Katsina 24/7 news

Katsina 24/7 news Gaskiya dokin karfe

Sarakuna Ku Girmama Matsayinku: Ku Fice Daga Rikicin Jam’iyyar ADC, Ku Bar Malam Nafi’u Bala Gombe Ya Cigaba Da Aikin Gy...
02/08/2025

Sarakuna Ku Girmama Matsayinku: Ku Fice Daga Rikicin Jam’iyyar ADC, Ku Bar Malam Nafi’u Bala Gombe Ya Cigaba Da Aikin Gyara Jam’iyya Cikin Gaskiya

Ofishinmu na Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) yana bayyana damuwarsa matuka kan yadda wasu sarakunan gargajiya ke kiran waya da nufin matsin lamba ga Shugaban rikon kwarya na jam’iyyar, Alhaji Nafiu Bala Gombe, domin ya sauya matsayinsa na kare tsarin dimokuradiyya da doka na jam’iyyar.

Wannan barazana da kuma kiran da ake yi ga wasu mambobin Kwamitin Zartaswa na Kasa (NWC) domin su ja da baya daga goyon bayan shugabansu, abin takaici ne kwarai, musamman ganin cewa sarakuna sun bar turbarsu ta raya al’adu da zaman lafiya, sun rungumi muradin wasu 'yan siyasa masu son karbe jam’iyya ta kowane hali.

MAKIRCI NA BAYA-BAYAN NAN

Bayanan sirri daga majiya mai karfi na nuni da cewa wasu manyan ’yan siyasa da s**a hada da Janar David Mark da Mallam Nasir El-Rufai da wasu gungun mutane sun hada wata kungiya da ke shirin tura dattawa su je Gombe domin matsawa mahaifiyar Shugaban rikon kwarya da nufin tilasta masa mika jam’iyyar da nufin cinma burinsu na siyasa a shekarar 2027.

Wannan yunkuri na ziyarar mahaifiyar Shugaban jam’iyyar abu ne da ba za mu lamunta da shi ba. Hakan na nuna cewa wasu sun sadaukar da dimokuradiyya ga son zuciya da yin coge don biyan muradinsu na 2027.

1. Muna da tabbaci daga bayanen sirri masu inganci cewa wadannan sarakuna na kokarin tilasta Alhaji Nafiu Bala Gombe ya mika jam’iyya ga 'yan siyasa masu matasanancin kwadayin mulki ta hanyar matsa masa da kiraye-kiraye a wayarsa tare da shisshigi a boye. Wadannan sarakuna ba su kyauta ba, saboda suna neman rage kima da martabar al'adunmu masu nagarta ta hanyar neman zama 'yan koren masu mayatar son mulkin siyasa a shekarar 2027. Wannan abin jimami ne ga dukkan mai kishin martabar masarautinmu.

2. Wannan kuskure ne mai muni daga bangaren sarakuna, wadanda ya kamata su tsaya a gefe su kasance iyayen kasa masu kima.

3. Mu na kara fayyacewa: Sarakuna ba su da hurumin shiga harkokin jam’iyyar ADC ko zama 'yan gada-gadar 'yan siyasa. Wannan ba shekarar 1983 ba ce; yanzu idon kowa a bude yake. ADC ba ta sayarwa ba ce!

4. Alhaji Nafiu Bala Gombe ba zai ja da baya ba, yana da cikakken goyon bayan dokokin jam’iyya da mambobinta masu kishin kasa.

5. Wadanda suke fakewa da cewa suna hidimar “sasantawa”, yaudarar jama'a suke, da nufin biyan muradin 'yan cogen Hadaka ta Zaben 2027. Su sani cewa za mu bayyana sunayensu da cikakken bayani game da boyayyiyar manufarsu, in bukatar yin hakan ta taso.

6. Ga wadanda suke matsayin sarakuna amma s**a tsunduma siyasa da goyon bayan hargitsi, muna ba ku shawara: ku koma ku kula da masarautunku. Kada ku sayar da martabarku da al'adunmu masu nagarta don biyan bukatun 'yan siyasan da s**a shahara wajen yaudarar al'umma shekara da shekaru.

