06/10/2025
An yi zabe gami da rantsar da Sabbin shuwagabannin kungiyar masu kiwon kaji na kasa reshen jihar katsina (Poultry Association of Nigeria).
Mataimakiyar shugaban ƙungiyar masu kiwon kaji na ƙasa reshen jihar katsina da ke shiyar Daura ta yaba ma gudunmuwar da matar shugaban majalisar dokokin jihar katsina ke ba ƙungiyar.
Hajiya Basira A.J ta yi wannan yabon ne a lokacin zaɓen shugabannin ƙungiyar wanda ya gudana a dakin taron tsohon gidan gwamnatin jihar katsina a ranar 5 ga watan Oktoba, shakarar 2025.
Ta bayyana jindaɗi ga mai ɗakin shugaban majalisar dokokin jihar Katsina Hajiya Safa Nasir Yahaya Daura bisa bada gudunmawar kuɗi a lokacin taron ƙungiyar.
A lokacin taron dai, an zaɓi sabbin shuwagabannin ƙungiyar na ƙasa reshen jihar katsina.
Da yake jawabi, ɗaya daga cikin shuwagabannin ƙungiyar na ƙasa Alhaji Musa Gambo Danhassan ya yi fatan alkhairi ga shuwagabanni masu barin gado, sannan ya yi kira ga sabbin shuwagabanni suyi ƙoƙarin ganin sun ƙara ɗaga darajar ƙungiyar a idon duniya.
Haka kuma, ya yi kira ga masu kiwon kaji, kada tsadar kaji, abincin kaji da magungunan kaji ta hana su kiwon.
A nashi ɓangaren, uban ƙungiyar Alhaji Bature Usman 'Yankyaure ya nuna farin cikin shi tare da yaba ma kwamitin zaɓe bisa ƙoƙarin da s**a yi wajen ganin anyi sahihin zaɓe.
Alhaji Bature Usman 'Yankyaure ya yi kira ga 'yanƙungiyar da suyi biyayya gami da bada goyon baya ga sabbin shuwagabannin da aka zaba domin ciyar da ƙungiyar gaba.
Sannan ya yi kira ga sabbin shuwagabannin suyi adalci a cikin shugabancinsu.
A tsakaninshi, shugaban ƙungiyar mai barin gado Alhaji Haladu Ashiru Kofar Sauri ya yi godiya ga kwamitin da s**a shirya wannan zabe da kuma wakilan masu zabe.
Ya yi ƙarin haske a kan irin ƙalubalen da s**a fuskanta a lokacin da suke kan mulki, wanda ya shafi faɗuwa cikin sana'ar, tsadar abincin kaji da tsadar magungunan kaji.
Daga ƙarshe dai, ya yi kira ga gwamnati ta taimaka ta gina masu cibiyoyin kyankyasar kaji a cikin jihar Katsina.
Sakataren kuɗin ƙungiyar mai barin gado Alhaji Nura Danshehu ya yi bayani mai tsawo a kan abubuwan da s**a shafi asusun ƙungiyar tun daga lokacin da s**a amshi mulki a ranar 30/08/2025 har zuwa ranar saukarsu.
Taron dai ya samu halartar tsaffin shuwagabannin ƙungiyar, wakilan masu zaɓe daga ƙananan hukumomi 34, 'yanjarida, jami'an Tsaro, da dai sauransu.
Mutanen da aka zaba sune kamar haka:
1. Umar Abdullahi Yaya- (Chairman)
2. Abubakar Hussaini Yar'adua - (Vice Chair Katsina zone)
3. Hajiya Basira AJ- (Vice Chair Daura Zone)
4. Dr. Abdulaziz Najeem- (Vice Chair Funtua zone)
5. Arc. Buhari Sodangi- (Secretary General)
6. Ahmed Rabiu Dankoli- (Asst. Sec. General)
7. Hajiya A'ishah Clinic- (Financial Secretary)
8. Nura Danshehu Matazu- (Treasurer)
9. Aliyu Abdulkarim - (Auditor)
10. Sade Muhammad - (Organising Secretary)
11. Barr.Abdurrahman Umar- (Legal Adviser)
12. Hajiya Binta Dangani - (Women Leader)
13. Falalu Bature Kanada - (Youth Leader)
14. Bishir Salisu- (Public Relations officer (PRO)
15. Ibrahim Bature Darma- (Ex. Officio Katsina Zone)
16. Mu'awiya Ishaq- (Ex. Officio Daura Zone)
17. Ibrahim Mustapha Babashi-
(Ex. Officio Funtua zone
Aliyu isah Bature Director Hausa7 tv Chairman media Sa'in Hausa +2348034763879