RBChausa

RBChausa Wannan Shafi zai kawo labarai ingantattu daga kwararrun 'yan jarida. Taken mu shine Madogarar Al'umma.

Gwamnan  jihar katsina Dikko Umar Radda, ya ƙaddamar da tawagar da zata jagoranci aikin hajjin wannan shekarar, ƙarƙashi...
26/04/2025

Gwamnan jihar katsina Dikko Umar Radda, ya ƙaddamar da tawagar da zata jagoranci aikin hajjin wannan shekarar, ƙarƙashin mataimakin gwamnan jihar Malam garuk Lawal joɓe, Amirul hajji.

A jawabin shin na ƙaddamar war, gwamnan ya ambaci sunan shugaban majalissar dokoki ma jihar katsina, Alh Nasir Yahaya Daura, da kuma wakilai daga masarautun Katsina da Daura a matsayin mambobin tawagar.

Sauran mambobin sun haɗa da kwamishinan kula da harkokin Addinai, Alh Shehu Abubakar Dabai, mai bawa Gwamna shawara akan tu'ammalinda miyagun ƙwayoyi, da takwaransanna babban kotun jihar katsina, Mai shari'ah Aminu Tukur ƙofar Bai, da kuma shugaban Hukumar HISBAH, na jihar katsina, Aminu Usman Abu Ammar.

Gwamnan ya bayyana sunayen sauran mambobin tawagar, ta jihar katsina da s**a haɗa da shugaban Gidan Rediyon juhar katsina, Malam Lawal Attahiru Bakori, da Sheikh Nazir ƙofar Baru, da kuma Usman Abubakar da dai sauransu.

Haka kuma ƙa'idojin tsare-tsaren da aka sanya ga tawagar da zata jagoranci aikin hajjin, sun haɗa da kula, tareda bibiyar yadda Mahajjatan zasu gudanar da ayyukan su na hajji cikin nasara, daga nan Najeriya har zuwa a ƙasa mai tsarki.

Yace ya k**ata a tabbatar da kula lafiyar Mahajjatan, samar da wal-wala, da kuma mutuncin su anan Najeriya da kasa mai tsarki, da kuma tabbatar da tashin alhazan da dawowar su gida katsina cikin aminci.

Gwamnan ya bayyana gamsuwar sa akan ƙwazo da jajircewar tawagar, da mambobin ta, wajen yadda zasu gudanar da aikin su yadda ya k**ata, ba tareda an samu wani tsaiko ba aikin hajjin wannan shekara.

Gwamna Dikko Umar Raɗɗa, ya tunatar da Malamai masu gudanar da wa'azi, don taimakon alhazan, su gudanar da aikin su, cewa Gwamnati tayi amfani da kuɗin al'umma wajen ɗaukar nauyin su, sannan akwai buƙatar suyi abunda ya Kaisu, domin sauke nauyin da ya rataya kansu.

Gwamnan ya kuma Umarci Shuwagabannin hukumomi, dasu kula, tareda sanya ido akan waɗanda aka ɗauki nauyin su Domin su taimakawa alhazan jihar, wajen gudanar da aikin su, tareda tabbatar da cewa, sunyi abunda ya kaisu.

Da yake maida martani,. Amirul hajjin, kuma shugaban tawagar aikin hajjin wannan shekara,. Malam faruq Lawal joɓe, ya godewa gwamna Malam Dikko Umar Radda, bisa damar da ya basu domin bada gudummuwar su wajen tabbatar da cewa, an gudanar da aikin hajjin wannan shekara cikin aminci.

Malam Faruq Lawal joɓe, ya bada tabbaci ga gwamnan cewar, zasuyi iya ƙoƙarin su wajen sauke nauyin da (A) ya ɗora masu.

