Katsina 24/7 news

Katsina 24/7 news Gaskiya dokin karfe

Kun Gaza Samar Da Tsaro a Najeriya Amma Kuna Neman Kujerar Dindindin a Kwamitin Tsaro Na UN – Comr Haidar H Hasheem........
29/09/2025

Kun Gaza Samar Da Tsaro a Najeriya Amma Kuna Neman Kujerar Dindindin a Kwamitin Tsaro Na UN – Comr Haidar H Hasheem
......Permanent peace a gida kafin Permanent seat a UN!

Na tabbata al’ummar Najeriya musamman mu a Arewacin ƙasar nan mun gaji da ji da gani: tsaro ya gagara, rayuka da dukiyoyin al’umma suna salwanta kullum, amma gwamnati ta kasa kawo mafita ta dindindin.

Abin takaici shi ne, duk da wannan gazawa, har yanzu ana neman kujera ta dindindin a Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya (UN Security Council). Tambayata ita ce: ta yaya za a nemi kujerar dindindin a wajen duniya alhali kuwa an kasa samar da tsaro na dindindin a gida?

Idan har gwamnati na son ta gina karɓuwa a kasashen duniya, to wajibi ne ta fara tabbatar da zaman lafiya da tsaro a cikin ƙasar nan. Ba za mu ci gaba da zama cikin halin kashe-kashe, garkuwa da mutane, da hare-haren ta’addanci ba, a lokacin da shugabanni ke neman kujerar yabo a waje.

Daga farko ya k**ata a samar da tsaro na hakika ga ‘yan ƙasa kafin a nemi tsayuwa kan babban kujerar duniya.

✍️ Comr Haidar H Hasheem
National Chairman, Arewa Media Writers

Zargin Badaƙalar Miliyan 23: Tsohon Shugaban Masu Rinjaye A Majalisar Dokokin Jihar  Borno, Hon. Idrisa Jidda, da Sa’ad ...
28/09/2025

Zargin Badaƙalar Miliyan 23: Tsohon Shugaban Masu Rinjaye A Majalisar Dokokin Jihar Borno, Hon. Idrisa Jidda, da Sa’ad Abubakar Isah Ana Zarginsu da Karɓar Naira Miliyan 23 a Badakalar Kwangila Da Aka Danganta Da Hon. Adamu Aliyu

Daga Tukur I. Tukur

Tsohon Shugaban Masu Rinjaye A Majalisar Dokokin Jihar Borno, Hon. Idrisa Jidda, tare da Sa’ad Abubakar Isah, ana zargin sun karɓi Naira miliyan 23 daga hannun Mohammad Jidda, wanda ya shigar da ƙara kan batun badakalar kwangila a Jami’ar Jos ƙarar tana hannun Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa da Sauran Laifuka (ICPC).

Wannan batu ya fito fili ne a wata hira da mai aikin, Mr. Lawal Abubakar, wanda yake cikin rashin lafiya a gidansa da ke Dutsin-Ma, Jihar Katsina. Ya ce Hon. Idrisa Jidda ɗan’uwan mai ƙarar ne, Mohammad Jidda.

Mr. Lawal Abubakar ya bayyana cewa Hon. Idrisa Jidda, wanda a halin yanzu yake matsayin Mashawarcin Gwamna kan Harkokin Gidaje ga Gwamna Babagana Umara Zulum na Jihar Borno, ya karɓi Naira miliyan 20 daga asusun Zenith Bank na kamfanin Imanal Concept Ltd, mallakar Sa’ad Abubakar Isah wannan kuɗi na daga cikin abin da ake tuhuma da shi da aka danganta da sunan Hon. Adamu Aliyu.

Mr. Abubakar ya ce shi dai kawai ya gabatar da Hon. Adamu Aliyu ga mai kasuwancin Mohammad Jidda, ya kuma umarce shi ya sanya kuɗi a asusunsa. Bayan kwangilar ta karye, “na faɗa wa Adamu ya mayar da duk abin da aka biya shi, kuma an shaida min cewa ya mayar.”

