Katsina Post HAUSA

Katsina Post HAUSA KATSINA POST HAUSA is a news medium based in Katsina State.

Katsina Post HAUSA kafar yada labarai ne da take maida hankali wajen fadakar da mutanen Katsina, Arewa da kuma Najeriya musamman ta fannin kawo masu ingantattun labarai kuma sahihai.

16/07/2026

Kai tsaye Karatun Alkur’ani mai girma na Manyan Gwanayen Alkur’ani daga gidan Alh. Audun Malam Kadimul Qur’an.

Daga ina kuke kallon mu?

Hukumar Samar da Hanyoyin Karkara da Bunƙasa Kasuwancin Amfanin Gona ta Jihar Katsina (RAAMP) ta gudanar da gangamin way...
23/06/2026

Hukumar Samar da Hanyoyin Karkara da Bunƙasa Kasuwancin Amfanin Gona ta Jihar Katsina (RAAMP) ta gudanar da gangamin wayar da kan al'ummar Ƙaramar Hukumar Ɗanja kan dokokin hanya da ababen sufuri

A cikin wasu shirye-shiryen da hukumar ta gudanar na tsawon kwanaki biyu, wato ranakun 22 da 23 ga watan Yuni, 2026, a ranar Talata 23 ga watan Yuni ta gudanar da gangamin wayar da kan al'umma game da dokokin hanya da kuma amfani da ababen hawa a garin Ɗanja, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Ɗanja ta jihar Katsina.

Hukumar ta haɗa gwiwa da wasu hukumomi da s**a haɗa da Hukumar Kiyaye Haɗurran Hanya ta Ƙasa (FRSC) reshen jihar Katsina, Hukumar Kula da Kiyaye Hanyoyi da Ababen Hawa ta Jihar Katsina, Hukumar VIO, Ƙungiyar Direbobi ta Ƙasa reshen Ɗanja, Ƙungiyar Direbobin Manyan Motoci, da kuma Ƙungiyar Masu Hayar Babura ta Ɗanja.

An gudanar da gangamin wayar da kan al'umma a Babbar Tashar Motoci ta Ɗanja, Makarantar Riyadu Nursery and Primary School, Tsintsiya Primary School, Doka Primary School, da kuma Government Pilot Junior Secondary School Bazanga.

A yayin da yake jawabin buɗe taron, Babban Sakataren Ma'aikatar Raya Yankunan Karkara da Kyautata Rayuwar Al'umma, Alhaji Muntari, ya gode wa al'ummar Ɗanja bisa tarbar da s**a yi wa tawagar da kuma haɗin kan da s**a bayar domin ganin an gudanar da shirin cikin nasara. A ƙarshe ya yi addu'ar Allah Ya sa a kammala lafiya.

Kwamandan Hukumar Kiyaye Haɗurran Hanya ta Ƙasa (FRSC) shiyyar Malumfashi, Alhaji Sale Ado, yayin da yake gabatar da maƙala kan alamomin hanya, ya yi bayani kan yadda masu tuƙi, masu tafiya a ƙasa da ɗalibai za su yi amfani da dokokin hanya da alamominta domin kauce wa haɗurra da kuma rage aukuwarsu.

Haka kuma, ya ja hankalin direbobi kan illar ɗaukar fasinjoji fiye da ƙa'ida, da kuma haɗa mutane da dabbobi ko wasu kayayyaki a cikin mota guda. Ya kuma yi ƙarin haske kan irin gudunmawar da al'umma za ta bayar wajen rage aukuwar haɗurran hanya.

Shi ma a nasa jawabin, shugaban Hukumar VIO ta Jihar Katsina, Alhaji Sama'ila Idris, ya yi magana kan yadda yanayin tuƙi ke sauyawa musamman a lokacin damina da kuma lokacin rani. Ya kuma yi bayani kan dokar hana ɗaukar fasinjoji fiye da ƙima da kuma hana rufe lambobin ababen hawa, yana mai cewa gwamnati ta ɗauki mataki kan masu aikata hakan, ciki har da 'yan siyasa.

