Dawisu Reporters

Dawisu Reporters Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Dawisu Reporters, Media/News Company, Katsina.

Hon. Mustapha Salmanu Matazu dan Takarar majalissar Jaha a Tutar Jam'iyyar ADC a karamar hukumar matazu a Jahar katsina....
26/10/2025

Hon. Mustapha Salmanu Matazu dan Takarar majalissar Jaha a Tutar Jam'iyyar ADC a karamar hukumar matazu a Jahar katsina.

ADC youth Support Foundation Forum

Aslm alkm Ina Mai farin cikin sanarma Al'ummar Karamar Hukumar matazu cewa insha Allah Kuna chikin Alkhairi Dumu Dumu, sbd Achikin Satin nan *Hon. Mustapha Salmanu* zai Gudanar da Empowerment na koyan sana'a ga Mata dakuma Matasan Karamar Hukumar matazu, insha Allah.
Nan kusa za'a gabatar da wannan Shiri domin kawo chigaba a karamar hukumar matazu dama Jam'iyyar ADC Baki Daya.

Fatan Alkhairi *Hon. Mustapha Salmanu* allah ya Ida nufi na Alkhairi Ga Al'ummar Karamar Hukumar matazu.

By:- Aliyu mustapha matazu *Chairman* ADC youth Support Foundation Forum

Jahar Katsina na cikin jahohin farko dazan fara ziyarta a cikin jahohin najeriya inji shugaban jam'iyar ADC na kasa Sen ...
28/09/2025

Jahar Katsina na cikin jahohin farko dazan fara ziyarta a cikin jahohin najeriya inji shugaban jam'iyar ADC na kasa Sen David Mark. Sanata Sadiq Yar'adua yafadi sakon ayau lokacin da yake ganawa da shuwagabannin ADC na karamar Hukumar Katsina

‎A yayin da zaman ke wakana daya daga cikin jagororin hadaka ta ADC a jahar Katsina Sanata Sadiq Yar'adua ya yabawa jagorin ADCn na jahar katsina akan haduwar kawunan su wari daya. Wanda hakan yasa har shugaban jam'iyar na kasa yace Jahar Katsina na daya daga cikin jahohin dazaya fara ziyarta saboda jahar ta samu jagororin da s**a hada kansu

‎Sanata Sadiq Yar'adua yakara da cewa nasara bata taba samuwa saida hadin kai wanda hakan yasamo asali tun daga lokacin da Ake kokarin ganin muslunci yasamu tsayuwa da kafafunshi saida Sahabban Manzon Allah SAW s**a hada kawunansu wuri daya sannan s**a samu nasarar tabbatar da addinin Allah. Toh yazama wajibi mu zamto masu hadakammu wuri daya domin tunkarar wannan gwamnati marar Alkibla wadda ko wanda ke cikinta baisan inda ta dosa ba

‎Sanata Sadiq Yar'adua Ya kuma yi kira ga Shugabannin ADCn na karamar Hukumar Katsina dama sauran kananan hukumomin katsina suyi kokari suyi koyi da shugabannin na jaha dan samun nasarar da ake bukata. Yaci gaba da jan hankalin su wurin bada shugabanci na jam'iya daga inda aka cire san rai akai abunda yadace to za'a samu nasarar da ake bukata

‎Sanata Yar'adua yaci gaba dacewa idan aka kalli tarihin wasu yan siyasar da s**ayi tsarin shugabannin jam'iyar a lokuttan baya amma Allah danashi ikon bai basu nasara ba duk da suna shugabannin jam'iyar wanda koshi hakan yataba faruwa dashi, Shiyasa yake kira a tsaya ayi abunda yadace kan hidimar inde nasarar ta ake nema.