MATSAYARMU A KAN WANNAN KATSALANDAN:

Jam’iyyar ADC ba ta sayarwa ba ce. Ba za mu bar makircin wasu mayaudaran 'yan siyasa ya kassara mulkin dimokuradiyyan kasar nan ba, ko ya lalata alkiblar jam’iyyar ADC ba. Kuma za mu fallasa kowane mai hannu a ciki — ko saraki ne shi ko dan bangar siyasa.

In kunne ya ji, jiki ya tsira.

Sanya hannu:
Dr. Aminu Sani Alhassan
Mai Baiwa Shugaban Rikon Kwarya Shawara kan Harkokin Jama’a
Jam'iyyar African Democratic Congress (ADC)
Abuja

DA DUMI-DUMI: Dan Gwamnan Jihar Katsina Alh. Muhammadu Dikko Umar ya zama sabon Hakimin Radda. Alhaji Muhammadu Dikko Um...
02/08/2025

DA DUMI-DUMI: Dan Gwamnan Jihar Katsina Alh. Muhammadu Dikko Umar ya zama sabon Hakimin Radda.

Alhaji Muhammadu Dikko Umar Radda yana cikin sabbin Hakimai Shidda da aka kara a masarautar Katsina, a Jihar Katsina.

Sauran sabbin Hakiman da aka kara sun hada da Sanata Hadi Sirika a matsayin Marusan Katsina Hakimin Shargalle dake cikin karamar hukumar Dutsi.

Alhaji Sanusi Katsina Usman a matsayin Karshin Katsina Hakimin Shinkafi dake cikin karamar hukumar Katsina.

Alhaji Ahmed Abdulmuminu Kabir Usman a matsayin Dan Majen Katsina Hakimin Dankama dake cikin karamar hukumar Kaita.

Alhaji Abubakar Dardisu a matsayin Sarkin Mudurun Katsina Hakimin Muduru dake cikin karamar hukumar Mani.

Alhaji Gambo Abdullahi Dabai a matsayin Dausayin Katsina Hakimin Dabai dake cikin karamar hukumar Danja.

Sai Alhaji Muhammadu Dikko Umar Radda a matsayin Gwagwaren Katsina Hakimin Radda dake cikin karamar hukumar Charanci.

Wannan yana kunshe a cikin wata takardar manema labarai da Sakataren masarautar Katsina Alhaji Bello Mamman Ifo (Sarkin Yakin Katsina) ya sanya ma hannu, a ranar 2/8/2025.

Rikicin ADC Ya Kara Ta'azzara: Bala Gombe Ya Ayyana Kansa a  Matsayin Shugaban Jam'iyya, Ya fatattaki su El-Rufa’iRikici...
31/07/2025

Rikicin ADC Ya Kara Ta'azzara: Bala Gombe Ya Ayyana Kansa a Matsayin Shugaban Jam'iyya, Ya fatattaki su El-Rufa’i

Rikicin cikin gida a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ya ƙara ɗaukar sabon salo, bayan Nafiu Bala Gombe, Mataimakin Shugaban ƙasa na jam’iyyar, ya ayyana kansa a matsayin Shugaban rikon kwarya.

A cewarsa, hakan ya zama dole sakamakon abin da ya kira ƙoƙarin wasu manyan 'yan siyasa – ciki har da tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufa’i – na mallake jam’iyyar tare da cusa son zuciya a harkokin tafiyar da ita.

Bala ya zargi tsoffin shugabannin jam’iyyar da mika madafun iko ga wasu 'yan bangar siyasa a cikin ADC, inda ya bayyana su a matsayin ‘sojojin gona’ masu burin hallaka tsarin dimokuradiyya da jam’iyyar ta gina tsawon shekaru.

Ya ce wadannan sojojin haya, wadanda ba su wata alaka da ADC, suna shirin mayar da ita jam’iyyar aljihun mutane irin su Elrufai, domin cimma muradun kansu na siyasa.

A cewarsa, El-Rufa’i da magoya bayansa suna kokarin amfani da ADC a matsayin wani tsani na wucin-gadi domin cimma wata manufa ta siyasa da ke nuni da shirinsu na fuskantar zaben 2027.