Ya ƙara da cewa a ƙarƙashin jagorancinsa, hukumar ba ta amince da cin zarafin direbobi daga jami'anta ba, kuma duk jami'in da aka samu da laifin cin mutuncin direba za a hukunta shi bisa doka.

Haka zalika, Shamshu Hamisu, shugaban Hukumar Kiyaye Hanyoyi da Ababen Hawa ta Jihar Katsina reshen Ɗanja, ya bayyana cewa gwamnatoci na kashe kuɗaɗe masu yawa wajen gina sabbin hanyoyi da gyaran tsofaffi. Ya ce idan gwamnati na yin wannan ƙoƙari, ya kamata al'umma su ma su kula da hanyoyin da kuma ababen hawansu. Ya kuma jaddada muhimmancin ayyukan hukumar wajen kare rayuka da dukiyoyin al'umma.

Wakiliyar Jami'in Tuntuɓa Kan Ayyukan Kiyaye Haɗurra, Engr. Okwudili N. Ikejiani, ta ja hankalin direbobi da su yi amfani da hotunan alamomin hanya da aka raba musu domin ƙara fahimta da ilimi, tare da gargadin kada a mayar da su kayan ado ko abin rufe tagogi da ƙofofi.

Shugaban Ƙungiyar Direbobi ta Ƙasa reshen Ɗanja, Alhaji Ɗanlami, ya nuna godiyarsa bisa wannan horo da aka ba su, yana mai cewa zai taimaka musu wajen kare kansu, fasinjojinsu da kuma ababen hawansu daga haɗurra.

A nasa jawabin rufe taro, shugaban Ƙungiyar Masu Hayar Babura ta Ɗanja, Alhaji Sama'ila Sani, ya gode wa Hukumar RAAMP da sauran hukumomin da s**a shirya wannan gangami, yana mai bayyana cewa shirin zai taimaka matuƙa wajen wayar da kan al'umma kan muhimmancin bin dokokin hanya da kiyaye haɗurran ababen

10/06/2026

J

Tabbas mun yi babban rashi na dattijo, malami, masanin fiqhu, kuma jajirtacce, mai amana - Inji Sheikh Dr. Abdullahi Bal...
26/01/2026

Tabbas mun yi babban rashi na dattijo, malami, masanin fiqhu, kuma jajirtacce, mai amana - Inji Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau

Shugaban Kungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa Ikamatis Sunnah na Kasa Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau ya shigo garin Katsina a ranar Asabar domin kara yi ma shuwagabanni da iyalai ta'aziyyar rasuwar Sheikh Habibu Yahayya Kaura wanda Allah yayi ma rasuwa a daren ranar Laraba din da ta gabata aka kuma yi jana'izar shi a ranar Laraba a hedkwatar Kungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa Ikamatis Sunnah ta kasa da ke Abuja

Wanda tun bayan rasuwar ya turo Shugaban Majalisar Malamai na Kasa Sheikh Dr. Ibrahim Jalo Jalingo da Sakataren Kungiyar na Kasa Sheikh Dr. Muhammad Kabir Haruna Gombe domin zuwa su samu Shugaban Kwamitin Amintattun Kungiyar, Daraktan Da'awah na Kasa kuma Shugaban Kungiyar na Jihar Katsina Sheikh (Dr.) Yakubu Musa Hassan Katsina Sautus-Sunnah domin jajantawa juna da yin ta'aziyya ma juna bisa wannan babban rashi

Haka shi ma bayan ansar baki da ke zuwa yin ta'aziyya a hedkwatar Kungiyar a Abuja ya baro Abuja ya shigo Katsina tare da tawagar shi a ranar Asabar domin haduwa da Shugaban Majalisar Malamai da Sakatare

