Katsina Reporters

Katsina Reporters Shafin Katsina Reporters jarida ce da ke kokarin kawo maku ingantattun labarai na gaskiya ciki da wajen Katsina.
(2)

20/09/2025

Kalli yadda shugaban 'yan bindigā na karamar hukumar Faskari Isya Kwashen garwa ya koka inda ya zargi Sojoji da kai masu hari bayan kulla yarjejeniyar zaman lafiya.

Jigo na jam'iyyar ADC a jihar Katsina Hon. Musa Ɗan Sadau, ya gana da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Alhaji Atiku Abuba...
20/09/2025

Jigo na jam'iyyar ADC a jihar Katsina Hon. Musa Ɗan Sadau, ya gana da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Alhaji Atiku Abubakar, a birnin Abuja.

Ana dai ganin ziyarar nada alaƙa da zaben 2027 kan yunkurin kafa sabuwar jam'iyyar haɗaka a Najeriya.

Gwamna Radda da iyalan Buhari sun tarbi shugaba Tinubu a Kaduna Shugaban kasar Najeriya Asiwaju Bola Tinubu ya ziyarci i...
19/09/2025

Gwamna Radda da iyalan Buhari sun tarbi shugaba Tinubu a Kaduna

Shugaban kasar Najeriya Asiwaju Bola Tinubu ya ziyarci iyalan tsohon shugaban ƙasar Najeriya Marigayi Muhammadu Buhari a garin Kaduna.

Tinubu ya samu tarba daga Gwamna Radda da Aisha Buhari da sauran zuri'arsa.

Innalillahi Wa'inna Ilaihi Raji'un.Allah Ya yiwa Tsohon shugaban ƙaramar hukumar Funtua Hon. Bishir Idris Nadabo wanda a...
19/09/2025

Innalillahi Wa'inna Ilaihi Raji'un.

Allah Ya yiwa Tsohon shugaban ƙaramar hukumar Funtua Hon. Bishir Idris Nadabo wanda akafi sani da Fiya-Fiya rasuwa, bayan fama da jinya a wata asibitin kasar waje.

Marigayin Hon. Bishir Idris Nadabo, ya taɓa zama dan majalissar Tarayya na Funtua a shekarun baya.

Allah Ya gafarta masa.

Da Ɗumi-Ɗumi:- Kāsurgumin Ɗan bìndigā Isya Kwashen garwa ya sako mutane 40 Maza da Mata ƴan garin Faskari da ya yi garku...
19/09/2025

Da Ɗumi-Ɗumi:-

Kāsurgumin Ɗan bìndigā Isya Kwashen garwa ya sako mutane 40 Maza da Mata ƴan garin Faskari da ya yi garkuwa da su, sak**akon sulhu a Katsina

Hakan na zuwa ne bayan zaman sasancin da al'ummar garin Faskari s**a yi barayin dajin a Katsina.

'Ƴar Asalin jihar Katsina Haj. Maryam Idris Bagiwa ta zama wakiliyar Najeriya a Kungiyar kasashe masu arzikin Man fetur ...
19/09/2025

'Ƴar Asalin jihar Katsina Haj. Maryam Idris Bagiwa ta zama wakiliyar Najeriya a Kungiyar kasashe masu arzikin Man fetur na Duniya (OPEC)

Kafin nada Haj. Maryam wannan muƙami ita ce Manajan daraktan kasuwancin kamfanin.

Wane fatan alheri za kuyi mata?

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda PhD, ya halarci ɗaurin auren Ɗan gidan Sen. Abdulaziz Yari, a masallacin S...
19/09/2025

Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda PhD, ya halarci ɗaurin auren Ɗan gidan Sen. Abdulaziz Yari, a masallacin Sultan Bello da ke garin Kaduna.

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Allah Ya yiwa babban Malamin addinin musulunci a Katsina Sheikh Sani Kerau rasuwa ba...
19/09/2025

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN:
Allah Ya yiwa babban Malamin addinin musulunci a Katsina Sheikh Sani Kerau rasuwa bayan fama da jinyar rashin lafiya.

19/09/2025

Yadda tawagar shugaba ƙasar Najeriya Asiwaju Bola Tinubu ta isa jihar Kaduna yau Juma'a 19 ga watan Sep. 2025.

🎥 -Al-mansoor Gusau.

Da Ɗumi-Ɗumi:- DWI Ta yi Allah-wadai da Zarge-zarge mara sa Tushe Na Abubakar Malami Kan ’Yan Majalisar Jihar KebbiKungi...
19/09/2025

Da Ɗumi-Ɗumi:- DWI Ta yi Allah-wadai da Zarge-zarge mara sa Tushe Na Abubakar Malami Kan ’Yan Majalisar Jihar Kebbi

Kungiyar Democracy Watch Initiative (DWI) ta bayyana takaici da ƙin amincewa da ƙorafin da tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami (SAN), ya shigar a kan ’yan majalisar jihar Kebbi da ke kira da a k**a shi tare da gurfanar da shi gaban doka.

A cewar kungiyar, zarge-zargen Malami cewa Gwamna Nasir Idris da shugabannin jam’iyyar APC suna shirin shigo da ’yan daba da mak**ai cikin jihar, ba su da tushe kuma manufarsu kawai ita ce tada hankalin jama’a da kawo fitina.

Kungiyar ta kuma yi nuni da cewa Malami da kansa ana zarginsa da shigo da ’yan daba daga jihohin makwabta, abin da ya haddasa rikici a Birnin Kebbi da kai hari ga ofishin APC na jihar. Wannan, a cewar DWI, ya nuna cewa maimakon ya zama mutum mai kare doka da adalci, Malami ya zamo wanda ke yada fitina da kawo rikici.

DWI ta yi kira da gaggawa ga hukumomin tsaro da Majalisar Ɗinkin Tarayya da su k**a Malami tare da gurfanar da shi domin kare zaman lafiya da mutuncin dimokuraɗiyya.

Kungiyar ta kammala da tabbatar da goyon bayanta ga ’yan majalisar Kebbi da al’ummar jihar wajen neman adalci da tabbatar da siyasa mai lumana da gaskiya.

19/09/2025

Kalli yadda Rarara ya waƙe NSA Malam Nuhu Ribadu. 🔥

Ɗa Ɗumi-Ɗumi:- Atiku ya dauki nauyin karatun daliba ƴar Najeriya da tazo na 1 a gasar Turanci ta duniya Tsohon mataimaki...
19/09/2025

Ɗa Ɗumi-Ɗumi:- Atiku ya dauki nauyin karatun daliba ƴar Najeriya da tazo na 1 a gasar Turanci ta duniya

Tsohon mataimakin shugaban ƙasar Najeriya Alhaji Atiku Abubakar, ya gana da Nafisa Abdullahi dalibar da ta zo na ɗaya a gasar Turanci ta duniya da aka yi a kasar Burtaniya.

Atiku ya taya ɗalibar Nafisa Abdullahi, da sauran wasu 'yan Najeriya biyu da s**a yi zarra murna a lokacin ganawarsu a Abuja.

📸 -Atiku Abubakar

Address

No. 12, Ramadan Plaza Ƙwaɗo Ring Road Katsina
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share