26/04/2026
Littafi mai tuna muna da lokacin ƙuruciya ! Wai ko kun san cewa:
1- Mawallafin littafin "Al-arabiyyatul Jadidah Fi Nijeriya" wanda aka fi sani da Littafin "Bāri wa Biba" shine Sarkin Kazaure mai martaba Mallam Hussaini Adamu, Wanda mahaifine ga Sarkin Kazaure na yanzu, an fara buga littafin a 1979
2- Yayi karatu a "School Of Arabic Studies Kano" S.A.S, yayi zamani da su Abubakar Imam da Sa'adu Zungur, ya zama Sarki a 1994 ya rasu a 1998
2- A littafan da aka rubuta cikin gida Najeria na shashen Larabci babu littafin da yayi shaharar littafin "Bāri wa Biba" daga samun ƴancin kai zuwa yanzu
3- Littafin akwai na 1 zuwa na 6 a iya sanina, Kuma shekarar Littafin 47 cib
4- Allah Sarki na san za ka tuna shekarun ƙuruciya ko 💔🥲 ? A wace Islamiyyah aka karantar da ku Littafin Bāri wa Biba ? Kuma wane Malami ne ya karantar da ku shi ?
(Garkuwan Ustazan Islamiyyah)
Shugaban tafiyar Ustazu tsaya da ƙafarka
Abdulkarim Hamisu Assuyudiw