YTD Hausa

YTD Hausa Domin Samun Ingantattun Rahotanni, Ilmantarwa,Fadakarwa Da Nishadantarwa

Tabkin Ramin-masu Ya Cinye Gidajen Da Ke Kewaye Da Shi, Al'umma Sun yi Kira Ga Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina Dr. Dikko...
01/09/2025

Tabkin Ramin-masu Ya Cinye Gidajen Da Ke Kewaye Da Shi, Al'umma Sun yi Kira Ga Mai Girma Gwamnan Jihar Katsina Dr. Dikko Umaru Radda Ya Kawo Masu Dauki Tare shugaban Karamar Hukumar Katsina Isah Miqdad AD Saude.

Da Su Ke Bayyana Damuwarsu Ga Gwamnati Al'umma Unguwar Gafai, Lungun makerar Farfaru Sun Bayyana Halin Da Su ke ciki ne Jiya Lahadi Gaban Tsohon Tabkin Na Ramin Masu Dake Kewaye Da Unguwannin Nasu Ya Na Cinye Masu Gidaje, Al'ummar Unguwar Sun Ce Suna Fatan Mai Girma Gwamnan jihar Zai Hada Wannan Aikin Da Aikin Titin Da Za a Gabatar Daga CPS Zuwa Kofar Yandaka.

Sun Bayyana Cewa Idan Aka Gabatar Da Rusan Aikin Gida 2 Ne Kacal Zai Rage Tsakanin Titin Da Wannan Tabkin Mai Cinye Masu Gidaje, Daga Karshen Al'umma Sun Ce Sun Sadaukar Da Filin Tabkin Idan Aka Cike Ga Gwamnati Ta Yi Makaranta Ko Asibiti Domin Amfanin Jama'a. Sun yi Addu'a Ga Fatan Alkhairi Ga Gwamnatin Malam Dikko Umar Radda Da Kuma Shugaban karamar hukumar Katsina Malam Isa Miqdad AD Saude.

Rahoton
Jaridar YTD Hausa

Yanzu-Yanzu Gwamnan Jihar Katsina Malam Umar Dikko Radda Ya Kai Ziyarar Jaje Garin Mantau Ta Ke Karamar Hukumar Malumfas...
27/08/2025

Yanzu-Yanzu

Gwamnan Jihar Katsina Malam Umar Dikko Radda Ya Kai Ziyarar Jaje Garin Mantau Ta Ke Karamar Hukumar Malumfashi. Bayan Ya Dawo Daga Hutu.

Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda Ya Katse Hutun Da Ya Je Kasashen Waje Ya Dawo Nigeria Cikin Gaggawa Domin T...
27/08/2025

Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Umar Radda Ya Katse Hutun Da Ya Je Kasashen Waje Ya Dawo Nigeria Cikin Gaggawa Domin Tunkarar Matsalar Tsaro Da Ke Addabar Jihar Katsina.

Gwamna Radda Ya Iso Najeriya, Ya Jagoranci Muhimmin Taron Tsaro a Abuja.Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ...
26/08/2025

Gwamna Radda Ya Iso Najeriya, Ya Jagoranci Muhimmin Taron Tsaro a Abuja.

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya dawo Najeriya daga ƙasashen waje inda ya tafi domin yin duba lafiyar da yake yi lokaci zuwa lokaci. Ya sauka a Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja da misalin ƙarfe ɗaya na dare (1:00am), sannan daga nan kai tsaye ya wuce Katsina House da ke babban birnin tarayya.

A can ne Gwamna Radda ya jagoranci wani muhimmin taron tsaro a rufe, wanda ya haɗa dukkan sanata uku da ke wakiltar Jihar Katsina a majalisar dattawa, tare da dukkan mambobin majalisar wakilai na tarayya daga jihar.

Wannan babban taro ya mayar da hankali kan matsalolin tsaro da ke addabar Katsina, tare da tattaunawa kan irin matakan haɗin gwiwar da ake buƙata domin fitar da mafita ga waɗannan ƙalubale.

Taron ya samu halartar manyan ‘yan majalisa daga jihar, ciki har da sanata ukun, da dukkan mambobin majalisar wakilai, tare da mai magana da yawun jam’iyyar APC na Katsina, Alhaji Shamsu Sule Funtua.

Gwamnatin Nijeriya ta gabatar da mutum 128 da ta ce ta yi nasarar kuɓutarwa daga hannun ‘yan bindiga a Kaura Namoda da k...
26/08/2025

Gwamnatin Nijeriya ta gabatar da mutum 128 da ta ce ta yi nasarar kuɓutarwa daga hannun ‘yan bindiga a Kaura Namoda da ke jihar Zamfara. Babban Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Tsaro Mallam Nuhu Ribadu ne ya gabatar da mutanen da aka ceto ɗin ga manema labarai a Abuja a ranar Talata, yana mai cewa za a kula da lafiyarsu da kuma ba su tallafi don komawa cikin iyalansu da al'ummominsu.

