Katsina Reporters

Katsina Reporters Shafin Katsina Reporters jarida ce da ke kokarin kawo maku ingantattun labarai na gaskiya ciki da wajen jihar Katsina.Call for more Inquiry TEL: 09038333537
(1)

Sabon Ɗan wasan Kungiyar Katsina United Chinedu Ozor Ya mutu Yayin da suke tsaka da buga wasan sada zumunta a KatsinaƘun...
11/08/2026

Sabon Ɗan wasan Kungiyar Katsina United Chinedu Ozor Ya mutu Yayin da suke tsaka da buga wasan sada zumunta a Katsina

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Katsina United FC ta sanar da rasuwar ɗan wasanta, Ozoh Chinedu, wanda ya rasu a lokacin wani wasan sada zumunta na share fage da aka gudanar ranar Talata.

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar ta ce Chinedu, ya gamu da ajalinsa ne yayin da ake gudanar da wasan, lamarin da ya jefa shugabannin ƙungiyar, ’yan wasa da magoya baya cikin alhini.

Katsina United ta bayyana matuƙar baƙin cikinta kan wannan babban rashi, tare da miƙa ta’aziyya ga iyalan marigayin, da yan uwansa da abokan aikinsa.

Ƙungiyar ta yi alhinin rashin Ozoh Chinedu a matsayin dan wasan da ya tafi yabar babban giɓi a fagen kwallon kafa.

Gwamna Dikko Radda Ya Yi Alkawarin Taimaka Wa UMYU Wajen Magance Kalubalen Kuɗi da Ababen More RayuwaGwamnan Jihar Katsi...
11/08/2026

Gwamna Dikko Radda Ya Yi Alkawarin Taimaka Wa UMYU Wajen Magance Kalubalen Kuɗi da Ababen More Rayuwa

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya yi alkawarin ci gaba da tallafa wa Jami’ar Umaru Musa Yar’adua (UMYU), domin taimaka mata wajen magance wasu daga cikin ƙalubalen kuɗi da na ababen more rayuwa da take fuskanta.

Gwamnan ya bayyana hakan ne ranar Talata lokacin da ya karɓi tawagar Hukumar Gudanarwar jami’ar, ƙarƙashin jagorancin Shugaban Hukumar, Sanata Hadi Sirika, a Gidan Gwamnatin Jihar Katsina.

Malam Radda ya ce gwamnatinsa za ta duba buƙatun da jami’ar ta gabatar tare da ɗaukar matakan da s**a dace gwargwadon damar gwamnati, musamman a fannonin da za su taimaka wajen inganta ayyukan jami’ar.

Ya jaddada cewa ingantaccen ilimi na daga cikin abubuwan da gwamnatinsa ta ba muhimmanci, yana mai cewa ƙarfafa jami’o’i zai taimaka wajen samar da ƙwararrun ma’aikata, bunƙasa bincike da ƙirƙire-ƙirƙire, tare da ƙarfafa tattalin arzikin jihar.

A nasa jawabin, Shugaban Hukumar Gudanarwar UMYU, Sanata Hadi Sirika, ya yaba wa Gwamna Radda bisa irin tallafin da yake bai wa fannin ilimi. Ya bayyana rashin isassun ababen more rayuwa, jin daɗin ma’aikata da kuma kuɗaɗen gudanar da ayyuka a matsayin wasu daga cikin manyan ƙalubalen da jami’ar ke fuskanta.

Shi ma Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Shehu Salihu Muhammad, ya gabatar wa gwamnan bayanai kan shirye-shiryen karatu, bincike da sauran ayyukan ci gaba da jami’ar ke gudanarwa, tare da gabatar da buƙatun da ake ganin za su taimaka wajen ƙara inganta ayyukanta.

A ƙarshe, Gwamna Radda ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da duba buƙatun jami’ar, musamman na gine-gine da sauran muhimman abubuwan ci gaba, gwargwadon albarkatun da jihar ke da su.

Da me Kujerar Maryam Idris Bagiwa ta amfanar da jihar Katsina?Maryam Idris Bagiwa ƴar asalin jihar Katsina ce kuma ita c...
11/08/2026

Da me Kujerar Maryam Idris Bagiwa ta amfanar da jihar Katsina?

Maryam Idris Bagiwa ƴar asalin jihar Katsina ce kuma ita ce Manajan Daraktan kasuwanci ta kamfanin NNPC bangaren sayar da ɗanyen Man-feur a Najeriya.

Ku bayyana ra'ayin ku?

Farfessa Isa Ali Pantami na ci gaba da samun karbuwa da karfin magoya a jihar Gombe gabanin zaɓen 2027Ɗan takarar Gwamna...
11/08/2026

Farfessa Isa Ali Pantami na ci gaba da samun karbuwa da karfin magoya a jihar Gombe gabanin zaɓen 2027

Ɗan takarar Gwamnan jihar Gombe na PDP a zaben 2027 Professor Isa Ali Pantami na cigaba da samun ƙarin karɓuwa da goyon bayan jama'a a sassa daban-daban na Jihar Gombe, yayin da harkokin siyasa ke ƙara ɗaukar sabon salo gabanin zaɓen gwamna na shekarar 2027.

