Katsina 24/7 news

Katsina 24/7 news Gaskiya dokin karfe

Da Yardar Allah Zaman Lafiya Ya Dawo A Karamar Hukumar Musawa - Inji Matawallen MusawaMatawallen Musawa kuma Darakta Jan...
01/09/2025

Da Yardar Allah Zaman Lafiya Ya Dawo A Karamar Hukumar Musawa - Inji Matawallen Musawa

Matawallen Musawa kuma Darakta Janar na Madabba'ar Jihar Katsina Malam Honorabul Rufa'i Musawa ya bayyana cewa da izinin Allah daga yanzu zaman lafiya ya samu wanzuwa a Karamar Hukumar Musawa.

Honorabul Abba Rufa'i Musawa ya bayyana hakan ne a sa'ilinda yake zantawa da Manema Labarai ciki har da Accuracy News Hausa, jim kadan bayan kammala zaman sulhu da yan bindigar a Karamar Hukumar Musawa.

Matawallen na Musawa ya bayyana cewa, da wannan zaman sulhu da aka yi da yan bindigar dajin, akwai kyakkyawan yakinin cewa yankin zai dawo da kumarin shi na cigaban tattalin arziki da zaman lafiya a tsakanin al'umma da Fulanin yankin.

Darakta Janar din ya bayyana Jin dadi akan yadda ya ga fuskokin yan bindigar da al'ummar yankin cike da Farin ciki da walwala bisa ga tabbatar da zaman sulhun, wanda a cewar shi Insha Allah zai zamo abinda zai kawo karshen zubar da jini a yankin.

Daga nan sai ya yabawa Shugabancin Karamar Hukumar akan kyakkyawan tsari da aka yi na yarjejeniyar zaman lafiyar, tare da jaddada yakinin cewa hakan zai dore har abada.

Haka zalika, ya yi roko ga jama'ar yankin akan kada su gajiya wurin cigaba da yin addu'oin dorewar wannan sulhu, domin kara samun cigaban tattalin arziki da zamantakewa da juna kamar yadda addini ya tsara.

Matawallen na Musawa ya yi amfani da damar inda ya yabawa Gwamna Dikko Radda akan jajircewar shi na ganin an samu ingantaccen tsaro a Jihar Katsina, sai ya roki jama'ar yankin akan su Taya shi da addu'a, domin cimma nasarar wannan kudiri nashi.

31/08/2025
Rashin Tsaro: Lokaci Yayi Da Gwamnati Za Ta Ɗauki Matakan Gaggawa Kan Matsalar Tsaro A Arewa ~ Cewar Shugaban Kungiyar M...
30/08/2025

Rashin Tsaro: Lokaci Yayi Da Gwamnati Za Ta Ɗauki Matakan Gaggawa Kan Matsalar Tsaro A Arewa ~ Cewar Shugaban Kungiyar Marubutan Arewa

Shugaban ƙungiyar marubutan Arewa a kafafen sadarwar zamani Arewa Media Writer, Comr Haidar H. Hasheem, yayi kira da kakkausar murya ga gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da gwamnatin jahohi da su dauki matakan gaggawa da na dindindin wajen kawo karshen matsalar tsaron da ta addabi al’ummar Arewa musamman a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da sauran sassa na Arewacin Najeriya.

Shugaban ya nuna matuƙar damuwa kan yadda yan ta’adda ke ci gaba da kai hare-hare cikin ƙauyuka, suna kashe mutane a masallatai, suna sace jama’a tare da ƙona gidaje da dukiyoyi. Wannan lamari ya jefa dubban mutane cikin tsananin fargaba, barin garuruwansu da kuma rasa amincewa ga gwamnati da hukumomin tsaro.

Ya kamata gwamnati ta fahimci cewa tsaron ƙasa ba abu ne da za a siyasantar da shi ba. Tsaro shi ne ginshikin ci gaban kowane al’umma, don haka wajibi ne a ɗauki matakin gaggawa domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a. Rashin yin haka na iya sa al’umma su rasa kwarin gwiwar dogaro ga gwamnati.

