Katsina Reporters

Katsina Reporters Shafin Katsina Reporters jarida ce da ke kokarin kawo maku ingantattun labarai na gaskiya ciki da wajen Katsina.
(1)

Da Ɗumi-Ɗumi:- Gwamnatin jihar Katsina za ta bai wa masu fama da zazzabin Typhoid kulawar lafiya kyauta.Me za ku ce?
28/07/2025

Da Ɗumi-Ɗumi:- Gwamnatin jihar Katsina za ta bai wa masu fama da zazzabin Typhoid kulawar lafiya kyauta.

Me za ku ce?

An samu mummunan hatsari tsakanin wata mota kirar Honda da Babur akan hanyar Daura zuwa Katsina Wata mota kirar Honda ta...
28/07/2025

An samu mummunan hatsari tsakanin wata mota kirar Honda da Babur akan hanyar Daura zuwa Katsina

Wata mota kirar Honda ta kaɗe wani Mai babur, sannan motar ta kwace ta bugi katangar kwalejin. Yanzu haka dai suna asibiti suna karɓar magani.

Hadarin ya faru a dai-dai bakin kofar shiga Federal Polytechnic Daura

📸 -Legend Fm.

28/07/2025

Yadda Gwamna Dikko Radda ya magantu kan matsalar tsaron jihar Katsina.

Da Ɗumi-Ɗumi:- Babu bukatar kirkiro sabbin jahohi a Najeriya - Kwamarad Bishir DaudaBabban sakataren kungiyar Muryar Tal...
28/07/2025

Da Ɗumi-Ɗumi:- Babu bukatar kirkiro sabbin jahohi a Najeriya - Kwamarad Bishir Dauda

Babban sakataren kungiyar Muryar Talaka na Najeriya kuma matashin dan gwagwarmaya dan asalin jihar Katsina Kwamared Bishir Dauda, ya bukaci gwamnatin Najeriya ta yi watsi da kudirin kirkirar sabbin jahohi a Najeriya.

Kwamarad Bishir Dauda ya fadi hakan, ya yin da yake bada gudummawarsa a wajen taron jin ra'ayin al'umma kan sauya fasalin kundin tsarin mulkin Najeriya.

A cewar, Kwamarad Dauda Najeriya ba ta bukatar sabbin jahohi, abinda tafi bukatar shi ne tsaro da zaman lafiya.

Ya kuma bukaci gwamnatin kasar ta maida hankali wajen kirkirar 'yan sandan jahohi, Inda ya ce hakan zai taimaka ma jahohi wajen magance tsaro da rashin aikin yi.

Tunda farko, Kwamarad Bishir ya nuna gamsuwarsa kan tabbatar da dokar bai wa kananan hukumomi 'yancin cin gashin kan su.

Taron ya haɗa jahohin Arewa maso yamma wanda aka gudanar a jihar Kano.

Sanata Sadiq 'Yar'adua, ya fice daga jam'iyyar APC ya koma jam'iyyar hadaka ta ADC.
28/07/2025

Sanata Sadiq 'Yar'adua, ya fice daga jam'iyyar APC ya koma jam'iyyar hadaka ta ADC.

Uwargidan Tsohon Shugaban Kasar Najeriya A’isha Muhammad Buhari ta koma gidan Buhari na jihar Kaduna domin ci gaba da ka...
27/07/2025

Uwargidan Tsohon Shugaban Kasar Najeriya A’isha Muhammad Buhari ta koma gidan Buhari na jihar Kaduna domin ci gaba da karbar gaisuwa.

Da Ɗumi-Ɗumi:- Gwamnatin Dikko Radda ta samar da tsaro ga al'ummar jihar Katsina fiye da baya - Inji Kwamishinan tsaro n...
27/07/2025

Da Ɗumi-Ɗumi:- Gwamnatin Dikko Radda ta samar da tsaro ga al'ummar jihar Katsina fiye da baya - Inji Kwamishinan tsaro na jihar

Menene ra'ayin ku?

