Katsina Reporters

Katsina Reporters Shafin Katsina Reporters jarida ce da ke kokarin kawo maku ingantattun labarai na gaskiya ciki da wajen jihar Katsina.Call for more Inquiry TEL: 09038333537

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, ya garzaya gidan Sen. Rabi'u Musa Kwankwaso domin tattauna batutuwan da ...
17/04/2026

Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, ya garzaya gidan Sen. Rabi'u Musa Kwankwaso domin tattauna batutuwan da s**a shafi kasa da siyasa.

Ya kuke kallon wannan ziyarar?

Shugaba Tinubu ya sanya hannu kan kasafin kuɗi na shekarar 2026 wanda ya kai kimanin Naira Tiriliyan 68.32.
17/04/2026

Shugaba Tinubu ya sanya hannu kan kasafin kuɗi na shekarar 2026 wanda ya kai kimanin Naira Tiriliyan 68.32.

Yanzu Ba Lokacin Alkawari Bane, Lokaci Ne Na Nuna Ayyuka - Inji Farfesa Isa Ali Pantami Tsohon ministan sadarwa na Najer...
17/04/2026

Yanzu Ba Lokacin Alkawari Bane, Lokaci Ne Na Nuna Ayyuka - Inji Farfesa Isa Ali Pantami

Tsohon ministan sadarwa na Najeriya Professor Isa Ali Pantami ya bayyana cewa yanzu ba lokacin alkawari bane, na cewa zanyi kaza da kaza, a'a lokaci ne na nuna miye nayi muku a lokacin da na samu dama.

Sheikh Isa Pantami yana daga cikin masu neman takarar Gwamna a jihar Gombe inda ya ce ku tambayi duk wanda yazo yace zai yi takara ya kawo muku abubuwan cigaba da yayi muku a lokacin daya samu dama.

Pantami ya ƙara da cewa ayyukansa ne zasu yi magana a madadinsa, inda yace ya aiwatar da ayyukan cigaba sama da guda 241, tare da samar da ayyukan yi ga ‘yan asalin Jihar Gombe sama da mutum 700 a gwamnatin tarayya.

Ya kuma bukaci al’umma da su tambayi sauran ‘yan takara, sannan su yi hukunci bisa la’akari da abin da kowanne ya aikata.

Kungiyar “Arewa Media Writers” Ta Gargadi Ƴan Siyasa Kan Amfani Da Matsalar Tsaro Domin Neman Kuri’unsu A Zaɓen 2027…Ƙun...
16/04/2026

Kungiyar “Arewa Media Writers” Ta Gargadi Ƴan Siyasa Kan Amfani Da Matsalar Tsaro Domin Neman Kuri’unsu A Zaɓen 2027

…Ƙungiyar ta ce amfani da matsalar tsaro wajen neman kuri’u zai zama tarihi a yankin Arewacin Najeriya.

Daga Ƙungiyar “Arewa Media Writers”

Ƙungiyar Arewa Media Writers ƙarƙashin jagorancin Comr Haidar H Hashim Kano, ta bayyana matuƙar damuwa kan yiwuwar sake amfani da matsalar tsaro da ake fama da ita a yankin Arewa a matsayin wata hanya ta yaudarar al’umma domin neman kuri’u a babban zaɓen shekarar 2027.

Ƙungiyar ta ce a lokutan zaɓe da dama da s**a gabata, an sha amfani da batun tsaro wajen ɗaukar alkawurran da ba'a iya cika su ba da zaran sunci zabe sai su manta da alkawuran da s**a yi kafin zaɓe, duk da cewa al’umma na ci gaba da fuskantar hare-hare, sace-sacen mutane da kuma sauran matsalolin tsaro.

A cewar ƙungiyar, wannan dabi’a ta amfani da matsalolin jama’a wajen cimma muradun siyasa ba rashin adalci ba ne kawai, har ma yana jefa rayuwar al’umma cikin haɗari, musamman ganin cewa tsaro lamari ne da ya shafi rayuwa da mutuwa.