A cikin 'yan makonnin nan, an samu ƙarin bayyanar da goyon baya ga takarar Pantami, musamman daga matasa, 'yan siyasa da masu ruwa da tsaki a wasu ƙananan hukumomin jihar. Rahotanni sun nuna cewa wasu daga cikin masu goyon bayansa sun kuma gudanar da taruka da tuntubar al'umma domin ƙarfafa tafiyar siyasar sa.

Haka kuma, wasu 'yan siyasa daga jam'iyyu daban-daban kamar Sen. Ɗan Kwambo da Ɗanjuma Goje sun bayyana goyon bayansu ga Pantami tare da komawa Jam'iyyar PDP, lamarin da ke ƙara nuna yadda takararsa ke samun ƙarfi a fagen siyasar jihar.

Masu lura da harkokin siyasar Gombe na ganin cewa ƙara samun goyon baya ga Pantami na daga cikin abubuwan da za su iya yin tasiri a fafatawar siyasar jihar yayin da ake tunkarar zaɓen 2027 da ke tafe.

Farfessa Isa Pantami shi ne dan takarar da ya tata kudirin maida tsarin ilimi irin na kasa Switzerland da kuma gina matasa kan tsarin horaswa na Cybersecurity.

Gwamnatin Dikko Radda Za Ta Kafa Cibiyar Binciken Noma da Kiwo a Katsina Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda,...
11/08/2026

Gwamnatin Dikko Radda Za Ta Kafa Cibiyar Binciken Noma da Kiwo a Katsina

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya sanar da shirin gwamnatin jihar na kafa Cibiyar Binciken Harkokin Noma da Kiwo, domin ƙarfafa bincike, inganta hanyoyin noma da kiwo, tare da bunƙasa amfani da sabbin fasahohi wajen ƙara yawan amfanin gona da dabbobi.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Litinin, lokacin da ya karɓi shugabannin Ƙungiyar Manoma ta Najeriya (AFAN), reshen Jihar Katsina, a Fadar Gwamnatin Jihar da ke Katsina. Ya bayyana noma da kiwo a matsayin ginshiƙan tattalin arzikin jihar, yana mai cewa kusan kashi 90 cikin 100 na al’ummar Katsina suna dogaro da waɗannan fannoni kai tsaye ko a kaikaice.

Ya ce gwamnatin jihar na ƙoƙarin sauya tsarin noma daga tsoffin hanyoyi zuwa tsarin zamani, ta hanyar samar da taraktoci, injinan noma, ban-ruwa, ingantattun iri, takin zamani da ƙara yawan malaman gona.

Gwamnan ya bayyana cewa an ɗauki malaman gona biyu daga kowace ƙaramar hukuma cikin ƙananan hukumomi 34 na jihar, tare da ba su babura da injinan feshi. Haka kuma, ana horas da mutum biyu daga kowace gundumar zaɓe cikin gundumomi 361 kan ingantattun hanyoyin noma da samar da iri masu inganci.

A wani mataki na bunƙasa noman rani, Gwamna Radda ya ce gwamnati na shirin gina rijiyoyin burtsatse guda 3,000, tare da farfaɗo da noman auduga a yankin Funtua da ƙarfafa noman zogale, ridi, waken soya, dawa da zobo.

Ya kuma bayyana shirin kafa cibiyoyin sarrafa amfanin gona da kuma gina katafaren wurin sarrafa nama na zamani a Katsina, domin ƙara darajar amfanin gona da dabbobi, samar da ayyukan yi da kuma ƙara samun kuɗaɗen shiga ga manoma da masu kiwo.

Gwamnan ya tabbatar wa manoma cewa gwamnati za ta ci gaba da ɗaukar matakan magance matsalolin da ke fuskantar noman kankana, shinkafa, dankalin turawa mai ɗauke da sinadarin Vitamin A, da kuma kiwo.

A nasa jawabin, Shugaban AFAN na Jihar Katsina, Hon. Ya’u Umar Gwajo-Gwajo, ya yaba wa gwamnatin jihar bisa matakan da ta ɗauka wajen inganta harkokin noma, musamman ƙara damar manoma samun filayen noma da kuma rarraba takin zamani cikin lokaci.

Wakilan manoman sun kuma nemi ƙarin saka hannun jari wajen sarrafa amfanin gona, samar da wuraren busar da amfanin gona, magance cututtukan amfanin gona da kuma ƙara samar da filayen noma.