Abdulrahman Musa Alƙali # #

23/04/2025

Majalissar Dokokin jihar katsina ta baiwa kwamitin kula da hanyoyi, daya binciki irin ƙoƙarin da hukumar kiyaye afkuwar haɗurra keyi, da sauran hukumomi kan yadda za'a rage yawan afkuwar haɗurra akan manyan hanyoyin jihar nan.

Haka nan kuma, majalissar ƙarkashi jagorancin Alh Nasir Yahaya Daura, ya buƙaci ɓangaren zartaswa, daya kafa kwalejin koyon aikin jinya da unguwar zoma a Fago dake cikin KH Sandamu.

Shugaban majalissar ya umarci akawun majalissar daya miƙa ƙudurin ga ɓangaren zartaswa don aiwatar wa.

Tun farko, wanda ya gabatar da ƙudurin farko, Sirajo Abdu kwaskwaro, dake wakiltar KH kaita a majalissar, ya koka akan yawan afkuwar haɗurran, akan yawan yin lodin da yawuce kima motoci keyi akan hanyoyin musamman ma irin ranar kasuwa.

Alh Sirajo kwaskwaro, yayi kira ga hukumomin da abun ya shafa, dasu bincika da kuma k**a duk direbobin manyan motocin wanda ke hidimar zuwa kudancin ƙasar nan, wanda suke ɗaukar mutane da dabbobi a tare.

Haka kuma, da yake kare ƙudurin kafin gabatar dashi a gaban majalissar, mamba dake wakiltar KH Sandamu, Sale Magaji, yace kafa wannam Makarantar ta koyon aikin jinya a yankin Fago, zai taimaka sosai wajen ɗaga darajar kiwon lafiya tun daga tushe.

Alh Sale Magaji ya bayyana cewa, Al'ummar mazabar shine s**a tuntuɓe shi da wannan buƙatar ta kafa kwalejin don a samu gurbin karatu, wanda sukeyin tattaki zuwa Malumfashi don samun gurbin karatu.

Mambobin dake wakiltar KHs Ɓaure, Jibia, da Kusada, sun goya ma ƙudurin baya. # # # #

Abdulrahman Musa Alƙali

Champions League: Real Madrid za ta kara da Atletico, Liverpool da PSG        Jadawalin zagaye na biyu wato last 16 na g...
21/02/2025

Champions League: Real Madrid za ta kara da Atletico, Liverpool da PSG

Jadawalin zagaye na biyu wato last 16 na gasar zakaurn turai ya fito, inda aka rarraba ƙungiyoyin da za su fafata da juna domin tsallakawa zuwa wasan kwata final a gasar ta bana.

Daga manyan wasannin da za su ja hankalin masu kallo, akwai wasan da za a fafata tsakanin Real Madrid ta Spain da Atletico Madrid ita ma ta Spain, da kuma wanda PSG ta Faransa za ta fafata da ƙungiyar Liverpool ta Ingila.

A sauran wasannin, ƙungiyar Barcelona za ta fafata da Benfica, Bayern Munich da Bayer Leverkusen, Club Brugge da Aston Villa, Borussia Dortmund da Lille, PSV Eindhoven da Arsenal sai kuma Feyenoord da za ta doka wasa da Inter Milan.

Haka kuma an shirya jadawanin wasannin na gaba wato kwata final, inda ƙungiyar da ta samu nasara tsakanin PSG da Liverpool za ta fafata ne da wadda ta samu nasara a wasan Club Brugge da Aston Villa.

Haka kuma ƙungiyar da ta samu nasara a wasan PSV da Arsenal ce za ta fafata da ƙungiyar da ta yi nasara a wasan Real Madrid da Atletico Madrid.

Ƙungiyar da ta samu nasara tsakanin Benfica da Barcelona za ta doka wasa da wadda ta yi nasara a wasan Borussia Dortmund da Lille.

