The Source News Hausa

The Source News Hausa Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from The Source News Hausa, Media/News Company, Rafin Dadi Street, Katsina.

Ku Zabi Dikko Radda Cikin Ikon Allah Ba Zamu Yi Nadama Ba - Sakon Jikamshi Ga KatsinawaKwararrarren Masanin Tattalin Arz...
07/08/2022

Ku Zabi Dikko Radda Cikin Ikon Allah Ba Zamu Yi Nadama Ba - Sakon Jikamshi Ga Katsinawa

Kwararrarren Masanin Tattalin Arziki kuma masani akan sha'anin Masana'antun wanda kuma shine Shugaban Hukumar Zuba Hannun Jari Ta Jihar Katsina, Alhaji Ibrahim Tukur Jiƙamshi, ya bayyana cewa al'ummar jihar Katsina ba zasu yi da na sani ba idan s**a ba Dr.Dikko Umar Radda damar zama Gwamnan Jihar.

Alhaji Ibrahim Tukur Jiƙamshi ya bayyana hakan ne jim kaɗan bayan kammala wata ganawa ta musamman da dan takarar gwamnan jihar Katsina a karƙashin jam'iyyar APC, Dakta Dikko Umar Radda a Ofishin yakin neman zaɓensa dake cikin garin Katsina.

Jikamshi ya ja hankalin yan Jihar akan su fito kwansu da kwarkwatarsu su zazzaga wa Dr. Dikko Umar Radda kuri'unsu don ganin ya samu nasarar lashe zaɓen Gwamnan Jihar zabe mai zuwa.

Ya kara tabbatar da cewa ba za su taɓa yin nadama ba, saboda saboda gogewar Radda a fannoni daban-daban da s**a shafi cigaban al'umma da kuma tarin Ilimin Addini da na boko da yake da shi da kuma hangen nesa.

Shugaban Hukumar Kula Da Zuba Hannun Jarin ya kara da cewar, a wannan zaɓe mai karatowa na 2023, al'ummar jihar idan s**a dubi kafatanin yan takarar gwamnan jihar Katsina a jam'iyyu mabanbanta yana da wahalar gaske a samu nagartaccen dan takarar kamar Dr. Dikko Umar Radda.

Al'ummar Najeriya gaba daya sun amfana da irin kyakkyawan shugabancinsa na yadda ya riƙe Hukumar Kula Da Kanana Da Matsakaitan Masana'antun Ta Najeriya da kuma irin sauye-sauye da ya kawo a Hukumar cikin shekara biyar.

Alhaji Ibrahim Tukur Jiƙamshi ya cigaba da cewa jihar Katsina ana buƙatar matashin dattijo irin Dr. Dikko Umar Radda saboda irin baiwa da basira da kokarin ganin ya inganta rayuwar al'umma musamman matasa da kuma Kananan Masana'antun wanda ya ke da gogewa akan fannin.

''Ina da tabbacin zai kawo sauye-sauye masu ma'ana da za su inganta rayuwar al'umma jihar Katsina idan har s**a bashi dama ya zama Gwamnan Jihar''.

Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Ma'aurata A Cikin Birnin Katsina.... Sun Harbe Yan Sintiri Biyu Har LahiraA Daren Ranar ...
07/08/2022

Yan Bindiga Sun Yi Awon Gaba Da Ma'aurata A Cikin Birnin Katsina
.... Sun Harbe Yan Sintiri Biyu Har Lahira

A Daren Ranar Asabar Ƴan Bindiga Sun Kai Hari A Unguwar Shola Dake Bayan Asibitin Koyarwa Ta Gwamnatin Tarayya Da Ke Cikin Garin Katsina Inda S**a Yi Garkuwa Da Mata Da Mijinta.

Kamar Yadda Majiyar Mu Ta Shaida Mana, Matashin Da Aka Yi Garkuwa Da Shi Da Matar Sa Sunan Shi Yusuf Bishir.