A cewar Mr. Lawal Abubakar, Hon. Idrisa Jidda da Sa’ad Abubakar Isah sun tunkari Mohammad Jidda s**a karɓi kuɗaɗe daga kamfaninsa, Mohibba Investment Limited, s**a raba su tsakaninsu.

“Sun yaudari Mohammad Jidda suna cewa an biya Hon. Adamu Aliyu. Amma a ranar 29 ga Disamba, 2023, Alhaji Idrisa Jidda ya karɓi Naira miliyan 20 da aka shigar masa a asusun Zenith Bank daga Imanal Concept Ltd. Ina da rasit ɗin banki da zai tabbatar da hakan. Dukkanin asusun da aka yi ma’amala da su suna a Zenith Bank,” in ji Mr. Lawal Abubakar.

Ya ƙara cewa akwai ƙarin takardu da hujjoji da ke nuna wasu ma’amaloli da s**a shafi Idrisa Jidda da Sa’ad Abubakar Isah.

“Sa’ad Abubakar Isah tare da Hon. Idrisa Jidda sun taɓa haɗuwa da mai ƙarar s**a ce suna wakiltar Mr. Lawal Abubakar. S**a karɓi Naira miliyan 23 s**a raba tsakanin su. Saboda haka ya k**ata mai ƙarar ya mayar da ƙarar ne a kan Hon. Idrisa Jidda da Sa’ad Abubakar Isah (mai kamfanin Imanal Concept Ltd), ba kan Hon. Adamu Aliyu ba,” ya yi nuni.

Ƙungiyoyin Magoya Bayan Gwamnan Jihar Katsina Haɗin Gwiwa Da Gwamnatin Jihar Katsina daga Ward 361 Karkashin Jagorancin ...
27/09/2025

Ƙungiyoyin Magoya Bayan Gwamnan Jihar Katsina Haɗin Gwiwa Da Gwamnatin Jihar Katsina daga Ward 361 Karkashin Jagorancin Engr. Abubakar Abdullahi Matazu Ta Raba Fitilu Masu Amfani da Hasken Rana Ga Magidanta Daga Mazabu (361) Dake Fadin Jihar.

Engr. Abubakar Abdullahi Matazu (Matawallen Matazu) Daraktan kula da wutar lantarki karkara da birane na jihar Katsina, Ya ƙaddamar fitilu masu amfani da hasken rana (Solar system light) da za'a raba ga magidanta daga mazabu (361 wards) dake fadin jihar Katsina,

Tare da waɗanda za'a raba makarantun allo domin samun wadaccen haske a yayin karantarwar addinin musulunci.

Karkashin kungiyar da yake jagoranta mai suna (Gwagware support groups) da take da alhakin kulawa da sha'anin kungiyoyi da magoya baya tun kafin zaɓe, tare da haɗin gwiwar gwamnatin jihar Katsina karkashin jagorancin Malam Dikko Umar Raɗda Phd. CON. a sashen samar da wutar lantarki dake kusa da filin wasa na Karkanda dake cikin birnin Katsina, Ranar Asabar

Shugaban Road safety na NIGERIA ya jinjina ma Gwamnan Jahar Katsina da kuma GM Abubakar Matawale Matazu Matawale.

Ya jinjina masu ne a taron da GM Abubakar Matawale Matazu ya kaddamar ma Gwamna Dikko Radda Rabon fitilu masu amfani da hasken Rana Solar ga makarantu 1,805 ga Ward 361 na jahar Katsina na Tsangaya

A nashi kokarin don tai maka ma gwamnatin jahar Katsina, SHIMA GM Abubakar Matawale Matazu ya raba Solar home system ga mutane daga Ward 361 wanda zasu iya chajin waya, kallon TV, fanka, da kuma samun haske.

Shugan yace dole yazo wurin program din GM Abubakar Matawale Matazu saboda Nigeria tana ji da irin su bama Katsina kadai ba.

Yace matashi ne da yasan darajar jama'a da kima, kuma wanda yasan abunda yake yi don ganin cigaban NIGERIA ba Katsina kadai ba

Dubbunan jama'a ne s**a halarci taron daga Ward 361 duk kuma jami'an Gm Abubakar Matawale Matazu.

