Hausa Trust ng

Hausa Trust ng Wannan Shafi ne dai zaku rika samun Tantagaryar shirye-shirye da ingantattun labarai

Siyasa...Wasu matasa 'Yan kishin Karamar Hukumar Danja sun fara kiran Matsahi Hon. Anas Aliyu Jobe domin tsaya takarar n...
08/04/2025

Siyasa...

Wasu matasa 'Yan kishin Karamar Hukumar Danja sun fara kiran Matsahi Hon. Anas Aliyu Jobe domin tsaya takarar neman Kujerar Majalisar Dokokin Jahar Katsina domin Wakiltar Karamar Hukumar Danja.

Shin ko zai amsa kiran nasu?

SAKON BARAKA DA SHAN RUWA ZUWAGA MAIGIDANA HON Sulaiman Dahiru Tandama.Ina mai Miko sakon barka da Shan ruwa zuwaga maig...
05/03/2025

SAKON BARAKA DA SHAN RUWA ZUWAGA MAIGIDANA HON Sulaiman Dahiru Tandama.

Ina mai Miko sakon barka da Shan ruwa zuwaga maigidana Hon Sulaiman Dahiru Tandama.

Allah Kuma yasa ibadar da mukayi karbabiyace.

Comrd Ibrahim Yakubu

Da Dumi Duminsa.  Budadiyar wasika zuwaga Yan Yan Jam'iyar PDP na Northwest, Northeast da Kuma North Central. H.E SIDI A...
05/03/2025

Da Dumi Duminsa. Budadiyar wasika zuwaga Yan Yan Jam'iyar PDP na Northwest, Northeast da Kuma North Central. H.E SIDI ABDUL BOMI KAURAN LAPAI danku ne.

Daga Comrd Ibrahim Yakubu

Wannan sakone Wanda zaitafi kaitsaye zuwaga Yan Yan Jam'iyar PDP na Arewa da kudancin Nigeria Maigirma. H.E SIDI ABDUL BOMI KAURAN LAPAI Dantakarar Chairman party na kasa a Karkashin Jam'iyar PDP baya Goya marayu da masu iyayenma.

Muna rokonku kufito kwanku da kwarkwata namu mu Zabi H.E SIDI ABDUL BOMI KAURAN LAPAI Domin hadakan Jam'iyar PDP, Shine Wanda zai jagoranci Jam'iyar PDP da membobinta Zuwa matakin nasara da yardar Allah.

SIDI ABDUL BOMI KAURAN LAPAI bashida wani bangaranci. Ba ataba samunsa da cin amanar al'ummarsa ba a kullum nasara itace agabanshi.

A Ranar 13-3-2025 Ranar da za'ayi taron NEC mutabbatar H.E SIDI ABDUL BOMI KAURAN LAPAI shimuka tsaida amatsayin Shugaban Jam'iyar PDP na kasa Kuma bazamuji kunya ba.

Munyi imani da Allah da Ranar alkiyama SIDI ABDUL BOMI. Bazaici Amana ba bakuma zaibari aci Amana ba.

Wannan Sakone daga Comrd Ibrahim Yakubu

Kungiyoyin Matasan Najeriya Ta Gudanar Da Zàñga-zàñĝar Neman A Gudanar Da Bincike Kan Sanata Shehu Buba Bisa Zargin Taim...
17/10/2024

Kungiyoyin Matasan Najeriya Ta Gudanar Da Zàñga-zàñĝar Neman A Gudanar Da Bincike Kan Sanata Shehu Buba Bisa Zargin Taimakawa Ta'addanci

DAGA Ƙungiyar Muryar PDP Ta Najeriya

A yayin wani gangamin nuna goyon baya da s**a gudanar, ƙungiyar gamayyar ƙungiyoyin matasa ta Najeriya, "National Coalition of Youths", ƙarƙashin jagorancin Bashir Gusau, ta gudanar da zanga-zangar lumana a birnin tarayya Abuja, inda ta yi kira kan a gudanar da bincike game da zargin hannu a ayyukan ƴan bindiga da ake yi kan Sanata Shehu Umar Buba, sanata mai wakiltar Bauchi ta Kudu.

