Humanity Today

Humanity Today Shafin wayar da kai ne game da rayuwa, ilimi, shugabanci da hakkokin al’umma. Tare muke gina al’umma muna da manufa mai kyau ga kowa
(1)

Muna taimaka wa matasa, iyaye, da shugabanni da dabarun rayuwa, kishin kasa da adalci.

Shin da gaske ne Shugaban Ƙasar Iran ya bada Takardar barin aiki ga Ofishin Jagoran Ƙasar Ayatollah Mojtaba Khamenei?Teh...
31/05/2026

Shin da gaske ne Shugaban Ƙasar Iran ya bada Takardar barin aiki ga Ofishin Jagoran Ƙasar Ayatollah Mojtaba Khamenei?

Tehran, 31 Mayu 2026– A yau, rahotanni masu zafi daga kafofin watsa labarai na adawa kamar Iran International, Fox News, da wasu majiyoyi na ƙasashen waje sun ba da labarin cewa Shugaban Ƙasar Iran Masoud Pezeshkian ya gabatar da takardar murabus (resignation letter) a hukumance ga ofishin Babban Jagora Ayatollah Mojtaba Khamenei. A cewar waɗannan majiyoyi, dalilin shi ne karfin ikon rundunar Sojojin Revolushin Musulmi (IRGC) wanda ya mamaye yanke shawara na gwamnati, inda shugaban ya bayyana cewa ba zai iya ci gaba da gudanar da ayyukansa na shari’a ba a wannan yanayi.

Rahoton ya nuna cewa a cikin takardar, Pezeshkian ya shaida cewa gwamnatin farar hula ta kasance waje daga muhimman shawarwari na ƙasa tun bayan yaƙin da Amurka da Isra’ila, kuma IRGC ta mamaye iko. Wannan rahoto ya bazu cikin sauri a kafofin watsa labarai na duniya.

Sai dai gwamnatin Iran ta karyata waɗannan rahotanni nan take, inda jami’ai s**a ce labarin “ƙage ne kuma an ƙirƙira shi don haifar da rikici da rashin amincewa tsakanin jagoranci.” Har ila yau, ba a samu wani tabbaci na hukuma daga ofishin shugaban ƙasa ko na Babban Jagora ba game da karɓar takardar ko amincewa da ita. Pezeshkian yana ci gaba da bayyana a cikin mahallin ayyukan gwamnati, kuma a kwanakin baya ya yi magana game da shirye-shiryen Iran don tattaunawa ta zaman lafiya.

A ƙarshe: Har yanzu ba a samu tabbacin hukuma cewa shugaban ya yi murabus ba, kuma rahoton na yau har yanzu unconfirmed ne kuma ana musantawa daga bangaren gwamnati. Ana ci gaba da lura da yanayin cikin gida na Iran wanda ke cikin sauri. Ana shawarar bin kafofin watsa labarai na aminci domin sabuntawa.

AN KAMMALA AYYUKAN HAJJI NA WANNAN SHEKARA Ma'aikatar harkokin cikin gida ta  kasar Saudiyya, ta sanar da kammala aikin ...
31/05/2026

AN KAMMALA AYYUKAN HAJJI NA WANNAN SHEKARA

Ma'aikatar harkokin cikin gida ta kasar Saudiyya, ta sanar da kammala aikin Hajji na wannan shekara ta 2026, tare da fara shirye-shiryen aikin Hajji shekara mai zuwa. Kamar yadda kamfani Dillancin labarai na Saudiyya (SPA) ya ruwaito.

Bisa ga alkaluman da Hukumar Kididdiga ta Ƙasar Saudiyya ta fitar, sama da alhazai milyan daya da dubu Dari bakwai ( 1.7) ne s**a gudanar da aikin Hajji a bana. Daga cikinsu akwai alhazai 1,546,655 daga ƙasashen waje, yayin da 'yan ƙasa da mazauna Saudiyya 160,646 s**a yi Hajji daga cikin gida.
Ma’aikatar ta bayyana cewa kammala wannan zangon Hajji na bana, yana nufin fara shirye-shiryen na shekarar gaba. Saboda haka, ana fara nazari da inganta tsare-tsaren tsaro da gudanarwa nan take daga Mina bayan an kammala ibadun Hajji.
Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida, masarautun yankuna, hukumomin tsaro da sauran abokan haɗin gwiwa sun yi aiki tare a duk lokacin Hajji domin kare lafiyar alhazai da kuma sauƙaƙa musu gudanar da ibadunsu cikin kwanciyar hankali a wurare masu tsarki.
Haka kuma, tsare-tsaren tsaro da kula da zirga-zirga sun taimaka wajen sauƙaƙa zirga-zirgar alhazai tsakanin Mina, Arafat da Muzdalifah, yayin da hukumomin tashoshin jiragen sama, kan iyakokin ƙasa da na ruwa s**a sauƙaƙa shigowar alhazai tare da tarbar su yadda ya kamata tun farkon zuwansu Saudiyya.