Ƙungiyar ta jaddada cewa lokaci ya yi da al’ummar Arewa za su ƙara wayar da kai tare da yin nazari mai zurfi kan manufofi da sahihancin masu neman mulki.

Haka kuma, ƙungiyar ta yi kira ga gwamnati da masu ruwa da tsaki da su ɗauki matakai da s**a dace wajen magance matsalar tsaro, tare da gujewa yin alkawurran da ba su da tushe.

A ƙarshe, "Arewa Media Writers" ta buƙaci al’umma da su kasance masu lura da faɗakarwa, su kuma yi amfani da ƙarfinsu na kuri’a wajen zaɓar shugabanni masu nagarta, domin kawo ƙarshen amfani da matsalolin su a matsayin hanyar samun mulki.

✍️
Comr. Muhammad Kwairi Waziri
National Editor I, Arewa Media Writers

Yadda Gwamna Radda ke ci gaba da karbar ta'aziyyar rasuwar Uwargidan shugaban ma'aikata na fadar gwamnatin jihar Katsina...
16/04/2026

Yadda Gwamna Radda ke ci gaba da karbar ta'aziyyar rasuwar Uwargidan shugaban ma'aikata na fadar gwamnatin jihar Katsina Haj. Maijidda Abdulkadir Nasir

Yayinda Arewa Muke Ta Fama Da Matsalar Rashin Tsaro: Su Kuwa Suna Cigaba Da Gina Yankin Su..Daga Muhammad Aminu Kabir Ar...
16/04/2026

Yayinda Arewa Muke Ta Fama Da Matsalar Rashin Tsaro: Su Kuwa Suna Cigaba Da Gina Yankin Su..

Daga Muhammad Aminu Kabir

Arewa an bar mu da yunwa rashin tsoro ɗumbin mabarata da ƙuncin rayuwa, masanaantun mu mafi yawa sun zama kufai.

A yau Gwamnan jihar Lagos Sanwo-Olu ya bayyana cewa sun karɓi sabbin jiragen ƙasa 24-car train don ƙarfafa layin dogo mai suna Red Line a Legas.

Gwamnatn yace wannan zai taimaka wajen ƙara yawan fasinjoji, rage tsawon jira da sauƙaƙa zirga-zirgar yau da kullum ga mazauna jihar.

Ya ce gwamnati na cigaba da mayar da hankali wajen gina tsarin sufuri mai inganci, dogaro da kuma sauƙin amfani ga kowa.

Mu anan Arewa muna ta fama da hanyoyin mu na cikin gida bamu ma fara tunanin jirgin ƙasa ba, jihar Kano ma da aka fara maganar har yanzu bata ga hasken rana ba.

Tsohon Gwamnan Jihar Katsina Kuma shugaban Hukumar gudanarwar hukumar kula da sufurin Jiragen ruwan Najeriya [NSC] Barr....
16/04/2026

Tsohon Gwamnan Jihar Katsina Kuma shugaban Hukumar gudanarwar hukumar kula da sufurin Jiragen ruwan Najeriya [NSC] Barr. Ibrahim Shehu Shema, ya jagoranci Membobin Hukumar domin kai ziyarar aiki Tashar Jiragen Ruwan Legas.

Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Jihar Katsina ta kafa Kotun Tafi da gidan ka domin hukunta kauraye da masu kwacen waya a fadin ji...
16/04/2026

Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Jihar Katsina ta kafa Kotun Tafi da gidan ka domin hukunta kauraye da masu kwacen waya a fadin jihar

Ya kuke kallon matakin?

An fara rade-radin APC za ta tsayar da Sheikh Professor Isa Ali Pantami takarar Gwamnan Gombe ba tare da zaɓen fidda gwa...
16/04/2026

An fara rade-radin APC za ta tsayar da Sheikh Professor Isa Ali Pantami takarar Gwamnan Gombe ba tare da zaɓen fidda gwani ba

Rahotanni sun bayyana cewa an cimma wannan matsaya ne a wani zaman tattaunawa da Gwamnan jihar, Alhaji Inuwa Yahaya, ya shirya a daren ranar Litinin 13, ga wata 2026. tare da masu takarar gwamna na jam’iyyar APC a jihar.