A rahoton da Jaridar Dokin Ƙarfe TV ta samu, Zàñga-zàñĝar wacce ta haɗa ɗaruruwan ƴan Najeriya, sun kuma yi zantawa da manema labarai inda s**a nemi a tabbatar da gaskiya da adalci.

Ƙungiyar ta maida hankali kacokan kan wannan zargi wanda ya faro a farkon wannan watan, inda ake tuhumar Sanata Buba da hannu cikin ayyukan ƴan biɲdiĝá. Duk da cewar babu wata tuhuma yanzu haka a hukumance, duba da girman lamarin akwai buƙatar hukumomin da abin ya shafa su gudanar da bincike na gaggawa musamman ma la'akari da yadda ƙasar ta ke cigaba da fuskar ƙalubalen tsaro can da can.

Kiran Gusau Kan A Tabbatar Da Adalci:

A yayin zantawarsu da manema labarai, shugaban ƙungiyar, Bashir Gusau ya nuna buƙatar gudanar da bincike na haƙiƙa. A cewarsa, babu wani mutum wanda ya fi ƙarfin a gudanar da bincike a kansa a duk lokacin da buƙatar hakan ta taso komai matsayinsa musamman ma kan lamarin da ya shafi tsaron ƙasa.

"Tsaro da zaman lafiyar al'ummarmu shi ne abin da ya zama wajibi kowane shugaba ya fi ba wa fifiko a ƙasar nan. Ba abu ne da za a yarda da shi ba a zaɓi mutum domin ya kare muradun al'ummar Bauchi ta Kudu ya kuma yi tarayya da ƴan bindiga ko wasu masu aikata miyagun laifuffuka ba. Hakan ya sa mu ke kira da a gudanar da bincike kan wannan zargi da ake yi wa Sanata Buba". Cewar Gusau.

Ya ƙara da cewa wannan Zàñga-zàñĝa tasu ba ta da alaƙa da siyasa face neman a tabbatar da adalci, zaman lafiya da tsaro a Jihar Bauchi da kewayenta. Ya ƙara da cewa matsalar tsaro ta ratsa kusan ko'ina a ƙasar nan ta jefa al'umma cikin firgici da razani duba da wannan dan mutum yana riƙe da wani matsayi bai kamata ya samu garkuwa daga neman tabbatar da adalci ba.

Neman A Ɗauki Mataki Na Gaggawa:

Ƙungiyar ta yi kira ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, majalissar ƙasa, da kuma hukumomin tsaro na ƙasa da su ɗauki ƙwaƙƙwaran matakin da ya dace. A cewar Gusau, barin wannan zargi batare da an yi bincike ba babu abin da zai haifar face jefa rashin yarda kan hukumomin Najeriya a zukatan jama'a gami da sanyaya gwiwar al'umma kan yaƙi da ta'addanci.

"Mun yi imani cewa idan aka gudanar da bincike har aka gano Sanata Buba ba shi da laifi, to adalci yana nan. Amma idan har akwai gaskiya a zargin ya zama wajibi doka ta yi aikinta a kansa batare da duban matsayinsa ba. Al'ummar Bauchi ta Kudu da dukkan ƴan Najeriya sun cancanta su san gaskiya kan wannan batu". Cewar Gusau.

Martanin Masu Ruwa Da Tsaki:

Tuni zanga-zangar ta fara samun martani daga masu ruwa da tsaki daban-daban. Wasu daga cikin al'ummar Bauchi ta Kudu sun yabawa matasan bisa tsayuwarsu kan ƙalubalantar ba daidai ba, yayin da wasu kuma suke kallon lamarin ta fuskar siyasa.

Duk da waɗannan ra'ayoyi daban-daban, ƙungiyar ta jaddada ƙudirinta na cigaba da bibiyar lamarin cikin lumana tare da jan hankalin sauran ƴan Najeriya da su shigo cikin wannan gwagwarmaya ta neman tabbatar da adalci.