Yayin da tawagar Shugaban, ta isa gidan Sheikh Habibu Yahayya Kaura da yake jawabi Sheikh Abdullahi Bala Lau ya bayyana cewa "babu shakka mun yi babban rashi na dattijo, malami, masanin fiqhu, kuma jajirtacce, mai amana

Sheikh Habibu Yahayya Kaura Allah ya gafarta ma shi, Allah yasa ya huta, Allah ya jikanshi da rahama. Babu shakka ba iyalansa ne kadai su kai wannan rashi ba, mu a wannan kungiya ta Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa Ikamatis Sunnah mun yi babban rashi

Duk wanda zai ambaci Sheikh Habibu Yahayya Kaura zai ambace shi da amana da ayyuka na alkhairi, duk wanda ya san shi ya san mutun ne da ke in zai gaya maka magana ba boye boye babu mujamala, abinda ke cikin ransa, abinda ya gani zai nuna maka domin gyara

Duk lokacin da ya turo sako zai zamanto sako ne na fadakarwa, shawara kuma ba mu da wani malami da yake tsayawa yana kallon Manara TV ya ga ko wane malami aka saka wane irin gyara ya kamata, wace irin shawara za'a ba shi

Duk lokacin da wani abu ya taso a kungiya ta ke neman wata shawara ko abinda zai haifar da rigingimu a cikin al-umma, yana daya daga cikin wadan da za su bada shawarar meye ya kamata ayi

Aikin sa na karshe shi ne sulhu da muka tura shi yayi a garin Funtua akan wani abu da ke faruwa, bayan mun tattauna da Shugaban Jihar Katsina Sheikh Yakubu Musa mun yanke tura kwamiti domin zuwa a tattauna kuma samar da mafita akan abinda ya faru. Sheikh Habibu Yahayya Kaura jagoranci kwamitin sun je an zauna an tattauna har an rubuta rahoto, amman bai iya mika mana rohoton ba, saboda yana sauka ya gamu da wannan ciwo wanda kuma yana ji ya kira waya tace yaji wani abu a jikinshi da baya tsammanin zan iya rayuwa

Nayi ma shi addu'ar Allah ya ba shi lafiya. Bayan an kwana daya ya turo sakon murya yace ina bar maku wasiya ina fatan wasiya ta ce itace ku tsaya kan littafin Allah da sunnar Annabi (S.W.A) duk yadda za'ayi shugaba kada ku canza daga wannan manhaji itace hanyar da zata kai mu ga tsira. Wannan shi ne maganar shi ta karshe tsakanin mu, bayan kwana biyu jiki yayi zafi. Wanda daga nan aka cigaba da jinya har zuwa lokacin da Allah yayi ma shi rasuwa"

Daga nan Sheikh (Dr.) Yakubu Musa Hassan Katsina (Sautus-Sunnah) a madadin iyalan Sheikh Habibu Yahayya Kaura da Kungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa Ikamatis Sunnah ta Jihar Katsina , yayi godiya ga Shugaba Sheikh Abdullahi Bala Lau bisa kulawa da dawainiyar da su kai tun farkon fara wannan jinya har zuwa yanzu da muke ma juna ta'aziyya

Bayan nan Sheikh Sautus-Sunnah ya jagoranci Shugaba Sheikh Abdullahi Bala Lau da tawagarsa domin shiga cikin gida wajen iyalai da yan'uwan Marigayi Sheikh Habibu Yahayya Kaura domin yi ma juna ta'aziyya a madadin wannan Kungiya ta Kasa baki daya

Haka kuma bayan fitowa daga cikin gidan Shugaban Kungiya na Kasa Sheikh Dr. Abdullahi Bala Lau ya gabatar da sakon godiya a madadin Kungiyar Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa Ikamatis Sunnah ta tarayyar Najeriya baki daya kamar haka

