18/08/2026
KARE KAI UMARNI NE DAGA ALLAH
Na kalli wani bidiyo da ya sani damuwa, wani dan iska ne rike da wata sharbebiyar wuka yana ikrarin sai ya dauki raยฅuwar Sheikh Bello Murtala Asada
Allah Madaukakin Sarki ya umarce mu a cikin Al-Qur'ani Maigirma Suratu Anfal aya ta 60, Allah (T) yace:
ูุฃุนุฏูุง ููู
ู
ุง ุงุณุชุทุนุชู
ู
ู ููุฉ...
Ma'ana: mu yi tanadin (makamai) kowani iri masu karfi...(don abokan gaba)
Ba daidai ba ne Malamanmu su zauna kamar alalen 'yan iska, ana salwantar da rayukansu masu daraja a banza ba tare da kariya ba, a irin haka muka rasa irinsu Sheikh Ja'afar, Malam Albaniy Zaria, Dan Mashiyya Sokoto (Allah Ya jikansu)
Malami mutum ne mai tsada da daraja a cikin alโumma, yana koyar da addini, tarbiyya da zaman lafiya, tabbatar da tsaron rayukansu abune mai matukar amfani
Ba daidai bane sai Malami ya girma, ya sha wahala da gwagwarmaya ya tara ilimi da zai amfanar da al'umma, sai rana tsaka a turo wasu 'yan iska makiya su salwantar da rayuwarsa, dole a basu kariya, ko kuma a barsu su mallaki abinda zasu kare kansu kamar yadda marigayi Sheikh Dr Idris Abdul-Aziz yayi
Dokar Nigeria ya bada damar a mallaki bindiga, ba sai Malami ba, duk wanda yake da bukata ya bi tsarin da doka ya tanadar ya mallaki bindigar da zai kare kansa, kar ka yadda wasu 'yan iska su zo su bugeka a banza su gudu
Sheikh Murtala Asada ya burgeni sosai da ya mallaki bindigarsa kuma ya nuna wa duniya, masu tunanin zasu kashe Malam su tsira sun yaudari kansu, duk wanda ya shirya tunkarar Malam da wata cutarwa to ya shirya barin duniya
Muna rokon Allah Ya tsare mana rayuwar Sheikh Asada