Kare rayukan al'umma wajibi ne ga gwamnatin kasa, haka kuma ya kamata ita gwamnati ta samarwa da jami'an tsaro kayan aiki na zamani tare da basu ƙarfin gwiwa wajen daƙile matsalolin tsaron da ake fama da su.

A madadin al’ummar Arewa baki ɗaya, da marubutan Arewa muna kira ga shugabanni a kowane mataki da su yi tsayuwar daka wajen ganin cewa an kawo karshen wannan matsalar tsaron da ta yi katutu a Arewa.

A ƙarshe, ina roƙon Allah Madaukakin Sarki Ya kawo ƙarshen wannan fitina, Ya ba Najeriya da Arewa zaman lafiya da tsaro nagari.

Rubutawa ✍️
Comr Haidar H. Hasheem
National Chairman, Arewa Media Writer's

Ya kamata kowane ɗan Najeriya ya koyi dabarar kare kai - Inji- Janar Christopher MusaBabban hafsan hafsoshin Najeriya, J...
22/08/2025

Ya kamata kowane ɗan Najeriya ya koyi dabarar kare kai - Inji- Janar Christopher Musa

Babban hafsan hafsoshin Najeriya, Janar Christopher Musa ya shawaraci ƴan Najeriya da su laƙanci dabarun kare kai daga haɗurra a matsayin mataki na ko-ta-kwana.

C.G Musa ya bayyana haka ne a wata tattaunawa da kafar talabijin ta Channels a yau Alhamis.

Matsalar tsaro na addabar yankuna da dama na Najeriya, inda masu ɗauke da makamai ke kashe mutane tare da tarwatsa su daga muhallansu.

Duk da cewa hukumomi na cewa suna bakin ƙoƙarinsu, amma lamarin na ci gaba da laƙume ɗaruruwan rayuka a yankunan da ake fama da irin waɗannan tashin-tashina, kamar arewa maso yamma da arewa maso gabas da kuma arewa ta tsakiyar ƙasar.

Lokacin da aka tambayi Christopher Musa kan ko ya kamata al'umma su koyi dabarun faɗa, ya ce "Ya kamata mutane su ɗauki wannan tamkar koyon tuƙi ne ko iyo, wannan abu ne da ake buƙata a rayuwa, ko da ana fama da yaƙi ko a'a".

"Ina ganin ya kamata a wayar da kan kowane ɗan Najeriya kan tsaro a kowane mataki. Kare kai na da matuƙar muhimmanci," in ji Musa.

Ko a ranar Litinin, wasu mahara sun kashe masu ibada aƙalla 28 a wani masallaci da ke karamar hukumar Malumfashi da ke jihar Katsina, arewa maso yammacin ƙasar.

Haka nan a watan da ya gabata masu garkuwa da mutane sun yi wa mutum 38 yankan rago cikin waɗanda suke garkuwa da su a jihar Zamfara mai maƙwaftaka.

Matawallen Musawa Ya Ziyarci Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Tukur JikamshiSabon Matawallen Musawa kuma Darakta ...
19/08/2025

Matawallen Musawa Ya Ziyarci Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Tukur Jikamshi

Sabon Matawallen Musawa kuma Darakta Janar na Madabba'ar Jihar Katsina Abba Rufa'i Musawa, ya kai ziyarar ban girma ga tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina Alhaji Tukur Ahmed Jikamshi.

Matawallen na musawa ya kai ziyarar ne ga Tsohon Mataimakin Gwamnan a gidan shi da ke Unguwar Kofar Marusa Low-cost a cikin Birnin Katsina.

Ziyarar na da nufin gabatar da takardar nadin Darakta Janar din sarautar Matawallen Musawa ga Tsohon Mataimakin Gwamnan, a matsayin shi na uba ga duk wani dan siyasa na Karamar Hukumar Musawa.

