04/06/2026
Wasu daga cikin iyalin margayi Sheikh Albany Zariya sun bayyana dalilin da ya sa s**a shigar da ƙara kotu kan dambarwar rabon gadon margayin da suke da shakku a kai.
A cikin wata sanarwa da guda daga cikin ‘ya’yan margayin da ke iƙirarin zama mai magana da yawun wasu daga cikin iyalin, Abdulhaleem Muhammad Auwal Adam, ya ce sun yi hakan ne domin tantance gaskiya da kuma adalci gare su.
Manyan abubuwan da dambarwar rabon ta ginu a kai dai sun haɗa da makarantar Sheikh Albanin ta Daarul Hadeethis Salafiyya, da kuma gidansa da yanzu haka iyalinsa ke zaune a ciki, da ake tantamar ko ya faɗa cikin gadon iyalinsa ko kuma waƙafi ne.
Tuni kotun dai ta kai ziyara wuraren da ma sauran kadarorin da ake dambarwar akansu, waɗanda s**a haɗa da gidaje, makarantu, filaye da sauran kadarori da ke Gaskiya Layout da wasu sassan Zariya da Kaduna, ciki har da Albaniy Science Academy, Saudatu Science Academy.
Sauran sun haɗa da filin da aka ware domin gina jami’ar Albaniy University of Information and Communication Technology da Albaniy University Teaching Hospital, tare da sauran kadarori.
Iyalin margayin dai na neman kotu ta bincika batun mallakawa wani ko wata ƙungiya, da a baya s**a faɗa rukunin waƙafi madadin gado in ji Abdulhaleem.
Ya kuma ce ba rikici suke nema da kowa ba, illa warware tsaba da tsakuwa, da kuma tabbatar da an yi adalci ga ɓangarorin da ke wannan dambarwar.