Wannan yana nuna zaman shi lafiya da yadda da Jama'ar Katsina suke ganin darajar shi.

Sign
Gwagware support Groups and association
Matawalle Matazu GM
GM Matawalle Matazu
Dr. Dikko Umaru Radda
Dr. Dikko Radda Social Media


DA DUMI-DUMI: Jam'iyyar PDP Ta Mutu A Karamar Hukumar Funtua Mai Ɗaukar Nauyin Ya'yan Jam'iyyar Ya Sauka Sheƙa Zuwa Jam'...
27/09/2025

DA DUMI-DUMI: Jam'iyyar PDP Ta Mutu A Karamar Hukumar Funtua Mai Ɗaukar Nauyin Ya'yan Jam'iyyar Ya Sauka Sheƙa Zuwa Jam'iyyar APC.

Wannan shine: Alhaji Sani Adamu Funtua matashi, attajiri, ɗan siyasa, kuma jigon jam'iyyar PDP a karamar hukumar Funtua jihar Katsina, Yana ɗaya daga cikin waɗanda s**a sauya sheka a ranar juma'a a gidan gwamnatin jihar karkashin jagorancin Sanata Muntari Mohammed Dandutse, Gwamna Malam Dikko Umar Radda PhD. CON. Ya karbe su hukumance.

K**ar yadda shuwagabannin jam'iyyar PDP waɗanda s**a sauya shekar s**a bayyana shine komai a jam'iyyar PDP a karamar hukumar Funtua duk wani abu idan ya ta so shine suke nema kai tsaye kuma ya taimake su, basu samun tallafin komai daga sama sai lokacin azumi kaɗai, Alhaji Sani Adamu shine mai daukar nauyin duk wata adawar siyasa a jam'iyyar PDP a karamar hukumar Funtua.

Daga: Shamsu Wapa Dandume

~Karaduwa post

Bisa ga umurnin mai Girma Gwamna Malam Dikko Umar Radda PhDKan saka Transformers Guda 5 a Kankia LGAAlhamdu lillahi REB ...
23/09/2025

Bisa ga umurnin mai Girma Gwamna Malam Dikko Umar Radda PhD

Kan saka Transformers Guda 5 a Kankia LGA

Alhamdu lillahi REB DA DEPARTMENT OF POWER sunyi ciki umurnin Mai Girma Gwamna.

Allah ya Saka mashi da mafificin alkairi ameen

Sign
Jama'ar cigaban garin Kankia.

A Yau Litinin 22_Sept_2025 Hon chairman na Musawa ya amshi bakoncin Gidauniyar Matawallen Foundation Karkashin Jagoran'c...
22/09/2025

A Yau Litinin 22_Sept_2025

Hon chairman na Musawa ya amshi bakoncin
Gidauniyar Matawallen Foundation Karkashin Jagoran'chi Shugabanta Kuma Shugaban Gudanar'wa Na Hukumar Kula Da Rarraba Wutar Lantarki Ta Jihar Katsina Watau Gm Abubakar Matawalle Matazu Founder Na Matawallen Foundation

Ta Sauka Karamar Hukumar Musawa Domin Tallafama Yara Yan Makaranta Musamman Marayu Da Yayan Wadan'da Basu Da Karfi

Gm Matawallen Matazu Yayi Alkawarin Yaki Da Rashin Ilimi Ta Hanyar Daukar Nauyin Karatun Yara Musamman Marayu Da Yayan Wadan'da Basu Da Karfi

Indai Za'a Iya Tunawa A Watan Daya Gabata Gidauniyar Matawallen Foundation Ta Dauki Nauyin Karatun Matasan'mu Da S**a Kammala Karatun Secondary Zuwa Makarantar Gaba Da Secondary Mutum Hamshin (50) Ne Gidauniyar Inda Ta Rarraba'su A Makarantun K**ar Haka
University
Polytechnic
ICT
FCE