Ya bayyana yunkurin Elrufai da 'yan korensa a matsayin babbar barazana ga tsarin shugabanci na jam’iyyar da dimokuradiyya gaba ɗaya.

Bala ya kuma bukaci Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da ta girmama kundin tsarin mulkin jam’iyyar ADC, tare da kin amincewa da duk wani yunƙurin da ya saba da tsarin. Ya ce matakin da ya ɗauka na zama Shugaban rikon kwarya yana da cikakken tushe a kundin tsarin mulkin jam’iyyar, kuma ya ti hakan ne don kare mutuncin ADC daga mamayar da ke neman hana ta numfashi.

Ya jaddada cewa ba za su yi shiru ba yayin da wasu ke yunƙurin lalata abin da s**a gina na tsawon shekaru, kuma duk wani yunkuri da El-Rufa’i da abokan tafiyarsa ke yi ba zai kai ga nasara ba.

A karshe ya bukaci Hukumar Zabe ta Kasa ta jaddada kasancewarsa shugaba a hukumance.

MUHIMMIN SAKO GA AL'UMMAR MAZABAR DAN MAJALISSAR TARAYYA NA MUSAWA/MATAZU....Ta Tabbata Karya Da Cin Fuska Aka Nemi Yi W...
29/07/2025

MUHIMMIN SAKO GA AL'UMMAR MAZABAR DAN MAJALISSAR TARAYYA NA MUSAWA/MATAZU
....Ta Tabbata Karya Da Cin Fuska Aka Nemi Yi Wa Dan Majalissar Mu(Dujiman Katsina)

Sako Daga Darakta Janar Na Madabba'ar Jihar Katsina,Hon.Abba Rufa'i Musawa

A kwanan nan ne aka samu wani dan baranda mai suna Nuhu Muhammad Aliyu da ya yi ikirarin cewa shi dan Karamar Hukumar Musawa ne,ya fitar da wata matunashiya akan cewa Dan Majalissar Tarayyar Musawa/Matazu Hon.Abdullahi Aliyu Ahmed(Dujiman Katsina)ya yi karyar takardun makaranta.

Idan dai za'a iya tunawa,Nuhu Muhammad Aliyu ya fitar da wannan matunashiya ne a Jaridar Daily Trust ta ranar 23 ga Watan Yuni na wannan shekarar,inda yake yin kira ga Hukumomi da su binciki takardun na Dujiman Katsina.

A yau Talata da muke ciki,ita wannan Jarida ta Daily Trust ta sake fitar da wata matunashiya da take bayyana cewa,wancan zargi na Nuhu Muhammad karya ne da kuma yunkuri na cin fuska da zubda mutuncin Hon.Abdullahi Aliyu Ahmed.

Sanin kowa ne cewar,ita wannan Jarida Kafar Yada Labarai ce mai kima,wadda ta saba fitar da sahihan labarai na gaskiya,sai gashi wannan dan tahaliki ya biya shafi a cikin ta domin cin fuskar Dujiman Katsina,sai gashi cikin ikon Allah yau gaskiya ta yi halinta,inda ita wannan Jarida ta sake buga matunashiya daga Ofishin Dujiman Katsina wadda ke karyata Nuhu Muhammad.

Yana da kyau al'ummar Mazabar Musawa/Matazu su gane cewa,akwai mutane da s**a kasance makiyan su, wadanda suke so su yaki Dujiman Katsina ta kowace fuska, ba dan komai ba sai dan bukatar kansu.

Duk wanda yake a wannan Mazaba yana sane da irin kyakkyawan wakilci da Honorabul Abdullahi Aliyu Ahmed yake yi masu,don haka akwai bukatar su yi watsi da duk irin wadannan mutane da ke neman yin bakin ciki ga ayyukan alkairi na Dujiman na Katsina.

Kamar yadda Jaridar Daily Trust din ta ruwaito,babu inda Honorabul Abdullahi Aliyu Ahmed ya taba yin karyar takardun makaranta a duk inda ya yi aiki,kuma babu inda aka taba bincikar shi akan hakan,don haka dai labarin Nuhu Muhammad Aliyu ya zama na cin fuska da zubar da kimar Dujiman Katsina.