A wasannin kusa da na ƙarshe kuwa, ƙungiyar da ta fito a wasannin da za buga tsakanin wadda ta yi nasara a wasan Barcelona da Benfica da na Borussia Dortmund da Lille ce za ta fafata da wadda ta fito a wasan da za a buga tsakanin wadda ta yi nasara tsakanin Bayern Munich da Bayer Leverkusen da na Feyenoord na Inter Milan.

A ɗayan wasan na kusa da na ƙarshen, ƙungiyar da ta fito a wasan tsakanin da aka buga tsakanin wadda ta yi nasara a wasan PSV da Arsenal da wadda ta yi nasara a wasan Real Madrid da Atletico Madrid ce za ta fafata wadda ta fito a wasan da za a buga tsakanin wadda ta samu nasara a wasan PSG da Liverpool da na da Club Brugge da Aston Villa.

21/02/2025

Jama'a barkan ku da wannan lokaci na yammacin Ranar juma'a.

Gwamnatin jihar katsina ta amince da fitar da sama da naira Miliyan dubu 2, da Miliyan ɗari 300, domin sawo hatsi da kay...
19/02/2025

Gwamnatin jihar katsina ta amince da fitar da sama da naira Miliyan dubu 2, da Miliyan ɗari 300, domin sawo hatsi da kayyayakin masarufi kafin isowar watan Ramadan mai ƙaratowa.

Hakan na da ƙudrinntaimaka ma marasaa ƙarfij gudanar da Azumin watan Ramadan a cikin sauki.

Kwamishinan ma'aikatar albarkatun gona, Farfesa Ahmad Muhammad Bakori,nya sanar da haka, a lokacin da yake jawabi ga manema labaru bayan zaman majalissar zartaswa na jiha.

Kwamishinan ya bayyana cewa, wannan kuɗi sun ƙunshi aikin ciyarwa ta musamman a tsawon watan Ramadan.

Farfesa Bakori, ya tuna sar cewa, angudanar da irin wannan ciyarwa ga al'ummar wannan jiha a shekarar data gabata.

Yace, yayin da wani ɓangare na wannan kayyayaki, za'a rabawa tsofaffi, da marassa ƙarfi, kyauta, da kuma wanda aka ware domin sayarwa, ga sauran al'umma a farashi mai sauƙi.

Kwamishinan yayi bayanin cewa, majalissar zartaswa, tana mince da fidda sama da naira Miliyan dubu 16, da Miliyan dari 5 domin sawo ton dubu 32 na takin zamani nau'in NPK da UREA.
Yace jihar katsina a halin yanzu bayan samun wannan ƙarin wannan adadi na takin juhar nada jimillar buhunnan taki dubu ɗari 4, wanda za'a ƙaddamar da rabasu a watan Aprilunmai zuwa kafin saukar ruwan sama. # # #

Abdulrahman Musa Alƙali

Why military can’t come back to power , by Gen. Abdulsalami      There’s no alternative to civil ruleINEC calls for inte...
31/01/2025

Why military can’t come back to power , by Gen. Abdulsalami

There’s no alternative to civil rule
INEC calls for internal democracy in parties
Soldiers cannot return to power because military rule is outdated, former Military Head of State, Gen. Abdulsalami Abubakar, said yesterday.

He noted that in the last 25 years, democratic rule has survived the onslaught of reactionary forces.

General Abdulsalami said he was proud of laying a solid foundation by handing over power to civilian authorities.

Urging Nigerians and the political parties to nurture the tree of democracy, the former military leader said, There is no alternative to civil rule.

Gen. Abdulsalami spoke at the launch of a book titled: “100 Years of Political Parties Evolution in Nigeria, 1923 – 2023’’ by the Inter-Party Advisory Council (IPAC) in Abuja.

The former head of state, who was represented by Gen, Abdulrasheed Aliyu, spoke on 100 years of political parties evolution in Nigeria – The imperative of Nigeria’s political stability issues and solutions.

Gen. Abdulsalami, who chaired the event, House of Representatives Speaker Abbas Tajudeen, said strong political parties and opposition were vital for good governance.