Yanayin Creditancial Din'ka Yanayin Inda Za'a Kaika Zasu Karatu Kyaune Har Su Gama Batare Da Biyan ko Sisin Kobo Ba Duk Gidauniyar Ta Dauki Nauyi

Hakazalika Gidauniyar Ta Raba ma dalibai Dubu biyar 5000 Littatafai Da Uniform A Karamar Hukumar Funtua

Yau Kuma Gidauniyar Ta sake Raba Littatafai ga dalibai Dubu Biyar (5000) A Karamar Hukumar Musawa Duk Domin Yaki Da Rashin Ilimi

Gm Yace Manufar Wannan Gidauniyar Baya Wuce Tallafama Al'ummar Ciki Da Wajen Jihar Katsina Musamman Matasan'mu Da Kananen Yara Masu Tasowa

Zaa Raba Littatafan A Kowace Karamar Hukuma Dake Fadin Jihar Katsina

Hon Chairman Na Karamar Hukumar Musawa Yayi Godiya Game Da Adduar Allah Yakara Daukaka Darajar' Wannan Gidauniya
GM Matawalle Matazu
Matawalle Matazu GM
Abba Rufai Musawa
Katsina 24/7 news

Gwamnatin Tinubu Ta Fi Duk Gwamnatocin Mulkin Soja Muni Da K**a Karya A Tarihin Nijeriya, Inji El-RufaiTsohon Gwamnan Ji...
22/09/2025

Gwamnatin Tinubu Ta Fi Duk Gwamnatocin Mulkin Soja Muni Da K**a Karya A Tarihin Nijeriya, Inji El-Rufai

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya jefa sabon kakkausan magana kan gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, inda ya bayyana cewa wannan gwamnati ta fi kowace gwamnatin soja da Najeriya ta taba fuskanta muni da zalunci, k**ar yadda jaridar Channel Television s**a wallafa.

El-Rufai ya jaddada cewa talakawa na cikin mawuyacin hali, matsin tattalin arziki ya yi tsanani, farashin kaya ya haura sama, sannan rashin tsaro ya kara ta’azzara. Ya ce idan aka kwatanta halin da ake ciki yanzu da lokacin mulkin soja, rayuwar ‘yan Najeriya ta fi ta yanzu sauki.

Wannan furuci na El-Rufai ya janyo cece-kuce a tsakanin ‘yan kasa, inda wasu ke ganin ya dace a saurari wannan kira saboda gaskiyar abinda ke faruwa, yayin da wasu kuma ke kallon shi a matsayin kalaman tunzuri na siyasa.

Ko me zaku ce?

Daga Comr Haidar H Hasheem

DWI Ta Yi Allah-wadai da Zarge-zargen Banza Marasa Tushe Na Abubakar Malami Kan ’Yan Majalisar Jihar KebbiKungiyar Democ...
19/09/2025

DWI Ta Yi Allah-wadai da Zarge-zargen Banza Marasa Tushe Na Abubakar Malami Kan ’Yan Majalisar Jihar Kebbi

Kungiyar Democracy Watch Initiative (DWI) ta bayyana takaici da ƙin amincewa da ƙorafin da tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami (SAN), ya shigar a kan ’yan majalisar jihar Kebbi da ke kira da a k**a shi tare da gurfanar da shi gaban doka.

A cewar kungiyar, zarge-zargen Malami cewa Gwamna Nasir Idris da shugabannin jam’iyyar APC suna shirin shigo da ’yan daba da mak**ai cikin jihar, ba su da tushe kuma manufarsu kawai ita ce tada hankalin jama’a da kawo fitina.

Kungiyar ta kuma yi nuni da cewa Malami da kansa ana zarginsa da shigo da ’yan daba daga jihohin makwabta, abin da ya haddasa rikici a Birnin Kebbi da kai hari ga ofishin APC na jihar. Wannan, a cewar DWI, ya nuna cewa maimakon ya zama mutum mai kare doka da adalci, Malami ya zamo wanda ke yada fitina da kawo rikici.