'Yan bindiga sun kashe kansila da daraktan karamar hukuma a Zamfara kan zargin alaka da LakurawaRahotanni daga jihar Zam...
30/05/2026

'Yan bindiga sun kashe kansila da daraktan karamar hukuma a Zamfara kan zargin alaka da Lakurawa

Rahotanni daga jihar Zamfara sun nuna cewa, Wasu 'yan bindiga sun kashe kansilan da ke wakiltar mazabar Jangebe, Habibu Jangebe, da kuma Daraktan Tsare-tsare na Karamar Hukumar Talata Mafara, Alhaji Jamilu Sani, a Jihar, bisa zargin suna da alaka da kungiyar ' yan ta'addan Lakurawa.
Majiyar mu ta bayyana cewa, An zargi jami'an biyu da cewa suna bai wa kungiyar Lakurawa kudi a kowane wata. Wanda a sakamakon hakan ya haifar da 'yan bindiga s**a kai musu hari wanda ya yi sanadin mutuwarsu.
Wata majiya ta bayyana cewa karamar hukumar na amfani da jami'an biyu wajen isar da kudi ga Lakurawa a matsayin wata yarjejeniya da ake zargin an kulla domin hana kai hare-hare kan al'ummomin yankin.
Majiyar ta kara da cewa ana zargin Karamar Hukumar Talata Mafara na bai wa Lakurawa wasu kudade a kowane wata, amma ba ta bada irin wannan kudaden ga 'yan bindigar da ke yankin.
Saboda haka, 'yan bindigar s**a yi garkuwa da jami'an biyu kimanin kwanaki 10 da s**a gabata, daga bisani kuma s**a kashe su domin nuna fushinsu.
Majiyar ta kuma yi ikirarin cewa:
"Tun da farko 'yan bindigar sun yi barazanar kashe shugaban karamar hukumar, Yahaya Yari, saboda zargin cewa an ware su daga tallafin da ake bai wa kungiyar Lakurawa."
Rahotanni sun ce an yi garkuwa da mutanen biyu ne a ranar 18 ga Mayu na wannan shekara ta 2026, yayin da suke tafiya daga Jangebe zuwa hedikwatar karamar hukumar domin shirye-shiryen aikin hajjin bana.
Da yake mayar da martani kan lamarin, shugaban karamar hukumar ya bayyana kisan jami'an biyu a matsayin abin takaici da ban tausayi. Sannan ya kuma musanta zargin cewa an kashe su ne saboda karamar hukumar tana fifita Lakurawa.
Ya ce, "wannan zargi ba shi da tushe b***e makama," yana mai jaddada cewa karamar hukumar ba za ta taba yin sulhu ko tattaunawa da 'yan ta'adda ba, ko su wanene.
Shugaban karamar Hukumar Yahaya Yari ya bayyana cewa, kungiyar CJTF daga Jihar Borno ce kawai ke samun tallafi daga karamar hukumar, domin tana taimakawa jami'an tsaro wajen yaki da matsalar 'yan bindiga a yankin.

‘Yan bindigar Igala sun yi mummunan kisan gilla ga jarirai, yara da mata Fulani a gidajensu da ke Jihar Kogi, Najeriya.B...
24/05/2026

‘Yan bindigar Igala sun yi mummunan kisan gilla ga jarirai, yara da mata Fulani a gidajensu da ke Jihar Kogi, Najeriya.