A sabili da haka,mai girma Honorabul Abdullahi Aliyu Ahmed zai dauki duk wani mataki na shari'a akan wannan cin fuska,domin ganin wasu sun kaurace aimatawa ko kusantar cin fuskar shi.

Allah ya kara yin jagoranci ga Honorabul Abdullahi Aliyu Ahmed,Allah ya iya mashi abinda baya iyawa,Allah ya bashi ikon sauke nauyinda aka dora mashi.

Sako Daga Darakta Janar Na Madabba'ar Jihar Katsina,Hon.Abba Rufa'i Musawa.

WATA SABUWA: Gwamnatin Nijeriya za ta fara karbar haraji a hannun marasa aure, don tallafawa masu riƙe da iyali, inji Mi...
27/07/2025

WATA SABUWA: Gwamnatin Nijeriya za ta fara karbar haraji a hannun marasa aure, don tallafawa masu riƙe da iyali, inji Minstan cikin gida na Nijeriya, Olubinmi Tunji-Ojo.

Me ka zu ce?

NASARA DAGA ALLAH :  Abba Kyari ya fara samun Nasara a Shari'arsa a Kotu, kan zargin Hodar Ibilis.Shaidu sun Tabbatar wa...
24/07/2025

NASARA DAGA ALLAH : Abba Kyari ya fara samun Nasara a Shari'arsa a Kotu, kan zargin Hodar Ibilis.

Shaidu sun Tabbatar wa Kotu cewa bayanan kira na Abba Kyari ba su nuna wata hulɗars da dillalin kwaya ba.

Wani shaida daga kamfanin MTN Nigeria ya bayyana wa Mai Shari’a Emeka Nwite na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja a ranar Alhamis cewa bayanan kiran waya na Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda, Abba Kyari, ba su nuna wata hulɗa da lambar da ake alakanta ta da wani wanda ake zargi da safarar kwaya mai suna “Mike Coke” ba.

Shaidan, mai suna Adeshina Fasasi, wanda ke aiki a matsayin shugaban ƙungiyar kula da matsalolin gaggawa a sashen gudanar da bincike na MTN, ya bayyana hakan ne yayin bayar da shaidar da ya bayar bisa sammacin kotu a ci gaba da sauraron shari’ar da ke gudana mai lamba FHC/ABJ/CR/57/2022.

Fasasi ya ce ofishinsa ne ke kula da buƙatun da s**a shafi rikicin abokan ciniki da binciken hukumomin tsaro, kuma sun duba bayanan kiran Abba Kyari, inda ba su gano wata hulɗa da wanda ake zargi ba.

DA-DUMI-DUMI: Farfesa Nentawe Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na ƘasaJam’iyyar APC ta naɗa Farfesa Nentawe...
24/07/2025

DA-DUMI-DUMI: Farfesa Nentawe Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

Jam’iyyar APC ta naɗa Farfesa Nentawe Yilwatda a matsayin sabon shugaban jam’iyyar na ƙasa, bayan wani taro da aka gudanar a Abuja da shugaba Bola Ahmed Tinubu da wasu gwamnonin jam’iyyar s**a halarta.

Farfesa Yilwatda daga jihar Filato ya maye gurbin Dr. Abdullahi Umar Ganduje wanda ya sauka daga mukamin a watan Yuni 2025 saboda dalilan lafiya. Kafin wannan naɗi, Yilwatda ya rike mukamin Ministan Jin Ƙai da Rage Talauci a gwamnatin tarayya.

Ya kuma kasance ɗan takarar gwamna a Filato a zaɓen 2023, kuma ya taba aiki a matsayin kwamishinan zaɓe na INEC tsakanin 2017 da 2021.

Naɗin nasa na da nufin ƙarfafa haɗin kai da wakilci a jam’iyyar, musamman ga yankin Arewa ta Tsakiya da addinin Kirista. Ana fatan zai taka rawar gani wajen daidaita jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.