‎Shima, a lokacin dayake tofa albarkacin bakinsa Ambasada Yakubu Muhammad ya jinjinama jagororin akan yadda duk s**a cire wani bangaranci suke kallan gina jam'iyar shine gaba akan komai dan haka yazama wajibi ga mabiya suyi koyi da wannan halayen na shugabannin mu daga karshe yayi addu'a ta

Abin Mamaki Ne A Ce Kungiyar Izala Ta Je Wa'azin Kasa Jihar Kebbi Amma Har Aka Gama Wa'azin Babu Wani Malami Da Ya Yi Ma...
10/09/2025

Abin Mamaki Ne A Ce Kungiyar Izala Ta Je Wa'azin Kasa Jihar Kebbi Amma Har Aka Gama Wa'azin Babu Wani Malami Da Ya Yi Magana Kan Matsalar Tsaro Da Ake Fama Da Shi A Yankunan Zamfara, Sokoto, Kebbi Da Sauransu, Tsoronsu Kada A Ce Sun Soki Gwamnati, Cewar Sheik Yusuf Sambo Rigachukun

Fadar shugaban kasa Villa babu ruwansu da lalacewar NEPA tunda sun hada Solar mai kyau da ta lakume kimanin Naira Biliya...
10/09/2025

Fadar shugaban kasa Villa babu ruwansu da lalacewar NEPA tunda sun hada Solar mai kyau da ta lakume kimanin Naira Biliyan 10.

Akwai shugabannin Hamas a ciin ƙasar mu, muna son ku kawo hari a kansu ku gani, ku kuma Qatar a lokacin da maƙiyanmu maƙ...
09/09/2025

Akwai shugabannin Hamas a ciin ƙasar mu, muna son ku kawo hari a kansu ku gani, ku kuma Qatar a lokacin da maƙiyanmu maƙiyanku suke kawo mana hari baku tare ba, amma idan mun kai musu hari sai ku riƙa tare musu kuna kakkaɓo makaman mu, yanzu gashi sun keta haddin ku, amma idan kun bamu dama zamu shigar muku mu tare faɗan—Khamenei

Yanzu-Yanzu: INEC ta fitar da sabbin bayanai kan adadin mutanen da s**a yi rajistar katin zaɓeHukumar Zabe Mai Zaman Kan...
09/09/2025

Yanzu-Yanzu: INEC ta fitar da sabbin bayanai kan adadin mutanen da s**a yi rajistar katin zaɓe

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta fitar da sabbin bayanai kan ci gaban da ake samu a aikin ci gaba da rijistar masu kada kuri’a na kasa baki daya.

Wannan bayanin na cikin wata sanarwa da Sam Olumekun, Kwamishina na Kasa kuma Shugaban Kwamitin Ilimantar da Masu Zabe, ya fitar a ranar Litinin.

Kwamishinan ya bayyana cewa a cikin sati uku ya nuna cewa an samu jimillar ’yan Najeriya miliyan 3,544,850 da s**a yi rajista ta yanar gizo.

A karon farko, Gwamnatin Saudiyya ta amince a fara gudanar da zagayen murnan haihuwar MANZON ALLAH SAW a biranen Makka M...
09/09/2025

A karon farko, Gwamnatin Saudiyya ta amince a fara gudanar da zagayen murnan haihuwar MANZON ALLAH SAW a biranen Makka Madina da Riyad, duk da cewa ba'a kira taron zagayen, da sunan Mauludi ba amma an bayyana shi a matsayin murnar zagayowar watan da aka haifi ANNABI SAW, yau an yi a Madina, gobe za a gudanar da zagayen a birnin Riyad, a ƙarƙare a Makka.

A Kokarin Inganta Rayuwar Al'ummar jahar Katsina, Jam'iyyar ADC Zata Kaddamar da Bukin Koyar da Sana'o in Dogaro dakai g...
09/09/2025

A Kokarin Inganta Rayuwar Al'ummar jahar Katsina, Jam'iyyar ADC Zata Kaddamar da Bukin Koyar da Sana'o in Dogaro dakai ga Matasa da Mata Acikin Garin Katsina, Bukin Koyar da Sana'o in da Zai Gudanane A Ranar 21-09-2025, a Harabar Babban Ofishin Jam'iyyar dake Kantitin IBB Way Kan Hanyar Zuwa KANO Acikin Birnin Katsina.

Shirin Koyar da Sana'o in Yakasance a Karkashin ofishin Shugaban Matasan Jam'iyyar ADC na Jahar Katsina, Hon Aliyu Umar Sarkin Yaki, Wanda Za'a Koyar da Sana'o Maban Banda Inda S**a hada da.

1- Koyar da Hada Manshafawa
2- Koyar da Sabulun Ruwa
3 Dakuma Koyar da Noman Dankali

Hakika Wannan Abune Mai Matukar Mahimmanci Musamman ga Matasanmu hadida Iyaye Mata

Muna taya wadan da S**a Samu Wannan gagarumar dama Tare da Fatan Zasu Kasance Sunyi Amfani da ita Domin Dogaro da Kawunansu Da Al'ummar jahar katsina.