Also, the Chairman of the Independent National Electoral Commission (INEC), Prof. Mahmood Yakubu, urged political parties to promote internal democracy.

Gen. Abdulsalami said the fact that democracy has survived in the country for 25 years attested to Nigerians’ resilience and belief in representative governance.

This He said, Despite military interventions, democracy has come to stay in Nigeria.

There is no substitute to the government of the people, by the people and for the people, which democracy represents as sovereignty resides with the people.

This year will also make it 26 years of unbroken democracy in Nigeria, the longest period of constitutional governance since 1st October 1960, when the country got Independence from the British colonial masters.

I am happy that my government, as the then military Head of State, ushered in this era of democracy when I handed over power to the elected President on 29th May 1999.

My government laid this solid foundation for democratic governance.

It also shows that when leaders are patriotic, passionate, resolute and unwavering in building strong democratic structures and institutions, democracy could flourish and yield its dividends to citizens.”

Gen. Abdulsalami added: “We should, therefore, keep watering and nurturing the tree of democracy as there is no alternative to civil rule.

“Our democracy has been tested and shaken by reactionary forces and survived.

“It is a testament to citizen’s belief and resilience in representative governance.

Gen. Abdulsalami called for party supremacy, adherence to party manifestoes and the formation of a party based on ideology.

Speaker Abbas said Nigeria’s return to civil rule in 1999 marked a new beginning for the nation after over 30 years of military rule.

He urged politicians to stop weaponising ethnicity for political and personal gains.

Abbas, represented by House Majority Leader Prof. Julius Ihonvbere, decried the hijack of parties by people with deep pockets.

Also speaking The Chairman of IPAC, Yusuf Dantalle, described the book as a beacon of knowledge and insight, highlighting the struggles and progress that had defined Nigeria’s political journey.

He said the document also served as a testament to the rich history, evolution and resilience of political parties in Nigeria.

Dantalle added that It is a reflection of the trials and triumphs, the challenges and achievements that have shaped our political landscape over the past century.”

Prof. Yakubu described internal democracy as the foundation upon which a credible general election is built.

The INEC Chairman, represented by the National Commissioner in charge of political parties and election monitoring, Sam Olumekun, said effective leadership recruitment is possible only when eligible persons with capacity are selected through duly conducted party primaries to run for elections.

An Rasa Rayuka da Wani Direba a Cikin 'Maye' Ya Bi Ta kan Sojojin Najeriya       Rahotanni da muka samu yanzu haka sun n...
31/01/2025

An Rasa Rayuka da Wani Direba a Cikin 'Maye' Ya Bi Ta kan Sojojin Najeriya

Rahotanni da muka samu yanzu haka sun nuna cewa sojoji da dama sun rasa rayukansu da wani hatsari ya afka kansu lokacin da s**a fito motsa jikin safe a Legas.

Lamarin ya faru ne lokacin da wani direba da ake zargin yana cikin maye ya murkushe sojojin waɗanda s**a fito daga barikin Myoung da ke Yaba a jihar Legas.


Rahotonni sun nuna cewa direban ya latse sojojin ne a lokacin da s**a fito atisayen motsa jiki na safiyar yau Juma'a, 31 ga watan Janairu, 2025.

Wannan mummunan al'amari ya jefa sojojin cikin tashin hankali da firgici saboda direban ya afka masu ne ba zato ba tsammani.

Wani soja da ya tsira daga hatsarin ya bayyana cewa, Jini ya watsu ko’ina, ni na tsira ne saboda ina a bayan su.

Rahotanni sun nuna cewa sojoji da dama sun rasa rayukansu da wani direba da ake tunanin yana cikin maye ya bi ta kansu da safiyar Juma'a a jihar Legas.

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El Rufa'i ya ce ya faɗa wa shugaba Bola Tinubu cewa ba ya son wani muƙami a gwa...
30/01/2025

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El Rufa'i ya ce ya faɗa wa shugaba Bola Tinubu cewa ba ya son wani muƙami a gwamnatinsa.

