Nigerian Poll

Nigerian Poll Kafar watsa Labarai ce mai zaman kanta da aka samar domin watsa labarai da rahotanni na gaskiya.

ABUJA
05/08/2024

ABUJA

Waye dan jarida? Menene aikin dan jarida? Wanda ya rubuta ✍️ Comr Abba Sani Pantami Waye dan jarida? Dan jarida shine ma...
03/05/2024

Waye dan jarida? Menene aikin dan jarida?

Wanda ya rubuta ✍️
Comr Abba Sani Pantami

Waye dan jarida?

Dan jarida shine mai nemo labarai yana yadawa a gidajen jaridu, gidajen Talabijin, gidajen Rediyo da kuma kafofin sada zumunta.

Akwai dan jarida mai zaman kansa akwai masu yiwa gidajen jaridu da kuma kafar yada labarai, ta Rediyo ko Talabijin aiki.

Menene aikin dan jarida?

Aikin jarida ya kasu kashi-kashi, gasu kamar haka;

1, Akwai mai rubutu da nazarin labarai.

2, Akwai wanda ke gabatar da labarai a gidajen Rediyo da Talabijin da kuma gidajen jaridun kafofin sada zumunta.

3, Akwai mai dauko rahoto daga nesa, daga gidajen Rediyo ko Talabijin ko daga gidajen jaridun kafofin sada zumunta ko daga wani gari mai nisa koma daga wata kasar.

4, Akwai wanda shi aikinsa duba kuskuren rubutu da duba gyare-gyaren yadda labari yake.

5, Akwai wanda ke gabatar da labarai da hira da mutane a jaridun kafofin sada zumunta da gidajen Rediyo da Talabijin da sauran shafukan sada zumunta.

6, Akwai dan jarida mai daukar hoto da bidiyo.

7, Akwai mai dauko rahoto daga lungu da sako na dukkannin abubuwan da ke faruwa a cikin gida.

8, Akwai dan jarida wanda yake bincike kuma ya rubuta rahoto.

9, Akwai dan jarida mai sharhi a kafofin sada zumunta ko rubuta sharhi a gidajen jaridu da kafofin sada zumunta.

10, Akwai kwararran dan soshiyal midiya da yake rikidewa ya koma dan jarida a kafofin sada zumunta ba tare da ya karanci aikin jarida ba.

Jan hankali....

Dolene masu rubuta labarai da sharhi su zama masu fadin gaskiya, fadin gaskiya yana da matukar muhimmancin gaske ga aikin jarida.

Idan Dan jarida ya zama baya fadin gaskiya a labaransa ko kuma rahotanninsa to yakan fuskanci hukunci na dakatarwa ko ma kora baki daya.

'Yan jaridu masu dauko rahoto na fuskantar matsaloli da dama wajen dauko rahoto, sau da yawa 'yan jarida kan samu kawunansu a hadura, musamman ma wajen da ake samun rikicin ta'addanci ko fagen yaki.

Kasashe da dama suna ta daure 'yan jaridu har ma da kasar mu ta Najeriya.

Kai a matsayinka na dan soshiyal midiya, marubuci kuma dan jarida a wane sashi kake?

Kasar Senegal tayi watsi da faransanci ta maida harahen larabci a matsayin harshen da za'a dinga amfani dashi a hukumanc...
02/05/2024

Kasar Senegal tayi watsi da faransanci ta maida harahen larabci a matsayin harshen da za'a dinga amfani dashi a hukumance a kasar.

Uwar Dakin Fatima Maizogale Ta Sallame Ta, A Dalilin Waƙar Da Mawaƙi Rarara Ya Yi Mata
25/04/2024

Uwar Dakin Fatima Maizogale Ta Sallame Ta, A Dalilin Waƙar Da Mawaƙi Rarara Ya Yi Mata

Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Faruk Lawal Jobe (Sarkin Fulanin Joben Katsina) Ya Gana Da Dillalan Man Fetur D...
22/04/2024

Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina, Alhaji Faruk Lawal Jobe (Sarkin Fulanin Joben Katsina) Ya Gana Da Dillalan Man Fetur Domin Lalubo Hanyar Magance Matsalar Man Fetur A Jihar Katsina, Yau Lahadi.

08/04/2024

Bayan kasar Nijar babu wata kasa a Duniya da 'yan kasarta s**a yi ikirarin sunga wata sai Nijar kadai.

LABARIN GANİN WATAN RAMADANHar zuwa yanzu bamu samu labarin ganin jinjirin watan Ramadan a kasar Najeriya ba, duk wanda ...
10/03/2024

LABARIN GANİN WATAN RAMADAN

Har zuwa yanzu bamu samu labarin ganin jinjirin watan Ramadan a kasar Najeriya ba, duk wanda yake da masaniya ya gaggauta sanar mana, inji Fadar Sarkin Musulmi.

Ya KUKA ji lokacin da Facebook da Instagram s**a dauke?
05/03/2024

Ya KUKA ji lokacin da Facebook da Instagram s**a dauke?

04/03/2024

Daga fadar gwamnatin Kano, inda ake ganawa tsakanin gwamnan jihar Abba Kabir Yusuf, da Malam Aminu Daurawa, ƙarƙashin jagorancin kungiyar malaman jihar.

Modern journalists Madogara TV/Radio

YANZU-YANZU: Jama'ar gari sun daka wawa a rumbun ajiyar kayan abinci na NEMA a birnin tarayya Abuja, da safiyar yau Laha...
03/03/2024

YANZU-YANZU: Jama'ar gari sun daka wawa a rumbun ajiyar kayan abinci na NEMA a birnin tarayya Abuja, da safiyar yau Lahadi.

Mene ne kuka fi saurare?Yau ce ranar ji ta duniya da Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin wayar da kan al'umma kan mahi...
03/03/2024

Mene ne kuka fi saurare?

Yau ce ranar ji ta duniya da Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin wayar da kan al'umma kan mahimmancin kula da jinsu.

Gamayyar kungiyoyin kwadago a Najeriya na gudanar da zanga-zanga a kan tsadar rayuwa da ake fuskanta a kasar. Daruruwan ...
27/02/2024

Gamayyar kungiyoyin kwadago a Najeriya na gudanar da zanga-zanga a kan tsadar rayuwa da ake fuskanta a kasar.

Daruruwan mutane ne s**a fito a biranen Abuja da Legas da kuma Kano.

Address

Masanawa
Katsina

Telephone

+2349024825403

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Nigerian Poll posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to Nigerian Poll:

Share