DWI ta yi kira da gaggawa ga hukumomin tsaro da Majalisar Ɗinkin Tarayya da su k**a Malami tare da gurfanar da shi domin kare zaman lafiya da mutuncin dimokuraɗiyya.

Kungiyar ta kammala da tabbatar da goyon bayanta ga ’yan majalisar Kebbi da al’ummar jihar wajen neman adalci da tabbatar da siyasa mai lumana da gaskiya.

Kisan Hakimin Dogon Daji A Zamfara Barazana Ce Ga Tsaron Ƙasa – In Ji Shugaban Arewa Media Writer’s, Comr. Haidar H. Has...
18/09/2025

Kisan Hakimin Dogon Daji A Zamfara Barazana Ce Ga Tsaron Ƙasa – In Ji Shugaban Arewa Media Writer’s, Comr. Haidar H. Hasheem

Shugaban ƙungiyar Arewa Media Writer’s, na ƙasa ya bayyana matuƙar takaici da bacin rai kan kisan gilla da ‘yan bindiga s**a yi wa Hakimin Dogon Daji a ƙaramar hukumar Tsafe ta jihar Zamfara, inda s**a yi masa yankan rago har lahira. Wannan lamari abin kunya ne ga ƙasa baki ɗaya kuma babban ƙalubale ne ga gwamnati da hukumomin tsaro k**ar yadda rahotan BBC Hausa da Leadership s**a kawo rahotan.

Wannan mummunan hari ya sake tabbatar da cewa lamarin tsaro a Arewacin Najeriya na ta ƙara tabarbarewa, inda ake ci gaba da kai hare-hare a ƙauyuka, sace jama’a, kona gidaje da gonaki, tare da hallaka shugabannin al’umma ba tare da tsoro ba. Wannan yanayi ya jefa dubban mutane cikin fargaba, gudun hijira, da rasa amincewa ga gwamnati.

Ya k**ata gwamnati ta gane cewa tsaro ba abu ne da za a siyasantar da shi ba. Tsaro shi ne ginshiƙin kowace al’umma, kuma kariya ga rayuka da dukiyoyi wajibi ne na gwamnati. Rashin ɗaukar mataki mai tsauri na iya ƙara dagula rayuwar jama’a da kuma barazana ga makomar ƙasa baki ɗaya.

A wannan yanayi, muna kira da:

1. Gwamnati ta tashi tsaye da gaggawa wajen murkushe ‘yan bindiga da duk wata ƙungiya ta ta’addanci a Arewa.

2. A samar da kayan aiki na zamani ga jami’an tsaro, tare da horo da ƙarfafawa domin su iya gudanar da ayyukansu yadda ya k**ata.

3. A shimfiɗa tsare-tsare na dindindin don tabbatar da tsaro a ƙauyuka da birane.

A madadin al’ummar Arewa da ƙungiyar Arewa Media Writer’s, ina kira da a ɗauki wannan kisan da aka yi wa hakimin Dogon Daji a matsayin kira na musamman ga shugabanni a dukkan matakai, domin lokaci ya yi da za a kawo ƙarshen wannan masifar tsaro da ta addabi yankinmu.

A ƙarshe, ina addu’a ga Allah Madaukakin Sarki Ya jikan hakimin da aka kashe, Ya ba iyalansa da al’ummarsa juriya, Ya kuma dawo da zaman lafiya mai ɗorewa ga Najeriya baki ɗaya.

✍️ Rubutawa:
Comr. Haidar H. Hasheem
National Chairman, Arewa Media Writer’s

Manyan limaman masallatan jummuah na dariqa da izala na funtua local government sunyi Addua ta musamman ga GM Abubakar M...
15/09/2025

Manyan limaman masallatan jummuah na dariqa da izala na funtua local government sunyi Addua ta musamman ga GM Abubakar Matawalle Matazu Shugaban matawalle foundation kuma Janeral manager na hukumar Samar da wutar lantarki na birni da karkara ta jihar katsina.

Adduar ta Gabata ne bayan ya Kaddamar da tallafin uniform da littattafai na dalibai Marayu Wanda akalla Marayu dubu biyar (5000)zasu ampana dashi a karamar hukumar funtua.

