Media Team Kerau Det, Katsina.

Media Team Kerau Det, Katsina. Domin Yada Ayyukan Alkhairi Na Wannan Detachment

Alhamdulillah yau malam ya karbi bakuncin rundunar yan agaji na Kerau detachment a gidan shi dake Kofar Marusa Katsina S...
27/03/2024

Alhamdulillah yau malam ya karbi bakuncin rundunar yan agaji na Kerau detachment a gidan shi dake Kofar Marusa Katsina
Shugaban agajin ya bayyan cewa wannan ziyara ba yanzu aka fara ba dama suna kai ziyara ga manyan malamai na sunnah a duk shekara domin yi masu barka da shan ruwa da neman shawarwari
Kan haka ne malam ya bayyana farin cikin shi da goyon bayan shi kuma ya basu shawarwari da zasu taimaka don inganta aikin shi
Kasancewa shima malam suna cikin yan agaji na farko ya bayyana kishin shi akan aikin agajin sannan kuma yayi masu fatan alkhairi da addu'a akan wannan aiki

17/09/1445
27/03/2024

17/02/2024

Shin da Gaske Malaman Darika suna Yakar Akidun ‘Yan Hakika?

Akwai wasu ‘Yan Darikar Tijjaniyya, sun fito suna bayyana cewa; Inyas Allah ne. Suna halasta alfasha da munkari, da sauran Akidu na Ilimin Hakika a cikin Sufanci.

Irin wadannan Akidu abu ne da dukkan mai hankali ya san cewa; Zindikanci ne da Kafirci, b***e kuma masu Ilimi da Imani. To wannan ya sa wasu ‘Yan Darika suke raya cewa; -wai- su ma suna yakar ‘Yan Hakikar.

To amma sai dai akwai abin tambaya a nan: Miye ne abin da ‘Yan Darikar suke yaka daga ‘Yan Hakikar?

Asali dai abin da ya kamata mutane su sani shi ne: Sufanci abu biyu ne:
1- DARIKA.
2- HAKIKA.
Ma'ana; akwai DARIKA, wato hanya wacce mutum zai bi ta kai shi ya isa zuwa ga HAKIKA. Idan ya isa zuwa ga HAKIKA to sai a ce: ya yi (WUSULI), ya isa kololuwar Sufanci.

To da zaran ya isa ga HAKIKA to ya fita daga SHARI’A ya shiga HAKIKA. Kawai zai yana aiki da Shari'a ne idan yana cikin jama'a.

Ilimin HAKIKA shi suke kira Ilmin Badini, Ilimin Sirruka.
Ilimin Shari’a kuma shi ne Ilimin Zahiri.

Ilimin HAKIKA, wato Ilimin Badini shi ne; sanin cewa:
- KOMAI ALLAH NE.
- Duk abin da mutum yake aikatawa Allah ne yake aikatawa, don haka aikin mutum kowane iri aikin Allah ne.
- Duk abin da mutum ya aikata da'a ma Allah ne, Allah yana sonsa.

Don haka zina, sata, da sauran alfasha da munkari duka aiyukan Allah ne - Subhanallahi - kuma Allah yana sonsu, ya yarda da su.

To wannan ya sa wanda zai yi aiki da Ilimin HAKIKA to zai aikata dukkan alfasha. Kuma a hakan da’a yake yi wa Allah, saboda Allah ne ya ga dama ya aikata.

To wannan Ilimi na HAKIKA kowane Sufiy dan Darika ya san ilimi ne ingantacce tabbatacce, kuma dadai ne, gaskiya ne. Wadanda suke inkarinsa dayan biyu ne; imma “Mahjubi” (wanda ba ya Darika, ba a yi masa kashafin ganin Ilimin Badini ba), imma dan Darika wanda bai yi WUSULI ba.

