a harka rayuwa da cigaba ba.

Wannan kisan Gillan ya wuce misali, ya firgitani, kuma nashiga dimuwa matuka! Kuma insha Allah muna magana da Manya manya Hukumomi, Kungoyoyin Kare hakkin bil’adam da kuma wasu masu kishin Arewa don samun matsaya akan wannan ibtila’in.

Haka kawai K**a Mutum da Ran shi, ka daure shi, ka saka shi cikin taya, ka zuba mishi petroluem ko kalanzir, ka Ketta masa wuta, kuma kashe shi , kana kallonsa yana ihu yana kuma kuma kana mishi Dariya har sai kaga ranshi ya fita, batare da wata Dalili ba kuma kai ba Hukuma ba!

Kai wannan Abu yayi muni!
Insha Allah sai mun bi kadin hakkin waenaan bayin Allah.

Muna Kira ga Jami’an tsaro da su gaggauta Kamo waenda s**ayi wannan Kisan Gillan don girban Abunda s**a aikata.

DA ƊUMI-ƊUMI: Mun Ķàma Mùtanê 14 Da Ake Źargin Šù Ďa Hannu Wajen Ķìsan Mafarauta A Jihar Edo, Cewar 'Ýan Saɲda.
28/03/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Mun Ķàma Mùtanê 14 Da Ake Źargin Šù Ďa Hannu Wajen Ķìsan Mafarauta A Jihar Edo, Cewar 'Ýan Saɲda.

YANZU-YANZU: Gwamnatin Jihar Bauchi Ta Fara Biyan Albashi Kafin Bikin Sallah na 2025Gwamnatin Jihar Bauchi ta fara biyan...
28/03/2025

YANZU-YANZU: Gwamnatin Jihar Bauchi Ta Fara Biyan Albashi Kafin Bikin Sallah na 2025

Gwamnatin Jihar Bauchi ta fara biyan albashin ma’aikata domin saukaka musu wajen shirye-shiryen bikin Sallah na 2025. Duk da cewa biyan albashi ba wani babban abu ba ne, wannan mataki yana da muhimmanci wajen tallafawa ma’aikata a lokacin bukukuwa.

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya tabbatar da cewa gwamnatinsa tana da kwarin gwiwa wajen inganta walwalar ma’aikata duk da sabbin tsarin biyan albashi a matakin kananan hukumomi da gwamnatin APC ke kokarin aiwatarwa. Ya ce: “Muna fahimtar muhimmancin biyan albashi a kan lokaci, kuma muna da niyyar ci gaba da bai wa ma’aikatanmu hakkokinsu.”

Wannan mataki ya zo ne bayan damuwar da ma’aikata s**a nuna kan jinkirin biyan albashi, musamman a matakin kananan hukumomi. Sai dai, da wannan biyan kudin albashi a lokaci, gwamnati na kokarin rage damuwa ga ma’aikata yayin da bikin Sallah ke karatowa.

Ma’aikata da dama sun nuna godiyarsu ga gwamnati, suna mai cewa hakan zai taimaka musu wajen biyan bukatun iyalansu. Biyan albashin a kan lokaci zai kara wa ma’aikata kwarin gwiwa da kuma taimakawa wajen gudanar da bukukuwan Sallah cikin jin dadi a fadin jihar Bauchi.

-Zamani TV

Dayyabu Yahaya Na Ɗaya Daga Cikin Matafiyan Da Aka Halaka Abokan Tafiyar A Jihar Edo Ya Bayyana Cewa Yan Bijilanti Na Ga...
28/03/2025

Dayyabu Yahaya Na Ɗaya Daga Cikin Matafiyan Da Aka Halaka Abokan Tafiyar A Jihar Edo Ya Bayyana Cewa Yan Bijilanti Na Garin Ne S**a Tare Su Kuma Basu Same Mu Da Komai Ba Sai Bindigún Farauta, Kuma Duk Suna Da Lasisi.

A Cewarsa Sunyi Bincike Basu Sami Komai Ba, Sai S**a Ce Ai Mu Yan Kidnàpping Ne, S**a Tara Mutanen Mu A T**i, S**a Kone Su, Muma Da Kyar Muka Tsira - Inji Shi.

Address

Katsina

Telephone

+2348039922227

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dawisu Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share