Wasu Matasa a Katsina Sun Shirya Gangamin Share Makarantar Primary.A madadin Kungiyar Muryar Cikin Birni Youth Organizat...
26/08/2025

Wasu Matasa a Katsina Sun Shirya Gangamin Share Makarantar Primary.

A madadin Kungiyar Muryar Cikin Birni Youth Organization tana gayyatar dukkan matasan yankin Wakilin Yamma II domin gudanar da aikin tsaftace makarantar firamare ta Gafai.

🗓️ Lokaci: 10:00am
📍 Wuri: Gafai Primary
🕐Rana: Asabar 30-08-2025

Manufar wannan aiki ita ce:

-Haɗa hannu wajen tsaftace muhalli.

-Kiyaye lafiya da tsaftar makaranta.

-Samar da kyakkyawar makoma ga ‘ya’yanmu.

Kira gare ku matasa da al’umma gaba ɗaya:

-Zo mu haɗu, mu yi aiki tare – domin al’umma mai tsabta da lafiya! ✊

Ga dukkan mahalar zuwa wannan aiki don Allah zaku iya zuwa da tsintsiyu ko shebura domin sauƙaƙa wannan aikin

Allah ya bamu ikon halarta Amin

Fahad Aliyu
P.R.O


Shugaban hukumar kare muhalli ta jihar Katsina, Alhaji Kabir Usman ya gwangwaje al’ummar unguwar Filin Kanada da sabuwar...
26/08/2025

Shugaban hukumar kare muhalli ta jihar Katsina, Alhaji Kabir Usman ya gwangwaje al’ummar unguwar Filin Kanada da sabuwar gadar tsallaka lambatu ta zamani.

Me za ku ce?

Da Dumi-Dumi- Kotun majistare ta Tarayya a Abuja ta umurci bankuna shida su bai wa babban Sufeton ‘yan sanda (IGP) bayan...
26/08/2025

Da Dumi-Dumi- Kotun majistare ta Tarayya a Abuja ta umurci bankuna shida su bai wa babban Sufeton ‘yan sanda (IGP) bayanan cikakkun takardun asusun kuɗi da dukkan mu’amaloli, ciki har da shigowa da fita, da s**a danganci Omoyele Sowore daga watan Janairu 2024 zuwa yanzu.

An Fara Gabatar Da Ranar Hausa Ta Duniya a Daura, Mai Martaba Sarkin Daura, Dr Umar Faruk Umar wajen bikin ranar Hausa t...
26/08/2025

An Fara Gabatar Da Ranar Hausa Ta Duniya a Daura, Mai Martaba Sarkin Daura, Dr Umar Faruk Umar wajen bikin ranar Hausa ta duniya

📷 RFI Hausa

Yanzu Yanzu: Jirgin Ƙasa Daga Abuja Zuwa Kaduna Ya Turguɗe Ya Sauka Kan Layi....A yau Talata yayinda jirgin ƙasa daga Ab...
26/08/2025

Yanzu Yanzu: Jirgin Ƙasa Daga Abuja Zuwa Kaduna Ya Turguɗe Ya Sauka Kan Layi....

A yau Talata yayinda jirgin ƙasa daga Abuja yake kan hanyar shi ta zuwa Kaduna Ya samu damuwa inda ya Turguɗe ya sauka daga kan hanyar shi.

Kawo yanzu dai babu tabbacin samun raunika domin ba'a fitar da wata sanarwa ba .

Allah ya kyauta gaba Amin

26/08/2025

Ƴan Bindiga Sun Dauki Miji Da Mata Mai Ciki Tare Diyarsu, Sun Kashe Mutum Ɗaya a Cikin Garin Katsina.
Jaridar YTD Hausa Ta Zanta Da Mai Unguwar Da Yan Bindigar Su Ka Shiga Cikin Daren Jiya.

Kamar Yadda Za Ku Ji Daga Bakin Shi.

DA ƊUMI-ƊUMI: Daga ƙarshe dai Ruƙayya Muhammd, Matashiyar da ta yi alƙawarin ba da kyautar kuɗi Naira Miliyan 50 da gida...
16/08/2025

DA ƊUMI-ƊUMI: Daga ƙarshe dai Ruƙayya Muhammd, Matashiyar da ta yi alƙawarin ba da kyautar kuɗi Naira Miliyan 50 da gida da mota ga wanda zai aure ta, ta yi aure. Muna fatan Allah Ya su zaman lafiya.

Wane fata za ku yi mata ?DA ƊUMI-ƊUMI: Daga ƙarshe dai Ruƙayya Muhammd, Matashiyar da ta yi alƙawarin ba da kyautar kuɗi Naira Miliyan 50 da gida da mota ga wanda zai aure ta, ta yi aure. Muna fatan Allah Ya su zaman lafiya.

Wane fata za ku yi mata ?

Address

Filin Polo Bayan Masallacin Hassan Da Husaini, Katsina State, Nigeria
Katsina
820252

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when YTD Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share