Haka zalika yan bindigar sun harbe wasu yan sintiri biyu dake aikin bayar da tsaro a Unguwar inda s**a kashe daya daga cikin su yayin d

Anya Kuwa Dagaske Gyara Suke So, Ko Dai Wata Boyayyar Manufa: Zauren Ƴan APC A GyaraDaga Muhammadu BelloDuk dai Hausawa ...
06/08/2022

Anya Kuwa Dagaske Gyara Suke So, Ko Dai Wata Boyayyar Manufa: Zauren Ƴan APC A Gyara

Daga Muhammadu Bello

Duk dai Hausawa na cewa gyara kayanka bai zama sauke a raba ba, kwatsam aka yi gari a jihar Katsina aka samu wasu tsirarun matasa da s**a kira kansu Zauren APC A Gyara kuma sun kira kansu masu son kawo gyara da kishin Jam'iyyar APC shi ne babban dalilin kafa wannan zaure a jihar Katsina. Amma abun tambaya anan shi ne shin dagaske gyaran suke so? Kuma wadanne hanyoyi s**a biyo na ankarar da gwamnatin jihar Katsina da Jam'iyyar APC ta jihar Katsina ƙarƙashin jagorancin Alhaji Sani Aliyu Daura, wanda s**a yi ko kuwa akwai wata boyayyar Manufa?

Jam'iyyar APC ta jihar Katsina ta kammala zaɓukan Fidda-gwaninta a matakai daban-daban ba tare da nuna banbanci ba, wadda a tarihin siyasar jihar Katsina ba'a taɓa samun haka na baiwa yan takara dama su nemi Jama'a tare da kokarin baiwa kowa damarsa ta dan Jam'iyya. A Zaɓen Fidda-gwani gwamna da aka gudanar gwamna Aminu Bello Masari ya yi kokarin matuka don gani an baiwa kowa damarsa ba tare da nuna Dan Bora da Mowa ba, wanda da yawa Jama'a sun yadda da sahihanci yadda aka gudanar da zaben. Yanzu haka babu wani korafi gaban kotu. Amma kwatsam sai ga Waɗannan matasa sun fito da rana tsaka suna kira a Gyara to gyaran yadda aka gudanar da zaben Fidda-gwani da mafi yawancinsu wadanda suke goyawa ma baya, sun tsaya takara a matakai daban-daban, Allah bai ba su nasara ba, shi ne saboda Allah suke so a zo gyara, don uwayen gidansu ba su samu nasarar ba, ina da tabbaci da ace Iyayen gidansu sun yi nasarar lashe zaɓukan da s**a tsaya da babu daya daga cikinsu zai fito ya ce a Gyara!

Idan muka koma tafiyar da gwamnati, gwamna Aminu Bello Masari yau shekararsa bakwai yana tafiyar da gwamnati a jihar Katsina. Tsakani da Allah cikin Waɗannan shekaru ba su taba fitowa da wani Zauren APC A Gyara sai yanzu da bai wuce saura watanni wa'adin Gwamnatinsa. Anya kuwa dagasken gyara suke so kuwa? Kamar yadda da yawa daga cikinsu sun bayyana cewa tare da su aka sha wahalar aka kafa gwamnatin Gwamna Masari a shekarar 2015, ba su taɓa sunsunar kafa wannan zaure ba, saboda Allah fa al'umma jihar Katsina ku yi mana alkalanci! Amma s**a yi gum da bakunansu.

Maganar shugaban Jam'iyyar APC na jihar Katsina, Alhaji Sani Aliyu JB kuwa duk tsohan dan Jam'iyyar APC ya san irin rawar da ya taka, saboda shi ne Sakatarenta na farko daga likkafarsa ta cigaba ya zama shugabanta a shekarar 2021. Duk wanda ya matsa kusa da shi mutum ne mai amsar gyara da kuma kokarin ganin an tafiyar da Jam'iyyar cikin adalci. Ina da yakinin cikinsu babu wanda ya taɓa kokarin yin mu'amalla da shi ko shigar da wani korafi na kawo gyara ace ya hau teburin na ki ba. Idan za ka yi adalci, farko ka fara kusantarsa kafin ka yanke masa hukunci.

Ni da a fahimta ta ko dai suna da wata boyayyar manufa, wadda nan gaba kadan al'ummar jihar Katsina za su fahimci haka. Yanzu dai babu abinda Gwamnatin Jihar Katsina da Jam'iyyar APC ke bukata, illa hadin kai yayan Jam'iyyar, ga zabe na tahowa na 2023, idan har nasarar Jam'iyyar APC suke so kyau su zo su marawa Jam'iyyar Baya ganin ta lashe zaɓukan, sannan duk wani gyara a zo ayi shi.