El Rufa'i ya bayyana haka ne a shafinsa na Twitter wato X yayin martani ga babban mai taimaka wa shugaban ƙasa kan sadarwar tsare-tsaren gwamnati, Daniel Bwala, wanda ya ce El Rufa'i ya ji tsoron Allah bayan da ya fito fili ya caccaki jam'iyyar APC da kuma kiran ta mai mulkin da ta "sauka daga aƙidun dimkoraɗiyya da aka kafa ta a kai.

Na faɗa wa Tinubu ƙarara cewa ba na buƙatar kowane irin muƙami a gwamnatinsa," in ji El Rufa'i.

Ya ce yana mamakin irin yadda Daniel Bwala da takwarorinsa da s**a koma jam'iyyar APC a baya-bayan nan ke ta yayata batun cewa an hana shi muƙami, abin da ya ce ba ya so tun da farko.

Ina mayar maka da martani ne saboda ina tunanin cewa kai mai fahimta ne wanda ke neman aiki, ba irin wasu mutane ba.

Ku mutane ne da ke karɓar albashi kowane wata don ku fara fitowa a shafukan sada zumunta wajen kare kowane irin abu da gwamnatin Asiwaju ta yi ko kuma ta ƙasa yi," in ji tsohon gwamnan na Kaduna.

Ya ce ko da ace yana cikin gwamnatin shugaba Tinubu - babu abin da zai hana shi furta kalaman da ya yi kan abin da ke faruwa a jam'iyyar da ya ce su s**a kirkiro - har ma da kawo gwamnati mai ci.

A.M Alƙali

Gwamnatin Tinubu Ta Samo Rancen Sama da N1bn don Tsame Najeriya daga Duhu     Bankin AfDB zai ba da Dala miliyan 200 dom...
30/01/2025

Gwamnatin Tinubu Ta Samo Rancen Sama da N1bn don Tsame Najeriya daga Duhu

Bankin AfDB zai ba da Dala miliyan 200 domin aiwatar da shirin wutar lantarki na Najeriya, wanda zai bai wa mutane 500,000 hasken lantarki

Wannan ya na daga cikin Dala biliyan 1.1 da Najeriya ta karɓa, domin aiwatar da ayyukan samar wa 'yan kasa hasken wutar lantarki zuwa shekarar 2026.

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya na ganin wannan makudan kuɗin da ya ke karbo wa, za su taimaka wajen raba Najeriya da duhu.

Mr bayo Onanuga ya ce shugaban ya bayyana hakan a yayin taron mak**ashi na Afrika da aka kammala a Dar es Salaam, a kasar Tanzaniya.

A cikin jawabin da Ministan mak**ashi Adebayo Adelabu, ya karanta a madadinsa, Shugaban kasa Tinubu ya ce: "Na yaba da taimakon Bankin Raya Afirka na dala biliyan 1.1, wanda za a yi amfani da shi wajen samar da wutar lantarki ga mutanen ƙasar nan

A wani labarin kuma, Tinubu zai karbo sabon bashi A halin yanzu, na fatan samun sabon tallafin dala biliyan 1.2 daga Bankin Afirka don aiwatar da shirin sahara zuwa mak**ashi.

Haka kuma ana jiran wani bashin na Dala miliyan 500 domin gina tashawa da za ta rika adana hasken wutar lantarki ta Nigeria-Grid Battery Energy Storage System.

A cewarsa: "Muna kuma sa ran samun dala miliyan 700 daga Bankin Raya Afrika don aiwatar da shirin sahara zuwa mak**ashi a Najeriya, tare da dala miliyan 500 da za a zuba a tsarin ajiyar wutar lantarki, wanda zai bai wa ƙarin mutane miliyan biyu damar samun lantarki.