Haka zalika, ziyarar ta kasance a matsayin wata dama ga Darakta Janar din domin ya nemi shawarwari da tubarakin Tsohon Mataimakin Gwamnan ta fuskar sauke nauyin da aka dora mashi.

Da yake magantawa a yayin ziyarar, Tsohon Mataimakin Gwamnan Alhaji Tukur Ahmed Jikamshi ya taya murna ga Daraktan din akan karamcin da Masarautar ta Musawa ta yi mashi.

Alhaji Tukur Ahmed Jikamshi ya bayyana sabon Matawallen na Musawa a matsayin hazikin matashi mai son cigaban al'umma, sai ya bukace shi akan ya cigaba da kasancewa jakade na kwarai ga Karamar Hukumar Musawa a duk inda ya samu kan shi.

Ya kuma bashi tabbacin cewa zai cigaba da bashi shawarwari a matsayin shi na uba, domin ya samu nasarar sauke nauyin da Gwamna Dikko Radda ya bashi na shugabantar Madabba'ar Jihar Katsina.

Tunda farko Sabon Matawallen na Musawa Honorabul Abba Rufa'i Musawa, ya nuna godiya ga Tsohon Mataimakin Gwamnan akan kyakkyawan fata a gareshi, sai ya ce zai cigaba da kasancewa da na kwarai ga Karamar Hukumar Musawa a duk inda ya samu kan shi.

Honorabul Abba Rufa'i Musawa ya kuma kara godewa Tsohon Mataimakin Gwamnan akan shawarwarin da yake bashi na tafiyar da Madabba'ar Jihar Katsina, Wanda hakan ya taimaka mashi wurin kawo cigaba ga ma'aikatar.

Daga karshe ya nuna godiya akan kyakkyawan tarba da Tsohon Mataimakin Gwamnan ya yi mashi da shi da yan tawwagar shi.

Matawallen Matazu Ya Sha Alwashin Cigaba Da Yin Bakin Kokarin Shi Na Gudanar Da Ayyukan Jin Kan Al'ummaShugaban Hukumar ...
17/08/2025

Matawallen Matazu Ya Sha Alwashin Cigaba Da Yin Bakin Kokarin Shi Na Gudanar Da Ayyukan Jin Kan Al'umma

Shugaban Hukumar Samar Da Hasken Wutar Lantarki A Yankunan Karkara Ta Jihar Katsina Injiniya Abubakar Matazu ya sha alwashin cigaba da aiwatar da ayyukan jin kan al'umma bakin karfin da Allah ya h**e mashi.

Injiniya Abubakar Matazu wanda shi ne Matawallen Matazu ya bayyana hakan ne a lokacin wani taro na karrama dalibai yan asalin Jihar Katsina da s**a samu maki mafi daraja a jarabawar share fagen shiga jami'a(JAMB).

Daliban dai sun fito ne daga Kananan Hukumomi 14 na Jihar Katsina.

Sanin kowa ne cewar,Injiniya Matazu mutum ne da ya saba aiwatar da ayyukan jin kan al'umma,musamman ma marayu da sauran masu karamin karfi a cikin al'umma.

Sau da dama Matawallen Matazu ya aiwatar da irin wannan aiki na taimakon Marayu da masu karamin karfi,musamman ma akan batun da ya sha ilimin su,domin su kasance masu alfanu ga al'ummomin su.

Baya ga wannan, Injiniya Abubakar Matazu yana tallafawa marasa lafiya masu karamin karfi da suke kwance a asibitoci da ma gidajen su, musamman ma a yankin Karamar Hukumar shi.

Haka zalika,batun tallafawa wadanda hare-haren yan bindiga ya shafa a Karamar Hukumar shi, shima wani muhimmin bangare ne da Matawallen Matazu yake bada taimakon shi.