El-Rufa'i Ya Saki Jumullar Kudi Naira Miliyan 860 Domin Biyan Hakkokin Ma'aikata Da S**a Ajiye Aiki Da Wadnda S**a RasuG...
05/08/2022

El-Rufa'i Ya Saki Jumullar Kudi Naira Miliyan 860 Domin Biyan Hakkokin Ma'aikata Da S**a Ajiye Aiki Da Wadnda S**a Rasu

Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufa'i, ya amince da sakin jumullar kudi naira miliyan 860 domin biyan hakkokin ma'aikata da s**a ajiye aiki da wadanda s**a rasu a matakin Jiha da Kananan Hukumomi.

Wadanda lamarin ya shafa sun kai su 339 da s**a ajiye aiki da wadanda s**a rasa rayukan su kafin lokacin ajiye aiki.

A sabili da haka ne Hukumar Kula Da Yan Fansho Ta Jihar Kaduna ke kira ga wadanda lamarin ya shafa da iyalan wadanda s**a rasu a cikin ma'aikatan akan su ziyarci Hedikwatar su domin tantance su.

Ba Zan Rintsa Ba Har Sai Na Tabbatar Da An Gudanar Sahihin Zabe A 2023 - Cewar Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Ta Bakin M...
05/08/2022

Ba Zan Rintsa Ba Har Sai Na Tabbatar Da An Gudanar Sahihin Zabe A 2023 - Cewar Shugaban Kasa Muhammadu Buhari Ta Bakin Monguno.

Matsalar Tsaro Bata Taba Harkar Noma Ba Yadda Ake Zuzuta Ta - Cewar Ministan NomaGwamnatin Tarayya ta bayyana cewa matsa...
05/08/2022

Matsalar Tsaro Bata Taba Harkar Noma Ba Yadda Ake Zuzuta Ta - Cewar Ministan Noma

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa matsalar tsaro bata shafi harkar noma sosai ba a Najeriya.

Ministan noma Abubakar Muhammad ne ya bayyan hakan a taron mako-mako da suke gudanarwa a fadar shugaban kasa a babban birnin tarayya.

Inda yace Najeriya itace kasa ta farko da tafi kowace kasa nomar shinka a nahiyar Afrika, sannan kuma itace ta hudu a Duniya bakidaya.

Ya kara da cewa tabbas matsalar tsaro ta shafi harkar noma musamman a arewacin Najeriya, amma ba sosai ba kuma har yanzu ana noma a Najeriya.

Yanzu-Yanzu : Tsohon Sufeto Janar Na Yan Sandan Najeriya Mustapha Bologun Ya Rasu.
04/08/2022

Yanzu-Yanzu : Tsohon Sufeto Janar Na Yan Sandan Najeriya Mustapha Bologun Ya Rasu.

Babu Abinda Ke Cikin Ayyukan Zulum Sai Farfaganda - Inji Muhammed JajariDaga Muhammad Dahiru ShugabaDan takarar gwamna a...
04/08/2022

Babu Abinda Ke Cikin Ayyukan Zulum Sai Farfaganda - Inji Muhammed Jajari

Daga Muhammad Dahiru Shugaba

Dan takarar gwamna a jam’iyyar adawa ta PDP a jihar Borno, Alhaji Mohammed Jajari, ya kalubalanci gwamnatin Zulum da gina manyan makarantu a fadin jihar ba tare da daukar kwararrun malamai da zasu gudanar da aikin koyarwa ba a makarantun.

Jajari ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga magoya bayansa na jam’iyyar PDP a ranar Alhamis a Maiduguri.

Jajari ya tabbatar da cewa, duk da rashin isassun malamai da jihar ta Borno ke fama da shi, gwamnatin Zulum ta fara shirin sallamar wadanda ake da su daga aiki babu gaira babu dalili.

Dan takarar ya bayyana cewa, aikin mayar da yan gudun hijira gidajen su da gwamnatin Zulum ke nunawa duniya yana yi ba haka bane a zahiri duk farfaganda ce ta siyasa ba gaskiya ba ne.

Ya ce yana zargin cewa mafi yawan yan gudun hijirar da s**a rasa gidajen su da aka kwashe daga Maiduguri, har yanzu suna sansanoni a hedikwatar Kananan Hukumomi daban-daban maimakon a mayar da su gidajen su.