Bayani Na Gaba

Daga ƙarshe ƙungiyar ta yi fatan saƙon nata zai isa ga gwamnati da hukumomin tsaro. Manufar ƙungiyar shi ne a tabbatar da gaskiya da adalci musamman kan lamarin da yake da alaƙa da tsaro da zaman lafiyar ƙasa.

Zàñga-zàñgar lumanar wacce Bashir Gusau da ƴan tawagarsa s**a jagoranta sun ja hankalin ƙasa kan zargin da ake yi wa Sanata Shehu Buba tare da fatan ƴan ƙasa, masu nazarin siyasa da hukumomin tsaro za su sanya Ido kan lamarin.

Yanzu haka, lamarin ya je gaban hukumomin tsaro daban-daban, al'umma kuma na cigaba da zaman dakon a gudanar da cikakken bincike na haƙiƙa duba da yanayin siyasa a yankin Bauchi ta Kudu.

Kamar yadda Najeriya ta ke cigaba da yaƙi da matsalar rashin tsaro, zanga-zanga irin wannan ta na nuna irin rawar da ya kamata ƴan ƙasa su taka wajen tabbatar da adalci a ƙasa. Ƙungiyar gamayyar matasan ta Najeriya ta tura saƙo mai ƙarfi kan lallai ya zama wajibi a gudanar da komai cikin gaskiya da adalci da daidaito kan yaƙi da ƴan bindiga batare da duba sanayya, girman matsayi ko sassautawa ba.

*KAURAN LAPAI YA HALARCI TARON BADA TALLAFI NA DANMAJALISA MAI WAKILTAR LAVUN, MOKWA, EDATI*06/07/2024Maigirma Dan Takar...
06/07/2024

*KAURAN LAPAI YA HALARCI TARON BADA TALLAFI NA DANMAJALISA MAI WAKILTAR LAVUN, MOKWA, EDATI*

06/07/2024

Maigirma Dan Takarar Shugaban Jam'iyyar PDP na kasa *HE Sidi Abdul Bomi Kauran Lapai Walin Gulu* Ya Halarci Taron bada tallafin ababen more rayuwa injina da Wanda Danmajalisa Mai wakiltar Kananan Hukumomin LAVUN MOKWA DA EDATI *Hon Joshua Audu Gana*

*HE Sidi Abdul Bomi Kauran Lapai* Yana Cikin Wadanda S**a Gabatar da bada Wannan tallafi ga wadanda Allah yasa za'a Basu

Daga bisani Kauran Lapai yakai Ziyara Bangirma ga Maimartaba *(EZONUWAN OF KUTIGI)*
Sarkin Kutigi a fadarsa

Kauran Lapai yayi Addu'a ga Wannan Dan Majalisar bisa Kokarinshi a wannan Mazabu nashi tareda Yabo akan wannan Kokari dayayiwa Al'ummar shi.

DG MEDIA
KATSINA MEDIA TEAM

ZIYARAR BARKA DA SALLAH DA MATASAN  JAM'IYAR PDP DA KUMA YAN SOCIAL MEDIA S**A KAIMA SHUGABAN RIQO NA KARAMAR HUKUMAR  D...
04/07/2024

ZIYARAR BARKA DA SALLAH DA MATASAN JAM'IYAR PDP DA KUMA YAN SOCIAL MEDIA S**A KAIMA SHUGABAN RIQO NA KARAMAR HUKUMAR DANJA HON MURTALA ABUBAKAR MAISALATI.

Gamayyyar matasa da yan media na jam'iyar PDP karamar hukumar Danja s**aiwa shugaban riko na jam'iyar Ziyarar barka da sallah da sada zumunci.

Matasan sun fito daga Gunduma Goma da karamar hukumar Danja take da ita.

Bayan tattaunawa da ziyarar bangirma da akayi Matasa da yan Media Suntuhumi Shugaban riko na PDP na karamar hukumar danja dangane da maganar tsayawa takarar shugaban jam'iya na dindin wanda yabaiyana ra'ayinsa akan kujerar tave shibazai tsaya takarar shugaban Jam'iya ba.