Haka kuma, wakiliyar mata masu kiwon dabbobi ta yaba da shirin rabon awaki da gwamnatin jihar ta aiwatar, tare da yin kira da a faɗaɗa shirin domin ƙarin mata su samu damar cin gajiyarsa.

Dr. Mustapha Inuwa Ya Yi Godiya Ga Magoya Bayansa Bayan Sauya Sheƙa Daga Jam'iyyar ADC Zuwa APC a Katsina Jagoran siyasa...
11/08/2026

Dr. Mustapha Inuwa Ya Yi Godiya Ga Magoya Bayansa Bayan Sauya Sheƙa Daga Jam'iyyar ADC Zuwa APC a Katsina

Jagoran siyasa, Dr. Mustapha Muhammad Inuwa, ya mika sakon godiya ga dubban magoya bayansa da s**a halarci babban taron sauya sheƙa daga jam’iyyar ADC zuwa APC, wanda aka gudanar a ranar Lahadi, 9 ga Agusta, 2026, a Jihar Katsina.

A cikin saƙon da Comrade Kabir Shehu Yandaki ya sanya wa hannu a madadin Dr. Mustapha Inuwa, ya yabawa dubban magoya bayan da s**a fito daga ƙananan hukumomi 34 na jihar Katsina, yana mai cewa fitowarsu ta nuna aminci, goyon baya da sadaukarwa ga tafiyar siyasar jagoran.

Dr. Inuwa ya kuma gode wa waɗanda ba su samu halartar taron ba saboda wasu dalilai, amma s**a ci gaba da nuna goyon baya ta hanyar addu’o’i, saƙonnin fatan alheri da kuma kafafen sada zumunta.

Haka kuma, ya yaba wa jami’an tsaro, ciki har da ’yan sanda, Civil Defence da sauran jami’an tsaro na farin kaya, bisa yadda s**a gudanar da ayyukansu wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya a lokacin taron.

Jagoran ya kuma mika godiyarsa ga ’yan jarida da kafafen yaɗa labarai na rediyo, talabijin, jaridu da kafafen sada zumunta, bisa rawar da s**a taka wajen isar da rahoton taron ga jama’a a cikin jihar Katsina da sauran sassan ƙasa.

Bugu da ƙari, Dr. Inuwa ya gode wa abokai da magoya baya da s**a zo daga jihohin makwabta da na nesa domin nuna goyon baya da kauna a lokacin taron.

A cewarsa, taron sauya sheƙar ba wai kawai sauyin jam’iyya ba ne, illa wata alama ce ta neman haɗin kai, mafita da ci gaban al’umma, tare da kare muradun talakawa.

Ya bayyana komawar zuwa jam’iyyar APC a matsayin wata babbar dama ta haɗa ƙarfi da sauran masu ruwa da tsaki wajen samar da mafita da gina makomar Jihar Katsina da Najeriya baki ɗaya.

Haka kuma Dr. Mustapha Inuwa yayi kira ga magoya bayansa da su yi aiki tukuru lungu da sako a fadin jihar domin samun Nasarar Jam'iyyar Apc a zaben 2027.

A karshe Dr. Mustapha Inuwa yayi addu'ar neman zaman lafiya ga jihar Katsina da Najeriya baki ɗaya.

Gwamna Radda Ya Halarci Sallar Jana’izar Marigayi Alhaji Abu Danmalam KarofiGwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Rad...
11/08/2026

Gwamna Radda Ya Halarci Sallar Jana’izar Marigayi Alhaji Abu Danmalam Karofi

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya halarci sallar jana’izar marigayi Alhaji Abu Danmalam Karofi a garin Katsina.

Gwamna Radda ya roƙi Allah SWT Ya gafarta wa marigayin kura-kuransa.

10/08/2026

Babu ruwan Tinubu idan kun ga ba'ayi maku daidai ba mu ne domin mune aka ba mu baku, muka hana ku –Inji Hon. Ibrahim Masari

Me za kuce?

10/08/2026

“Duk wanda yace wahala ake sha a mulkin Tinubu karya yake - Inji Sheikh Dr. Abu Ammar shugaban Hukumar Hisba ta Katsina.

Sai dai kalaman Sheikh Abu Ammar sun jawo cece-kuce a Kafafen sadarwar zamani.

Me za kuce?

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN:Allah Ya yima tsohon mai baiwa Gwamnan Katsina shawara kan ayyukan ƙananan hukumomi d...
10/08/2026

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN:
Allah Ya yima tsohon mai baiwa Gwamnan Katsina shawara kan ayyukan ƙananan hukumomi da masarautu Alhaji ABU DAN-MALAN KAROFI (ADK) (Raya Karkaran Katsina) rasuwa.

Katsina Reporters ta samu cewa, za ayi jana'izarsa da karfe 1:30pm a masallacin Rafukka a garin Katsina.

Address

No. 12, Ramadan Plaza Ƙwaɗo Ring Road Katsina
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share