
26/04/2025
Gwamnan jihar katsina Dikko Umar Radda, ya ƙaddamar da tawagar da zata jagoranci aikin hajjin wannan shekarar, ƙarƙashin mataimakin gwamnan jihar Malam garuk Lawal joɓe, Amirul hajji.
A jawabin shin na ƙaddamar war, gwamnan ya ambaci sunan shugaban majalissar dokoki ma jihar katsina, Alh Nasir Yahaya Daura, da kuma wakilai daga masarautun Katsina da Daura a matsayin mambobin tawagar.
Sauran mambobin sun haɗa da kwamishinan kula da harkokin Addinai, Alh Shehu Abubakar Dabai, mai bawa Gwamna shawara akan tu'ammalinda miyagun ƙwayoyi, da takwaransanna babban kotun jihar katsina, Mai shari'ah Aminu Tukur ƙofar Bai, da kuma shugaban Hukumar HISBAH, na jihar katsina, Aminu Usman Abu Ammar.
Gwamnan ya bayyana sunayen sauran mambobin tawagar, ta jihar katsina da s**a haɗa da shugaban Gidan Rediyon juhar katsina, Malam Lawal Attahiru Bakori, da Sheikh Nazir ƙofar Baru, da kuma Usman Abubakar da dai sauransu.
Haka kuma ƙa'idojin tsare-tsaren da aka sanya ga tawagar da zata jagoranci aikin hajjin, sun haɗa da kula, tareda bibiyar yadda Mahajjatan zasu gudanar da ayyukan su na hajji cikin nasara, daga nan Najeriya har zuwa a ƙasa mai tsarki.
Yace ya k**ata a tabbatar da kula lafiyar Mahajjatan, samar da wal-wala, da kuma mutuncin su anan Najeriya da kasa mai tsarki, da kuma tabbatar da tashin alhazan da dawowar su gida katsina cikin aminci.
Gwamnan ya bayyana gamsuwar sa akan ƙwazo da jajircewar tawagar, da mambobin ta, wajen yadda zasu gudanar da aikin su yadda ya k**ata, ba tareda an samu wani tsaiko ba aikin hajjin wannan shekara.
Gwamna Dikko Umar Raɗɗa, ya tunatar da Malamai masu gudanar da wa'azi, don taimakon alhazan, su gudanar da aikin su, cewa Gwamnati tayi amfani da kuɗin al'umma wajen ɗaukar nauyin su, sannan akwai buƙatar suyi abunda ya Kaisu, domin sauke nauyin da ya rataya kansu.
Gwamnan ya kuma Umarci Shuwagabannin hukumomi, dasu kula, tareda sanya ido akan waɗanda aka ɗauki nauyin su Domin su taimakawa alhazan jihar, wajen gudanar da aikin su, tareda tabbatar da cewa, sunyi abunda ya kaisu.
Da yake maida martani,. Amirul hajjin, kuma shugaban tawagar aikin hajjin wannan shekara,. Malam faruq Lawal joɓe, ya godewa gwamna Malam Dikko Umar Radda, bisa damar da ya basu domin bada gudummuwar su wajen tabbatar da cewa, an gudanar da aikin hajjin wannan shekara cikin aminci.
Malam Faruq Lawal joɓe, ya bada tabbaci ga gwamnan cewar, zasuyi iya ƙoƙarin su wajen sauke nauyin da (A) ya ɗora masu.
Abdulrahman Musa Alƙali # #