04/03/2025
Ɗan Majalisar Tarayya Mai Wakiltar Ƙananan Hukumomin Kurfi da Dutsanma ya gwangwaje Dagattai da Babura, ya raba dubban buhunan shinkafa, Taliya da Makaroni
Ɗan Majalisar Tarayya Mai Wakiltar Ƙananan Hukumomin Kurfi da Dutsanma Hon. Aminu Belele Ɗan Arewa ya bayar Mashina 30 ga dagattan Kurfi da Dutsanma dukkanin su.
Haka zalika, Aminu Belele Ɗan Arewa ya bayar da buhu dubu 3000 na shinkafa da Makaroni dubu 3000, da kuma taliya dubu 3000 gami da kuɗaɗe ga Al'umma domin su gudanar da Azumin su cikin sauƙi.
Shugaban Ma'aikatan Fadar Gwamnatin Jihar Katsina Hon. Abdulkadir Mamman Nasir ya ƙaddamar da bayar mashinan ga dagattan gami da shinkafa ga al'umma.
A jawabinsa, Shugaban Ma'aikatan Fadar Gwamnatin Jihar Katsina Hon. Abdulkadir Mamman Nasir ya bayyana cewa Gwamna Dikko yana yaba mashi kan yadda yake taimakawa al'ummar sa domin shaida Kyakkyawan shugabanci.
A jawabinsa, Hon. Aminu Belele Ɗan Arewa ya bayyana cewa zai sake gina wasu Masallatai na fada dana bakin Kasuwa a Dutsanma domin gudanar da ibada.
Aminu Belele Ɗan Arewa yace zai kuma sake gina gidajen sarauta na Dagattai daga faɗin ƙananan hukumomin, inda zai fara dana garin Tsauri kafin sauran wuraren.
Sauran waɗanda s**a tofa albarkacin bakinsu akwai mai ba Gwamna Shawara kan siyasa Hon. Ya'u Umar Gwajo-Gwajo da Ɗan masanin Kurfi da Shugaban ƙaramar hukumar Mannir Shehu Wurma da shugaban Jam'iyyar APC da sauran su.Ɗan Majalisar Tarayya Mai Wakiltar Ƙananan Hukumomin Kurfi da Dutsanma ya gwangwaje Dagattai da Babura, ya raba dubban buhunan shinkafa, Taliya da Makaroni
Ɗan Majalisar Tarayya Mai Wakiltar Ƙananan Hukumomin Kurfi da Dutsanma Hon. Aminu Belele Ɗan Arewa ya bayar Mashina 30 ga dagattan Kurfi da Dutsanma dukkanin su.
Haka zalika, Aminu Belele Ɗan Arewa ya bayar da buhu dubu 3000 na shinkafa da Makaroni dubu 3000, da kuma taliya dubu 3000 gami da kuɗaɗe ga Al'umma domin su gudanar da Azumin su cikin sauƙi.
Shugaban Ma'aikatan Fadar Gwamnatin Jihar Katsina Hon. Abdulkadir Mamman Nasir ya ƙaddamar da bayar mashinan ga dagattan gami da shinkafa ga al'umma.
A jawabinsa, Shugaban Ma'aikatan Fadar Gwamnatin Jihar Katsina Hon. Abdulkadir Mamman Nasir ya bayyana cewa Gwamna Dikko yana yaba mashi kan yadda yake taimakawa al'ummar sa domin shaida Kyakkyawan shugabanci.
A jawabinsa, Hon. Aminu Belele Ɗan Arewa ya bayyana cewa zai sake gina wasu Masallatai na fada dana bakin Kasuwa a Dutsanma domin gudanar da ibada.
Aminu Belele Ɗan Arewa yace zai kuma sake gina gidajen sarauta na Dagattai daga faɗin ƙananan hukumomin, inda zai fara dana garin Tsauri kafin sauran wuraren.
Sauran waɗanda s**a tofa albarkacin bakinsu akwai mai ba Gwamna Shawara kan siyasa Hon. Ya'u Umar Gwajo-Gwajo da Ɗan masanin Kurfi da Shugaban ƙaramar hukumar Mannir Shehu Wurma da shugaban Jam'iyyar APC da sauran su.