Ya kuma zargi Gwamman Zulum da yin amfani da yan kwadago kai tsaye wajen gina hanyoyin da s**a lalace, ana gina wadanda basa dadewa kafin su lalace cikin watanni don kawai gwammna Zulum ya azurta yan uwa da abokan arzikin da yake tare dasu ba dan al'umma ba.

Madogara: Rariya

Kwamarad Aliyu Mamman Dan Ummah Ya Yanki Tikitin Neman Takarar Shugaban Kungiyar Dalibai Yan Asalin Jihar KatsinaDaya da...
04/08/2022

Kwamarad Aliyu Mamman Dan Ummah Ya Yanki Tikitin Neman Takarar Shugaban Kungiyar Dalibai Yan Asalin Jihar Katsina

Daya daga cikin daliban jami'ar Umaru Musa Yar'adua da ke Katsina, Kwamarad Aliyu Mamman Dan Ummah ya yanki tikitin neman takarar kujerar Shugaban Kungiyar Dalibai Ta Kasa yan asalin jihar katsina, ( NAKATSS NATIONAL BODY).

Wakilin Horizon News Hausa wanda ya shaida yankar tikitin ya bayar da rohoton cewar, mai neman takarar Kwamarad Dan Ummah, ya samu rakiyar wasu daga cikin abokan gwagwarmayar shi da magoya bayan shi daga makarantu daban-daban.

Da yake magantawa jim kadan bayan sayen tikitin, mai neman takarar ya bayyana cewar, wannan shine karo na biyu da zai nemi takara a Kungiyar.

Ya bada tabbacin cewa idan har ya'yan kungiyar s**a bashi dama, zai yi bakin kokarin shi wurin neman hakkin su a duk inda ya kamata.

Ya Zama Wajibi Mu Lashe Zabe Mai Zuwa A Duk Fadin Najeriya - Cewar Shugaban APC Shugaban jam’iyar APC na kasa Abdullahi ...
04/08/2022

Ya Zama Wajibi Mu Lashe Zabe Mai Zuwa A Duk Fadin Najeriya - Cewar Shugaban APC

Shugaban jam’iyar APC na kasa Abdullahi Adamu ya bayyana cewa, ya zama wajibi jam’iyar ta lashe kafatanin zabukan da za’a gudanar a babban zaben shekarar 2023.

Adamu ya ce, wajibi ne APC ta samu gagarumin nasara a zaben shugaban kasa, Yan majalissu, da zabukan gwamnonin jihohi a 2023.

Adamu ya bayyana haka ne a sa'ilinda da yake zantawa da manema labarai a jiya Laraba a babban birnin tarayya Abuja Adamu ya jaddada cewa, Da yuwuwar Jam’iyar APC ba zata lamunci kashi 25 cikin dari kacal ba.

Jam'iyyar APC Ta Sanar Da Gwamna Solomon Lalong A Matsayin Darakta Janar na Kwamitin Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Asi...
04/08/2022

Jam'iyyar APC Ta Sanar Da Gwamna Solomon Lalong A Matsayin Darakta Janar na Kwamitin Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa Asiwaju Bola Tinubu A Fadar Shugaban Kasa a yau .

Atiku Ya Nada Dino Melaye Da Daniel Bwala A Matsayin Masu Magana Da YawunsaDan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP ku...
04/08/2022

Atiku Ya Nada Dino Melaye Da Daniel Bwala A Matsayin Masu Magana Da Yawunsa

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP kuma tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya, Atiku Abubakar ya nada Sanata Dino Melaye da Dokta Daniel Bwala a matsayin masu magana da yawun sa a yakin neman zaben shugaban kasa mai zuwa.

A cewar sanarwar da mai baiwa Atiku shawara kan harkokin yada labarai Paul Ibe ya sanyawa hannu, nadin na biyu ya fara aiki nan take.

Malaye dan siyasa ne kuma dan majalisar dattawa ta 8, wanda ke wakiltar mazabar Kogi ta Yamma. Ya fito daga Ayetoro Gbede da ke karamar hukumar Ijumu a jihar Kogi

Bwala, a daya bangaren, kwararre ne a fannin shari’a, dan siyasa kuma manazarci harkokin jama’a. Ya fito daga jihar Borno.

Address

Rafin Dadi Street
Katsina

Telephone

+17033444156

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when The Source News Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to The Source News Hausa:

Share