Da yake magantawa a lokacin taron,Injiniya Abubakar Matazu ya taya daliban murna akan wannan nasara da s**a samu,sai ya yanawa kungiyar akan wannan karamci da ta yi masu.

Ya ce wannan karamci da Kungiyar ta yi masu zai kara masu kwarin guiwa wurin jajircewa wurin karatun su na gaba da sakandire.

Daga nan sai ya h**e su akan su kasance jakadu na gari ga Jihar Katsina a duk makarantun da s**a samu kan su.

Sarakuna Ku Girmama Matsayinku: Ku Fice Daga Rikicin Jam’iyyar ADC, Ku Bar Malam Nafi’u Bala Gombe Ya Cigaba Da Aikin Gy...
02/08/2025

Sarakuna Ku Girmama Matsayinku: Ku Fice Daga Rikicin Jam’iyyar ADC, Ku Bar Malam Nafi’u Bala Gombe Ya Cigaba Da Aikin Gyara Jam’iyya Cikin Gaskiya

Ofishinmu na Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) yana bayyana damuwarsa matuka kan yadda wasu sarakunan gargajiya ke kiran waya da nufin matsin lamba ga Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar, Alhaji Nafiu Bala Gombe, domin ya sauya matsayinsa na kare tsarin dimokuradiyya da doka na jam’iyyar.

Wannan barazana da kuma kiran da ake yi ga wasu mambobin Kwamitin Zartaswa na Kasa (NWC) domin su ja da baya daga goyon bayan shugabansu, abin takaici ne kwarai, musamman ganin cewa sarakuna sun bar turbarsu ta raya al’adu da zaman lafiya, sun rungumi muradin wasu 'yan siyasa masu son karbe jam’iyya ta kowane hali.

MAKIRCI NA BAYA-BAYAN NAN

Bayanan sirri daga majiya mai karfi na nuni da cewa wasu manyan ’yan siyasa da s**a hada da Janar David Mark da Mallam Nasir El-Rufai da wasu gungun mutane sun hada wata kungiya da ke shirin tura dattawa su je Gombe domin matsawa mahaifiyar Shugaban rikon kwarya da nufin tilasta masa mika jam’iyyar da nufin cinma burinsu na siyasa a shekarar 2027.

Wannan yunkuri na ziyarar mahaifiyar Shugaban jam’iyyar abu ne da ba za mu lamunta da shi ba. Hakan na nuna cewa wasu sun sadaukar da dimokuradiyya ga son zuciya da yin coge don biyan muradinsu na 2027.

1. Muna da tabbaci daga bayanen sirri masu inganci cewa wadannan sarakuna na kokarin tilasta Alhaji Nafiu Bala Gombe ya mika jam’iyya ga 'yan siyasa masu matasanancin kwadayin mulki ta hanyar matsa masa da kiraye-kiraye a wayarsa tare da shisshigi a boye. Wadannan sarakuna ba su kyauta ba, saboda suna neman rage kima da martabar al'adunmu masu nagarta ta hanyar neman zama 'yan koren masu mayatar son mulkin siyasa a shekarar 2027. Wannan abin jimami ne ga dukkan mai kishin martabar masarautinmu.

2. Wannan kuskure ne mai muni daga bangaren sarakuna, wadanda ya kamata su tsaya a gefe su kasance iyayen kasa masu kima.

3. Mu na kara fayyacewa: Sarakuna ba su da hurumin shiga harkokin jam’iyyar ADC ko zama 'yan gada-gadar 'yan siyasa. Wannan ba shekarar 1983 ba ce; yanzu idon kowa a bude yake. ADC ba ta sayarwa ba ce!

4. Alhaji Nafiu Bala Gombe ba zai ja da baya ba, yana da cikakken goyon bayan dokokin jam’iyya da mambobinta masu kishin kasa.