To amma wannan Ilmi na HAKIKA, wato Ilimin Badini, Sirri ne, ba a bayyana shi. Bayyana shin kafirci ne. Shi ya sa Gazaliy yana cikin bayanin Tauhidin “Mushada”, wato ganin komai ya zama abu daya, sai ya warware wata mushkila ya ce:
"فإن قلت: كيف يتصور أن لا يشاهد إلا واحد، وهو يشاهد السماء، والأرض، وسائر الأجسام المحسوسة، وهي كثيرة؟ فكيف يكون الكثير واحدا؟
فاعلم أن هذه غاية علوم المكاشفات. وأسرار هذا العلم لا يجوز أن تسطر في كتاب، فقد قال العارفون: إفشاء سر الربوبية كفر".
إحياء علوم الدين (٤/ ٢٤٦)

“Idan ka ce: ta yaya zai yiwu a ce ba a ganin komai sai abu daya, alhali mutum yana kallon sama da kasa, da sauran abubuwa na zahiri, ana kallonsu abubuwa masu yawa? Ta yaya abubuwa masu yawa za su zama abu daya?
To ka sani lallai isa zuwa ga wannan matsayi (ganin abubuwa masu yawa sun zama abu daya) shi ne kololuwar Ilimin KASHAFI. Kuma sirrukan wannan Ilimi bai halasta a rubata su a littafi ba. Hakika Arifai sun ce: Tona sirrin Rububiyya kafirci ne”.

Don haka Ilmin HAKIKA SIRRI ne, ba a bayyana shi, saboda Ilmi ne na Badini. Duk wanda ya bayyana shi to ya yi laifi, Sufaye za su iya ce masa: kafiri, saboda ya tona sirrin da ya wajaba a boye.

Shi ya sa hatta su ma manyan Sufayen suke boyewa, Sha’araniy ya hakaito daga Junaidu:
"وكان الجنيد لا يتكلم قط في علم التوحيد إلا في قعر بيته، بعد أن يغلق أبواب داره، ويأخذ مفاتيحها تحت وركه، ويقول: "أتحبون أن يكذب الناس أولياء الله تعالى وخاصته، ويرمونهم بالزندقة والكفر؟".
الطبقات الكبرى للشعراني (١/ ١٠)

“Junaidu ya kasance ba ya magana a kan Ilimin Tauhidi (na Sufanci) sai a wuri mafi zurfi a gidansa, bayan ya rufe kofofin gidan, ya sanya makullayen a karkashin mazauninsa, sannan sai ya ce: “So kuke yi mutane su karyata Waliyyan Allah, kuma kebantattunsa, a jefe su da Zindikanci da kafirci?”.

Haka ya kawo kissar wani Arifi, ya ce:
“أبو عبد الله القرشي: أن أصحابه طلبوا منه أن يسمعهم شيئا من علم الحقائق، فقال لهم: كم أصحابي اليوم؟ فقالوا: ستمائة رجل. فقال الشيخ: اختاروا لكم منهم مائة، فاختاروا. فقال: اختاروا من المائة عشرين، فاختاروا. فقال: اختاروا من العشرين أربعة، فاختاروا. قلت: وكان هؤلاء الأربعة أصحاب كشوفات ومعارف، فقال الشيخ: لو تكلمت عليكم في علم الحقائق والأسرار لكان أول من يفتي بكفري هؤلاء الأربعة”.
الطبقات الكبرى للشعراني (١/ ١٠)

"Almajiran Abu Abdillah al-Qurashiy s**a nemi ya fada musu wani abu daga Ilimin HAKIKA, sai ya ce musu: Yau Almajiraina nawa ne?
Sai s**a ce: mutum 600 ne.
Sai ya ce: to a cikinsu ku zaba mini mutum 100. Sai s**a zabo.
Sai ya ce: ku zaba mini 20 daga 100. Sai s**a zabo su.
Sai ya ce: ku zaba mini mutum 4 daga 20. Sai s**a zabo su.
Na ce: Kuma wadannan mutum 4 suna da ILMOMIN KASHAFI da MA’ARIFA.
Sai Shehin ya ce: Da a ce zan yi magana a ILIMIN HAKIKA da SIRRUKA da farkon wadanda za su yi Fatawan na kafirta su ne wadannan mutum 4”.

Wadannan kissoshi guda biyu, mai littafin “Jawahirul Ma’aniy” ya kawo su a “Muqaddima”, a (1/ 19).

Saboda haka wannan Ilimin HAKIKAN Kafirci ne da Zindikanci a madubin Shari’a. Don Ilimi ne mai warware Shari’a ya rusa ta. Amma kuma shi ne kololuwar Sufanci. Wanda ya isa gare shi to shi ne ya zama Waliyyi, Arifi, cikakken Sufiy dan Darika, wanda ya yi WUSULI.

Saboda haka a wajen Sufaye, abin da ‘Yan Hakika suke fada asali ba laifi ba ne, dadai ne, gaskiya ne, amma sai dai Sirri ne da ba a bayyana shi. Duk wanda ya bayyana to shi ne ya yi laifi.