Da jin haka daga bakinsa matasa da dama basuji dadi ba yayinda s**ayi yunkurin tsaida ranar da zasuyi Zanga Zangar lumana akaramar hukumar Danja Matukar bashi aka bari yacigaba da shugabanci ba.

Matasa da dama sungargadi yunkurin dawo da maciya amana domin cigaba da shugabanci.
Zuwan Barrister Murtala Abubakar maisalati yasa jam'iyar PDP taciga da samun mabiya a kowanne yanki dan haka matukar aka kaudashi to tamkar babu jam'iyar PDP ne akaramar hukumar danja.

Daga Wakilinmu
Comrd Ibrahim Yakubu Tandama.

IDAN RANA TA FITO  TAFIN HANNU BAYA BOYETA MAIGIRMA H.E SIDI ABDUL' BOMI KAURAN LAPAI DANTAKARR SHUGABAN JAM'IUAR PDP NA...
06/06/2024

IDAN RANA TA FITO TAFIN HANNU BAYA BOYETA

MAIGIRMA H.E SIDI ABDUL' BOMI KAURAN LAPAI DANTAKARR SHUGABAN JAM'IUAR PDP NA KASA WANDA YACIKA DUK SHARUDDA NA ZAMA NATIONAL CHAIRMAN OF PDP.

Muna kira da masu ruwa da tsaki da kuma commiteen amintattu namu na PDP nakasa matukar cigaban Jam'iyar PDP ake nema da kuma neman nasara a kowanne mataki to subawa H.E SIDI ABDUL BOMI kujerar national chairman.

H.E SIDI ABDUL BOMI mutum ne jajirtacce kuma wanda yasan aiki.

H.E SIDI yakasance yana daga cikin mutane masu alfarma gurin kowaye a kasarnan .

Zamubi lungu da sako domin rokon Al'farma gurin wadanda mukeda ita da wadanda zasu bamu shawara.

Katsina State Media Team
Comrd Ibrahim Yakubu Tandama

FITAR BARRISTER IBRAHIM SHEHU SHEMA JAM'IYAR PDP  BA ABU BANE DA ZA'AYI BAKIN CIKI SAIDAI MURNA.Daga Comrd ibrahim Yakub...
02/05/2024

FITAR BARRISTER IBRAHIM SHEHU SHEMA JAM'IYAR PDP BA ABU BANE DA ZA'AYI BAKIN CIKI SAIDAI MURNA.

Daga
Comrd ibrahim Yakubu Tandama

Fitar tsohon gwamnan jihar katsina daga PDP ba abu bane wanda jam'iyar pdp zatace tayi rashi saidai tace masha Allah anyarda kwallon mangwaro an huta da kuda.

Shidai barrister bashi da wasu mutane jihar katsina wadanda za'ayi takama dasu za'ace idan basu baza'ayi nasara ba a siyasa.

Idan kuka kalli yanayin da ake ciki a jam'iyar pdp shema bashi da abinda zai iya taimakon al'umar dake cikin pdp, yagaza taimakon kowa dakowa.

Kowa yasani babu wani mai fada aji a jam'iyar pdp kamar SEN YAKUBU LADO DANMARKE sakamakon yadauki duk wani dan jam'iyar pdp ya rike amana. Yana taimakon shuwagabannin pdp sannan kuma yanabi lungu da sako wajen fito da al'umma cikin duhu da suke ciki.

Sam yadda shema yacutar da pdp haka zai cutar da APC ku rubuta ku aje Shi mabaraci ne kuma kowa yasa mabaraci abashi yasani.

PDP YOUTH LEADER TANDAMA WARD.

DA DUMI DUMINSA.KIRAGA DELEGATE MASU ZABEN NATIONAL DELEGATE NA JAM'IYYAR PDP NA KARAMAR HUKUMAR KATSINA Hajiya Nana Yus...
01/05/2024

DA DUMI DUMINSA.