Ubangiji Allah Yasa Afara lafiya agama lafiya, Allah Yakara Nasara ga Jam'iyyarmu Mai Albarka African Democratic Congress -ADC.

Signed by,
Met JKMALUMFASHI Katsina State ADC Media Department.

ZAƁEN 2027: A halin yanzu dai Arewacin Najeriya sun duƙufa wajen yin katin zaɓe tare da wayar da kai game da zaɓe, a lok...
09/09/2025

ZAƁEN 2027: A halin yanzu dai Arewacin Najeriya sun duƙufa wajen yin katin zaɓe tare da wayar da kai game da zaɓe, a lokaci guda kuma ƴan kudu suna can su ma suna yin rijistar katin zaben ta Intanet.

A ganin ku wa zai kafa shugabancin ƙasa?

Shugaban Jam'iyar ADC na jahar Alhaji Musa Usman Wamba yayi kira ga al'ummar jahar Katsina dasu fito su yanki katin jefa...
05/09/2025

Shugaban Jam'iyar ADC na jahar Alhaji Musa Usman Wamba yayi kira ga al'ummar jahar Katsina dasu fito su yanki katin jefa kura'a da hukumar Zabe mai zaman kanta ta fara a fadin kasar

‎A Yau juma'a 5 Sep 2025 Mai girma shugaban Jam'iyar ADC na jahar katsina yayi wannan kira ne ga al'umma ta bakin mataimakin Hon Umar Shu'aibu a yayin gudanar da taron Shugabannin jam'iyar ADC na kananan Hukumomin wanda taron ya wakan a Babban Ofishin Jam'iyar na Jaha dake cikin Birnin Katsina.

‎Hon Umar Shu'aibu Yakara godewa shugannin da s**a hada Sakatere, Shugabar Mata da Shugaban matasan jam'iyar duk na kananan Hukumomi 34 dake fadin jahar akan namijin kokarin da suke wurin tabbatar da jam'iyar ta shiga lungu da sako na jahar, Ya kara dacewa shugaban Jam'iyar Alhaji Musa Wamba ne yace ayi wannan godiyar a madadinshi

‎A lokacin da take nata jawabin Shugabar matan ADC na jahar Katsina Hajiya Hauwa Jibrin (Yargata) tayi kira ga shugabanni matan na kananan hukumomin jahar Katsina da suci gaba aikin da suke na tallata jam'iya a duk inda s**a samu kansu misali Gidan suna, gidan Biki, kasawa Wurin saye da sayarwa da sauran su.

‎Hon YarGata taci gaba dacewa mata sune zabe domin sune masu jurewa duk zafi zasu tsaya suyi zabe kuma sune ake saurin yaudara da dan abu kalilan a canja musu tinani dan haka aikine gare mata kutashi ku wayar ma mata da kai akan wannan muhimman batutuwan.

‎Shima shugaban Matasan Jam'iyar ADC na jahar Katsina Hon Aliyu Umar (Sarkin Yaki) ya kara godewa matasan jam'iyar Musamman Wa'inda ke amfani da kafafen sadar wurin tallata jam'iyar da Fadin manufofinta na Alkhairi ga mutanen jahar katsina, Haka kuma Hon Sarkin Yaki yaci gaba da cewa jam'iyar ADC Jam'iyace wadda take da nagartattun shugabanni tunda daga sama harkasa musamman nan Jahar Katsina da Allah yabamu shugabannin Jam'iya da S**a Hada. Alhaji Musa Wamba, Dr Mustapha M Inuwa, Sanata Ahmad Babba Kaita, Sanata, Surajo Aminu Makera, Arch Ahmed Aminu Yar'adu, Sanata Sadiq Yar'adua dadai sauran su

Da Dumi Dumi Gwamnan jihar Neja Mohammed Umar Bago, ya sauke dukkanin kwamishinonin sa.DCL Hausa
01/09/2025

Da Dumi Dumi

Gwamnan jihar Neja Mohammed Umar Bago, ya sauke dukkanin kwamishinonin sa.

DCL Hausa

Address

Katsina

Telephone

+2348039922227

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Dawisu Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share