Karya Ce Tsagwaronta: Muhammad Babangida Bai Ƙi Nadin Da Shugaba Tinubu Yayi Masa Ba Wasu mutane masu ƙazamin nufi sun b...
21/07/2025

Karya Ce Tsagwaronta: Muhammad Babangida Bai Ƙi Nadin Da Shugaba Tinubu Yayi Masa Ba

Wasu mutane masu ƙazamin nufi sun bazu da wani labari mara tushe a kafafen sada zumunta da ke cewa Muhammad Babangida, ɗan tsohon shugaban kasa Ibrahim Badamasi Babangida (IBB), ya ƙi amincewa da nadin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya masa na chairman BOA.

Mun tabbatar da cewa wannan labarin ƙarya ne tsagwaronta, domin ba Muhammad Babangida bane ya fitar da sanarwar da ke yawo ba. Lambar da ke jikin takardar da aka yaɗa da kuma sa hannun da ke cikinta duk ba nasa ba ne.

Wannan wata makirci ce ta ɓatanci da ƙoƙarin jefa shakku a tsakanin shugaban ƙasa da manyan 'yan Najeriya, musamman waɗanda ke da sunaye da martaba a cikin al'umma.

Muhammad Babangida bai fito ya musanta nadin ba, kuma babu wata cikakkiyar shaida daga gare shi ko daga hannunsa da ke nuna ya ƙi karɓar kujerar. Wannan yana nuni da cewa an ƙirƙiri wannan labari ne domin yaudarar jama'a da haddasa ruɗani.

Muna kira ga 'yan Najeriya da su yi hattara da labaran ƙarya da ake yawan yaɗawa, su nemi gaskiya daga ingantattun majiyoyi kafin yarda da kowace irin sanarwa.

Allah ya ƙara haɗin kanmu da cigaban ƙasar nan.

LABARI MARA DAƊI: Yanzu Muke Samun Labarin Maigirma Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Radda, Yayi Haɗari A kan Hanyar Da...
20/07/2025

LABARI MARA DAƊI: Yanzu Muke Samun Labarin Maigirma Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Radda, Yayi Haɗari A kan Hanyar Daura Zuwa Birnin Katsina.

Allah Ya Kiyaye Gaba, Ya Allah Ya Kara Bashi Kariya!

Kada Ku Sake Yin Amfani da Mutuwar Buhari Don Cimma Manufarku Ta Siyasa — Matasan Arewa Sun Gargadi Atiku da El-RufaiKun...
19/07/2025

Kada Ku Sake Yin Amfani da Mutuwar Buhari Don Cimma Manufarku Ta Siyasa — Matasan Arewa Sun Gargadi Atiku da El-Rufai

Kungiyar Matasa Ta Arewa (Northern Youth Frontiers) ta bayyana damuwarsu kan yadda wasu 'yan siyasa ke ƙoƙarin amfani da rasuwar tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari domin yaudarar mutane da neman samun goyon bayansu.

A cewar kungiyar, Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai sun nuna kamar su abokai ne na Buhari domin su karɓi ƙaunar jama'a, alhali sun shafe shekaru suna adawa da akidu da manufofin Buhari tun yana raye.

Wannan abin da suke yi ruɗi ne, karya ce, kuma cin fuska ne ga marigayin shugaban da ya sadaukar da rayuwarsa ga ƙasar nan.

Kungiyar ta ce waɗannan 'yan siyasa ba su taɓa goyon bayan Buhari ba, kuma yanzu suna ƙoƙarin nuna soyayya ta bogi domin su karɓi ra'ayin mutanen Arewa — musamman bayan mutuwar sa.

“Matasan Arewa ba za su bari a ci zarafin Buhari ba.”

Matasan sun ce ba za su yarda a yi amfani da mutuwar Buhari a matsayin hanyar da za a fake domin yaudarar al’umma ba. Sun kuma roƙi jama’ar Arewa da su yi hankali da siyasar ruɗu da wasu ke ƙoƙarin kawowa a cikin lokaci mai muhimmanci na jimami da girmamawa.

Mutuwar Buhari ba siyasa bace. Lokaci ne na tunani da haɗin kai, ba na neman karɓuwa da nuna ƙarya ba.”

Kungiyar ta ƙara da cewa Atiku da El-Rufai su dakata da wannan salon siyasa, su girmama Buhari, su kuma bar mutanen Arewa su zaɓi gaskiya da amintattu, ba masu nuna soyayya ta ɗan lokaci ba.