"A madadin wannan Kungiya ta mu ta Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa Ikamatis Sunnah ta kasa baki daya a madadin shugabanni, madadin kuma iyalai na marigayi Sheikh Habibu Yahayya Kaura wanda nan muna gidansa bayan mun shiga zuwa ga iyalinsa, bayan kuma mun yi ta'aziyya ga sauran yan'uwa bayan mun mika ta'aziyyar mu ga kowa da kowa daga cikin al-ummar mu na wannan kasa harma da makwabtan mu

Bayan godiyar ga Allah (S.W.A) muna isar da godiya ta musamman ga Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu da ya aiko da tawaga ta musamman domin zuwa ayi mana ta'aziyya, a tausaya mana saboda wannan gibi da rashi babba da wannan Kungiya tayi

Mai Girma Shugaban kasa muna godiya, tawagar da ka turo sun zo, Allah ya saka da alkhairi, ya bar zumunci. Haka ya kamata duk lokacin da aka shiga damuwa a nuna mana tausayi domin nuna ana jagorantar mu, kuma ana mana yadda ya kamata don bada hakkin da mu ke da shi a jagorancin

Bayan haka muna godiya ga mai girma gwamnan Jihar Katsina Dikko Umar Radda. Gwamnan Jihar Katsina ya cancanci ayi ma shi godiya ta musamman Allah ya saka ma shi da alkhairi. Tun farkon lokacin da Sheikh Habibu Yahayya Kaura yayi kwanciyar rashin lafiya, yayi iya kokari na ganin duk abinda za'ayi na jinya a nan Katsina ya dauki dawainiya

Lokacin da Kungiya tace a maido shi Abuja nan ma yace a Abuja din zai bada gudummuwar da za'a kai shi asibitin Nizamiye, mu kuma mun ce a kawo shi asibitin kasa (National Hospital) amman duk da haka yace tunda mun ce akai can ya hakura a je can. Saboda haka an je asibitin kasa amman daga karshe an koma Nizamiye wanda ya koma ya cigaba da daukar dawainiya nauyin dukkan abinda aka kashe har zuwa lokacin karshen rayuwarsa

Mai girma gwamna muna godiya Allah ya saka da alkhairi, gudummuwar da aka bayar da kuma kokarin da ake niyyar cigaba da kara tallafama gidan, da sanya yaran kan hanya, da ma ba su abinda za su yi na sana'a ko shigar da su ayyuka da aka ce za'ayi daga gareka da kuma sauran abokanan ka. Muna godiya

Haka kuma muna godiya ga Sanata Abdulaziz Yari Abubakar, Hon. Abdulmalik Zannan Bungudu bisa irin gudummuwar da su ka bada wurin samar da kokari a dawo da abinda ake iya yi da hali a lokacin da Sheikh yake da rai da kuma irin gudummuwar da su ka bada domin tallafama gidan, Allah ya saka masu da alkhairi da sauran daidai kun da su ka bada gudummuwa ta dukiya don tallafawa wurin jinya, sannan bayan baya raye su ka bada gudummuwa da tallafi don tausayawa gidan. Muna addu'a duk wanda ya bada gudummuwa Allah ya saka ma shi da alkhairi

Alh. Ibrahim Masari mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin siyasa yazo asibiti ya duba duk abinda ya kamata ayi ana yi har ma ya bada tabbacin cewa idan da halin a dauke shi zuwa kasar waje duk za su dauki dawainiya sai dai yana yin jikin ba zai bari ba ayi haka kuma daga lokacin da ake jinya har zuwa bayan rasuwar har zuwa wannan lokaci duk irin gudummuwar da ya kamata ya bayar, yayi iya kokarin shi, shi da sauran abokanan shi irinsu gwamnan Yobe Mai Mala Buni da sauran wadan da ya kamata ace sun bada tallafi da gudummuwa. Muna godiya Allah ya saka da alkhairi

Tsohon gwamnan Katsina Rt. Hon. Aminu Bello Masari shi ma da shi akai duk abinda ya kamata ayi. Allah madaukakin sarki ya saka da alkhairi