Don haka a Sufanci, duka abin da ‘Yan Hakika suke fada gaskiya ne, dadai ne, amma laifinsu daya shi ne BAYYANA SIRRI.

Da wannan za ka fahimci cewa; masu inkari ga 'Yan Hakika cikin Sufaye, ba Akidun 'Yan Hakikar suke inkari ba, a'a, bayyanawa suke inkari.

Dr. Aliyu Muh'd Sani

Muna farin cikin gayyatar Yan uwa musamman daliban ilimi zuwa  Daurah mai taken "Mahangar Yan Alkuraniyun a kan Alkurani...
31/12/2023

Muna farin cikin gayyatar Yan uwa musamman daliban ilimi zuwa Daurah mai taken "Mahangar Yan Alkuraniyun a kan Alkurani da Kuma raddi zuwa ga shubhohin su" wadda Malaminmu Sheik Murtala Abdurashid zai gabatar kamar haka:
Wuri:. Sabon Masllacin Sokoto Rima, Katsina
Rana: Litanin 1/1/2024
Lokaci: 9:00 na safe

Shiryawa
Cibiyar Darul Hadith, Katsina

Sanarwa
HK Media

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUN!Allah Yayiwa Sheikh Giro Argungu Rasuwa, Bayan Jinya Da Ya Samu A Daren Jiya, Bayan Ka...
06/09/2023

INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUN!

Allah Yayiwa Sheikh Giro Argungu Rasuwa, Bayan Jinya Da Ya Samu A Daren Jiya, Bayan Kammala Tafsir Magriba Zuwa Ishaa, Allah Yayi Maka Gafara Sheikh Amin..

Wednesday!
6th September, 2023.

27/06/2023

Yau Take Arafah
✍️Prof Mansur Sokoto, mni
Daga rubutun
Alhamis 8 Dhul Hajj 1442H (07/07/2021)
(tareda editing kaɗan)

1. Yau talata 9 ga Dhul Hajji ita ce ranar Arafa.

2. Ita ce rana ta 9 daga cikin kwanukan shekara mafi daraja da falala a wurin Allah.

3. A ranar Arafat ne Allah ya kammala saukar da Alkur’ani ga Manzonsa a wurin Hajjin bankwana.

4. A wannan ranar Allah yana gafarta zunubai, ya yafe kurakurai, ya karba addu'oin bayinsa.

5. Allah ya rantse da wannan rana a inda ya ce:
(واليوم الموعود * وشاهد ومشهود)
Al-Yaumul Mau'úd shi ne yinin alkiyama, Sháhid shi ne ranar Arafa, Mashhúd shi ne ranar Jum'ah.

6. Kuma Allah ya rantse da ranar Arafa inda yake cewa: "والشفع والوتر" Shafa'i shi ne ranar layya, witiri shi ne ranar Arafa.

7. Hadisi ya inganta daga Manzon Allah (S) cewa, "babu wani yini wanda yake mafifici a wurin Allah fiye da yinin Arafa. Allah yana saukowa zuwa saman duniya sai ya yaba da mutanen kasa, ga mutanen sama". Sahihu Ibn Hibban 3583. Akwai hadisai da dama ingantattu a kan wannan. Duba Sahihu Muslim 1348 da Musnad Ahmad 8033.

8. A ranar Arafa ana son yawaita zikiri da addu'a. Kuma mafificiyar addu'a a ranar ita ce: "LA ILAHA ILLALLAHU WAHDAHU LA SHARIKA LAHU, LAHUL MULKU WALHUL HAMD, WAHUWA ALA KULLI SHAI'IN QADEER".
Ana kuma son a yawaita fadin: "SUBHANALLAH, WALHAMDU LILLAH, WA LA ILAHA ILLALLAH, WALLAHU AKBAR".

9. Magabata sun kasance a ranar Arafa suna aikata ayyuka iri daban daban na neman lada don samun gafarar Allah mahalicci.

10. An sunnanta yin azumi ga wanda ba ya aikin Hajji a wannan rana. Kuma ana fatar Allah zai yafe ma wanda ya yi shi zunubin bara da na bana.