Ku dakata da fakewa da mutuwar Buhari. Mutumin da kuka ƙi a raye, ba ku da ikon fakewa da shi bayan ya rasu.

✍️ Northern Youth Frontiers
Sakon Gargaɗi daga Matasan Arewa

Ba Za Mu Lamunci Atiku Da El-Rufai Su Siyasantar Da Mutuwar Buhari Ba, Tare Da Cin Moriyar Mutuwar A Wajen Zaman Makokin...
18/07/2025

Ba Za Mu Lamunci Atiku Da El-Rufai Su Siyasantar Da Mutuwar Buhari Ba, Tare Da Cin Moriyar Mutuwar A Wajen Zaman Makokinsa Ba, Cewar Kungiyar DWI

Kungiyar Democracy Watch Initiative (DWI) ta bayyana matuƙar ɓacin ranta da yadda Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai s**a nuna halayen son zuciya da ƙaŕaiŕàyi a lokacin jana’izar tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari. A yayin da mutane ke cikin alhini, su kuma sun sauya jana’izar zuwa wata dama ta siyasa don yaudarar jama’a da neman tagomashi.

Atiku da El-Rufai sun nuna kansu kamar su ne masoyan Buhari na hakika, alhali tarihi ya tabbatar da cewar sun sha s**a da yakar manufofinsa da akidunsa. Wannan yunkuri nasu, ba wai kawai rashin gaskiya ba ne, har ma da rashin mutunta irin gudunmawar da Buhari ya bayar ga ƙasa, da kuma wulakanta ra’ayin al’umma da ke makoki.

Ya kamata a tuna cewa Atiku ya fara zama babban abokin adawar Buhari tun shekarar 2003, inda ya tsaya takara da shi a zaɓuka da dama. A tarihi, Atiku yana canza jam’iyya bisa la’akari da ribar kansa, ba don wata akida ba. Ya bar PDP ya koma APC lokacin da Buhari ke da tasiri, sannan ya sake komawa PDP da zarar Buhari ya ci zaɓe. Wannan yana nuna halin rashin gaskiya da son zuciya da ke tattare da siyasar Atiku.

A gefe guda kuwa, El-Rufai wanda ya dade yana jinƙayar Buhari da jama’arsa, ya bayyana a jana’iza yana kokarin nuna wata tsantsar goyon baya da ba ta taɓa kasancewa da shi ba. Wannan hanya ce ta neman amincewa da mutanen Arewa cikin lokaci mai rauni da radadi.

Kungiyar DWI tana kira ga al’ummar Najeriya musamman ‘yan Arewa da su kasance masu hankali da fahimta. Kada mu bari wasu yan siyasa su ci moriyar makokinmu da tarihin mutanen kirki kamar Buhari. Ya kamata a tuna da makircin da waɗannan mutane s**a aikata a baya da kuma yadda s**a kasance masu son kansu da rashin kishin kasa.

DWI tana nan daram a kan matsayinta na cewa siyasar yaudara ba za ta samu karbuwa ba. Muna roƙon kowa da kowa da ya mutunta rayuwa da gado da Buhari ya bari – rayuwar gaskiya, tsantseni da kishin kasa.

A ƙarshe, muna tir da yunkurin Atiku Abubakar da Nasir El-Rufai na sauya jana’izar Buhari zuwa dandamalin siyasa. Muna kira da a ci gaba da tuna irin gudunmawar Buhari ba tare da bari wasu su yi amfani da sunansa don biyan bukatunsu na siyasa ba.

Democracy Watch Initiative

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Ƴan Bìñďiga Sun Sace Kansilan Daudawa, Honarabul Buhari Aliyu Daudawa, Da Wasu Mutan...
15/07/2025

INNALILLAHI WA'INNA ILAIHI RAJI'UN: Ƴan Bìñďiga Sun Sace Kansilan Daudawa, Honarabul Buhari Aliyu Daudawa, Da Wasu Mutane Da Dama A Garin Daudawa Dake Karamar Hukumar Faskari Ta Jihar Katsina A Daren Jiya Litinin

Allah Ya Kuɓutar Da Su Cikin Aminci!

Address

Katsina

Telephone

+2349032126222

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina 24/7 news posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share