5. Wadanda suke fakewa da cewa suna hidimar “sasantawa”, yaudarar jama'a suke, da nufin biyan muradin 'yan cogen Hadaka ta Zaben 2027. Su sani cewa za mu bayyana sunayensu da cikakken bayani game da boyayyiyar manufarsu, in bukatar yin hakan ta taso.

6. Ga wadanda suke matsayin sarakuna amma s**a tsunduma siyasa da goyon bayan hargitsi, muna ba ku shawara: ku koma ku kula da masarautunku. Kada ku sayar da martabarku da al'adunmu masu nagarta don biyan bukatun 'yan siyasan da s**a shahara wajen yaudarar al'umma shekara da shekaru.

MATSAYARMU A KAN WANNAN KATSALANDAN:

Jam’iyyar ADC ba ta sayarwa ba ce. Ba za mu bar makircin wasu mayaudaran 'yan siyasa ya kassara mulkin dimokuradiyyan kasar nan ba, ko ya lalata alkiblar jam’iyyar ADC ba. Kuma za mu fallasa kowane mai hannu a ciki — ko saraki ne shi ko dan bangar siyasa.

In kunne ya ji, jiki ya tsira.

Sanya hannu:
Dr. Aminu Sani Alhassan
Mai Baiwa Shugaban Rikon Kwarya Shawara kan Harkokin Jama’a
Jam'iyyar African Democratic Congress (ADC)
Abuja

DA DUMI-DUMI: Dan Gwamnan Jihar Katsina Alh. Muhammadu Dikko Umar ya zama sabon Hakimin Radda. Alhaji Muhammadu Dikko Um...
02/08/2025

DA DUMI-DUMI: Dan Gwamnan Jihar Katsina Alh. Muhammadu Dikko Umar ya zama sabon Hakimin Radda.

Alhaji Muhammadu Dikko Umar Radda yana cikin sabbin Hakimai Shidda da aka kara a masarautar Katsina, a Jihar Katsina.

Sauran sabbin Hakiman da aka kara sun hada da Sanata Hadi Sirika a matsayin Marusan Katsina Hakimin Shargalle dake cikin karamar hukumar Dutsi.

Alhaji Sanusi Katsina Usman a matsayin Karshin Katsina Hakimin Shinkafi dake cikin karamar hukumar Katsina.

Alhaji Ahmed Abdulmuminu Kabir Usman a matsayin Dan Majen Katsina Hakimin Dankama dake cikin karamar hukumar Kaita.

Alhaji Abubakar Dardisu a matsayin Sarkin Mudurun Katsina Hakimin Muduru dake cikin karamar hukumar Mani.

Alhaji Gambo Abdullahi Dabai a matsayin Dausayin Katsina Hakimin Dabai dake cikin karamar hukumar Danja.

Sai Alhaji Muhammadu Dikko Umar Radda a matsayin Gwagwaren Katsina Hakimin Radda dake cikin karamar hukumar Charanci.

Wannan yana kunshe a cikin wata takardar manema labarai da Sakataren masarautar Katsina Alhaji Bello Mamman Ifo (Sarkin Yakin Katsina) ya sanya ma hannu, a ranar 2/8/2025.

Rikicin ADC Ya Kara Ta'azzara: Bala Gombe Ya Ayyana Kansa a  Matsayin Shugaban Jam'iyya, Ya fatattaki su El-Rufa’iRikici...
31/07/2025

Rikicin ADC Ya Kara Ta'azzara: Bala Gombe Ya Ayyana Kansa a Matsayin Shugaban Jam'iyya, Ya fatattaki su El-Rufa’i

Rikicin cikin gida a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ya ƙara ɗaukar sabon salo, bayan Nafiu Bala Gombe, Mataimakin Shugaban ƙasa na jam’iyyar, ya ayyana kansa a matsayin Shugaban rikon kwarya.