Majalissar tarayya ta amince da bashin wutar lantarki.

A wani labarin, Majalisar Dattawa ta amince da bukatar gwamnatin tarayya na karɓo bashin dala miliyan 500 domin sayo mitoci da za a rarraba a gidajen ‘yan kasa.

Abin da Shugaban BoT Ya Faɗa a Wurin Taron PDP bayan an Mari Babban Jigo a Abuja      Shugaban BoT na PDP ta ƙasa, Sanat...
30/01/2025

Abin da Shugaban BoT Ya Faɗa a Wurin Taron PDP bayan an Mari Babban Jigo a Abuja

Shugaban BoT na PDP ta ƙasa, Sanata Adolphus Wabara ya ce ya zama dole a shirya taron kwamitin zartarwa watau NEC nan kusa.

Wabara ya bayyana haka ne a taron BoT karo na 76 wanda rigima ta kaure kan rikicin kujerar sakataren PDP na ƙasa a Abuja ranar Laraba

Ya kuma soki gwamnatin APC yana mai cewa har yanzun ƴan Najeriya na kallon PDP a matsayin jam'iyyar da za ta iya ceton ƙasarsu

Shugaban Majalisar Amintattu (BoT) na jam’iyyar PDP, Sanata Adolphus Wabara, ya jaddada cewa dole ne a gudanar da taron kwamitin zartarwa (NEC) da aka shirya yi a watan Fabrairu.

Sanata Wabara ya ce duk da rikicin shugabanci da ke ci gaba da addabar PDP, ya zama dole a shirya taron NEC nan kusa don warware wasu matsalolin.

Manyan ƙusoshi 2 sun yi arangama a wurin taron majalisar amintattun PDP a Abuja.

Shugaban BoT ya nanata bukatar gudanar da taron NEC k**ar yadda aka tsara a watan Fabrairu, 2025


Wabara ya yi wannan bayani ne a taron BoT karo 79 da aka yi a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja a ranar Laraba, k**ar yadda Daily Trust ta rahoto.

Yadda rigima ta ɓarke a taron BoT Taron BoT na wannan karon ya zo da tashin-tashina, inda masu rigima kan kujerar sakatare, Samuel Anyanwu da Sunday Ude-Okoye s**a yi arangama.

Rahoto ya nuna cewa faɗa ya kaure a wurin taron har sai ta kai ga marin Ude-Okoye tare da fitar da shi daga ɗakin taron da ƙarfin tsiya.

Rikicin ya yi ƙamari a jiya Laraba har dai da jami'an tsaro s**a shiga tsakani, sannan komai ya lafa a hedkwatar PDP ta ƙasa.

Abin da shugaban BoT ya faɗa a taron Da yake jawabi a wurin taron, ya bukaci ƴan PDP a kowane mataki su haɗa kansu kuma ya ja hankalinsu da su fifita ci gaban jam’iyya fiye da bukatun kansu.

Bayan kiran El Rufa'i, Peter Obi ya ce ya yarda da hadakar 'yan adawa a 2027 "Wannan taro ya zo ne a daidai lokacin da hadin kai, manufa, da ƙimar jam’iyyarmu ke fuskantar kalubale.
Abin takaici ne har yanzu ba a warware rikicin shugabanci a kwamitin gudanarwa NWC ba. "Rashin shawo kan waɗannan matsaloli yana rage wa jam’iyyarmu mutunci," in ji Wabara.
Ya k**ata PDP ta shirya taron NEC inda Ya kara da cewa yana da matukar muhimmanci a gudanar da taron NEC k**ar yadda aka tsara a wata mai k**awa.
NEC ita ce mai alhakin yanke shawara a jam’iyyarmu, dole ne a gudanar da taron ba tare da bata lokaci ba domin mu tabbatar da an rungumi hadin kai, ɗa’a, da manufofin da s**a hada mu wuri guda.