Gidauniyar “Guga Global Foundation” ta raba tallafin kayan Islamiyya ga daliban makarantar ta “Al-khana'a Tahfizul Qur'a...
27/07/2025

Gidauniyar “Guga Global Foundation” ta raba tallafin kayan Islamiyya ga daliban makarantar ta “Al-khana'a Tahfizul Qur'an a Katsina

Gidauniyar taimakon Al'umma ta Guga Gloabal Foundation ta shiyar katsina ta bayar da tallafin kayan makaranta ( School Uniform) ga Makarantar Koyon addini wato Islamiyya ta Al-khana'a Tahfizul Qur'an dake Unguwar Ambassador bayan makarantar National Open University Katsina.

A ranar Asabar 26/07/2025 ne wannan Gidauniya mai suna a sama ta gabatar da bayar da tallafin kayan makaranta ( School Uniform ) ga ɗaliban Islamiyyar Al-khana'a Tahfizu Dake Bayan makarantar National Open University Katsina Unguwar Ambassador, wannan yana daga cikin ayyukan taimakon Marayu da masu ƙaramin ƙarfi da Gidauniyar ta saba tsawon Shekaru masu Yawa.

An bayar da wannan tallafi ne ƙarƙashin jagorancin Babban Kodinata na Shiyyar Katsina Malam Muttaqah Abdullahi tare da sauran masu taimaka masa.

Ita dai wannan Gidauniya ta Guga Gloabal Foundation Dai Sanin kowa ne Dr Abduljabbar Surajo Guga ( Sarkin Hanyar Katsina) shine yake ɗaukar nauyinta a duk Faɗin jihar Katsina.

Falalu Lawal Katsina
P. R. O Guga Gloabal Foundation Katsina Zone Office
27/07/2025

Hukumar Hisbah ta jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Sheikh Dr. Abu-Ammar za ta aurar da samari da 'yan mata da zawarawa...
27/07/2025

Hukumar Hisbah ta jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Sheikh Dr. Abu-Ammar za ta aurar da samari da 'yan mata da zawarawa auren gata domin inganta rayuwar samari da 'yan mata a fadin jihar.

Ya ce hakan na daga cikin tsare-tsaren gwamna Malam Dikko Radda don ganin an inganta rayuwar mata.

Da Ɗumi-Ɗumi:- Jam'iyyar ADC a Najeriya ta naɗa Dr. Mustapha Inuwa da Sanata Ahmad Babba Kaita a matsayin waɗanda za su ...
26/07/2025

Da Ɗumi-Ɗumi:-

Jam'iyyar ADC a Najeriya ta naɗa Dr. Mustapha Inuwa da Sanata Ahmad Babba Kaita a matsayin waɗanda za su jagoranci jam'iyyar zuwa babban zaben 2027 a jihar Katsina.

Ya kuke kallon tasirin ADC a Katsina?

Yadda al'ummar garin Kandarawa da Kakumi Guga na Bakori a jihar Katsina s**a yi zanga-zangar lumana kan matsalar tsaron ...
26/07/2025

Yadda al'ummar garin Kandarawa da Kakumi Guga na Bakori a jihar Katsina s**a yi zanga-zangar lumana kan matsalar tsaron da ya addabi yankin.

Masu zanga-zangar sun rufe hanyar shiga Bakori daga Funtua wanda hakan ya shafi matafiya da yawa.

Da Ɗumi-Ɗumi:- Gwamnatin jihar Katsina ta goyi bayan kirkirar jihohi 2 Karadua da Bayajidda daga jihar Katsina a taron j...
26/07/2025

Da Ɗumi-Ɗumi:- Gwamnatin jihar Katsina ta goyi bayan kirkirar jihohi 2 Karadua da Bayajidda daga jihar Katsina a taron jin ra'ayin al'umma kan sauya fasalin kundin mulkin Najeriya

Menene ra'ayin ku?

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share