Bisa ga bayanan shaidu da rahotannin kafafen yaɗa labarai, sun ruwaito cewar an yi wani mummunan hari da ya yi sanadin k4she mutane tara (9), ciki har da jarirai, yara da mata, a ranar 21 ga Mayu, 2026, a ƙauyen Iko da ke Ƙaramar Hukumar Ankpa, Jihar Kogi, a yankin Arewa ta Tsakiyar Najeriya.

Rohoton yace mutane biyu sun jikkata kuma suna asibiti, ɗaya daga cikinsu na cikin mawuyacin hali.

An kuma ƙone gidajen Fulani tare da sace shanunsu.

Har yanzu ba a bayyana dalilin wannan hari ba. Amma babu wani dalili da zai taɓa halatta irin wannan dabbancin kisan gillar da aka aikata. Ga sunayen waɗanda aka kashe:

1. Samsiya Alhaji Lawal
2. Asma’u Alhaji Lawal
3. Hauwa Ikaru, matar Alhaji Lawal
4. Usmanu Alhaji Lawal
5. Muhammed Alhaji Lawal
6. Ismail Alhaji Lawal
7. Abdullahi Alhaji Lawal
8. Maude Alhaji Lawal
9. Umar Alhaji Lawal

Gwamnatin Jiha da ta Tarayya dole su ɗauki mataki cikin gaggawa, ƙarfi da bayyane domin kamo waɗanda s**a aikata wannan ta’asa tare da hukunta su bisa doka.

TATTAUNAWA DA WANDA YA CE A GABANSA AKA KASHE DADIYATATambaya: A wane lokaci ne ka haɗu da Dadiyata?Amsa: Bayan da aka m...
11/05/2026

TATTAUNAWA DA WANDA YA CE A GABANSA AKA KASHE DADIYATA

Tambaya: A wane lokaci ne ka haɗu da Dadiyata?

Amsa: Bayan da aka mayar da ni Kaduna ne na fara haɗuwa da Dadiyata. Kafin wannan lokaci ban taɓa jin labarinsa ba, b***e na san tarihinsa. A lokacin da na gan shi, yana cikin wani hali mai matuƙar tausayi. Yunwa da rashin abinci sun galabaita shi ƙwarai, har ya rame sosai.

A wurin ba sa ba kowa isasshen abinci. Ni kaina na shafe watanni biyar a hannunsu, har na koma kamar ƙasusuwa kawai saboda yunwa. Akwai dakuna uku a ofishin: Cell 1, Cell 2 da Cell 3. Ni ina Cell 3 ne, shi kuma yana Cell 2, kuma dukkan dakunan suna kusa da juna.

A cikin cell, ana ƙwace wa mutum mutuncinsa da kimarsa. Ba ka da takalmi, ba ka da tufafi masu kyau, kuma rayuwa tana tafiya cikin ƙunci. Wani da ake kira Presido, wanda shi ne shugaban dakunan, shi ne ya fara ba ni bayanin Dadiyata. Na yi ƙoƙarin ba shi abinci, amma Presido ya gargade ni cewa idan jami’an nan biyu s**a gan ni ina ba shi abinci, zan shiga matsala.

Tambaya: Shin ka taɓa yin magana da shi kai tsaye?

Amsa: Eh, wata rana na yi masa magana a taƙaice, kuma ya gaya mini sunansa. Na kuma tambaye shi inda danginsa suke. Amma washegari wani jami’i mai suna Hussaini ya tambaye ni cewa: “Akwai wani da muke tsare a can, ka yi magana da shi?” Na amsa masa da cewa a’a.

Sai s**a juya wajen Presido s**a tambaye shi: “Kana ganin Musa yana magana da wancan mutumin?” Wato Dadiyata kenan. Presido ya ce eh.

A gaskiya, idan mutum yana cikin waɗanda suke kira “special suspect”, babu wani ɗan sanda, har da CROs (Charge Room Officers), da zai yi magana da kai kai tsaye. Idan kana da wata matsala, CROs ɗin za su sanar da jami’in da ya tsare ka ne kawai, shi kuma zai zo ya kula da lamarin.

Tambaya: Mene ne ya faru da Dadiyata daga baya?

Amsa: Da misalin ƙarfe ɗaya na dare ne Hussaini Gimba ya zo shi kaɗai ya fitar da Dadiyata daga cell ɗinsa. Na san jami’an sosai kuma zan iya gane su cikin sauƙi. Tun daga wannan dare ban ƙara ganin Dadiyata ba har sai da aka sake ni daga Kaduna.