Kamar yadda Katsina Reporters ta samu, an gudanar da zaman ne domin samar da haɗin kai da kuma kauce wa rikice-rikicen cikin gida kafin zaɓe.

Sai dai har yanzu babu wata sanarwa a hukumance daga jam’iyyar ko ɓangarorin da abin ya shafa da ke tabbatar da wannan mataki.

Karin bayani na nan tafe!

An Roki Gwamna Radda Ya Tabbatar Da Dokar Da Za Ta Inganta Rayuwar Mutane Masu Buƙata Ta Musanman A Katsina Ƙungiyar Mur...
15/04/2026

An Roki Gwamna Radda Ya Tabbatar Da Dokar Da Za Ta Inganta Rayuwar Mutane Masu Buƙata Ta Musanman A Katsina

Ƙungiyar Muryar Matasa Initiative ta yi kira ga Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya tabbatar da cikakken aiwatar da dokar mutane masu bukata ta musamman ta shekarar 2023 Jihar.

An bayyana wannan kira ne a yayin wani taron manema labarai da shuwagabannin ƙungiyar “Muryar Matasa s**a shirya a sakatariyar NUJ da ke Katsina.

Sanarwar taron, wadda Sakatare Janar na ƙungiyar, Nasir Dauda Yansiliyu ya karanta, ta nuna cewa duk da cewa an rattaba hannu kan dokar a gwamnatin da ta gabata, har yanzu ba'a fara aiwatar da ita ba, Kuma wannan ne ya sa s**a buƙaci gwamnatin jihar ta ɗauki mataki cikin gaggawa.

A cewarsa, idan aka aiwatar da dokar, za ta samar da damar kafa Hukuma ko Sashen kula da masu bukata ta musamman a Jihar Katsina.

Haka kuma, aiwatar da dokar zai tabbatar da kare haƙƙoƙin masu bukata ta musamman da inganta rayuwarsu da samar da daidaito da haɗin kai, tare da ba su damar samun ilimi kyauta a jihar.

A cewar Nasir Dauda Yansiliyu, fiye da Jihohi 20 sun riga sun fara aiwatar da irin wannan doka, yana mai tunatar da cewa an fara aiwatar da ita a matakin ƙasa a zamanin marigayi shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari.

Sakataren kungiyar ya ƙara da cewa, masu bukata ta musamman a Jihar Katsina sun kai sama da mutum 800,000, don haka aiwatar da dokar zai sa su ji suna da muhimmanci a cikin al’umma.

Ya kuma yi amfani da damar wajen yaba wa Gwamna Dikko Umaru Radda, bisa irin tallafin da yake bai wa masu bukata ta musamman ta hannun masu taimaka masa na musamman.

A ƙarshe, yayin da ya tabbatar da cikakken goyon bayansu ga manufofi da shirye-shiryen gwamnati, Nasir Dauda Yansiliyu ya nuna kyakkyawan fata cewa gwamnan zai duba bukatarsu da idon basira.

15/04/2026

Duk abinda al'umma ke bukata na more rayuwa da samar da ababen ci gaba a Katsina Dr. Haruna Maiwada yayi hada ɗoriya - inji Usman Rafukka, Matashi a Jam'iyyar APC

Ya kuma bayyana irin gudumuwar da Dr. Haruna Maiwada Ke bayarwa don ci gaban al'ummar jihar Katsina.

15/04/2026

Kai tsaye: Taron manema labarai wanda kungiyar “Muryar Matasa Initiative” ta shirya a Katsina

Daga Ina kuke kallon mu?

Address

No. 12, Ramadan Plaza Ƙwaɗo Ring Road Katsina
Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Reporters posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share