A cewarsa, hakan ya zama dole sakamakon abin da ya kira ƙoƙarin wasu manyan 'yan siyasa – ciki har da tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa’i – na mallake jam’iyyar tare da cusa son zuciya a harkokin tafiyar da ita.

Bala ya zargi tsoffin shugabannin jam’iyyar da mika madafun iko ga wasu 'yan bangar siyasa a cikin ADC, inda ya bayyana su a matsayin ‘sojojin gona’ masu burin hallaka tsarin dimokuradiyya da jam’iyyar ta gina tsawon shekaru.

Ya ce wadannan sojojin haya, wadanda ba su wata alaka da ADC, suna shirin mayar da ita jam’iyyar aljihun mutane irin su Elrufai, domin cimma muradun kansu na siyasa.

A cewarsa, El-Rufa’i da magoya bayansa suna kokarin amfani da ADC a matsayin wani tsani na wucin-gadi domin cimma wata manufa ta siyasa da ke nuni da shirinsu na fuskantar zaben 2027.

Ya bayyana yunkurin Elrufai da 'yan korensa a matsayin babbar barazana ga tsarin shugabanci na jam’iyyar da dimokuradiyya gaba ɗaya.

Bala ya kuma bukaci Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da ta girmama kundin tsarin mulkin jam’iyyar ADC, tare da kin amincewa da duk wani yunƙurin da ya saba da tsarin. Ya ce matakin da ya ɗauka na zama Shugaban rikon kwarya yana da cikakken tushe a kundin tsarin mulkin jam’iyyar, kuma ya ti hakan ne don kare mutuncin ADC daga mamayar da ke neman hana ta numfashi.

Ya jaddada cewa ba za su yi shiru ba yayin da wasu ke yunƙurin lalata abin da s**a gina na tsawon shekaru, kuma duk wani yunkuri da El-Rufa’i da abokan tafiyarsa ke yi ba zai kai ga nasara ba.

A karshe ya bukaci Hukumar Zabe ta Kasa ta jaddada kasancewarsa shugaba a hukumance.

MUHIMMIN SAKO GA AL'UMMAR MAZABAR DAN MAJALISSAR TARAYYA NA MUSAWA/MATAZU....Ta Tabbata Karya Da Cin Fuska Aka Nemi Yi W...
29/07/2025

MUHIMMIN SAKO GA AL'UMMAR MAZABAR DAN MAJALISSAR TARAYYA NA MUSAWA/MATAZU
....Ta Tabbata Karya Da Cin Fuska Aka Nemi Yi Wa Dan Majalissar Mu(Dujiman Katsina)

Sako Daga Darakta Janar Na Madabba'ar Jihar Katsina,Hon.Abba Rufa'i Musawa

A kwanan nan ne aka samu wani dan baranda mai suna Nuhu Muhammad Aliyu da ya yi ikirarin cewa shi dan Karamar Hukumar Musawa ne,ya fitar da wata matunashiya akan cewa Dan Majalissar Tarayyar Musawa/Matazu Hon.Abdullahi Aliyu Ahmed(Dujiman Katsina)ya yi karyar takardun makaranta.

Idan dai za'a iya tunawa,Nuhu Muhammad Aliyu ya fitar da wannan matunashiya ne a Jaridar Daily Trust ta ranar 23 ga Watan Yuni na wannan shekarar,inda yake yin kira ga Hukumomi da su binciki takardun na Dujiman Katsina.

A yau Talata da muke ciki,ita wannan Jarida ta Daily Trust ta sake fitar da wata matunashiya da take bayyana cewa,wancan zargi na Nuhu Muhammad karya ne da kuma yunkuri na cin fuska da zubda mutuncin Hon.Abdullahi Aliyu Ahmed.

Sanin kowa ne cewar,ita wannan Jarida Kafar Yada Labarai ce mai kima,wadda ta saba fitar da sahihan labarai na gaskiya,sai gashi wannan dan tahaliki ya biya shafi a cikin ta domin cin fuskar Dujiman Katsina,sai gashi cikin ikon Allah yau gaskiya ta yi halinta,inda ita wannan Jarida ta sake buga matunashiya daga Ofishin Dujiman Katsina wadda ke karyata Nuhu Muhammad.