A lokacin da nake tsare, sun azabtar da ni, sun wulakanta ni, kuma sun yi mini barazanar kashe ni. Bayan wasu kwanaki da s**a ɗauke Dadiyata, Officer Hussaini Gimba ya gaya mini kai tsaye cewa idan ban ba su haɗin kai ba, za su kashe ni kamar yadda s**a kashe Dadiyata.

Ban ce an kashe shi a gabana ba, amma sun yi mini wannan barazanar kai tsaye, suna danganta hakan da Dadiyata. Wannan magana ta firgita ni sosai saboda ban yi tsammanin zai furta hakan ba. Tun daga lokacin na ƙara jin tsoron rayuwata, domin na fahimci cewa ba ni da cikakken tsaro a hannunsu.

Tambaya: Yaushe ka tabbatar cewa mutumin da ka gani shi ne Dadiyata?

Amsa: Bayan an sake ni ne na fara ganin hotunansa a shafukan sada zumunta, inda mutane ke cewa har yanzu ya ɓace. Da na ga hotunan, nan take na gane cewa shi ne mutumin da na gani kuma na yi magana da shi a ofishin Operation Yaki.

Ba shi kaɗai ba ne. Akwai wasu mutane da s**a mutu ko s**a ɓace a irin wannan yanayi. Bayan an sake ni ma har na tuntubi iyalan wasu daga cikinsu. Wasu sun shafe shekara ɗaya, wasu shekaru biyu, wasu ma fiye da haka ba tare da an kai su kotu ba.

Yanzu haka ina jiran hukuma kawai ta gayyace ni domin in bayyana duk abin da na sani. A shirye nake na faɗi gaskiya.

TUNAWA DA MARIGAYI SHUGABA UMARU MUSA YAR’ADUA: Shugaban da ya haɗe kan kudu da Arewa a matsayin Nigeria guda a lokacin ...
05/05/2026

TUNAWA DA MARIGAYI SHUGABA UMARU MUSA YAR’ADUA: Shugaban da ya haɗe kan kudu da Arewa a matsayin Nigeria guda a lokacin rayuwar sa

A yau, ranar 5 ga watan Mayu, ta cika shekaru goma sha shida (16) da ƙasar nan ta yi babban rashi na gwarzo, mutum mai cikakken nagarta da gaskiya, kuma ɗan ƙasa mai kishin ƙasa ba tare da son kai ba, wato marigayi Umaru Musa Yar'Adua.

Bayan shudewar waɗannan shekaru, ayyuka da manufofin da ya shimfiɗa har yanzu suna ci gaba da zama shaida ga irin gudunmawar da ya bayar wajen gina ƙasa. Tarihinsa na shugabanci mai tausayi da rikon amana ya sanya aka san shi da lakabin “Shugaba Mai Ladabi” (Gentleman President).

A yayin da ake ci gaba da tuna wannan jagora na gari, akwai buƙatar mu ƙara jajircewa wajen ɗaukar darasi daga kyawawan manufofinsa da ya aiwatar da ƙwazo da sadaukarwa, musamman a fannoni na gaskiya, adalci da kyautata rayuwar al’umma.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki (SWT) da Ya gafarta masa, Ya yalwata masa rahama, kuma Ya ba shi aljanna Firdausi. Amin.

Da me kuke tunawa da marigayi Ƴaradua dashi?

A gurguje..Gwamnan Jihar Kano, Malam Abba Kabir Yusuf, ya aika wa Majalisar Dokokin Jihar Kano da sunan Hon. Murtala Sul...
22/04/2026

A gurguje..

Gwamnan Jihar Kano, Malam Abba Kabir Yusuf, ya aika wa Majalisar Dokokin Jihar Kano da sunan Hon. Murtala Sule Garo a matsayin wanda ya tsayar domin mukamin Mataimakin Gwamnan jahar, domin tantancewa da yanke hukunci kan amincewa da naɗin nasa.

Ana sa ran ƙarin bayanai kan wannan lamari za su biyo baya nan kusa.