KIRAGA DELEGATE MASU ZABEN NATIONAL DELEGATE NA JAM'IYYAR PDP NA KARAMAR HUKUMAR KATSINA

Hajiya Nana Yusif Katsina Uwar Marayu Shugabar Kungiyar NANA YUSIF FOUNDATION tafito Takarar National Delegate a Jam'iyyar PDP a Karamar Hukumar Katsina

Don haka Muke kira ga masu ruwa da tsaki na Jam'iyyar PDP a Karamar Hukumar Katsina a duba Kokari tareda jajircewarta a Jam'iyyar PDP

Abata damar Kuma a zabeta amatsayin National Delegate ta Karamar Hukumar Katsina a Jam'iyyar PDP kasantuwarta mace jajirtatta Mai kishin Jam'iyyar PDP

Sako daga
Yankwamitin yakin Neman zaben Nana Yusif Katsina

*BAKI DAYAN SHUGABANNIN JAM'IYYAR PDP NA KANANAN HUKUMOMI 25 NA JIHAR NEJA SUNYI MUBAYI'A GA SIDI ABDULL*23/04/2024Cikin...
24/04/2024

*BAKI DAYAN SHUGABANNIN JAM'IYYAR PDP NA KANANAN HUKUMOMI 25 NA JIHAR NEJA SUNYI MUBAYI'A GA SIDI ABDULL*

23/04/2024

Cikin Ikon Allah tareda yardarshi yau Bakidayan Shugabannin Jam'iyyar PDP na Kananan Hulumomi 25 dake Jihar Neja Sunyi Mubayi'a tareda Goyon bayansu ga Maigirma Dantakarar Shugaban Jam'iyyar PDP na Kasa HE Sidi Abdull Bomi Kauran Lapai

Wannan Babbar Nasarce garemu tareda Dukkan Magoya Bayanshi a Cikin Wannan takàra tareda Farin Ciki a Wannan Lamari

Dukkansu Sunyi (Endorsing) Watau sun Jaddada Goyon Bayansu ga Maigirma Dantakarar Shugaban Jam'iyyar PDP na Kasa HE Sidi Abdull Bomi Kauran Lapai Tareda yimashi Fatan Nasara a Wannan Kudiri

Allah yacigaba da bamu Nasara a kowane Lokaci Amin.

KATSINA STATE MEDIA TEAM
COMRADE IBRAHIM YAKUBU T

DA DUMI DUMINSA.DANTAKARAR  SHUGABAN JAM'IYAR PDP NA KASA H.E SIDI ABDUL BOMI KAURAN LAPAI A FADAR MAI MARTABA ETSU NUPE...
21/04/2024

DA DUMI DUMINSA.
DANTAKARAR SHUGABAN JAM'IYAR PDP NA KASA H.E SIDI ABDUL BOMI KAURAN LAPAI A FADAR MAI MARTABA ETSU NUPE

20/04/2024

Cikin Hukuncin Allah yau Maigirma Dantakarar Shugaban Jam'iyyar PDP na Kasa HE Sidi Abdull Bomi Kauran Lapai Walin Gulu yasami Halartar Fadar Maimartaba Shugaban Sardaunan Neja ETSU NUPE Alh Yahaya Abubakar

Wannan Ziyara tana kunshene da Neman Nuna Goyon bayanshi ga KAURAN LAPAI tareda yimashi Fatan Alkhairi akan Wannan Kudiri nashi na Fatan zama Shugaban Jam'iyyar PDP na Kasa

Mai Martaba ETSU NUPE yayi Addu'a tareda Fatan Alkhairi Cikin Wannan takàra tareda nuna goyon bayanshi ga Wannan da nasu kasan cewarshi Dan cikin Wannan masarauta

Muna Godiya kwarai da kulawa tareda nuna mana Goyon Baya cikin Wannan Ziyara da mukazo

Muna Addu'ar Allah yayi mana Jagora Amin

Katsina State Media
Comrd Ibrahim Yakubu Tandama.

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Trust ng posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share