Yana da kyau al'ummar Mazabar Musawa/Matazu su gane cewa,akwai mutane da s**a kasance makiyan su, wadanda suke so su yaki Dujiman Katsina ta kowace fuska, ba dan komai ba sai dan bukatar kansu.

Duk wanda yake a wannan Mazaba yana sane da irin kyakkyawan wakilci da Honorabul Abdullahi Aliyu Ahmed yake yi masu,don haka akwai bukatar su yi watsi da duk irin wadannan mutane da ke neman yin bakin ciki ga ayyukan alkairi na Dujiman na Katsina.

Kamar yadda Jaridar Daily Trust din ta ruwaito,babu inda Honorabul Abdullahi Aliyu Ahmed ya taba yin karyar takardun makaranta a duk inda ya yi aiki,kuma babu inda aka taba bincikar shi akan hakan,don haka dai labarin Nuhu Muhammad Aliyu ya zama na cin fuska da zubar da kimar Dujiman Katsina.

A sabili da haka,mai girma Honorabul Abdullahi Aliyu Ahmed zai dauki duk wani mataki na shari'a akan wannan cin fuska,domin ganin wasu sun kaurace aimatawa ko kusantar cin fuskar shi.

Allah ya kara yin jagoranci ga Honorabul Abdullahi Aliyu Ahmed,Allah ya iya mashi abinda baya iyawa,Allah ya bashi ikon sauke nauyinda aka dora mashi.

Sako Daga Darakta Janar Na Madabba'ar Jihar Katsina,Hon.Abba Rufa'i Musawa.

WATA SABUWA: Gwamnatin Nijeriya za ta fara karbar haraji a hannun marasa aure, don tallafawa masu riƙe da iyali, inji Mi...
27/07/2025

WATA SABUWA: Gwamnatin Nijeriya za ta fara karbar haraji a hannun marasa aure, don tallafawa masu riƙe da iyali, inji Minstan cikin gida na Nijeriya, Olubinmi Tunji-Ojo.

Me ka zu ce?

NASARA DAGA ALLAH :  Abba Kyari ya fara samun Nasara a Shari'arsa a Kotu, kan zargin Hodar Ibilis.Shaidu sun Tabbatar wa...
24/07/2025

NASARA DAGA ALLAH : Abba Kyari ya fara samun Nasara a Shari'arsa a Kotu, kan zargin Hodar Ibilis.

Shaidu sun Tabbatar wa Kotu cewa bayanan kira na Abba Kyari ba su nuna wata hulɗars da dillalin kwaya ba.

Wani shaida daga kamfanin MTN Nigeria ya bayyana wa Mai Shari’a Emeka Nwite na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja a ranar Alhamis cewa bayanan kiran waya na Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda, Abba Kyari, ba su nuna wata hulɗa da lambar da ake alakanta ta da wani wanda ake zargi da safarar kwaya mai suna “Mike Coke” ba.

Shaidan, mai suna Adeshina Fasasi, wanda ke aiki a matsayin shugaban ƙungiyar kula da matsalolin gaggawa a sashen gudanar da bincike na MTN, ya bayyana hakan ne yayin bayar da shaidar da ya bayar bisa sammacin kotu a ci gaba da sauraron shari’ar da ke gudana mai lamba FHC/ABJ/CR/57/2022.

Fasasi ya ce ofishinsa ne ke kula da buƙatun da s**a shafi rikicin abokan ciniki da binciken hukumomin tsaro, kuma sun duba bayanan kiran Abba Kyari, inda ba su gano wata hulɗa da wanda ake zargi ba.

Address

Katsina

Telephone

+2349032126222

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina 24/7 news posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share