Almayadeen ta ruwaito cewa:Bayan Iran ta sanar da Amurka ta hannun Pakistan mai shiga tsakani cewa tawagarta ba za ta je...
22/04/2026

Almayadeen ta ruwaito cewa:

Bayan Iran ta sanar da Amurka ta hannun Pakistan mai shiga tsakani cewa tawagarta ba za ta je birnin Islamabad a ranar Laraba ba, Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa za a ƙara wa’adin tsagaita wuta har sai Iran ta gabatar da shawararta, sannan a kammala tattaunawa—ko da wane irin sakamako ne zai biyo baya.

Ya kuma ce: “Bisa buƙatar Field Marshal Asim Munir da Firayim Ministan Pakistan Shehbaz Sharif, an roƙe mu mu dakatar da harin da muka shirya kai wa Iran har sai shugabanninsu da wakilansu sun samar da matsaya guda ɗaya da aka amince da ita.”

Haka zalika, Trump ya ƙara da cewa ya umarci sojojin Amurka da su ci gaba da killacewa (blockade), tare da kasancewa cikin cikakken shiri da ƙarfi domin aiwatar da duk wani mataki a kowane lokaci.

20/04/2026

Matasa kun san alheran dake cikin kiwon Awaki kuwa?

Da ace matasa sun fahimci alheran dake cikin kiwon dabbobi musamman awaki da sun daina jiran ayyukan albashi, da sun fahimci ɓata lokaci ne tsantsa jiran sai ƙarshen wata a baka wasu kuɗaɗen da basu taka kara s**a karya ba da sunan albashi.

Zamu riƙa kawo muku dubarun kiwo na zamani, kuma zamu riƙa tattaunawa da masana harkar

20/04/2026

RAHOTO: Dabarar Siyasar Iran da Matsin Lamba kan Amurka a Batun Tattaunawar Zaman Lafiya

Wannan wani mataki ne mai kaifin basira sosai daga ɓangaren Iran, wanda ke nuna yadda take amfani da dabarun siyasa domin cimma burinta a fagen ƙasa da ƙasa.

Dalilin da ya sa ake ganin wannan mataki mai kaifin basira ne shi ne, Amurka tana cikin matsananciyar buƙatar cimma yarjejeniyar zaman lafiya. A baya-bayan nan, Trump ya sanar da cewa Amurka za ta koma Islamabad domin ci gaba da tattaunawa. Sai dai Iran ta bayyana cewa ba za ta halarci wannan tattaunawa ba.

A cewar rahotanni, Iran ta kuduri aniyar koyawa Amurka darasi. Duk da cewa ta amince ta sake buɗe mashigar ruwa ta Hormuz bayan sanar da tsagaita wuta a Lebanon, Trump ya ci gaba da takunkumin jiragen ruwan soja, wanda hakan ya sa ake ganin ya karya yarjejeniyar da aka cimma. Ana zargin cewa hakan wani yunƙuri ne na nuna wa jama’ar Amurka cewa Iran ta miƙa wuya ga matsin lamba.

Sai dai Iran ta sake rufe mashigar ruwa cikin gaggawa, tare da sanar da cewa ba za ta je Islamabad domin tattaunawa ba. Ana sa ran tsagaita wutar zai ƙare cikin ‘yan kwanaki, lamarin da ya jefa Trump cikin zaɓi mai wahala—ko ya tsawaita yarjejeniyar tsagaita wuta ko kuma ya koma amfani da ƙarfin soja.

Wasu nazari na nuni da cewa akwai yiwuwar Trump zai zaɓi tsawaita tsagaita wutar tare da bayyana cewa ana ci gaba da tattaunawa kuma ana samun ci gaba. Wannan mataki na Iran na kin halartar tattaunawa yana nufin ƙara matsa wa Amurka lamba domin ta ɗage takunkumin ruwa kafin a koma teburin sulhu.

A ƙarshe, wannan lamari yana nuna cewa Iran na amfani da dabarun siyasa da nufin tilasta Amurka yin sassauci kafin a samu wata yarjejeniya mai dorewa ta zaman lafiya.

Address

Katsina
820001

Opening Hours

Monday 09:00 - 17:00
Tuesday 09:00 - 17:00
Wednesday 09:00 - 17:00
Thursday 09:00 - 17:00
Friday 09:00 - 17:00
Saturday 09:00 - 17:00
Sunday 09:00 - 17:00

Telephone

+2348024449793

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Humanity Today posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Humanity Today:

Share

Category