Wanda s**a tarbe shi wajen kaddamar da Kayan karatun sun hada da
1. Chairman na funtua LG
2. ⁠Hakimin maska
3.shugaban subeb Wanda PM 2 ya Wakilce shi
4 .vice chairman na funtua LG
5.ES ta education funtua LG
6.zonal director na education
7.Shugaban union na Malamai na katsina state
8.Hon Abubakar Wada Nas funtua
9.manyan limamai
10.headmasters na funtua
Da sauran jamaa da dama dasu ka halarta.

Ayayin kaddamar wa, Shugaban matawalle foundation GM Abubakar matawalle matazu , dama in ba a manta bah ya sha alwashin taimaka wa ilimi na kana nan hukumomi talatin da hudu na katsina state,

Inda ya sha alwashin taimaka ma gwamnati bangaren ilimi na kana nan hukumomi talatin da hudu musamman Marayu da marasa Karfi.

A jawabin chairman Shugaban karamar hukumar funtua LG yayi godia da wannan Gaggarumin tallafi Wanda yace wannan shine gaggarumin tallafi na farko Wanda aka taba yi a funtua LG.

A jawabin Shugaban Malamai na Marayu na funtua LG yace tun Lokacin marigayi ummaru Musa raban da su samu tallafi akan harkar ilimi sai yanzu da matawalle foundation ta kawo masu tallafi karkashin jagorancin GM Abubakar matawalle matazu.

Jamaa da dama sunyi Bayani na godia yanda yai tsaye wajen ganin an tallafawa Marayu da marasa Karfi bangaren ilimi.
Daga karshe kuma anyi Addua Allah ya maida GM Abubakar matawalle matazu gida lhy da sauran Alummah Baki daya.

Al'umma A Jihar Imo Sun Yiwa El'rufai Tofin Alatsine, Sun Yi Watsi Da Shi Tare Da Nuna Ƙyma Da Irin SiyasarsaDaga Abdul-...
09/09/2025

Al'umma A Jihar Imo Sun Yiwa El'rufai Tofin Alatsine, Sun Yi Watsi Da Shi Tare Da Nuna Ƙyma Da Irin Siyasarsa

Daga Abdul-Azeez Suleiman

Nasir El-Rufai, tsohon gwamnan Kaduna, ya gamu da zanga-zangar ƙin karɓarsa a Owerri, Jihar Imo, lokacin da ya halarci Taron Odenigbo 2025 a Assumpta Cathedral. Jama’a sun fito da kwalaye da ƙorafe-ƙorafe, suna zarginsa da kalaman wariya kan kabilar Igbo a baya.

Wannan martani bai tsaya kan shi kaɗai ba, ya kuma fito da tsohuwar matsalar rashin haɗin kai, raunin Yaƙin Basasa, da kuma gajiyar jama’a ga shugabannin da ake ganin sun rabu da halin rayuwar talakawa.

Masu zanga-zangar har sun yi kira ga a tsawatar wa Peter Obi saboda kusancinsa da shi, abin da ya nuna cewa kowane ɗan siyasa na iya fuskantar tambaya muddin yana da alaƙa da mutanen da ake kallon masu raba kan ƙasa.

Zanga-zangar ta zama alamar cewa jama’a na da ƙarfi wajen kalubalantar manyan ‘yan siyasa, musamman a wannan zamani na kafafen sada zumunta. Darasin da ke ciki shi ne shugabanni su daina rarrabuwar kawuna, su rungumi tattaunawa, su girmama tarihi, domin kawai haka za a samu haɗin kan ƙasa mai bambance-bambance.

Jama’a Sun Yi Masa Watsi, Sun Nuna Ƙiyayya da Siyasar Rarrabuwar irin ta El'rufai, sun kuma shawarci Peter Obi da ya gaggauta nesanta kansa da El'rufai don tsira da mutuncinsa.

Address

Katsina

Telephone

+2349032126222

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Katsina 24/7 news posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share