11. Ana son mutum ya umurci iyalansa da yayansa - har kanana - su yi azumin ranar saboda gamewar falala da gafara.

12. Mutum yana iya yin azumin Arafa ko da ana bin sa bashin azumi. Idan kuma ya yi ramko a ranar babu laifi; ana sa ran zai samu karin falala saboda darajar wannan rana.

13. Babu laifi matafiyi ya yi azumin wannan rana idan ba zai sha wahala a kai ba.

14. Daga sallar asuba ta ranar Arafa ana so yin kabbarori bayan sallah "ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR, LA ILAHA ILLALLAHU, ALLAHU AKBAR, ALLAHU AKBAR, WA LILLAHIL HAMD" daga nan har zuwa sallar la'asar a rana ta uku bayan sallah.

15. Daga cikin abubuwan da Annabi (S) ya roka a wannan rana akwai: gafara da jinkai da afuwa, da shiriya da tsarkin zuciya da sutura da wadatar arziki da lafiya da kamun kai da kariya da nasara da aminci da mafi girma kuma uwa uba; samun aljanna firdausi. Don haka ana son mutum ya dukufa da tsarkin zuciya da magiya ga ubangiji musamman a yammacin wannan rana domin neman bukatunsa na duniya da lahira da neman gafara ga kansa da iyayensa da iyalansa da kasarsa da al'ummar musulmi.

16. Akwai matukar hatsari ga yin sabon Allah a ranar Arafa saboda girmanta da darajarta a wurin Allah.

17. Alhazai a wannan rana suna cikin gafarar Allah, kuma Allah yana shaida ma Mala'iku haka.

18. Wanda bai samu tsayin Arafa ba, ya tsaya a kan iyakokin Allah. Wanda ba zai samu yanka dabba a gobe ba, ya yanka son zuciyarsa.

19. Rana ta 10 ita ce ranar Idi babba, kuma ranar layya. Ta fi duk sauran ranaku muhimmanci kuma babu abinda Allah ke so a ranar kamar kwararar da jinin dabbobi ana kiran sunansa.

20. Ranaku 3 bayan Sallah su ne Ayyamut Tashriq. Ana son musulmi ya darajta su, ya ci abinci, ya ziyarci yan uwa, ya caba ado, ya yi sadaka da sashen naman da ya yanka.

Allah ya yi mana muwafaqa da samun gafara, ya saukar mana da aminci da zaman lafiya da yalwantar arziki a kasarmu, ya daukaka addinin Musulunci da Musulmi.

LOKUTTAN SALLAR IDI (BABBA) 1444-2023 NA GARIN KATSINA DA KEWAYEHk Media
25/06/2023

LOKUTTAN SALLAR IDI (BABBA) 1444-2023
NA GARIN KATSINA DA KEWAYE

Hk Media

Ranar Laraba 28 ga watan Yuni za a yi babbar salla a NajeriyaKwamitin ganin wata na mai Alfarma Sarkin Musulmin Najeriya...
19/06/2023

Ranar Laraba 28 ga watan Yuni za a yi babbar salla a Najeriya

Kwamitin ganin wata na mai Alfarma Sarkin Musulmin Najeriya ya ayyana ranar LItinin 19 ga watan Yuni a matsayin ranar 1 ga watan Zul-Hijjah.

A wata sanarwa da kwamitin ya wallafa a shafinsa na Twitter, ya ayyana ranar Laraba 28 ga watan Yuni a matsayin ranar da za a gudanar da babbar salla a faɗin Najeriya.

Sanarwar ta ambato mai alfarma Sarkin Musulmin Muhammad Sa'ad Abubakar lll na yi wa al'ummar musulmin ƙasar fatan alkari da fatan yin sallah lafiya

MU SAN JUNA:-Wannan Shine "Malam Nasir Ibrahim Kagara" Kuma Shine Sabon Shugaban mu na Shinkafi Division Katsina, Wanda ...
26/04/2023

MU SAN JUNA:-

Wannan Shine "Malam Nasir Ibrahim Kagara" Kuma Shine Sabon Shugaban mu na Shinkafi Division Katsina, Wanda shine ya gaji "Marigayi Alh. Aminu Garba Goga" (Allah ya gafarta masa).

Shugaba muna maka fatan nasara cikin Shugabancinka, Allah (S.W.T) yayi riko da hannayenka ya datar da Kai ya kare Mana Kai da kariyarsa.

Mukhtar Umar
Div. Publicity Secretary

19/04/2023

Address

Katsina

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Media Team Kerau Det, Katsina. posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share