Mr Adolphus Wabara ya kuma caccaki jam’iyyar APC, yana mai cewa PDP ce kadai za ta iya ceto Najeriya, k**ar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
Kasar mu tana wahala a karkashin mulkin APC. ‘Yan Najeriya na kallonmu a matsayin haske da fatansu na gari, dole ne mu cika wannan buri," in ji shi.

Haka kuma jamiyyar APC ta yi kaca kaca da Ɗan takarar shugaban ƙasa Atiku Abubakar, ta fadi wanda ke haddasa rikici a PDP.

Har ila yau, Umar Damagum ya zargi wasu shugabanni a taron BoT,

A wani labarin kun ji cewa muƙaddashin shugaban PDP na ƙasa ya zargi wasu shugabanni da hannu a rura wutar rikicin da ke faruwa a NWC.

Umar Damagum ya ce lokaci ya yi da za a haɗa Kai wuri guda, domin farfaɗo da jam'iyyar PDP wacce ƴan Naheriya ke da sa rai a kanta.

Hukumar kula da ƴan najeriya mazauna ƙasashen waje, ta sanar da cewa FG tabshirya karbar yan najeriya, da za'a maido dag...
30/01/2025

Hukumar kula da ƴan najeriya mazauna ƙasashen waje, ta sanar da cewa FG tabshirya karbar yan najeriya, da za'a maido daga ƙasar Amurka.

Daraktan watsa labari mai kuma da harkokin hukumar, Abdulrahman Balogun, ya bayyana haka a wata tattauna wa da yayi, cewa, maaikatar kula da harkokin ƙasashen waje zata kula da wannan aiki.

Yace tuni Gwamnatin tarayya ta kafa kwamitin shiga tsakanin ƙasashe domin hannata mashi lamarin.

Kwamitin ya ƙunshi ma'aikatar harkokin ƙasashen waje, hukumar kula da ƴan najeriya mazauna ƙasashen waje, da ma'aikatar jinƙai ta ƙasa, da kuma ofishin mai bada shawara akan harkokin tsaro.

An bada rohoton cewa, a ƙalla ƴan najeriya 3,690 ke zaune a ƙasar Amurka,wanda sabon shugaban ƙasar Donald Trump zai fitar a ƙasar.

30/01/2025

Sakataren Ilimi na KH Ɗanmusa, ya bayyana cewa, daga cikin makarantu 24 a cikin 30 waɗanda aka rufe sak**akon rashin tsaro a yankin, yanzu an buɗe su.
Alh Zaharadden Umar, ya bayyana haka, a lokacin da ya jagoranci tawagar manema labaru don duba makarantu n dake yankin.
Ya bayyana wasu sauran makarantu guda 10, an haɗesu da Ɗalibai da malamai don yin aiki yadda ya k**ata.
Sakataren Ilimin, ya dangana samun nasarar buɗe makarantun, ga Gwamnatin jiha mai ci yanzu, na jajircewa wajen ganin jihar nan ta samu tsaro.
Haka kuma ya yaba ma Gwamna MDUR, na naɗa Dr Kabir Magaji Gafiya, a matsayin babban sakataren hukumar SUBEB, a matsayin wanda ya can-canta.
Shuwagabannin makarantun Primary daga Makarantar Mara primary school, Malam Ali Almu, da Makarantar primary ta Pilot Dutsinma, Ya'u Sada, sun nuna godiyar subga sakataren Ilimin akan ƙoƙarin shi na kawo cigaban sashen.
Haka kuma sun bayyana godiyar su ga Gwamnatin jiha, akan faɗi tashi na ganin an samu tsaro a yankin.
Da yake jawabi a madadin maigari Mara, Muhammad Abdullahi, ya bayyana godiyar sa ga sakataren Ilimin akak aikace-aikacen da yakeyi na kawo sauyi a yankin. # # #

Abdulrahman Musa Alƙali.

Address

Katsina

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when RBChausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to RBChausa:

Share