Akwai kuma wadanda su ma sun bada gudummuwa wadan da ba zamu iya tunawa ba kowa da irin abinda ya bayar na gudummuwa da wadan da su kai addu'o'i da wadan da kuma su ka zo su kai mana ta'aziyya daga Janhuriyar Niger da sauran kasashe makwabta da nan cikin gida Najeriya da Shuwagabannin wannan Kungiya na Jihohi kowa yayi iya abinda ya kamata

Ba za mu gushe ba shugaban wannan Kungiya ta Jihar Katsina Sheikh Dr Yakubu Musa Hassan Katsina Sautus-Sunnah kuma Daraktan Da'awah wajen tsayawa da jajircewa da yayi wajen ganin duk abinda ya kamata ayi wa Sheikh Habibu Yahayya Kaura yana raye an yi da kuma abinda ya kamata ayi na kulawa da gidan muna mashi addu'ar Allah ya saka mashi da alkhairi, Allah ya bada ikon kulawa, Allah ya sanya albarka

Daga karshe ina kira ga 'ya'yan sa da sauran makwabta da al-umma baki daya a cigaba da addu'a Allah ya gafarta ma Sheikh Habibu Yahayya Kaura. Sannan duk inda ya ke da zumuncin da yake sadarwa a cigaba da sadar da shi

Kuma wannan kungiya ba zata manta da shi ba kuma kaman yadda ta ke kulawa da sauran gidajen na marigaya hakan za mu cigaba da kulawa mu GA abinda ke gudana cikin wannan gidaje

Ina addu'a Allah maɗaukakin sarki ya gafarta ma Sheikh Habibu Yahayya Kaura, Allah kada ya jarabci bayansa, Allah ya kyautata karshen mu baki daya, Allah ya kara sanya mana albarka, Jihar Katsina da sauran jahohin mu Allah ya kara tabbatar mana da zaman lafiya"

Daga karshe Shugaban ya jagoranci tawagar domin zuwa dubiyar jinya ga Mataimakin Shugaban Majalisar Malamai na Kasa Sheikh Barr. Ibrahim Sabi'u Jibia ya ke yi a gida sanadiyyar kara da ya samu a kafarsa

Shugaban ya duba jikin na shi tare da yi mashi addu'ar kara samun lafiya

08/01/2026

"Tunda Akayi Jihar Katsina Ba'a Taɓa Gwamna Irin Malam Dikko Umar Radda Ba" - Inji- GM Usman Rabi'u Mahuta

Kwamishinan Muhallin Jihar Katsina, Sadaukin Kasar Hausa Hon Hamza Sulaiman tare da ɗumbin tawagarsa daga Katsina sun ha...
04/01/2026

Kwamishinan Muhallin Jihar Katsina, Sadaukin Kasar Hausa Hon Hamza Sulaiman tare da ɗumbin tawagarsa daga Katsina sun halarci bikin naɗin sarautar amininsa Sulaiman S Rubadu a Adamawa

Kwamishinan muhallin jihar Katsina, Hon Hamza Sulaiman Wamban Faskari kuma Sadaukin Ƙasar Hausa, ya niƙi gari daga Katsina zuwa jihar Adamawa tare da tawagarsa domin sada zumunci ga babban amininsa da ƙud-da-ƙud Sulaiman S Ribadu (Amir) da Lamidon Fufore ya naɗa a matsayin Gwagware

Haka kuma kwamishinan ya shedi bikin nadin uwa a gare shi wato, Hajiya Zara Nuhu Ribadu (Amma) da aka naɗa a matsayin Sarauniyar Belel da kuma Gimbiyar Kolkol

Kwamishinan ya roki Allah Ya yi masu jagoranci wajen wannan babban jagorancin al'umma da aka ɗora masu

Address

Katsina Motropholis
Katsina
234

Telephone

+2348067205524

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina Post HAUSA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Katsina Post HAUSA:

Shortcuts

Share