05/09/2025
Shugaban Jam'iyar ADC na jahar Alhaji Musa Usman Wamba yayi kira ga al'ummar jahar Katsina dasu fito su yanki katin jefa kura'a da hukumar Zabe mai zaman kanta ta fara a fadin kasar
A Yau juma'a 5 Sep 2025 Mai girma shugaban Jam'iyar ADC na jahar katsina yayi wannan kira ne ga al'umma ta bakin mataimakin Hon Umar Shu'aibu a yayin gudanar da taron Shugabannin jam'iyar ADC na kananan Hukumomin wanda taron ya wakan a Babban Ofishin Jam'iyar na Jaha dake cikin Birnin Katsina.
Hon Umar Shu'aibu Yakara godewa shugannin da s**a hada Sakatere, Shugabar Mata da Shugaban matasan jam'iyar duk na kananan Hukumomi 34 dake fadin jahar akan namijin kokarin da suke wurin tabbatar da jam'iyar ta shiga lungu da sako na jahar, Ya kara dacewa shugaban Jam'iyar Alhaji Musa Wamba ne yace ayi wannan godiyar a madadinshi
A lokacin da take nata jawabin Shugabar matan ADC na jahar Katsina Hajiya Hauwa Jibrin (Yargata) tayi kira ga shugabanni matan na kananan hukumomin jahar Katsina da suci gaba aikin da suke na tallata jam'iya a duk inda s**a samu kansu misali Gidan suna, gidan Biki, kasawa Wurin saye da sayarwa da sauran su.
Hon YarGata taci gaba dacewa mata sune zabe domin sune masu jurewa duk zafi zasu tsaya suyi zabe kuma sune ake saurin yaudara da dan abu kalilan a canja musu tinani dan haka aikine gare mata kutashi ku wayar ma mata da kai akan wannan muhimman batutuwan.
Shima shugaban Matasan Jam'iyar ADC na jahar Katsina Hon Aliyu Umar (Sarkin Yaki) ya kara godewa matasan jam'iyar Musamman Wa'inda ke amfani da kafafen sadar wurin tallata jam'iyar da Fadin manufofinta na Alkhairi ga mutanen jahar katsina, Haka kuma Hon Sarkin Yaki yaci gaba da cewa jam'iyar ADC Jam'iyace wadda take da nagartattun shugabanni tunda daga sama harkasa musamman nan Jahar Katsina da Allah yabamu shugabannin Jam'iya da S**a Hada. Alhaji Musa Wamba, Dr Mustapha M Inuwa, Sanata Ahmad Babba Kaita, Sanata, Surajo Aminu Makera, Arch Ahmed Aminu Yar'adu, Sanata Sadiq Yar'adua dadai sauran su